Showing 63001 words to 66000 words out of 185716 words
Chapter 22 - MAR'ADAM'S book Complete BY AYSHA A BAGUDO.txt
yadda ta sheida masa kallon da takewa mahaifinta só take yace a fasa auren da mrym gbdy ya aureta shi kuwa baba qarami a hakan ma maganar tayi masa dadi "fatana mu hadu muyi addua akan lamari sannan mu nemi zabin allah allah kuma yasa gogan naka ya yarda ya amince ya hadasu su biyu din , ku bani lokaci kadan zan yi magana dashi duk abinda mukayi dashi zan nemeka da wannan maganar suka kawo karshen zance sukayi mata sallama ."
Suna shiga dakin baba qarami hindu ta fara zubar da hawaye acikin slow voice tace " baba ina ji ajikina ya adam bazai aureni ba dan dai idan amincewarsa zaa tsaya nema wallahi bazai ta'ba amincewa ba bugu da qari ni banason sharing dinsa da kowa nafi son ni kadai dan sam ban dace da zama da wata aba kishiya ba zan só mu rayu dagani sai shi ta karashe mgnr tana shesheka murmushi baba qarami yayi tare da fadin "hindu kalleni nan " ta tsura masa idanunta Kmr yadda ya bukata "ki kwantar da hankali babu wani abu acikin ya haduku biyu din amincewarsa shine abinda muka fi bukata a yanzu dan zaki iya kawar daita byn auren ki zauna ke kadai keda kike da baiwa iri iri nasan zaki bawa babanki mamaki haka dai baba qarami ya tasa hindu a gaba yana kwantar mata da hankali babu laifi hindu ta saki jikinta tare da karfafa zuciyarta sai dai ta rantse muddin bata samesa babu wata mace da zata mallakesa tana raye ."
****
Sanye ATA yake cikin farin yadin vol mai shegen haske da tsada a hankali yake taku yana gyara zaman hullarsa baki haka zali takalmin dake sanye da kafafunsa black cover shoes ne tsintsiyar hannunsa daure da agogon rolex yana dumfaro falon kamshi turarensa ya mamaye koina Kmr shagon turare yana gama qarasowa yace wa hisham "muje ko ".kai me yasa bakasan ka bawa mutun rai ka bashi hakuri ba duk lokacin dana bata ina zaman jiranka da muje ko zai qare " ina laifin kace hisham Afuwa kayi hakuri muje abokina km danuwana."
Dogon tsaki yaja kawai batare dayace uffan ba .
"matsalata da kai kenan ka gama bata lokaci amman zaka wani jawa mutane tsaki still bai ce komai ba
ya nufi hanyar dakin mami tana zaune ya shigo ta dago a natse tana duban kofar ganin shine cikin shigar da tafi qauna ta saki fuska cikin tsananin farinciki tace "Masha allah adamcy nah kayi kyau sosai allah yayi maka albarka ,sai dai wannan uban wanka da kashi haka kmr yau daurin aurenka, ai ko yau né daurin aurenka sai iyakarka hk kai ni kamar ma har da hoda ka shafa ko? Tsuke bakinsa yayi dan tsokanar sweetheart dinsa na yau yazo da wani salo ana zaman lfy me zai yi da wani hoda shi ba mace ba ."
"sweetheart ni zan fita amman zan dan jima ban dawo ba dan yau zaa bude kamfanin tace mai petir da sinadarin gas "Alhamdulillah masha ,allah allah yasa albarka arayuwarka data kasuwancinka allah ya tsare min kai ,yadda zaka fita lafiya allah ya dawo da kai lafiya sharrin mutun da aljani Allah rabaka dashi yace "Ameen !atakaice ya juya a natse yana taku tmkr wani jinin saurata "sai na dawo sweetheart ." a dawo lafiya adamcy nah ta fad'a tana cigaba da kallon bayansa "yau tsawon kwana uku kenan tana son sheida masa bukatar baba qarami amman ta kasa, ita kanta tana jin tsoron tunkararsa , tayi dukkanin tunaninta ta rasa ta ina zata fara shigo masa da maganar , auren mrym ma da yaya ya amince yanzu kuma ta sake kawo masa mgnr wata tasan tattara wa kawai zai yi ya gudu ya barta dasu ."
