Showing 159001 words to 162000 words out of 185716 words

Chapter 54 - MAR'ADAM'S book Complete BY AYSHA A BAGUDO.txt

23 Nov 2024

4704

son juna ."


"Na tambayeki ?
"Ina jinki ! mu ajiye maganar wasa zaki aure adamcy ne saboda kina son shi ko kuma zaki auresa ne dan biyayya wa mahaifiyarsa ? "zan aureshi ne dan ina son shi "akan wani dalili kenan zaki so shi ? tambayar tabawa maryam mamaki amman sai ta kawar da mamakinta tace "akan dalilai masu yawa ."ko Kinsan akwai wacce ta fiki son shi da son mallakarsa wacce zata iya komai akansa ?


"Eh nasani "!
"Wacece ?ke mana na samu labarin kina mutuwar sonshi Kmr Kiyi hauka afirgice hindu ta juyo gareta tana cewa "tabbas bakiyi karya ba ina mutuwar son shi irin son da zan iya yin komai akanshi dan haka abinda zan iya ce miki ki rabu dashi ki kuma fasa aurensa saboda adamcy raina ne akanshi babu abinda bazan iya yi ba ".


"ni kuma akan na rabudashi na bar miki gara na rasa raina." shine nima abinda na gani kenan, kuma nake tunani akai, kmr mutuwar ce zata fiye miki sauki akan ki cigaba da rayuwa a doron duniya , dan zan kasheki tun wa'adin kwanakin mutuwarki bai cika ba, zanyi sanadin rasa ranki batare da kin shiryawa hakan ba, ta karasa mgnr cike da matsanancin zafin rai tana fitar da hucin kishi.




"wai meye haka ne hindu kike kokarin aikatawa ruhin da bai d'aukar miki laifin komai ba? "gsky zan gayawa mami . "ba sai kin rayu ba tukun zaki gaya mata ina tabbatar miki daga nan sai kabarinki, domin kuwa zan miki aika aika ,zakiyi mutuwa mafi muni da rad'ad'in azaba wanda ko makiyinki yaga gawarki sai ya koka miki "aikin banza kawai daman da wata manufa kika daukoni a motarki ?


"Yes of course da wata manufa na dauko ki mana ,amman da yake Ke jaka ce kika qasa ganewa tana gama fadar hk taja wani irin wawan birki sannan taja motar aguje ta soma hajijiya da motar akan titi bata tsaya akoina ba sai atsakiyar titi , ta fito da hanzarinta, kafin maryam tayi wani yunkurin fitowa daga cikin motar , tuni har hindu tayi lock din motar gbdy , ta tsaya rike da kugunta tana dubanta tana murmushin mugunta ,"wai meye hk ne hindu ?


"mutuwa kenan !"


"ki budeni karki kasheni da wasa nake miki wallahi bana son shi nima zan auresa a dole sbd mahaifiyarsa "hhhhhhhhhhhh karyarki yarinya ai wasan ya rigada yazo karshe sai ki jirasa a lahira har zuwa sanda zai iso gareki so that kwa auri juna acan inda wata katuwar tanka mai ta nufo motar gadan gadan a matukar tsorace maryam ta saka wata razananniyar k'ara me sauti "tana toshe kunnuwanta duka tare da runtse idanunwata .......




Mmn sudai


💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗




*AYSHA A BAGUDO*


WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim


Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.




Page 26


hankalin maryam ya qara tashi Kuka take sosai da iyakacin karfinta tana furta duk wata adduar data zo bakinta domin neman cikawa da imani dan gabadaya ta sadaukar da rayuwarta akan mutuwa zatayi yayinda hindu ke tsaye rungume da hannuwanta duka a qirji tana sakar mata murmushi farinciki tana kallon yadda motar ke tahowa wajen motarta da maryam ke ciki ."


maryam ta kamkame jikinta sosai tana mai sake fashewa da wani gigitaccen kuka jira kawai take taji saukar motar akanta amman sai taji shiru sai ma jiniyar motar ' yansanda ta jiyo dan haka da sauri ta ware idanunta dan tabbatarwa kanta gaske ne ?ganin motar yansanda ta sha gaban motar yasa ta sauke wani naunayen ajiyar zuciya da numfashi atare ,yayinda mutumin dake ciki motar ya soma qoqarin fitowa domin ya tsire amman cike da hanzari yansanda suka samu nasarar damke bala ,cikin tsananin tashin hankali yake masu bayanin komai dan gabadaya ya gama rud'ewa "


Yayinda hindu ke tsaye awaje kamar an dasata tsabar firgitar da tayi zufa ce kawai ke karyo mata dan kana kallonta zaka fahimci yadda hankalinta yayi mugu mugun tashi , gashi tana son guduwa kamar yadda bala yayi qoqarin yi amman ta kasa aiwatar da hakan har sanda ' yansanda suka samu nasarar daba masa ankwa a hannuwansa tana tsaye kikam kamar mashi ."


