Showing 75001 words to 78000 words out of 129912 words
Chapter 26 - MATAR GWAMNA COMPLETE Document from Abdallah.txt
da waje wallahi ina sonka mijina mutuwace kadai zata rabani dakai ashagwabe nace" my Mijina? " na'am My Matata duniyar dadin chocolate menene fadamun? " my babyna gwamna ina sonka wlh ni nama manta ankoma makaranta yo ka shagalar dani Ka kaini kololuwar dadi ina zan sani. murmushi yasaki zaiyi magana wayarsa ta dauki ringing kan table din ya kalla ganin boos ne ya Mike da teemah tana rungume jikinsa ya haura sama da ita sai kyalkyala dariya take" My Alina yau munji dadinmu sosai ko? " bari kedai yar babyna my dadin duniyata. kaya ya saka mata doguwar Riga ta shadda milk color ya saka mata hijabi chima milk din jaka milk takalmi milk komai milk ya dauko wayarta yasa mata ajaka ya goyata suka fito saida ya sabko k'asa ya sabketa ta dauko jakarsa da ta shirya masa kayan tafiya ta danne kukanta da damuwarta ya kwashe wayoyinsa ya kalleta murmushi na sakar masa "my Noor muje ki dan zauna gun bintu anjima boos zaizo ya kaiki bayan son dawo daga Airport ya fadi yana kama hannuna kasa magana nayi ina rike da jakarsa da tawa ya bude kofar da yakebi muka shiga bangaran Bintu ni na manta ko yan aikina banma sallamaba.a parlo muka isko bintu zaune tana waya tana kwasar dariya ita da matar Jamal Abokin Aliyu dan yau sunada meeting Akan yada zasu koyama mata sana'o'in hannu da temakawa nakasassu da gajiyayu. dan duk yaunin ya rataya wuyan bintune amatsayinta na matar gwamna hannun Aliyu teemah ta saki ta nufi gun bintu da gudu ta fada jikinta. Bintu ta kashe wayar ta rungume teemah"my Fatima ykk yau nayi missing dinki Aliyu yace "my bintu nifa ya fadi yana daukan zahara dariya tayi tace"my man harka mana. "to zo na ganki jirgi na jirana. Murmushi tayi tace "wlh dazu da kafito nazata wasa kakemun dan kasani kukane ashe da gaskene. ta fadi tana janye teemah ta Mike tabi bayansa a zaune ta iskoshi ya bata hannun ta kama ya fizgota jikinsa "my bintuna zan tafi sai nayi kwana uku insha Allah zanzo gareki ki gyaramun kanki da kyau ya fadi yana kissing dinta ya janyeta jikinsa ya Mike"to lokacin yayi zan tafi kimun Addu'a anjima za'akai my zahara gidan Malika.rungomeshi tayi ta masa Addu'a acikin kunnensa yana murmushi yana rungume da zahara suka fito teemah na zaune ta kurawa Tv idanu wayar Aliyu ta dauki ringing ya daga "hello Boos angama shiyar komai kazo kofar parlon Bintu ganinan fita ya fadi yana katse Kiran wayoyinsa biyu suka soma ringing atare kin dauka yayi Bintu ta dauki jakar ta kama hannun teemah suka rakoshi har kofar parlo teemah jikinta har rawa rawa yake ta kure Aliyu da ido shiko da gangan yaki kallonta dan yasan hankalinsa zai tashi kuma kuka zatayi bintu na bude kofar tabshi jakara boos na tsaye Aliyu yaba Boos jakar yayi gaba yace"Bintu ki gaishemun da yarana sai nadawo my zahara bye ya fadi yana wucewa da Sauri bintu kanta idanunta sun ciki da kwalla hannu teemah
