Showing 138001 words to 141000 words out of 185716 words

Chapter 47 - MAR'ADAM'S book Complete BY AYSHA A BAGUDO.txt

23 Nov 2024

4700

kwanta tana shafa qirjinsa zuwa kan nipples dinsa wani irin d'auke numfashi yayi da karfi dan alokacin da'ace akwai wani a d'akin dan dole ya fahimci yana cikin wani hali .wani irin juyi tayi har rigar dake sanye a jikinta ya zame wanda daman dashi da babu duk daya ganin abinda yafi so ajikinta wato dukiyar fulaninta ya tashi zaune acikin mafarkinsa ya rike hannunta gam cikin nashi yana murzawa "my princess ina kika shiga two day's baki zo min ba ? banje koina ba ina tare da kai ,tayi masa mgn tana kai harshenta qirjinsa ta fara lasa wani irin abubuwa yake ji suna yi masa yawo a gbdy ilahirin jikinsa ."




tsigar jikinsa gbdy suka mike yayinda jijiyarsa ta dinga harbawa da sauri sauri rungumota yayi sosai ya sakata a tsakiyar qirjinsa hancinsa ya cusa cikin suman kanta daya zubo har gadon bayanta ahankali ya dinga shakar kamshin jikinta tare da lumshe ido yana jin wani sanyayyen abu a zuciyarsa".




"kina sona ?ta gyada masa kai alamun "eh !,to ki taimaka ki bayyana min kanki tun kafin ayi min auren dole ,wani bayyana maka kaina zanyi byn gashi muna tare ?ni da kai muna tsananin son juna ko ka manta tsawon lokacin da muka kulla soyayya a tsakaninmu ?ya gyada mata kai ," alaka soyayyarmu mai karfi ce domin kai din nawa ne na har abada ,sake matsota yayi sosai ya kai hannunsa kan karan hancinta yayi kasa da hannunsa har zuwa kasan marata , yana jin lokacin data sauke numfashi zuciyarta na bugawa da karfi hakan yasa ta shige masa tun daga wuyanta ya fara shafata itama tana shafashi ,kamkameta yayi ajikinsa ya had'e bakinsu waje daya yana wa bakin wani irin tsotsa na fitar hankali ."




Bangaren marym itama kwance take tana faman juyi akan katifa dan ta kasa runtsawa tana saka da warwara kwalkwaluwarta na sake nitso cikin kogin tunani ta yadda zatai rayuwar aure da mutun irin mr ata ,mutumin da baza tace ga ranar data ga murmushinsa ba ,hasalima fuskarsa koda yaushe a had'e take tmkr hadari juyi kawai take tana tunanin abubuwa dayawa akan aurenta dashi bai sonta ,gashi tunda akace ita zai aura bata sake samun isashen bacci ba kullum da abubuwan da take facing ,sai ta dinga jin kamar ana farautarta, wani lokacin idan ta runtsa idanunta sai taga mutun akanta ana qoqarin caka mata wuka da zarar ta bud'e idanunta ta kunna wuta sai taga wayam babu ko alamun mutun dan wani lokacin tashi take tayi alwala ta gabatar da sallar nafila.




yayinda take nan kwance cikin tsananin tunani da fargaba shi kuma mr ata yana can duniyar mafarkinsa ."ajiyar zuciya ta sauke ta kalli nana hauwa'u dake sharar baccinta hankalinta kwance "allah sarki sister kin huta, kina rayuwarki hankali kwance baki da wata damuwa ,ya allah kasa auren yaya adam arayuwata alkhairi ne ta furta
hakan a fili ,ganin har kusan karfe biyu da wasu yan mintuna na dare bata runtsa ba ga gari ya dauki shiru sosai baka jin motsin komai ,taji kamar ta tashi taje tayi alwala ta roki Allah alkhairi daga cikin alkhairun dake cikin dare amman sai taji ta kasa tashi domin alokacin idanunta sun fara mata yaji alamun bacci ahankali bacci barawo ya d'auketa ."


