Showing 132001 words to 135000 words out of 185716 words

Chapter 45 - MAR'ADAM'S book Complete BY AYSHA A BAGUDO.txt

23 Nov 2024

4725

hade rai sosai kana kallonsa kasan yana cikin damuwa mai tsanani maganganun sweetheart dinsa yake tunowa a wayar da sukai daita a wannin data gabata. inda take sake jadda masa alqawarin da yayi mata kafin ya bar qasar , koda yayi qoqarin sake lallabata cewa tayi "kada kace min komai bana son jin wani kalaman yaudararka gareni ,kasani a wata biyu din da kace zakayi yau sauran sati daya ka dawo ."amman idan bazaka dawo ba ,ka cigaba da zama adamcy kayi son ranka kayi abinda kaga dama kayi abinda kaga yafi maka arayuwa ,amman kuma idan ka san zaka dawo ka dawo kamar yadda mukayi alkwari da kai ,karka dawo da wani abu a zuciyarka ka bar duk wani mugun nufinka a inda kake ,karka dawo gareni da mugun nufi ka barni na cigaba da rayuwa babu kai domin dawowarka da wani sabon salon yaudara ko mugun nufi zai sa nayi maka abinda har ka mutu bazaka daina mamakina ba abun bazai mana kyua ba adamcy ta fad'a tana kashe wayarta."




zuciyarsa ta sake cika da tashin hankali "ina zai ma
iya karya alqawarin da yayi sweetheart dinsa ?
ya shiru kawai yana ciza gefen lips dinsa ,ina bazai iya ba bazai iya karyar mata da zuciya ba ita din jigon rayuwarsa ce zai iya yin komai domin yaga ya faranta mata kamar yadda yasan zata iya sadaukar masa da faricinta haka shima a yanzu ma da yaji muryarta tausayinta ya cika zuciyarsa "


ahankali ya daga tsumammun idanunshi ya sauke su akan agogon dake daure a hannunsa 11:44 am tsaki yaja "what a heck sannan ya gyara zamansa "kada kace min komai bana son jin wani kalaman yaudarar ka gareni ,kasani a wata biyu din da kace zakayi yau sauran sati daya ka dawo ."amman idan bazaka dawo ba ,ka cigaba da zama adamcy kayi son ranka kayi abinda kaga dama kayi abinda kaga yafi maka arayuwa ,amman kuma idan ka san zaka dawo ka dawo kamar yadda mukayi alkwari da kai ,karka dawo da wani abu a zuciyarka ka bar duk wani mugun nufinka a inda kake ,karka dawo gareni da mugun nufi ka barni na cigaba da rayuwa babu kai domin dawowarka da wani sabon salon yaudara ko mugun nufi zai sa nayi maka abinda har ka mutu bazaka daina mamakina ba abun bazai mana kyua ba adamcy ."


"shine kawai abinda yake ta yawo acikin kwa kwaluwarsa "why sweetheart ?me yasa kika kasa fahimtata instead ki barni tunda na nuna bana son auren nan ya allah ka kawo dalilin da zai sa a fasa auren nan na huta tsaki yayi inda fuskar princess keta masa yawo a cikin idanunsa da sauri ya runtse idanunshi dan a halin yanzu baya son ko tunawa daita ahankali akayi knocking din kofar parlour'n yana daga kwance yayi nisa cikin tunani shiru bashiri yana jiran a bashi izinin shiga amman shiru daya daga cikin masu tsaronsa ya dan leko dakin yana ringine amman bai bawa mai yin knocking din izinin shiga ba ."