ta kamo muryata asark'e tace "zahara muyi hakuri zai dawo kinji kawai sai ta fashe da kuka ta rungume bintu itama bintun kukan ta Saki ta rungume teemah dan ayanzu tafi teemah bukatarsa ta tsumu sosai gashi tafiya ta fado masa kai tsaye bintu ta tsayar da kukanta ta lallashi teemah har tayi shiru tajata suka zauna tana bata labarin dariya amma teemah Sam batada nutsuwa dan zazzabima ya zubo mata Bintu ta dauko mata magani ta bata tasha ta rungumeta ba jimawa tayi bacci Bintu ta kwantar da ita saman kujera tana mamakin yada yarinyar tayi yar kiba tayi jajir komai.nata mai kyau murmushi ta Saki "Aliyu zaki na bintu da Bintu Baban Bintu aikinka na kyau har ka harba Zahara taka da wuri haka masaha Allah Allah ya raba lfy nikam nasan fitinar Fatima sai mai Sabon ciki mik'ewa tayi ta nufi bedroom tana shiga taji karan knocking din kofar parlo saida tayi abunda ya kaita ta fito lokacin jiddah taje ta bude musu Fadila ce da Safina ta gansu zaune sun zubama teemah idanu Safina haushine yasata ta ingiza teemah da tayi daidaya tana bacci saman doguwar kujera zata fado ga wani karamun table glass kusan inda zata fado Bintu tayi Sauri da gudu tayi kan teemah tana cewa Fadila kutarota karta fado Sabon cikine da ita don Allah ku temakeni ku rufamun Asiri.............✍🏻
💃🏻Yar Janafty ce😘
Rahma ce ummu Fareesa😘
*👰🏻MATAR👰🏻*
*💖💖GWAMNA💖💖*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
____________________________________
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
____________________________________
*Written By*
Rahma AbdulNasir
Yar mutan Niger🤙🏻
*Uwa mabada mama Janafty kaunarki gareni daban take Tun daga farkon matar gwamna har karshe Sadakarwar kice my Sweet momy Janaf👌🏻😘*
*Bismillahir Rahamanir Raheem*
*Page 3⃣3⃣*
....aikuwa kafin Fadila ta iso ta tareta sai ga teemah ak'asa ta fadi table din ya goce ta tayi k'asa rufda ciki ta fadi saman kafafun table din ta Saki Kara saboda azababban zafin da taji ta karce ahannu ga cikin na mata mugun ciwo. da gudu Bintu ta iso ta kamata ta tayar da ita hankalinta atashe duba da yada teemah ta rike cikinta tana hawaye bintu tace"Fatima sannu ina yake miki ciwo? " wayyo Aunty cikina wayyo cikina arikice Bintu ta jata kujere ta zaunar da ita ta dauko wayarta ta kira number Dr zubaida bugo daya ta daga " Dr kina hospital ne... ? dagacan ta bata amsa" eh ranki shidade ko nazone" no gamuna zuwa. Kitt ta kashe kiran
ta kira number direban ta tace ya fito da mota zasu hospital.Teemah kuka take sosai tana rike da cikinta sai murkususu takeyi bintu ta kalli Safina wacce tayi tsuru tsuru da idanu batace komai ta shiga d'aki da gudu ta canza kaya ta Goya zahara tace" fadila kuje gida kawai safina nagode yau kin nunamun kauna mutikar kikayi sanadiyar salwantar Abu biyu daga cikin daya ko duka wlh bazan. taba yafe miki ba. ta kama teemah suka nufi kofar parlo teemah ta galabaita sai zuface take keto mata jikinta na rawa kofar bintu ta bude tana Addu'ar kar Boos ya Gansu dan tasan tabbas sai ya fadawa gwamna. suna fitowa direban na tsaye da mota kusan part din bintu da security guda biyu suka bude masu.
