Showing 21001 words to 24000 words out of 129912 words
Chapter 8 - MATAR GWAMNA COMPLETE Document from Abdallah.txt
shakota tana magana "ke yar gidan uban wacece da Sauri gwamna yaja hannunta " haba my bintuna me hadinki da almajira " my man to ta bude fuskarta wlh baza'a Kara bata sadaka ba kuma bazata Kara zauwaba" Oya muje idan ta bude fuskarta muninta ya firgita mun ke fa ina zan samo maganin firgita cikin tsiwa teemah tace " wlh... bata idasaba ta kusanta ta rufe mata baki jikinta na rawa saboda sojojin da suka nufo gunsu lokacin Aliyu sunbar gurin yana rike da bintu tsawa ya bugawa sojojin yana tambayarsu me zasuma Almajirai suka bar gurin suna biye da Ogansu har cikin gida sai da suka kaisu har kusan kofar parlo suka juya
suna shiga parlo ta kafa masa rigima ahana almajiran zuwa amsar sadaka ya almajira zata rainata ta fizgi kudi ahanunta tana hararata sai lallabata yakeyi tayi hakuri tana turjewa"my man wlh sai..da Sauri ya cafke bakinta yajata kan kujera suka zube kissing dinta yayi sosai ya rikirkitata da salonsa saida ya kashe mata jiki ya saketa ya Mike yana murmushi ya nufi bedroom. d'insa bai jimaba ya fito " bintuna sai na dawo " my man kaje ka biyomun da my Rauda kai ya girgiza mata " my bintuna suko sauran yarana fah ya fada yana ficewa ana kirasa awaya ya amsa yana fita daga parlon,, Teemah yau iya kuluwa ta kulu matar kusanta tace"ke ko wace irin yarinyace da bakida hakuri Dan yace muninki zai tsorata matarsa kikaso kimasa rashin kunya ai da kinsa an koramu bakiga sojojin da sukayo kanmuba "ni ai banason raini yo ina ruwana da soyayyarsu ai basai sun nuna awajeba yo meye na rike mata hannu a waje dan jaraba da wani katon cikinta kuma da kezan bama kudin Dan bana bukatarsu amma tunda kin koma bayanta wlh bazan bakiba gwara na cicirasu ta fada tana mik'ewa rumgume da Alquran Ninta ta tafi sai cika take tana batsewa
tayi tafiya kadan ta kalli kudin da bintu ta bata " wlh bazan shiga gida da kudinan ba yo uwar mema zan da kudin kishiya bari na yagashi har zata yaga ta fasa bari dai na bada sadaka tana gangarawa taci Karo da Dan liti mai ruwa wajansa ta nufa " Dan liti ina yini yanaga itace ya Kara Sauri "ke nifa bana harakarki wlh bazaki jazamun masifa ba da Sauri ta iskoshi Tasha gabansa" dallah can Ana binka da arziki kana gudu"kokuma kina bina da tsiyaba ni matsamun na wuce kudin ta meka masa " amshi dama sadakace zan baka saida ya waiga baiga kowaba ya washe baki " kai amma na gode dama yau kasuwar ruwan sai ahankali dariya nayi na beka masa shima yana dariya ya beko hannu zai amsa mota ta taka burki da karfin tsiya boos ya fito aguje yayo gunsu ai bai amshi kudinba ya rumtuma adubu " Dan liti ka dawo wlh kafiye tsoro kudin ta cikuikuye ta NASA masa cikin hularsa da take sarkafe abaro" ke meyasa kika raina mutane muje Oga na kiranki tsayuwa na gyara na rike k'uguna " wlh Boos kufita bayana nifa banason naci dazu fa kace kun rabu dani wlh da nasan zan hadu daku bazan fitoba ina dalili can an batamun rai nan ma ku batamun to kace masa baza'azoba sai me najima dukansu sun ficemun araina gwara na nemi Mara's mata Dan nima inada kishi waya ya kira" Oga wai bazata zoba sai wasu maganganu take? ok na fasa kanta da bindiga kenan idanu na zaro ganin yana saita bindiga da gudu nayi wajan motar Dan har ga Allah na dauka harbina zaiyi da gaske dariya ta