Dan haka ya dawo ya bawa bashir izinin ya shiga dan ya rigada yasan ko waye bashir din a wajensa kuma tun safe ya sheida masu zuwansa,bash ya shigo parlour'n bakinsa dauke da sallama shiru mr ata bai amsa ba ."bashir ya zauna yana fuskantarshi sai dai kusan mintuna goma mr ata bai bude kwayar idanunshi akan bashir ba haka zalika bai ma san da shigowarsa ba ya yunkura ya tashi ya isa inda mr ata yake ya dafa shi a matukar zuciye ya bude idanunshi da niyyar saukewa wanda ya dafa shi maseefa ganin amininsa yasa ya sauke naunayen ajiyar zuciya "kai mutumina meke damunka ne haka duk kayi wani irin ina lura da kai tunda ka sauka a qasar nan kake yawon tunani ?bashir ya fad'a tare da zama a gefensa kallonsa yayi zuciyarsa na zafi "yaushe ka shigo kuma me yasa ka shigo baka nemi izinina ba ?"


Ajiyar zuciya bashir ya sauke sannan yace "kai dai anyi dan iska ina tmbyarka kana tmbyta yanzu dai fara bani amsar tmbyata tukun sai na baka taka numfashi ya sauke mai zafi ,kai dai bari kawai ina cikin rudani auren dole zaa min , bashir ya zaro idanuwa "Ata din dana sani zaawa auren dole ? no no it can be possible ya qarasa mgnr yana dan murmushi,kai ma dai ka fadi haka wai kamata zaayiwa auren dole kamar muna in does day nan ya kwashe komai ya fad'a ma bashir har da alqawarin da yayi wa mami , wallahi bana son yarinyar nan kiyayyarta bazata misaltu a zuciyata ba gbdy zuciyata bata bugawa idan na ganta, kaga mutuwa kusa kenan dariya sosai bashir yayi tuni mr ata ya kule kallonsa yayi rai a bace ,kaji min dan iska ina fad'a maka damuwa kana mun dariya to wallahi maza tashi ka bar nan yanzu ."


"Sorry my friend hukunci mami ne ya bani dry kai da yanzu bata zatar da wannan hukunci akanka ba haka zaka qare rayuwarka kana yaudarar kanka shin zaka tuna kafin mu rabu da kai last na fad'a maka wannan yarinyar mafarkinka ba mutun bace sannan ka guji ranar da mahaifiyarka zata gaji tayi maka irin wannan auren kace bazatayi ba ?kaso wannan yarinyar marym karkazo hannu kazo kana sonta ta samu dama akanka."


" dan Allah bash ka bar wannan maganar ka bar kawo min maganar zan sota ya zaayi na sota ma ?"mr ata ya fad'a cikin tsananin damuwa zan cigaba da rayuwata haka zan bar zuciyata babu kowa cikinta yadda zan cire soyayyar princess a zuciyata bazan bawa kowace mace damar shiga ba sai dai na qare rayuwata haka ,haka dai suka cigaba da tautaunawa bashir na bashi kwarin gwiwar yayiwa mahaifiyarsu biyayya ."




Ana sauran kwana hud'u mr ata ya dawo ya kira mami ya sheida mata ai kuwa taji dadi har ta kasa boye murnar ta , ta tattara kan masu aikinta domin su gyara gida da kuma sauya wasu abubuwa dake gidan sakamakon dawowar dan lelenta jirgin karfe hudu daidai na yammaci ranar lahadi zai sauke su tare da babban yaronsa da masu tsaronsa da sukayi tafiyar tare dan haka mami ta hana kowa sakat acikin gidan daga masu aiki har maryama babu wanda ya zauna suna tsaye bisa kafafunsu duk da tun jiya sun yi redy wasu abubuwa da suka san yafi bukata maryam tana wanke hannunta tana qoqarin fitowa daga kitchen sai ga mami abakin kofar kitchen din suka hadu mami ta kalleta da murmushi kwance a fuskarta ."




"tun daga parlour nah na biyu nake ji kamshin girki fatan kice kikayi komai da kanki ?Allah mami ki tambayi tabawa duk ni nayi su kawai wanke wanke sukeyi gsky idan duk wannan kamshi daga hannunki ne naji dadi Kwarai da gaske dan tun banga abincin ba miyona ya tsinke muje kawai na fara da jin dandanon girkin kafin adamcy ya qaraso ,ai mami idan kikaci sai kunnenki yayi rawa ,haka né hajiya duk ita tayi gsky babu abinda muka tayata sai wanke kwanuka ,hakika tayi qaqari sosai ."