mota Bintu tasaka teemah ta shiga ta zauna ta rungumeta sojojin suka shiga motar direba yaja suka nufi get. teemah wata irin Azaba cikinta ke mata sai ciza baki take ta rike bintu gam" wayyo Anty zan mutu wayyo ciki. " yi hakuri zahara dan Allah kirufamun asiri babu abinda zai sameki insha Allahu. ana bude musu get suna ficewa direba gudu yayi sosai jin yada teemahr take kuka. cikin yan muntuna suka isa hospital din cikin gagawa aka amshi teemah dan har jini ya bata mata zaninta abinka da milk color din zane Bintu ganin jini jikin teemah ya bata kujera da ta zauna zuface ta fara keto mata hankalinta atashe ta kasa tsaye ta kasa, zaune hawaye ya wanke mata fuska tabbas tasan cikin zahara zubewane yayi ina ne zatakai tashin ahankalin Aliyu me zatace masa ya zatayi bayan tasan duk abinda yawakana idan baya gari tun tana ita daya sai ya kalla a ccTV camera
zuface ta karyowa bintu ta rasa meke mata dadi. can ciki ko Dr zubaida ce tsaye kan teemah ta gama ganowa cikine jikin teemah na tsawon sati uku cif amma tayi kokarin temakawa wajan tsayar dashi amma ina abun yaci tura saboda ta bugu kan cikin dayawa ga marata ma ta bugu sosai teemah wata irin naunin azaba takesha ta fice haiyacinta jitake tamkar mutuwa zatayi ga wani irin azababban ciwon ciki Wanda saida ta sume zubaida tayi iya yinta amma ina hukuncin Allah babu mai dakatar dashi dan cikin ya zube ga teemah cikin mawuyacin hali dan har cikin ya gama zubewa batasan idan kanta yakeba gashi ta zubar da jini allurai zubaida ta hada da maguguna ta sakamata Karin ruwa tasan azabace zata dawo haiyacinta zuwa jimawa idan maguguna da Karin ruwan sun ratsata bayan ta gama ta fito. Bintu najin karan bude kofar ta nufi gunta. "Dr ya
jikin nata...? zo mushiga daga ciki dakin da teemah take suka koma bintu ta zuba mata idanu cike da tausayinta tana hawaye. Dr zubaida tace" wlh nayi yina amma cikin ya fita gashi ta bugu sosai garin yaya haka ta faru a saman me ta fadane...? Bintu hankalinta a tashe tace" daga saman kujerane ta fado ta bugi table ya goce ta fada saman kafafunsa. "to Allah yasa kada ta samu wata matsala yanzu sai tadawo haiyacinta zan sake bincikata ko babban doctor da kansa kidaina kuka zata warke insha Allah yanzu kije ki kawo mata kaya kafin ta farka da abunci mai kyau za'a kulata sosai har ki dawo.Kai bintu kawai ta daga hankalinta amugun
tashe dan batasan ya Aliyu zai amshi abunba suna fitowa ta nufi gun motar sojan ya bude mata mota ta shiga suka nufi gida. Suna zuwa ta iske Boos na nan yana ganinta ya nufi gunta" ranki shidade ina kukajene Oga yace nakai amarya gidan yayarta. " Boos mu dan kebe zamuyi magana can kusan part din bintu tace" Boos dan Allah karka fada masa wlh bata lfy tana hospital kuma kasan idan yasani zaice ya dawo gashi taron nada mahimmanci zan kula da ita sosai pls idan ya kiraka kace ka kaita. " to shi Kenan madam Allah yabata lfy. "Ameen nagode ta fadi tana shiga ciki. Kiran Malika tayi tace tazo yanzu. agaguce tasa aka hadawa teemah girki mairai da lfy kayanta kala biyu ta daukarwa teemah abayoyi ne dan dinkita yama teemah yawa sosai pant ko tanada sabbi Wanda bata saba sunyi kananu su ta hado acikin kayan ta zauna jiran agama girki kafin Malika ta Iso. Malika ko hankalinta
atashe ta kai yaranta gidan hajiyar Mu'azzam ta nufo gidan gwamna.jiddah sun gama hada komai malika ta iso bintu ta tarbeta cikin sakin fuska dan kar ta daga mata hankali. Bintu tace" jiddah zan koma hospita kirawo Asma'u mai kula da yara. da sauri taje ta kirawo Asma'u sukazo tare. " yauwa Asma'u ki kula da yara idan sun dawo daga school sai nadawo jiddah keda zuwaira kuyima yarana girkiki mai kyau pls. atare sukace "insha Allahu hajiya zamu rike Amana" yauwa nagode kuje sha'aninku sai nadawo. Malika tace"Aunty ban fah ganeba. "Malika muje zaki gane jiddah zo dauki kayan muje mota. da gudu tazo ta dauki kwandon abuncin da yar jakar suka fito Malika hankalinta duk atashe yake. suna fitowa. suka nufi gun motar direban na jiranta da security guda biyu suka bude musu motar suka shige direba yana suka tafi.