cikin bacci mrym taji numfashinta baya sauka yadda ya kamata kamar an danneta ta kai hannunta tana qoqarin cire abinda taji ya danne mata fuska wanda take tunani pillow ne akayi amfani dashi amman sai taji an sake danneta da iyakacin karfi ta yadda ko sautin muryar ta bazaa iya ji ba nan fa ta fara mutsu mutsu da kafafunta tana kokarin kwatar kanta cikin ikon allah ta samu nasarar rike hannun mai shi nan fa suka fara kokuwa mrym na qaqarin ta amshi pillow amman ana sake danne fuskarta ita km sai qoqarin ceton ranta take ."




inda tayi wata irin zabura ta fixge pillow ta kwalla wata razananniyar qara wanda yasa gidan gbdy ya dauki sauti kuwar qararta ,nan da nan nana hauwa'u ta farka daga naunayen baccinta tana kiran sunan da take kiranta dashi " sister lafiya tare da qoqarin kunna wutan dakin ? mrym bata amsa mata ba sakamakon inuwar mutun data ga yana qoqarin ficewa daga dakin tayi wata irin sufa sai gata ta rike gefen rigar mai shi adaidai lokacin da nana hauwa'u ta samu nasarar kunna wutar d'akin adaidai lokacin mai shi tasa hannuwanta duka ta ingiza mrym da iyakacin karfinta tayi baya luuuuu sai dai ido cikin ido suke kallon kwayar idanun juna sanye take cikin bakaken kaya tun daga samanta har kasanta babu abinda zaka iya gani ajikinta sai kwayar idanunta ."




a kallon da mrym take ma yanayinta ya nuna mata mace ce hannunta daya rike da wuka duk da suna kallon lokacin da tayi fillinging da wukar a tsakiyar daki ta fice da sauri tana haki nana hauwa'u ta sauko a rude ta tare bayan mrym tana rungumeta ajikinta "sister ki bita karki bari ta fice wallahi kasheni take qoqarin yi duk suka rude sai zufa suke fitarwa mrym tace "wallahi kasheni zata yi ta sake fad'a tana qoqarin mikewa domin tabi bayanta ."




Mrym na qoqarin mikewa tsaye alokacin mami tare da masu aikin gidan suka shigo cikin dakin cikin tsananin tashin hankali a matukar firgice maryam ke matsu bayanin komai mami tace "Inna lillahi !a garin yaya ? ta yaya ma hakan ta faru ?wallahi mami da gaske yau kwanana ne kawai Ke gaba dana bakunci lahira daman kullum ina jin ana yunkurin kasheni ,wallahi mami nafi tsawon wata biyar ina jin ana farautar rayuwata cikin dare maryam ta fad'a cikin matsanancin tashin hankali "to akan wani dalili kenan ?"wallahi bani sani ba ta fad'a cikin muryar kuka har da shesheka nan da nan nana hauwa'u ta fashe da kuka ta kamkame mrym magana take son yi amman muryarta ta kasa fita tana kallon wukar dake yashe kasa ,sabuwa fil da alamun baa ta'ba amfani daita ba ."




"Mami kalli wukar datazo daita nasan wallahi kwana ne kawai agaba yasa ta fara amfani da pillow bancin haka tana daba min wukar nan cikin bacci sai dai na farka najini a lahira, mami ta qarasa inda wukar take ta tsura mata ido muryarta a sanyaye tace auta miko min wukar data yar , ta dauki wukar ta mika wa mami " wannan kamar irin wukar daa aka kashe mubina ko ?gbdy suka sake shiga rudani nana hauwa'u ta matso kusa da mami sosai tana cewa "tabbas mami irin tace nima kallon da nake ma wukar kenan dan lokacin rasuwar mubina nima na ga wukar " .