Zuciyar hindu ta shiga bugawa da matsanancin karfi nan take ta shiga sake sake hade da jerowa kanta tmby "wa yasan shirinta ?wa ya turo 'yansanda ?"yaakayi suka san inda zata aiwatar da shirinta akan maryam ?ita dai tasan daga Allah sai bala da zasu yi aikin tare suka san komai dan hatta babanta bata bari ya sani ba ."


shiru tayi kawai har zuwa lokacin da yansanda suka qaraso zuwa inda take tsaye suka tsaya a gabanta
a wulakace ta d'aga kanta tana kallonsu d'aya bayan d'aya tare da bude bakinta zata soma zazzaga masu ruwan bala'in 'bata mata shirinta da sukayi amman sai taga daya daga cikin police din dake tsaye a gabanta ya ciro I'd card daga gaban aljihunsa yana nuna mata kasancewar babu uniform ajikinsu da alamun cid ne ."




wani dogon tsaki taja tana cewa "ai ni ba makauniya bace, ko baka fito da I'd card dinka ba nasan ku din yansanda ne "? dan sanda ya gyada mata kai kawai yana kallonta a tsanake kafin daga baya ya soma magana "da fari ki miko mana key motar hannnunki a fito da wacce kikayi yunkurin kashewa " furzar da iska mai zafi tayi daga bakinta kafin daga baya cike da maseefa tace "bazan bayar ba ,dan tunda nayi niyyar kawar da maryam daga duniya a yau din nan sai nayi babu fashi idan yaso nima daga baya akasheni tana qarasa maganar tabi gefensa zata wuce har tayi taku biyu taga wata gajeruwar macen yansanda ta harde mata kafafu sai gata dim a kasa ta zube bisa gwiwowinta inda key'n hannunta ya fadi kasa ."




Macen yansanda ta qaraso inda hindu take wargaje a kasa cikin azaba ,kallo daya zaka ma macen yansanda kasan babu rahma a fuskarta ta d'auki keyn daya fadi ta mikawa d'ansandar dake tsaye a kusa daita"ungo naziru maza ka fito da yarinyar" ya karba keyn daga hannunta da sauri ya nufi inda motar take ."


Macen yansanda ta fito da ankwa daga cikin aljihunta tana duban hindu a tsanake kafin daga bisani ta soma qoqarin kamo hannunta domin da'ba mata ankwa amman hindu ta fixge tana zabga mata harara "ki miko hannunki na saka miki ankwa ko kuma na harbe kwakwaluwar kanki yanzu ." wani murmushin bakinciki ya bayyana akan fuskar hindu "bazan so faruwar haka ba ,dan bazan so na bar duniyar nan batare dana kawar da mutun biyu din nan a duniya ba,wannan hatsabibiyar yarinyar da kuma wanda zai aureta, duk da na shiga hannu amman ban yi nadama ba ,dan ni kadai nasa me nake ji a zuciyata yadda zan rasashi dole itama ta rasashi ."






Ta sake yin murmushi wanda kana gani na takaici da bakinciki né da rashin cimma buri "duk da na shiga hannun amman nasan zan fito dan mahaifina zai yi iya qoqarinsa sannnan zai kashe ko nawa ne akan yaga na fito tana gama fadar haka ta mika mata hannuwanta duka , sai da suka kalli juna da sauran yansanda nan take suka fahimci yanayin cewar hindu bata cikin hayacinta ,ta daba mata ankwa a hannuwanta tana cewa "duk abida kike taqama dashi wanda yasa muka bibiyi rayuwarki har zuwa yau din nan ya fiki kuma yafi mahaifinki komai ."


"idan taqamar mahaifinki nada kudi ya zartashi dan haka kisani matsawar bashi ne ya lamunce ki fito ba ubanki bai isa ba ,kuma bashi da kudin da zai fito dake oya muje ."ta qarasa mgnr alokacin da aka qaraso da maryam wacce ke kuka har lokacin ga wata zufa dake tsatsafo mata a dukkanin ilahirin jikinta kallo daya zaka wa maryam ta baka tausayi ."