"ai kam yau zan bada maki mai yawa dan tun daga parlour'na nake jiyo kamshi muje suka koma cikin kitchen din tare mami na bude manya kuloli kula farko alkubus da miyar naman rago kula ta biyu shimkafa bastimatic ce da teaw wanda yaji naman kaza sai kula ta uku wanda sakwara ce da miyar egusi wanda yaji ganye ugu da nama da busashen kifi "masha allah mami ta furta a fili "lallai adamcy nah zai ci dadi ,yau kam nasan har da santi zai yi murmushi mrym tayi tana cewa" allah yasa mami allah yasa ya yaba da girkin tayi maganar cikin sanyin murya ,karkiji komai diyata zai yaba ta fada tare da daukar qaramin spoon ta dibi miyar farko ta kai bakinta ".




"Woww miyar nan tayi dadi sosai daya bayan daya ta dinga d'an dana miyar tana lumshe idanunta tana santi da yabawa maryam din ,da gaske mami tayi dadi?sosai tayi kawai abu daya ne zan gyara miki shima idan mutun ya kasance mai son cin maggie dayawa a abinci ne bazai ta'ba miki gyara ba "meye shi mami ?ta tmbyeta cikin tsanani damuwa jikinta har rawa yake ,ki natsu ki kwantar da hankalinki ba wani abu bane maggie zaki rage zubawa miya dayawa ,tun daga tafashe kinsa maggie kuma kinga zakiyi amfani da ruwan miya wajen hada miya dan haka baki bukatar zuba maggie dayawa acikin miyarki yanzu kenan maggie yayi yawa ta fada cikin tashin hankali?bawani yawa bane kawai na gyara miki ne dan gaba idan hannunki yana zarcewa a maggie matsala ne."




" wannan ne kawai maggie yayi yawa ko duka miyar né ?Ki kwantar da hankalinki kusan duka ne amman karki damu aa mami dole na damu dan wallahi idan yasan ni nayi na shiga uku gara kawai na sake wani ."What ? "mami ta furta tana dubanta babu abinda zaki sake anan haka zai ci har yayi santi
ta sauke numfashi tana cewa "amman mami karki ce ni nayi kice kece kikayi dan allah idan yasan ni nayi wallahi karshenta bazai ci ba ,mami ta kalli agogon dake hannunta kinga karki damu muje ki shirya dan jirgin adamcy ya kusan sauka nima bari nayi sauri na shirya kafin a dauko shi yazo yana yiwa mutane naci dan tun jiya yace bazai ci komai ba sai ya dawo ."




Mami ta bawa masu aikinta dake tsaye umarnin su fito da kulolin zuwa dinning suna shirya dinning suna hira suka jiyo sallamar hindu gabdaya suka amsa mata kallo daya mami tayi mata ta dauke kanta tana sanye cikin wani irin ado tasha tamkar wacce zata turakar miji cikin ratsatsen lace maron colour touch of green dinki yaji stone ta koina dan hasken fatarta ya sake haskawa sam bataji dadin ganinta ba bata qaunar abinda zai kawowa adamcynta matsala arayuwarsa ta fada mata tayi hakuri dashi ta nuna a fuska duk wata hanya da zata nuna mata ta hakura dashi tayi amman sam kamar bata fahimta ."




"Mami fatan kin shirya muje tarbo ya adamcy ,dawa kenan zakuje?hindu tayi shiru tana dubanta ,ai wannan sai dai matarsa ni kam na yafe ,tô shikenan ni bari naje AirPort tarbosa "allah ya tsare sai kin dawo tace ameen mami ta fada haka né dan tasan halin kayanta bata són taje ya disgata cikin mutane amman hindu ba irin mutunen nan masu fahimta bane ."Mami tana kallonta ta juya tana rausaya cike da farinciki kamar wacce akayiwa albishiri da zata mallakinsa taso ta tsaidaita amman ta barta sai da hindu ta fice daga falon sannan mami ta dawo da kallonta ga maryam zan shiga dakina na shirya kema idan kin gama kije ki shirya mrym tace "tô!


