Showing 156001 words to 159000 words out of 185716 words

Chapter 53 - MAR'ADAM'S book Complete BY AYSHA A BAGUDO.txt

23 Nov 2024

4720

suka samu nasarar gangarowa bisa kuncinta cikin sauri ta shiga gogewa wasu na sake gangarowa cikin muryar kuka ta soma magana "da fari dai mlm yahuza ne yazo "mlm yahuza kuma ?me yazo yi?tayi mata tmbyr a jere tana dubanta qirjinta na bugawa da karfin gaske "wai ya dawo ! shiru aunty tayi tana nazarinta sannan tace "shine dalilin shigarki damuwa ?maryama ta girgiza mata kai tana cewa "bashi bane!


"to menene ni ?" abinda Ke damunki nake bukatar sani "ban san me yasa baba gali baya qaunata ba ta qarasa mgnr tana zubar da wani hawaye "Kawai dan baya qaunarki shine zaki zauna kina kuka kina damun kanki ?ai ba dole sai ya soki ba, rayuwar nan fa da kike ganinta ba kowa bane zai soka, sai ku fito ciki daya da mutun yace bai sonka bare shida dan uwa yake a wajen mahaifinki ."


aunty ta kamo hannunta daya cikin nata sannan ta kai dayan hannunta tana goge mata hawaye "ki cire wannan damuwar ki manta da batun bai sonki wata rana sai labari kuma maganar dawowar mlm yahuza karta daga miki hankalinki tunda nan kusa zakuyi aure da yusif naunayen ajiyar zuciya ta sauke tana sake matso ruwan hawaye idanunta "Allah sarki aunty ai shima ya zama ba rabona ba ta fad'a a kasan ranta zama aunty tayi tana rarrashinta har bacci ya dauketa sannan ta mike ta bar dakin ."


*****
A yammacin ranar litini wanda yayi daidai da kwanan nuzla uku a police station labarin halin da take ciki ya samu jama'ar dake rayuwa acikin abdullahi estate kowa ya shiga damuwa matuka amman banda hindu dan ita murna tayi sosai dan ta fahimci itama tana cikin masu son abinda take so , hisham kam yafi kowa shiga damuwa yayinda hjy salema banda kalmar inna lillahi wa inna ilaihi rajiun babu abinda take furtawa da zubar da hawaye ."


"Ya'yan hjy salema suna zaune gbdynsu a cikin parlour'nta cikin jimami har hisham wanda ya fita haiyacinsa ATA ya shigo bakinsa dauke da sallama ,baa kai ga amsa masa sallamar da yayi ba hisham ya tashi a matukar fusace ya soma magana cikin zafin rai "me ya kawo ka ?" me kake takama dashi ?ya tmbyesa .ATA ya zauna yana duban screen wayarsa" laifin me nuzla tayi maka? me ta tsare maka ?komai zata maka ai bata cancanci kayi mata haka ba ? zaka iya yiwa nana hauwa'u haka ko zaka iya yiwa zabiba haka ?" ATA bai kulasa ba dan yasan baya haiyacinsa so ya rigada ya zautar dashi."




"Mutumin banza dan rainin hankali kawai da bai san mutuncin na gaba dashi ba ,kace baka son yarinya amman gashi akanta kasa an kama yarinyar mutane ATA bai dago idanushi ba ya cigaba da kallon screen din wayarsa yana cewa "ka shiga hankalinka hisham zaka iya fad'ar komai na barka dan nasan a haukace kake ,amamn idan ka sake hadani da yarinyar nan zan ajiye haukan soyayyar dake damunka a gefe nayi maka wulakanci."


"Kai ne dai mahaukaci amman ni lafiyata lau "hisham zamu samu matsala !mun dade bamu samu ba ,nace kana sonta !! baka sonta me yasa zaka sa akama nuzla ?nan zuciyar ATA ya motsa ya somawa hisham wani kallo mai tattare da tashin hankali ganin kar abun ya zama fad'a a tsakaninsu baba babba ya takawa hisham burki ."




ahankali ATA ya soma warware komai da sakon da nuzla ta aika masa dashi "nayi wannan bayanin ne saboda hjy da kuma baba Babba sai ku yanuwanta dan kusan dalilin da yasa ta shiga hannun hukuma "ban bada umarnin ayi mata komai ko a ta'ba lafiyar jikinta ba ,abinda yafi zama mai mahimanci shine bincike kuma ana kanyi abinda nake son gbdynmu mu fahimta yana da kyau mun san daga inda matsalar take wacece ta kashe mubina ?


"wallahi ni ba akan yunkurin kashe wannan yarinyar yasa na damka nuzla hannun hukuma ba dan ko nana hauwa'u aka kama da laifin kisa ko yunkurin kisa da kaina zan damkata ga hukuma haka zalika nuzla qanwata ce Kmr yadda nana hauwa'u take a wajena ,tayi kuka tayi rantsuwa akan bata aikata ba amman wacce ta aikata tana tare damu kuma nasan muddin ba nuzla bace hakika muna tare da mai yin kissan dan haka da zarar an kammala bincike da kaina zan dawo daita gida mu san abun yi amman ya zama dole mu san wacece ta kashe mubina acikinmu ."




parlour'n ya dauki shiru duk suka zuba masa ido kawai suna kallonsa da sauraronsa bayan kamar minti goma ATA ya numfasa sannan ya kalli inda hajiya salema take zaune tana faman kuka "kuyi hakuri hjy km ki kwantar da hankalinki matsawar babu hannun nuzla acikin zakiyi farinciki yana gama fadar haka yayiwa baba babba sallama ya nufi kofar fita yana zabgawa hisham harara ."