Wani wulakantaccen kallo hindu tayiwa maryam sannan ta yunkura ta mike tsaye cike da d'agawa da isgilanci ta kalli macen yansanda tace "koma waye shi ina mai tabbatar miki mahaifina yana da karfin ikon da zai sa shi ya lamunce a fito dani ta qarasa maganar tana sake watsawa maryam mugun kallo "Ke kuma ki jira fitowata wallahi karon mu bazai yi kyau ba, bazan ta'ba barin kiji dadin rayuwarki ba, baqar makira wallahi nice ajalinki ki rubuta ki ajiye ."




wasu hawaye masu zafi suka gangaro acikin idanun maryam hankalinta ya qara tashi fiyye da lokacin da take cikin mota ,yayinda zufa ke sake karyo mata muryarta a raunane. tace "police kunji abinda take fad'a wai zata kasheni itace ajalina "ki kwantar da hankalinki babu abinda zata iya miki daga hannunmu sai kotu zaa kaita daga kotu kuma sai gidan kurku kinga babu wata hanyar data sauran mata "karya kake munafukin Allah bani ce zani kurku ba uwarka ce zata kurku shegu matsiyata kawai tass tasss!! taji saukar mari har sau biyu ajere akan kuncinta nan da nan ta rikice ta dinga zaginsu tana tsine masu albarka mrym tana kallo aka tasa keyar hindu da bala abayan motar yansanda ita kuma aka sakata cikin wata motar aka d'auki hanyar gida daita ."


Acikin mota hindu ta kalli macen yansanda taja wani dogon tsaki ta bude baki zatayi magana kenan taji sauka mari tasss!! ta sauke mata wani lafiyayyun mari "kina sake bude mana wannnan rubabben bakin naki zan qara miki wasu marukan dan haka ki kama kanki ki bari salin alim mu kai ki office idan ba haka ba zan sakar miki harsashi yadda taga matar tana mgn tana zazzaro mata idanuwa tana huci tasan da gaske take zata iya aikata fiyye da haka amman bata jin zatayi shiru ."




Ta dinga kallon matar zuciyarta na cigaba da yi mata zafi ranta da zuciyarta na wani irin tafasa ta dinga zagin yarsadar can kuma tayi shiru tana son sani waye yyi mata wannnan shishigi da katsalandar cikin rayuwarta ? cure hannuwanta tayi waje daya tana bugawa da juna batayi tsamanin shirinta zai ruguje haka ba ta dauka zatayi komai ta gama babu wanda yasani taci bulus ,wato mutuwar maryam ya tafi a banza bata kawo abun zai zame mata haka ba ."


Suna isa police station ta ciro wayarta daga cikin jaka zata kira number babanta amman taji an bata warning tare da kwace komai dake hannunta aka turata cikin wani qaramin daki wanda aka tanada domin masu laifi irin nata sannan suka maida kofar suka rufe garam ."kukan bakinciki bata cima burinta ba gashi kuma ta shiga hannun hukuma ya kufce mata ,dan haka ta soma maganganu cikin zafin rai tana zage zage tana tsine masu amman babu wanda ya kulata har sai data gaji dan kanta tayi shiru ta fara bin d'akin da take ciki da kallo kusuruwa kusuruwa banda duhu da zarni ba abinda ke tashi ciki ,ga kukan tsoro tun yanzu data kasance ranar allah ce ina ga dare yayi ? tsayuwa tayi taki zama dan bata ga wajen zama ba koina ta kalla kazanta né shiru tayi kawai tana tunanin mafuta ."




Cikin wani irin tashin hankali maryam ta shiga part din hajiya zulai tana kuka a parlour'n ta iske nana hauwa'u da mami zaune suna ganinta gabadayansu suka mike cikin tsananin damuwa suka isa inda take mrym ta zube jikin mami tana yi mata bayani abinda ya faru gaban mami yayi wata irin faduwa "yanzu d'an rashin imani hindu tayi qoqarin kasheki ? ta qarasa mgnr tana mai sake kamo maryam din zuwa jikinta ta rungume tana cewa " yanzu ina hindu take ? police sun wuce daita ."




Mami ta dafe kanta cikin yanayi na tsarkakkiya da shiga tashin hankali ,cikin tsananin' bacin rai mami ta zaunar da maryam ta soma magana "aikuwa wannna karon bazan yarda ba ,bazan zuba ido su kashe min ke ba ,"wannan ma ai rashin sanin darajan d'an adam ne ,wallahi da nasan police station din aka kaita da sai naje naci ubanta inji cewar nana hauwa'u " zagi kam babu wanda hindu bata sha shi a wajen nana hauwa'u ba, ita kuwa mami har da kwallar takaici ta zubar tana mai jin tausayin maryam wacce har lokacin kuka take ."