Sai data tabbatar da komai yayi daidai sannan ta wuce dakinsu inda ta iske nana hauwa'u kwance tana karanta wani hausa novel acikin wayarta mai suna cutar da kai ,har yanzu kina kan karatun nan sister?ina kai ko akwai abinda zan miki né ?bazakiyi shirin tarban ya adam ba gashi har ya kusan sauka koma mace ya sauka ?ta qarasa mgnr tana duba makeken agogon dake manne da bangon dakin ,wannan kuma kece zan tmby dan ni tsakanina dashi sannu da zuwa né ke dai kije yi maryam bata sake cewa komai ta shige bayi


Wanka tayi ta fito ta goge jikinta ta zauna akan kujerar mirrow ta d'auko mai ta fara shafawa ahankali haka nan take jin faduwar gaba mai tsanani ,kinyi shiru bazaki shirya ba sai ya shigo mami tazo tana daga miki hankali ta tsaida hannunta akan damtsen hannunta tana kallon nana hauwa'u ta cikin mirrow sai data numfasa sannan ta mike wallahi sister haka nan nake jin mummunar faduwar gaba jikina har rawa yake gabadaya bana cikin natsuwata tunda mami tace zai dawo yau na tsinci kaina cikin damuwa bare gashi na kwabsa kadan a girki mami tace Maggie ya dan só yayi yawa tsorona kar ya tambayi wanda yayi tace nice ta qarasa magana tamkar zata zubar da hawaye ."


"gsky kina tare da aiki marsi wai shi yaya dodo ne da Kike jin tsoronsa haka ?numfashi ta fitar da karfi ta mike tana cewa "ban san me yasa wani lokacin kike manta kiyayyarsa gareni ba ,ki daina cewa kiyayya yaya baya kinki halinsa né km kowa yakewa amman kema zuwa yanzu ya kamata ki saba dan da nice dana maidashi man shafawana ,uhm baki san halin wannan yayan naki ba idan yana kin mutun halinsa dabam kiyayyarsa dabam ta fada tana taku har ta qarasa in da Kwabar kayanta yake ta ciro doguwar rigar lace mai shege kyau da tsada sabuwa ce bata taba sakawa ba sai a lokacin bata tsaya yin wata doguwar kwaliya ba ta zauna zaman jiran kiran mami ."


Tana zaune ta jiyo hayaniyar shigowar motoci haraban estate din ahankali cikin sanyin jiki ta mike ta isa jikin window dakin ta dage labule ahankali idanunta ya sauka akan motocinsa da motocin ss guda shida inda masu kula da lafiyarsa mutun uku suka fito da sauri mutun daya ya bude masa murfin mota ya fito ya tsaya bisa kafafunsa ."


A natse ya soma taku mutane suka sakashi a tsakiya wanda dayawan su yan tarbosa ne yayi matukar kyau sanye cikin riga da wondo na black suit mai tsaida da sheki yayinda sumar kansa Ke kwance luf yana zuba sheki alamun yana samun kulawa haka zalika farinsa ya qara fitowa alamun yana cikin koshin lafiya sai wani ipod dake manne da kunnensa na jin mgn gaba daya mutanen dake tare dashi ya zartasu a komai hasken fata da tsawo cike da Kamala tana tsaye suka gama wuce wa ta lumshe idanunta na second biyar sannan ta bude idanunta ahankali suka sauka akan hindu tsaye fuskarta murtuke cikin bacin rai aranta tace ko me ya bata mata rai ita da tayi kamkamba da shishigin zuwa tarbosa?."


"Uhm yanzu haka halin nasa yayi mata nan wani murmushi ya bayyana akan lip's dinta haka nan ta tsinci kanta da jin dadin yanayin dataga hindu ai kin iya shishigi kuma karshen masu irin halinki kenan ajiyar zuciya ta sauke tana sakin labule ta juyo idanunta cikin na nana hauwa'u,"kin gama kallonsa ."