har ya kai bakin kofa yana shirin d'aura hannunsa akan handling din kofar ya tsaya cak ya waigo
bayansa adaidai lokacin da mami ta sauke numfashi da girasa ya tambayeta ,ta girgiza masa kai kawai tamkr wata marainiya "ko akwai damuwa ne ?ta sake numfasa wa kana tace " babu komai adamcy nah ina dai kallonka ne kayi min kyau sosai shigar ta amshi jikinka "me yasa bazanyi amfani da wannan damar na fad'a masa bukatar kanin mahaifinsa ba ? tayi mgnr acikin ranta da sauri zuciyarta ta gargadeta "karki soma yace ya fasa auren gbdy gashi goben nan zaa je neman masa auren mrym numfashi ya fesar "saboda Ke nayi shigar dan nasan zaki ji dadi gaahi yau juma'at "ai kuwa naji dadi kwarai da gaske na kuma gode sosai allah ya baka zuria masu albarka yadda kake ji dani kake min biyayya Allah baka masu yi maka bai amsa ba ya sa kai ya fice daga dakin zama ta cigaba da yi tana tunanin mafuta zata jajurce da tsayuwar dare domin neman zabin allah dan shine kawai mafuta agareta."
Aunty abinda na gama jin bayanin ibrahim taji kafafunta suna barazanar kasa daukarta lokaci daya zuciyarta na barazanar tarwatsewa Ibraheem ya matso yana girgiza Aunty abinda wacce ta dawo tmkr mutun mutumi "abida abida!! lafiyarki what's wrong abida?abida tayi shiru kawai tana sauke numfashi batare data amsa ba " baba babba zasuje nemawa ATA auren maryam gobe goben nan idan dai ba karya kunnuwanta suka jiye mata ba haka taji ya fito daga bakinsa " ibrahim me naji kace ? tana bukatar ya sake maimaitawa babu bata lokaci ya sake maimaita mata " wai tukunna wace maryam zai aura ?"maryam dai wacce Ke zaune a gidan mami diyar kaninta ita zai aura "da gaske ka tabbatar mrym zai aura ? ya gyda mata kai kawai yana maida hankalin Kan wayarsa dake qara "
"ina sam sam wannan aure bazai taba yuwa ba ta runtse idanunta da karfi ATA jarumin nmj né uwa uba kyau da natsuwa da Kamala ga tarin dukiya dasanin yakamata ai babu macen data dace dashi sai sultana gani yana mata wani irin kallo tayi saurin dawowa haiyacinta sunanta ya sake kira tare da jawo hannunta ya zaunar daita akan kujerar daya tashi cike da rauni tare da yin kasa da murya yace "abida meke damunki ?babu abinda ke damuna nidai dan Allah kar aje neman auren nan wai ma waye ya hada wannan auren ?shi ATA din da kasan ne ya zabi auren mrym din ?"ta karasa maganar cikin tsananin tashin hankali da bacin rai akan fuskarta ."
"me yasa ?saboda me kar aje neman auren ?"
Meye damuwarki da aurensu ? kanta ta rike da duka hannuwanta ta fuskancesa cikin sanyin murya tace "sbd sultana né bazan só ATA ya auri wata ya bar sultana ba "ita sultana tana son shi ne ?eh ammm daman umma ce ke ...."sai km tayi shiru ta kasa qarasa mgnr. "auren nan fa kamar anyi shi an gama domin babu wani abu ko mahalukin daya isa ya hana wannan auren mami da kanta ta hadata wannan auren ,ATA nason yarinyar ko baya sonta wannan shine bansani ba amman zuwa neman aure wannan dole ne gara ma ki binne duk abinda ke ranki karki shigo da wata magana da zata janyo matsala cikin jin haushi tace "idan kuma rabon sultana né fa ?har ya bude baki zai bata amsar tmbyrta wayarsa ta sake daukar qara ya dauka yana duba screen din wayar sunan ATA yaga yana yawo cikin sauri ya mike ya dauka ya soma mgn yana juyawa zuwa kofar fita tana ganin fitarsa ta mike tsaye ta soma zagaye falon tana maimaita abinda ya fada mata ashe kuwa zaayi wulakanci acikin gidan nan ko ta wani hali koda tsiya koda tsiya tsiya sai tayi duk abinda zatayi sultana ta shiga gidansa koda ata biyu ce ."