ba Aminullah yada take zaro idanu kamar ba yanzu ta gama ma boos rashin kunya ba motar ya bude kafin ta iso ya kauda kansa shigowa motar nayi ina maida numfashi na ajiye Qura'an dina gefe wani irin ni'imataccen kamshin ne yake tashi jikinsa mai dadin gaske Boos ya Iso ya rufe motar ya shiga driver yaja suka tafi kallonsa nayi baima San Allah yayi ruwana ba Nima kaina na dauke na ciro wayata ina danna wa shiru bashida niyar magana nasake kallonsa ido muka hada ya tsareni da lumsasun idanunsa gabana ne ya fadi da Sauri na dauke kaina adakile yayi magana can k'asa cikin amon muryasa mai dadi"ke baki iya gaisuwaba ne? " ina yini nace na kauda kaina bai amsaba yace"inaso nasan dalilinki na rainamun hankali d'azu wani zai kamamiki hannu an dakatar dashi sai gashi yanzu da wani k'azami Wanda ko baruwan Flowers gidana bazai munba shima zai dafaki haka halinki yake?? " kaina na dago na kallesa raina abace " ni wai meye damuwarka dani ne duk kabi ka takuramun yau so kuke ku kasheni ko ina ba dadi ni wlh ba halina bane ba" karya kikeyi wlh idan baki kiyayeni bako Ham wai nine kikacewa kinason wani ko ya fada cikin fushi ya kamo fuskata ransa abace ba tambayarki nakeyi ba kikamun shiru ai Dama nace miki wlh sai na horaki ya fada yana tallabo kaina ya janye niqab Dina mai hade da hijab kadan ya fito da bakina waje Dama hancina waje yake ya had'e face d'inmu wanin irin kamshi kefitowa daga bakinsa idanu na zaro cikin rawar murya bakina na rawa na bude zanyi magana naji tattausan lips d'insa saman nawa ya kama lips d'ina wani irin dumi naji da wani fitunana kamshi kafin na tantance naji ya gantsaramun cizo a labbana sama da k'asa da karfi yake cici zawa hawaye kawai suke sulalowa daga idanuna na azaba saida yaji shashekar kukana ta fito sosai ya saki fuskata cikin fada yace "gobe ki sake mun tsiwa awaya kice kinason wani sosai na tsorata da yanayinsa ga labbana suna mun radadi kai nagama da gwiwa ina rusar kuka ga inajin Sonsa yau sosai cikin zuciyata, banza yayi da ita amma kukan ya damesa ya rasa sukuni Dole ya kalleta har yanzu cikin fushi yake
"my zahara kiyimun shiru banason kukan ki haka kawai kimun laifi Dan na hukuntaki kuma kiyi kuka wlh idan kika sake cinye bakin nakima zanyi naga bakin rashin kunya, kinci sa'a ba haka naso tsawaba amma wancan din natafe sai kinzama tawa idan kinmun ba daidai ba zan miki hukunci dashi ban dagoba cikin shashekar kuka nace" Dama ai basona kakeba shiyasa kake wulakantani harda cizona gashi bakina sai zogi yakemun yau ni ban tashi asa'aba Dama yanzu gwamna yagama cimun fuska shida matarsa wai nice mai muni zan tsorata masa matarsa idan taga fuskata sadakarma da tabani banaso itace naba mai ruwa amma kakece min wai zan gama hannuna ni daga yau baruwana da My Haidar Dama baisan daniba nice nake haukana kuma Aminullah kaima baruwana da kai Dama naji ina sonkane saboda my Haidar da yana yinku iri daya da maganarku amma nafasa tunda kamun mugunta na fada cike da shagwaba ina kuka tausayinta yaji sosai da tsantsar kaunarta na ratsa jininsa da tsokarsa tattausan hannunsa yasa ya dagota da fuskarta ya janye niqab din ya kalli kyakyawar fuskata ya shafo hawayen fuskarta ya kai bakinsa ya shanye " wow my beautiful kiss yama yatsar hannusa ya doramun Akan lips Dina da ya kumburo " wayyo zafi " Sorry Fatimana yi hakuri bari kukan bazan Kara cizonki ba ai duk laifinki