"inna lillahi wa inna ilaihi rajiun daman acikin estate din nan makashin mubina take ? domin babu tantama acikin estate din nan ne domin babu wanda zai tsallake masu tsaro sama da goma sha biyar banda securities ya shigo esatate din nan lallai acikin estate din nan ake qoqarin kashe mrym nana hauwa'u ta gyada mata kai alamun haka maganarta take .""auta taso min adamcy da mugun sauri ta fice daga dakin zuwa nashi bata tsaya neman izini ko sallama ba ta banka dakin baccinsa yana kwance rungume da pillow "yaya !yaya! cikin bacci yaji ana tabashi hade da kiran sunansa ya bude idanunshi cikin tashin hankali yana cewa "Lafiya ?wai kazo inji mami da sauri ya kalli qaramin agogon dake ajiye akan bedside dinsa karfe uku yanzu ta wuce saukowa yayi da sauri dan yasan koma meye ba lafiya ba da wannan tsohon dare tace a kirasa ."




Jallabiyarsa ya dauka ya zira ya fito rike da gefen Jallabiyar dan ya samu damar daga kafafunsa da kyau biyu biyu ya dinga taka step yana gama saukowa ya karya zai shiga parlour'nta na biyu nana hauwa'u tace "tana dakin mu kai tsaye ya wuce bai tsaya jin dalilin ba atare suka shiga dakin cikin tashin hankali mami take masa bayanin abinda ya faru ."




shiru kawai yayi yana duban mrym dake wani irin kuka bai yi mamaki jin abinda mami ta fad'a ba sannan babu wacce tazo cikin tunaninsa sai nuzla domin ta tura masa da sakon lallai idan bai amincewa aurenta ba zata ga byn mrym sai dai itama idan ta kasheta a kasheta lokacin daya ga sakon shi ko ajikinsa dan kuwa da allah yasa tayi nasara kasheta data taimaka wa rayuwarsa ita taje da Allah shi kuma ya huta da qaya."




kiran mutanen estate din mami tasa nana hauwa'u ta dinga yi suna nan tsaye a daren sai ga jama'ar gidan duk suka rude iyayen mubina sunfi kowa shiga tashin hankali yayinda mrym Ke kuka har lokacin mahaifiyar mubina kam ta yarda domin kuwa me wukar tazo yi dakin maryam kuma exactly irin wukar ce babu tantama ,mami ta qaraso ga mrym dake zubar da hawaye "me yasa zasu kashe min mrym ?ince duk esatate din nan yanuwan juna ne babu bare acikinmu ?
"me yasa zaa dauki ran wani ?dan girman allah ku taimaka ku fad'a min cewar duk wannan abun dake faruwa a mafarki ne domin bana tunanin haka daga cikin ahlin nan, bana tunanin wani zai iya aikata min haka kuce min wasa ne ba niyyar kashe min mrym akayi ba ?"mrym ta sake fashewa da sabon kuka tana rungume mami ajikinta gbdy ta tsure ta nemi natsuwarta ta rasa itama mami rungumeta tayi tana shafa bayanta ."




"Sweetheart kukan ya isa ki bar kuka ki kwantar da hankali kowaye acikin estate din nan zan fito dashi Ke kuma malama kin cikawa mutane kunne da hayani just keep queit I don't want to hear any sound please ya juya ya kalli wadan da suka hallara a dakin dan ba kowa ya shigo ba, dan wasu na can na bacci bama su san meke faruwa ba na kusa kusa ne suka samu damar shigowa yace "kowa ya tafi ya kwanta zai dauki mataki , ya dauki wukar ya fice .


daya byn daya suka dinga fita daga dakin cike da jima min , mrym da nana suka bi mami dakinta kowace ta haye gado sai dai ba da niyyar bacci ba dan mrym kam kuka take sosai babu abinda take gani sai mubina cikin jini shikenan da yanzu wani labarin ake ba wannan ba ,da yanzu tana cikin jini tana wannan imagenation din tana kuka nana hauwa'u kuwa zaman dirshan tayi da mami suna tautaunawa dan bacci kam ya kaurace masu ."