*****
"Maryama kyakkyawar budurwa ce mai kyan gaske doguwa ce sambal dan tsawonta bai sa ta rankwafa ba sai dai ita din ba fara bace haka zalika baza'a kirata da baka kirin ba chocolate colour ce tsayinta ya fito sosai domin irin matan nan ne masu shape din cocakola tana da siririn hanci da manya idanuwa masu matukar d'aukar hankali dan duk wanda tsautsayi yasa ya kalli cikin kwayar idanunta sai ya kusan suma saboda wasu sirrika da Allah ya hallita acikinsu masu kallon cikinsu ne kawai zasu iya karar da yanayin da suke tsintar kansu ."
idan tayi murmushi kuwa zaka ga siraran wushiriyarta sama da kasa sun bayyana wanda sune suke qara haskaka kyawunta ,ga gaban goshinta kwance suke da suma luf luf !! duk da kanta a daure yake a koda yaushe da d'ankwali amman kallo daya zaka mata ka gano irin matan nan ne masu yalwan gashi sannan tana da kafa mai kyau haka ma yatsun kafafunta zara zara ne lullube da farata masu matukar haske haka zalika muryarta idan tana magana dan dole ka tsaya ka saurareta kuma dole ka kalleta ."
Maryama ta samu tarbiya mai kyau daga gurin mahaifiyarta tayi karatunta na primary har zuwa matakin jami'an acikin jahar lagos kuma duk akarkashin kulawar gwanaty , haka bangaren karatun alqurni baa barta abaya ba domin tun tana primary ta sauke alqurni km hakan bai sa ta daina zuwa islamiyya ba idan kaga bataje ba sai dai wani aiki ne ya sha kanta ."
kyawun maryama mai tsayawa ne arai sai dai duk da wannan kyawu nata bata da wani tsayayyen saurayi duk wanda yazo neman aurenta dayazo sau d'aya zuwa sau biyu zai daina zuwa batare da wani dalili ba koma karshe taga ya koma gurin kaulat diyar kanwar babanta Aunty hassana gata da kyau sosai na bugawa a jarida amman mutane na mata kallon mai bakin jini abun yana d'an damunta sai dai bata nunawa dan ba samari bane a gabanta karatunta ya fiyye mata komai mahimanci koda yaushe ka kalli fuskar maryama zaka ganta a daure sakamakon rashin farinciki shiyasa mutane suke mata kallon mai tsananin girman kai ."
Sannu ahankali maryama take tafiya tamkar tana jin tausayin qasa ko macijiya dan babu wani karfi a tattare daita cikin shiga ta Kamala riga da sket dinki zamani da kuma dogon hijab mai hannu har qasa fuskarta manne yake da bakin nikaf kalar hijab din jikinta wanda ya zame mata jiki a duk sanda zaka ganta a waje ko a makaranta da wannan nikaf din zaka ganta sam bata yarda ta fita koina batare dashi ba a cikin gidansu ne kawai zaka iya ganinta sadaka yayinda kafad'arta Ke makale da jaka baka mai dogon igiya ,a zahiri kana kallonta kasan a matukar gajiye take dan yanayin tafiyarta ma ya qara yin slow sa'banin na sauran lokuta sakamakon ranar data kwaso gefe da gefenta qawayenta ne subai'a da sumaiya ne suka sakata a tsakiyarsu ."
Tafiya suke a natse suna hirar yadda jarabawar su ta qarshe ta kasance adaidai jeaction din ummahani street suka rabu da kawarta sumaiya tayi hanyar hagu da zai kaita unguwar daji suka cigaba da takawa da subai'a itama dai tafiya kadan sukai tayi dama wato markaz ya saura ita kadai ta cigaba takawa zuwa unguwarsu market street batayi wani doguwar tafiya ba ta qaraso unguwarsu bata tsaya akoina ba sai kofar qaramin get din gidansu wanda kallo daya zaka masa kasan na masu rufin asiri ne dan bazaa kira gidan da gidan mai kudi ba haka zalika bazaa kiran gidan da gidan talaka fútik ba daidai misali gidansu ginin da ne kuma ginin kasa ne filasta ne ya rufawa ginin gidansu asiri da kuma jamar dake rayuwa acikin gidan ."