ne ya fada ashagwab'e " to ai Kane kacijeni ko "to yi hakuri nine na tabaki ko cikin kukan shagwaba nace" ku biyune kuka tabani na fada ina Kara sautin kukan hawayen na ya rika daukewa yana shanyewa amma naki dainawa kaina ya kwantar kafadarsa yana shafa kaina cikin wata irin murya yace" my haskena yi hakuri banason kukan yada yayi maganar yasa na tsayar da kukan ina sabke ajiyar zuciya inajin sonsa da kaunarsa na ratsani Dan babu abinda yarabasu da gwamnana sai Abu kadan "ai gwara da suka cimiki fuska haka kawai kinaso kima mace kwacan miji da rana tsaka wai ma me yafini dashine da kika nace masa kina nufin kudin da matarsa ta baki bakiso kinba wani ashagwab'e nace" eh banaso mezanyi dasu shima kishinsa yamun yawa na hakura wai Nice zan firgita matarsa da muni Hamm murmushi yayi aboye" wai kina nufin kin daina sonsa?? " yo danme zaimun wulakanci saboda matarsa kaima mun
bata tunda ka cijeni abaki na fada ina kukan shagwaba ashagwab'e yace" wayyo zan mutu my Fatimana bata sona ni sai kinsoni munyi aure mun zuba love agidanmu kin rika goyona ya fada cikin shashekar kukan wasa da Sauri ta dago ta kalleshi bakinta na rawa ta kamo fuskarsa tana hawaye " Aminullah yi hakuri ina Sonka tunda gwamna baya sona kaiko kana sona kuma kuna yanayi dashi wannan kadai ya isa yasa naso ka Dan Allah kabar kuka ina Sonka amma zan rika cemaka My Haidar na fada ashagwab'e ina shafa fuskarsa Wanda babu alamar yayi wani kuka saima idanunsa farare tas da suke haske wani irin murmushi yakeyi afakaice ya dago ya na kallonta ya hade face ashagwab'e yace" ni banason haidar bari nasake wani kukan da Sauri tace" to yi hakuri bari nace My man da Sauri yace" banaso shagwab'ewa nayi" to my chocolatyna ko?? gira ya daga min yana murmushin gefen baki a ashagwab'e nace "Allah ni idan bakaso shikenan " gud my life thanks inaso ina sonki har na koma ga Allah ya fada ashagwab'e " ni my chocolatyna sai karikamun shagwaba inajin wani irin sonka kabari Allah zanyi kuka fah?? " please karkiyi kuka my Fatimana amma bazaki Kara komawa amsar sadakaba ko?? " ni ba ruwana da My Haidar matarsa kadai yakeso ni baya sona tunda kuna kama shikenan suje can su cinye junansuma ba ruwana wlh kaima idan kasan matarka irin ta Haidar ce wlh gayamun tun wuri Nacireka araina Allah bazan auri iri kuba saboda ina da kishi bari gani na yar yarinya dani
Cike da mamaki ya kalleta " da gaske kike my life?? " eh wlh yo ni bazan yada inason mijina arikamun iko dashiba Allah bazan aureka in dai kanada mata hankalinsa ba karamin tashi yayi ba amma ya dake ya shiga lallabata da kalamai masu tsada amma fur ta bijire" Ok naji zamuyi maganar my Teemah nasan maganinki wlh bazan yada kisamun hawan jiniba zanyi wa abun tufkar hanci tun wuri gwara daga baya asan abunyi motar tayi tsaye kofar gidansu Teemah ashagwab'e tace"my chocolatyna kalleni nama hoto ko mun rabu zai debemun kewa hannusa ya Dora kan bakina " wlh zan baki mamaki My life ayanzu kinyi karya ki bujiromun sokike kisani a masifa Oya matso muyi pic ya janyota kusansa amma ko kusa bai rabeta ba Dan baya fatan hakan ya amshi wayar hannuta ido cikin ido suke kallon junansu cikin wani irin shauki na so kala uku ya duka yanaso ya rumgumota amma hakan ba ra'ayinsa bane saboda gudun raini wayar ya bata" Oya shiga gida ki turomun pic din ina Jiranki zamuyi waya wlh idan baki dagaba duk ranar