Suna zuwa hospital direct room din da aka warema teemah suka nufa saida Bintu takira zubaida awaya tazo ta bude musu suka shiga Malika tayi kan teemah da gudu ta rungumeta itako baccin walaha takeyi kuka malika ta fashe dashi" Anty meye yasami Fatima.? " malika cikintane ya zubo satinsa uku ajikinta inji Dr zubaida. Bintu zama tayi gefen gadon tana hawaye tarasa meke mata dadi. Malika saida taci kukanta tayi shiru ta rungume kanwar tata tana shafa kanta tace" Aunty Bintu sannu Allah yabaki ladanki wlh idan watace bazata temaketa ba saide ta mutu Allah ya Kara hada kanku. Bintu tace"malika babu komai wlh ni kanwata na dauketa Allah yabata lfy. sai wajan karfe daya teemah ta Motse cikinta na mata ciwo Bintu da malika suna mata sannu malika ta kamata ta Mike suka shiga toilet ta hada mata ruwan gumi ta cire mata kayanta da kanta ta gasata sosai teemar sai kuka take saboda zafin ruwan ga ciwon ciki na damunta. bayan ta gama mata wanka bintu ta beko mush kayan malika ta saka Mata teemah tana cije baki ta kimtsa soka fito. ahaka suka lallabata taci abunci kadan Dr zubaida ta mata gwaje gwaje taga akwai sauran gudajin jini acikinta Dole saida aka mata wankin ciki Wanda
ba karamar azaba tashaba duk saida suka zubar da hawaye bintu sai Allah ya isa takewa Safinar bayan an gama mata alluran bacci da Karin ruwa yasha maguguna sai karfe biyu Bintu ta tafi gida ta duba yaranta ta dawo. Bayan sallahr la'asar malika na tare da teemah har yanzu bacci take tana rungume jikin malika Aliyu ya kira wayar teemah ba adadi sai yanzu malika taji ringing din wayar ta janye jikinta ta janyo jakar teemah ta bude zip din ta ciro wayar tayi picking ta Kara akunneta. tayi sallama dagacen ya amsa" malika lafiya kuwa me yasami Zahara bata daukan kirana. idanu malika ta fara rabawa sai tayi saurin cewa" mura take Tasha magani shine take bacci. " wayyo baiwar Allah OK zan kira zuwa dare lokacin ta Tasha dan Allah kikulamun da ita karki barta cikin damuwa kitt ya tsinke kiran. ajiyar zuciya Malika ta sabke.
tana jinjina son da Aliyu yakema kanwar tata tabbas idan yasan da maganar ta bintuce dawowa zaiyi. teemah bata farkaba sai dare lokacin bintu tazo Dr ta sake duba teemah da kyau Alhmdllh bataga matsalar komaiba ah maharfarta lfy lau take. Bintu ta gaya mata cikine da ita ya zubo teemah mamaki tayi ciki kuma basarwa tayi abun bai dametaba ita dadima taji ai gani take bata isa ajiye yaraba. matsalar daya ciwon ciki dayake. damunta kuma tana zubar da jini shiyasa Dr tace sai tayi kwana biyu ta huta sun Kara dubata sosai Bintu ta roki Dr karta fadawa Aliyu teemah tace ita bazata fadaba dama batason ciki haka suka binne maganar agurin tunda bayanan bai saniba Bintu ta samu nutsuwa sosai hankalinta ya kwanta niko nace bintu kin manta gidanku akwai cctv camera sai karfe Tara tabaro hospital malika ita da yarta mai sunan iyayye su shuraim suna can gidansu Aliyu da yakira teemah haka ta daure sukasha hira tana ciza baki dan ciwon ciki na damunta sai can dare sukayi sallama yana Kara jadadda mata gobe ta koma gida. Dr tazo ta Kara dubata tayi musu sallama teemah ba jimawa bacci ya dauketa malika kuwa tunani takeyi idan Aliyun yasan da cikinsa fa ya kenan ahaka har bacci ya dauketa bangaran bintu taji ta samu nutsuwa tunda tanada tabbacin Aliyun baisan da cikin ba
************************************
Bayan kwana biyu yau teemah kwananta biyu hospital tayi sauki sosai ciwon cikin yayi sauki jinin ya tsaya ta murmure sosai tanacin abunci Bintu da malika suna bata kulawa ta musamman har yau Aliyu baisan meke faruwaba teemah ta ajiye hankalinta suna waya da Aliyu bata masa rigima sosai da koke koke saide shagwabar da tazama jinin jikinta har mamaki yake ya akayi bata masa kuka niko nace Aliyu Dama cikinka ne dan fitina yanzu kuwa yazube Bintu tayi kokari sosai wajan kulawa da teemah koda wasa bata yardaba yaranta suka sani dan karma suyi subutar baki su fadawa dadynsu watarana. Yau tin asubah Malika ta shirya musu kayansu tana jiran Dr tazo ta sallamrsu saboda teemah zata school. Karfe shida da rabi Dr Zubaida tazo ta sallamesu bayan ta Kara duba lafiyar teemah taji dadin yada ta warware sosai Bintu ta turo direba aka daukesu harda security suka nufi gida.