a natse ta shigo haraban gidan nasu idanunta ya sauka akan kaulat wacce ta sha kwaliya cikin atamfar chiganvy gold black touch of milk ,kallo daya tayi masu ita da wanda ta gani tsaye ta dauke idanuwanta zuwa wani bangaren tana cigaba da tafiya dan wanda suke tsaye da kaulat din ba bako bane a wajenta tasha ganinsu tare ."duk da bilal baya ganin faukarta amman duk sanda ya ganta yana rasa natsuwarsa a kullum burinsa yaga fuskarta yaga yaya take ,kasa cigaba da motsi yayi daga inda yake tsaye yabi tafiyar maryama da wani irin kallo komai nata a natse most especially tafiyarta abun burgewa shi kam ina ma zata yarda ko sau d'aya ta bude nikaf din yaga fuskarta yasan zatai kyau duk da bai ta'ba ganin fuskarta ba."
Kaulat na ganin irin kallon da yake mata taja dogon tsaki yayinda maryama bata sake duban inda suke tsaye ba ta cigaba da tafiya zuciyarta na matukar jin tausayi kaulat dan babu abinda tasa gaba sai aikin tara masu samari marasa inganci a gida maimakon tai concentrate akan karatunta da kullum yake yin baya sai ta maida hankalinta ga tara samari marasa amfani , tare suka shiga jss one ,sukai jss1 tare, sukai jss 2 tare sukai exam na zuwa jss3 ta barta suka wuce ss 1 ita da sakina itama sakina lokacin da zasu shiga ss2 tayi fail ta wuceta sai dataje ss3 sannan kaulat taje ss1 sakina taje ss2 gashi ita yanzu daga rubuta jarabawar karshe ta fito amman ita kuma har kullm cikin repeating take a qalla a tunaninta tayi repeating ya kai sau hudu allah yayi mata jarabawa ta rashin ilimin dan babu abinda tasani daga bokon har islamiyyar zero ce amman ita da mahaifiyarta kullum cikin cin zarafin mutane suke barin ma ita da tarasa dalilin dayasa suka tsaneta suka tsani ganin wani tare daita duk wanda zasu gani tare daita wala mace wala nmj sai sunyi qoqarin rabasu "
"Wai bilal meye haka ne ? ka wani karkace kai kana kallon maryama gbdy ma ka manta ina tare da kai idan kasan ba wajena kazo ba na qara gaba dan na fahimci duk sanda kaga wucewarta sai ka maida attention dinka wajenta ko zuciyarka na kanta ne sai kayi min bayani nasani ba wai ka raba hankalinka gida biyu ba alhalin ina tare da kai "?
"wallahi da tun asali ita na fara gani to da babu abinda zai kawoni wajenki yayi mgnr acikin zuciyarsa amman a zahiri cewa yayi "meye laifi dan kalli halitta mai natsuwa ? ta zaro idanuwata waje tana masa wani irin kallo kafin daga baya cikin d'aga murya cike da maseefa tace "ko zaka koma wajenta ne ko me kake nufi da wannan maganar ?da zan samu haka wallahi da naji dadi sosai "ya sake fad'a acikin ransa "ai daman haka halinku maza yake da zara kunga mata sai kama 'bare 'bare to du ka gama 'bare 'barenka ka hakura dan ita wannnan dai ko ka koma wajenta ma dole ka gudu da kafarka dan idan kasan akanta matsalar duniya ta qare, kana fara soyayya daita komai daka mallaka zai qare idan kayi sa'a ma wani mummunar bala'i bai sameka ba tayi samari day day sun kai guda hud'u kuma duk da aure suke sonta amman da zarar sun fara zuwa zance wani mummunar bala'i Ke samunsu ganin ta inda take shiga ba nan take fita ba yasa ya matsota sosai ya rage murya ya soma magana ."
"Haba kaulat banda sharri fa dan kawai mutun yace yana sonta sai wani mummunar bala'i ya samesa sai kace wata annoba ,wannan ai tafi annoba "to ko zaki hadani daita kawai ina son naga tasirin bala'in dake tattare daita ?tayi shiru kawai tana nazarin maganarsa idan zata kintata daidai son maryama yake cikin karayar da murya kaulat tace "me kake nufi da wannan mgnr ?ya tsura mata idanunshi kawai "kaga bilal banason wannan maganar karka qara min hk da kuka ta qarasa maganar dan duk cikin samarinta tafi qaunar bilal "ya salam !meye kuma abun kuka anan daga wasa ?kuka kaulat take sosai ganin haka hankalinsa ya tashi sosai "kinga wallahi ni wasa nake ya