da kika shigo hannuna zaki raina kanki baki na tura na kwakwab'e fuska idanuna sun kawo kwalla" wlh idan kikamun kuka zan baki mamaki ni banyi kuka ba kinason tarwatsamun zuciyata sai kece zakiyi,hadiye kukan nayi saida na bude motar na fito na leko " wlh my chocolatyna da gaske nakeyi na fasa Sonka haushin abunda Haidar yamun har yanzu araina jinka nakeyi kamar shine tunda kuna kama baki ya ciza ya matso da Sauri zai damkeni na zuba da gudu kai ya kada yana bin motar da yagani kofar gidansu teemah da kallo, har direba yaja motar sukabar gun tsaf ya saita nutsuwarsa ya dawo Aminullah sak yace" Boos inason kusama yarinyarna idanu da kyau daga yau karku Kara bari taganku har bayan na kammala daideta ruwan da takeson bullomun dashi? "Ok Oga angama waya ya dauka yakira wata number bugo biyu aka daga" Alhaji Saif girman na baka ya Niger? Ok gud akwai bincike da nakeso kamun daga gobe zuwa jibi ka bani bayani zan turoma da komai da nake baukatar sani arubuce ina jira ok thanks bye ya tsinke kiran ya dafe kansa hankalinsa duk baya jikinsa yana jin tsoron wani Abu karya biyo baya da zai tarwatsa masa mafarin cikinsa motar ta karya kwana har ta bacewa ganina Teemah na shigowa gida suka hada idanu ya harde Hannayensa akirjinsa tayi turis tana nunashi da yatsa " mekazo yi....... ✍🏻
Yar ilu ce🤪
Rahma ce ummu Fareesa😘
*👰🏻MATAR👰🏻*
*💖💖GWAMNA💖💖*
*بسم الله الرحمن الرحيم* ___________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
___________________________________
*Written By*
Yar ilu😉
Yar mutan Niger
*Uwa mabada mama Janafty kaunarki gareni daban take Tun daga farkon matar gwamna har karshe Sadakarwar kice my Sweet momy Janaf👌🏻😘*
*Bismillahir Rahamanir Raheem*
*Page 1⃣0⃣*
......"lfy dai ko naga kadawo?? ta fada bakinta na rawa murmushi ya sakar mata "lafiya kanwata wlh naji bazan iya hakura bane na dawo amma meye hadinki da wannan mutumin da yanemi hallakani?" yaya Haseem kayi hakuri sasune akeyi cikin fada fada yace "to wlh basu isaba kowama Dan iskan kansane akanme za'a takuraki haka kawai idanu nazuba masa ina kallon ikon Allah warsu mai gadima dariya abun ya bashi kamar ba d'azu ya gama maruwaba" yanzu dai kayi hakuri zamuyi magana anutse zan shiga cikin kar anty tamun fada" OK kije din zamuyi magana gobe insha Allah ki gaida Aunty? " to taji na fada ina tafiya kai ya girgiza ya fito kenan zai shiga mota yaga boos gindin motarsa atsaye fuskarsa ya hade ya iso gun motar " kasan abin da nakeso da kai wlh ka fita daga harakar wannan yarinyar cikin fada ya dago "bazan fitaba ubanwaye ya turoku wani gigitaccen Mari boos ya zabgawa Haseem har ukku a take hancinsa da bakinsa jini ya rika zuba ya shakesa ya Nuna masa bindiga "wlh mutarkar baka rabu da ita ba zan maka illa duk Oga ya hana duka amma kai taurin kaine dakai ya fada yana sakinsa ya fadi k'asa wanwar ya nufi mota yashiga sukabar gun haseem ya Mike yana Allah ya isa,