Suna zuwa gida part din teemah suka nufa suna shiga Nasira ta taresu "hajiyata kika tafi gida ba sallama sai anty bintu mukaje muka tambaya. murmushi teemah tayi tace"Afuwa yanzu ina saurine zamuyi magana idan na dawo Makaranta zani anty muje na shirya. sama suka haura dakin teemah suka shiga agagauce tayi wanka ta shirya ta saka Riga da siket na less blue takalmi jaka mayafi komai nata blue colour ta saka batayi kwalliya ba amma tayi masifar yin kyau yarintarta ta fito karara ta kwashe takardunta ta zuba ajaka Malika tace"masha Allah kanwata bazaka saka hijabi ba kuwa...? "Haba anty muje na makara ko zaki taimaka kimun gyaran daki. "Wlh bazan tsayaba dariya teemah tayi sauka sabko k'asa teemah tama su walida sallama suka fito Boos na jiransu ya bude musu mota suka shige. direba yaja suka tafi. direct Matrix international Academy suka nufa. lokacin da sukaje tuni
har anshiga aji an rufo kofar get amma da yake matar manyace tana zuwa aka bude mata kofar har kofar aji Boos ya rakata aciki gun zamanta ma daban saida
ta zauna Boos ya fito ya shiga motar direba yaja ya tafi gidan malika suka nufa sai yanzu ta tuna basuma bintu sallama ba. tana zuwa gida ta kirata ta bata hakauri bintu tace ba komai ai tasani gagawa sukeyi Fatima ta makara zuwa zana jarbawa. Malika bayan ta huta ta tafi gidan surukanta ta dauko yarnata dan tayi kewarsu
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
teemah basu baro makarantarba sai karfe uku da rabi bintu ta aika mata abunci ran teemah duk adagule saboda wani matashin saurayi tunda yaga teemah ya rasa nutsuwarsa adakin jarabawar ya kasa sukuni sai ya fakaici jama'a yake mata magana yana mata wani shegen kallo tayi me tsiwar har tagaji gashi ba wani dadin jikinta takejiba batason takura daket adadafe suka gama har ta tafiyarta Ashe biyosu yayi dan baisan matar gwamna bace ai yanaga gidan da aka kawo teemah yayi baya amotarsa domun daura damara samun yar gidan gwamna dan lokaci daya Allah ya zuba masa azababban sonta. Dan yaji zaiyi yaki da duk Wanda yace zaima katanga da yar kyakyawar yar gidan gwamna sai yayi duk yada yayi yajawo hankalinta gareshi.
teemah agajiye tazo direct part din bintu ta yada zango a parlo tayi kwanciyarta sai bacci bintu na tsokarnata Raudah na jikinta azaune bintu ta korata sai yamma lilus teemah ta tashi bintu tasa aka kawo mata abunci taci atakaice teemah sai darena ya kaita gidanta tabiyewa su muneerat da Asif suna game a tv bintu nayi musu dariya. tana zuwa wanka tayi tayi sallah ta kwanta dan taga jinin ya tsaya wayarta ta kashe danma kar Aliyu ya hanata bacci baima kiraba dan bashida lokaci sosai.
***
Washe gari da misalin karfe biyar teemah da bintu suna zaune a parlo Bintu anci uwar kwalliya ta hade cikin wani rantsarsan material Ja mai ratsin baki kasancewarta farar mace tayi kyau sosai ansha kunshi da kitso haka teemah hafsat ce ta musu kanwar mu'azzam domin