Washgari baba babba ya tara manya gidan tun daga kan kannensa har zuwa kan yayyansa na sama dasu dana kasa dasu dake esatate din acikin dakin na musamman da suke ganawa a duk sanda abu makamancin hk ya faru ,ya dade yana bayanin abinda ya faru a daren jiya tare da jan kunne da nasiha mai ratsa zuciya a karshe yace zaa yi bincike duk wanda aka samu da sa hannusa zaa mikasa hannun hukuma dan maganar da nake daku yanzu haka nayi report wajen police har na mika masu wukar domin a fara bincike duk hankulansu a tashe mrym kuwa har wanna lokacin kuka take aunty shahida da khadija kaf yayan mami tun safe suka yiwa gidan diran makiya jama'a kuwa sai zuwa jaje suke yi wa mami haka ma iyayen maryam sun kira yafi sau babu adadi wuni ranar haka mrym tayi shi cikin dakin mami cikin tsananin tashin hankali ."




Bayan kwana biyu da faruwar lamarin da misalin Karfe hud'u sauran wasu mintuna mr ata ya shigo estate dinsu drivenshi na tsayawa batare da bata lokaci ba masu kula da lafiyarsa ta hukumar dss suka fito da sauri kafin ma su bude masa ya bude ya fito yana gyara zaman rigar jikinsa kai tsaye masalacin dake cikin esatate din ya nufa domin gabatar da sallah bayan ya idar da sallah ya nufo gidansu nana hauwa'u da da maryama na zaune idar da sallar su kenan sai ga diyana ta shiga hira suke kadan kadan mrym na bawa diyana labarin abinda ya faru daita "amman Kinsan wani abu diyana duk yadda muke da nuzla bangata ba kuma nasan taji abinda ya faru dani har cikin daki aka biyoni zaa kasheni amman ta kasa zuwa tayi min jaje tunanina ni kuwa laifin me nayi mata? wallahi har da kwalla nayi na rashin zuwanta saboda banyi tunanin hk daga gareta ba ."


"gsky da mamaki kuma kinga ai ba haka take ba tana da kulawa da mutane most especially idan abu ya sameka na farinciki ko akasinsa amman Kiyi mata uzuri wata killa tana nan hanyar zuwa tunda duka yau kwana biyu ne da faruwar abun ,wannan gsky ne nuzla bata da haka amman baku lura a tsakankanin lokacin nan ta dan canza ba ?inji cewar nana hauwa'u"eh ta canza kam sosai ko Kinsan damuwarta ?ko daya ban sani ba wallahi na dai kula ta canza ko a yanayin jikinta zaki fahimci akwai abinda ke damunta mrym tace " to koma meye allah yafi mu sani Allah ya yayewa kowa damuwarsa Suna zaune mr ata ya shigo gbdy suka masa sannu da dawowa ya amsa Kmr yadda ya saba aciki sannan ya kalli auta yana tmbyr mami "ke auta ina sweetheart. ? "tana ciki ta shiga tayi sallah yana gama ji ya haye sama suka cigaba da hirarsu ."




Bai sauko ba sai bayan awa daya sanye da shirt ajikinsa da wondo ficewa yayi bai tsaya akoina ba sai gidansu nuzla ya tmbyi mahaifiyarta ta sheida masa tana dakinta bata jin dadi a natse ya nufi kofar dakinta ya tura kofar ya shiga tare da sallama akan lip's dinsa tana ganinsa ta mike zaune tana ware fararen idanunta akanshi tayi qoqarin ta sakashi cikin nashi idon sanda yake takowa zuwa inda take tana masa duban mamaki dan bata ta'ba expecting zata ganshi har cikin bedroom dinta ba ."


sosai ya dauki hankalinta yayi wani fresh yayi qara kyau kaman zane ta koina ya hadu matsalar dai shi din mugun miskili ne sai dai hakan ma qara masa kyau yake ahankali ya janye idanunshi acikin nata ya maida dakin yana qarewa koina kallo "Lafiya
yaya adam da wannan zuwan naka na bazata ?"