Ya shiga motarsa yabar gun amma ya tsorata da lamarin tun kafin yarinya tasan yana sonta har ya fara shan dukan maza akanta Dole zai gagauta janyota jikinsa ta soshi idan yaso komai amasa ma, Teemah tana shiga parlo bedroom ta wuce malika bata parlo wayarta ta buye ta ajiye Alqura'anin ta shiga bedroom ta dauro Alwalla Ana kiran magarib ta fito tayi sallah koda ta gama bata tashi tana Adu'ar Allah ya cire mata son Haidar da Aminullah Dan taji haushin abinda gwamna ya mata, saida aka kira sallahr isha tayi ta Mike wayarta ta dauko taga bai kiraba zama nayi bakin gado ina kallon pic din da mukayi da Aminullah tsantsar kamarsu da Aliyu nake gani jinayi sonsa ya lumku azuciyata sai dai kishi ya rinjayeni yanzu nafi son Mara mata Malika ce ta kirani da Sauri na Mike na boye wayar na fito "Fatima me kike kinki fitowa? "Aunty sallah nayi kusanta na zauna muna hira "yayanki yana gaisheki? " Aunty kiramun shi Dan Allah "yanzu bazamu samesa ba bari na kira miki Abba "yauwa yayata nagode bugo biyu Abba ya daga suka gaisa ta bani"Abbana wlh kamar nazo nakeji" auta yi hakuri zakizo kiyi karatu dai yanzu ai kunkusa samun hutu "Abba ina iyayye?? " gata Auta amshi ku gaisa kinsa nawalu da lado sun adabeni wlh har tausayi suke bani goro da kifi baya gabce mana kukan shagwaba nasama Abba sai daket yashawo kaina nayi shiru yaba iyayye wayar "iyayye ina yini? " Auta ya karatu kursiya kawarki ta haihu fah? " wayyo dadi iyayye ku gaidamun ita wlh da dahali da nazo sunah
"ta haifi danta namiji saura ke duk abin ana zaginmu wai kin girma ba aure har shekara16 bakida aure" dan Allah iyayye kibarsu basuda aiki a birni wlh ko yayeni ba'ayiba daga nono bare wani aure "mudai dan Allah ki tsayar da miji ayi magana yar uwarki ma tanada17 year aka mata aure kema kiyi qoqari kafin lokacin" iyayye mubar maganar bani Abbana wayar ta bashi mukaci GABA da hiramu munjima sosai kafin muyi slm na kashe wayar "Anty Malika kursu gawata ta haihu na girma nayi d'a wlh dukan wasa ta kaimun "wlh ke ko Allah shirya ai ba yau kikeda yaraba ko shuriem "eh momy Aunty mune diyanki Rasheed yace "Aunty kinfi sona ko "wlh dukanku ina sonku Malika tace"ku tashi muje muci abunci kan dining mukaje yau tuwan tukakiyar shikafane da danyar miyar kub'ewa taji busasan kifi mukaci mukayi dam muka dawo parlo muna hira sai karfe goma nama Aunty saida safe mai sunan iyayye sai kuka take na dauketa saida Malika ta samata nono abaki tayi shiru, ina zuwa wanka nayi nasaka kayan bacci na Haye gado wayata aikuwa kira ya shigo kin dauka nayi dan nayi Alkawalin bazan sake daukan kiransaba bare muryasa ta tadamun hankali naji duk bana ra'ayinsu da ya dameni da kira pic dinsa na kalla na sumbata na kashe wayar baki daya na boyeta da alkawalin bazan sake kunnawaba nayi Adu'ar bacci na shige cikin bargo har bacci yayi gaba dani,
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Zaune yake a hamshakin parlonsu Wanda ya gaji da haduwa saman wata lumtsumemiyar kujera farin gilashi manne kan kyakyawar fara fuskarsa Laptop ne gabansa amma baya dannawa yaransa yake kallo yana murmushi yada suka cika parlon da hayaniya game sukeyi na mota jikin makekiyar TV yar bango Rauda ta kafa musu rigima sai sun bata alhalin ba iyawa tayiba bintu da ke gefe tanashan kayan itatuwa ta kallesa "My Man juyowa yayi ya daga mata gira" ka musu magana suje su kwanta ni inada bukatar mijina murmushi ya saki dama yasan yau tunda ta kafa masa rigima da botsanci na banza sex takeso daket ya bude baki ya kira Rauda"baby Rauda zo kiji da gudu tayi wajan babanta ta fada kansa"dady gani rumgumeta yayi yamata kiss "baby kin fiye rigima kibarsu suyi wasansu bintu ta matso gunsa"my man ni ina magana fah dariya Rauda tayi ta sabka daga jikin dadynta ta koma gun bintu ta rumgumeta"umma me akayi "bakeba ce kika gudu gun dady ta fada tana