Suna cikin wannan halin na tashin hankali ATA ya turo kafar parlour'n ya shigo tare da sallama duk da bai bude muryarshi sosai ba fuskarshi kamar koda yaushe, cike da ladabi ya gaishe da mami yana mai zama akan kujera idanunshi a runtse ta amsa tana masa bayanin abinda ya faru "yanzu da wani abu ya faru da maryama shikenan taci bulus "


"Ina fa taci bulus ".
ya fad'a haka acikin ransa amman a filli yace "ai ni data samu nasarar kasheta ma da ta taimakawa rayuwata "ya fad'a yana ciza gefen lip's dinsa da d'an karfi yanayin yadda yayi maganar ya bala'i daurewa hajiya zulai kai ,tayi matukar mamakin jin abinda ya fad'a, ba ita ba hatta nana hauwa'u tayi mamakinsa kuma taji babu dadi aranta "yanzu abinda zaka fada kenan adamcy ? yayi shiru kawai yana lumshe idanuwanshi "rayuwar mutun kake fadar haka kamar rayuwarta baa bakin komai yake ba "?me zan fada sweetheart da wuce haka nifa kasancewarta a raye babbar matsala ce arayuwata ."


"Ka kuwa san abinda kake fada adamcy "?
"iyakar gskiyata kenan na fada sweetheart kuma kin san bana fadar abinda bashi né acikin zuciyata ba ,wannan kawai ya isa ki fahimci irin rashin son da bana mata ,wallahi da zata mutu da gaske da zanfi kowa jin dadi " ni kake fadawa haka adamcy ?a gabana kake wulakata min 'ya dan baka da mutunci na rantse da girman allah sai na sa'ba maka akan wannan maganar kuma matsawar baka d'auki mataki akan abinda akayiwa maryama ba sai ka had'u da fushina da baka gani ba ."


maryam ta sunkuyar da kanta kasa tana sheshekar kuka zuciyarta na wani irin bugawa da karfin gaske wani irin tsoro ne ke ziyartar zuciyarta bata ta'ba sanin qiyayyar da yake mata ta kai haka ba sai yau din nan cike da fushi mami ta cigaba da magana "idan banda rashin mutunci irin naka agabana adamcy ,nice fa da kaina na zaba maka maryam yau ko aljanna ce maryam nace ka aura ai baka mata fatan mutuwa ba bare diyar mutun diyar ma tawa ko ka manta matsayin maryam ne a wajena "?


Yana jin mami yayyi shiru dan duk abinda ta fad'a din ya sani "wallahi ban ta'ba sanin rashin mutuncinka ya kai haka ba sai yau ,mutun sukuntu guda kuma jininka da ubanta da ni uwarmu d'aya ubanmu d'aya fa, amman dan rashin mutunci kayi mata wannan fatar ,wallahi yadda zakayi farinciki da mutuwar maryama nima nasan zakayi farinciki idan na fadi na mutu "ya bude baki zai yi magana tayi saurin katseshi ta hanyar cewa "wallahi idan ka sake min wata maganar banza a nan zan iya kafa maka hakora "bai ce uffan ba ya mike tsam ya haye samansa, jiki a matukar sanyaye mami ta mike tana goge kwallar idanunta ta nufi hanyar d'akinta."




tashin mami ya bawa maryam damar rushewa da wani kuka "banason na kawo damuwa acikin familes ,sister ya zaa yi a fasa auren nan kowa ya huta ? nana hauwa'u ta rungumeta tsam ajikinta tana rarrashinta"sister ki duba yadda yake nuna tsanata qarara wannan wani irin kiyayya ne haka me na kashe masa ?"."yasan adadin mutane dake bukatar aurena aka daukeni aka bashi ba dan ya cancata ba ?" wallahi gara na mutu tun kafin zuwan auren nan dan nima zanfi bukatar mutuwa ina jin kamar na kashe kaina da kaina kowa ya huta har ma dashi mai tsanartawa dasu masu bukatar ganin rayuwata ta tagayyara dan nasan aurena da
yaya Adam babu abinda zan tsinta acikinsa sai bakinciki ?ta qarasa mgnr tana sheshekar kuka ."


"maryam !
nana hauwa'u ta kira sunanta "me yasa kike fadar haka ai bashi zaki duba ba "sister wa zan duba ?zan rayu tare dashi ?karki manta tare zamuyi rayuwa dashi kuma acikin gida

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login