Shiru yayi yana cizan lips dinsa na kasa kafin daga bisani yace "bai kamata kiyi min wannan tmbyr ba domin kuwa Kinsan dalilin zuwana "ya fad'a alokacin daya jingina jikinsa da mirrow dinta yayi crossing leg's dinsa ya rungume hannuwansa duka a saman faffadan qirjinsa yayi da idanunshi ke kallon zara zaran yatsun kafafunsa."


da kyar ta mike daga zaunen da take tana cewa "ni ban san abinda ya kawoka ba idan dai ba kazo da niyyar karbar soyayyata bane amman kafin nan me zan kawo maka ?"yayi mata banza zuciyarsa na zafi jin yayi shiru km ta rigada tasan halinsa tayi tunanin ta kawo masa ko ruwa ne har tayi taku biyu taji ya fixgota da karfi yana watsa mata wani kallo da idanunshi dake cike taf da bacin rai gbdy taji ta fara muzanta daga kallon da yake mata taji gwiwarta tayi sanyi ."Idanushi ya tsareta dashi yana kallonta yayinda gabanta ya fara faduwa tana adduar allah yasa ba wani laifi tayi masa ba ."


Sai daya gama kallonta sannan ya watsata akan katifa ta sauka da karfi sai da hantar cikinta ya kada still bai dauke idanunshi akanta ba ,nan take ta soma sheshekan kuka sannan ta fara mgn "yaya idan wani laifi nayi maka ya dace ka fad'a min amman wannan kallon naka na hargitsa min lissafi .kallonta ya cigaba da yi bai ce uffan ba har sai data gama ,cikin izza ya motsa labbansa "nasan kin san abinda kikayi sannan kuma kinsa shine dalilin zuwana " cikin mamaki da tsoro take kallonsa ya tsareta fes da idanunshi yana mata kallon banza ."


ranshi a bace ya daidaita tsayuwarsa yana cigaba da kallonta kallon dake qara kashe mata jiki da tsoratarwa "hakika kin tabbatar min da abinda kika turo min a kwanaki uku da suka gabata na zakiga byn mrym , kinyi yunkurin kasheta Kmr yadda kika kashe mubina dan tace tana sona ko?"Idanuwa ta zaro gabanta na faduwa a fili tace" na shiga uku tana dafe qirjinta tare da nuna kanta "ni din na kashe mubina sannan nayi yunkurin kashe mrym ?wani kallon banza yake mata yana jin Kmr ta raina masa wayo ne babu abinda yafi tsana sama da karya yafi son duk abinda ya tmbyeka ka fad'a masa gsky ta haka zaka samu sausauci daga garesa "ban kashe mubina ba me yasa zan kasheta ?"wallahi ban aikata komai ba sannan banyi yunkurin kashe mrym ba tabbas na tura maka sakon zanga bayanta amman wallahi ban aikata hakan ba ,amman ina da niyya to waye yasan da wannan shiri nawa da har ya rigani aiwatarwa?


"Lafiyayyen mari ya zuba mata yana cewa "ni kike wa wannan tmby ?nan take ta rude ta dafe kuncinta inda marin ya sauka abinda yafi damuna kashe mubina da kikayi me tayi miki nuzla ?kuka ta saka mashi tare da durkushewa kasa "wallahi sharri ake son min dan ban san komai akai ba .wani kallo ya watsa mata sannan ya juya mata baya "nasan tabbas kece kika kashe mubina dan hatta wukar da kika kasheta kinyi kuskuren barinta a yunkurin kashe mrym ."


"Da mrym kika kashe wallahi bazai ta'ba damuna ba saboda neman kai nake daita ,ni da zaki kashe min ita amatsayinki na yartaada kafin ta zama mallakina lallai ni kuma da nayi akawarin aureki .nuzla ta sake rudewa ta gigice ta soma jan gwiwowinta ta qaraso inda yake tana kuka "na baki kwanaki goma masu zuwa ki kashe min mrym kafin ta zama mallakina batare da an samu wata hujjar cewar kece kika aikata hakan ba , sannan kada asirinki ya tono ni kuma zan aureki idan kuma kika gagara kasheta har lokacin dana baki ya cika ni kuma nayi miki alkwarin zan damkaki a hannun hukuma a kwatarwa mubina hakinta kin dai sani idan hukuma ta tabbatar da kece kika kasheta karshenki biyu ne, kisa ta hanyar rataya ko kuma zaman gidan yari na har abada muddin rai kenan yana gama fadar haka ya soma qoqarin ficewa daga dakin .."




Mmn sudais


💗💗💗💗💗💗

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login