"Shi wa ?"
"Ya adam !ta bata amsa atakaice,kai haba sister kai haba sister ko gsky Ke na gama karantarki fa kema kin fad'a sawun masu son ya adam kar muyi haka dake sister ."allah ba wasa nake ba kina son shi son ..."
nan da nan idanun maryam ya cika da hawaye nana hauwa'u ta zaro ido ke fa matsalata dake kenan saurin kuka kamar wata qaramar yarinya daga na fadi gsky ."


"Aa sister wannan ba gsky bace taya zaki fada min haka ?me yasa zan so mutumin da bai sona?
nana hauwa'u ta sauko daga saman gado ta dafa kafadanta zaku so juna wuyarta ayi aure muamular miji da mata ya sha bambam da rayuwar waje fatanmu allah yasa ya sauko da wuri ."


" sister bazai sauko ba kema Kinsan halinsa yana son mutun ma ya ya qare bare ni da yake jin Kmr ya kasheni ,ni ban san ya zanyi da rayuwata ba gashi kowa son shi yake kalli hindu fa har airport taje tarbosa " kinga matsalata dake kishin maseefa ."


"allah ba maganar kishi bane sister da me zan ji da rashin son da bai me ko kuma da yammatan dake sonshi "kyale wannan mahaukaciyar kema Kinsan bazai sota ba dan hk ki saki ranki kisawa ranki kece sauraniya a gidansa in sha allahu kece glashin idanunsa naunayen ajiyar zuciya mrym ta sauke sai lokacin taji natsuwa ajikinta tana damke hannun nana hauwa'u cikin nata "na gode da addua Sister Allah yasa hakan ya kasance ."


Gyada kai nana hauwa'u tayi ta zare hannunta ta nufi kofar fita "ni na tafi tarban babban yaya sai kin fito mami na tsaye a tsakiyar parlour'n fuskata dauke da murmushin farincikin dawowar tilon danta yana gama shigowa tsumammun idanunshi ya sauka akanta cikin shiga na alfarma fuskarsa kamar koda yaushe babu annuri amman duk da haka yayi farincikin ganin sweetheart dinsa cikin koshin lafiya atare suka soma daga kafafuwansu domin isowa ga juna suna gama qarasowa yana qoqarin durkusawa mami tayi saurin rike kafafunsa ta rungumeshi ajikinta tana shafa bayansa "sweetheart mun samuku lafiya ?lafiya lau adamcy nah da fatan ka dawo lafiya ? ajiyar zuciya kawai ya sauke ta zaresa ajikinta ta qarasa dashi kan kujera mai zaman mutun uku ta zauna a kusa dashi tana rike da hannunsa rayuwarta né adamcy tana matukar qaunarsa shiyasa yake mata abinda yaga dama ."




nana hauwa'u tai masa sannu da zuwa ya amsa da kyar yana zaune mutanen gidan suka dinga shigowa daya byn daya suna masa sannu da zuwa ita kam maryam bata fito ba tana daki ta kwanta rigingine jiran mami ta nemeta mami bata nemita ba har akayi sallah magrib da ishai sai data ga babu alamun mutanensa a falo dashi kansa ata ta fito ta zauna tare da nana hauwa'u da mami aka cigaba da hira daita "




Karfe tara daidai mr ata ya sauko cikin blak long sleve da farin wando na shan iska sai kamshi turarensa na Reed ke tashi akoina ajikinsa ya samu waje ya zauna a daya daga cikin kujerun falon yana duban mami dake zaune tana waya nana hauwa'u ta sake gaishesa ya amsa aciki, ganin haka yasa maryam ta bud'e bakinta da kyar cikin in ina "ya..ya sannu da zuwa da fatan ka dawo lafiya ?"banza yayi mata tamkr bai ji abinda ta fada ba nan kuwa yajita sarai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login