tsaye hindu take tare da jingina jikinta da bangon dakinta ta hade hannuwanta duka waje daya ,sosai tayi nisa cikin duniyar tunanin yadda zata kawar da maryam a doron duniya tun kafin akai ga daura masu aure da adam ,dan ta gwamaci ta kasheta idan yaso itama akasheta kowa ya rasa adam din gbdy ."


ji tayi an dafa kafadarta ta juyo a hankali idanunta ya sauka akan baba qarami ta sauke naunayen ajiyar zuciya tana runtse idanunta yayinda gabanta Ke dokawa da wani irin karfi "karki illa kanki akan wannan dan iskan yaron da bai san mutuncin mutane ba "kafi kowa sani baba ina mutuwar son shi wannan maratuncin da dukkanin rayuwata kuma kafi kowa sanin bazan iya rayuwa babu shi ba, amman kana ji kuma kana gani kana da ikon da zaka sa umarni kawai zaa bashi ya aure ni amman kaki kayi komai akai wallahi baba ji nake kamar na mutu ta kamo hannun baba qarami ta kai daidai saitin qirjinta yaji yadda qirjinta ke bugawa da sauri sauri ."


gbdy ya sake shiga rudani duk tunaninsa ya tsaya ya rasa ta ina zai fara ga matsalarsu ta kamfani da kullum cikin rigima ake ga qaddarar data dade da fadawa diyar daya fi so da qauna "idan bazakayi komai akai ba ni zanyi koma nace na fara zan kuma cigaba daga inda na tsaya dan bazanyi asararsa ba sai dai duk mu taru muyi asararsa ,wallahi idan ban kashe mrym acikin estate din ba zan shirya inda zan kasheta "tsaki yaja yana cewa "ban san me yasa kike son Kiyi kisa akan wannan dan iskan yaron ba baba qarami ya fad'a yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa ."


matsawa tayi kusa dashi ta qarasa bakin gadonta tana jan zanin gadon tana sake shimfidawa "hakika zanyi abinda yafi kissa akanshi idan akwai ,kuma zan mutu amman kafin na mutu duk sai na rabashi da masu sonshi idan kuma nayi nasara asirina bai tono ba zan mallakesa idan kuma ban mallakesa ba shima zan kashesa a karshe na kashe kaina da kaina shikenan na mutu cikin salama ta qarasa mgnr tare da kwanciya tana mai kamkame jikinta waje daya wani son ATA ne Ke sake ratsa koina a sansar jiknta yayinda tsumammiyar soyayyarsa data dauki tsawon shekaru tana yi masa ya dinga taso mata kuka ta fashe dashi dan tana son rage wa kanta radadin dake makale a tsokar dake qirjinta a fusace baba qarami ya fice ya bugo kofar dakin da karfi har sai da qararrawar zuciyarta ta amsa ."


Ammi da nana hauwa'u diyana humaira suna zaune a saman kujera,yayinda maryam ke zaune a qasan carfet humaira na yi mata kitso hirar abinda ya faru da nuzla suke kadan kadan suna mamakinta diyana tana cewa "wallah gara da yaya adam yasa aka ka mata ni yanzu nake tunanin ma itace ta kashe mubina "babu mamaki dan mutun abun tsoro ne inji cewar humaira ."


"A'a karki ce haka diyana Allah ne kadai yasan wanda ya kashe mubina tunda ita ba anan aka kasheta ba kuyi wa yaruwarku kyakkyawan zato , mami Kiyi tunani da kyau da irin wukar da akayi yunkurin kashe maraym da ita aka kashe mubina , me yasa zakiyi zarginta ?sannna akan wani dalili har zata aikata hakan akan mubinarmu bayan gabadayanmu muna son mubina nana hauwa ta tmyta ? Wannna fa ba zargi bane tunda yaya adam yasa aka kamata kunsan akwai wata a kasa babu rami me ya kawo rami ."?


"Ni kuma nafi tunanina akan yaya adam ne inji cewar humaira "akan yaya adam kamar ya ? duk suka kalleta fuskarsu da alamun tambaya "ai ta dade tana son shi kusan ranar da mubina ta furta agabanmu cewar tana mutuwar son yaya adam hankalinta ya tashi .
duk suka natsu suna sauraron humaira ta cigaba ai bayan mun rabu ni ta fad'a min amman alaokacin cewa tayi tunda mubina ta rigata furtawa ita ta hakura sai kwatsam sai ga mutuwarta ni tun lokacin naso na fasa maganar amman nayi shiru gudun abinda zai je yazo ."nana hauwa tayi shiru kafin daga baya ta numfasa bata tunanin nuzla zatai haka dan ko byn mutuwar mubina ta dade tana jin mutuwar ,ita kam maryam ta yarda da hakan dan lokacin da akayi yunkurin kasheta kowa yazo amma ita bata zo tayi mata jaje ba ."


"Lallai mami danki yayi kasuwa dan ita karon kanta a ynzu ta fara jin son shi aranta amman kuma meye a attare dashi da kowa Ke son shi haka ? tana jinsu suka cigaba da hira batare data tsoma bakinta ba ."suna cikin hirarsu ATA ya sanya hannunshi ya turo qofar falon tare da sallama akan labbansa duk da bai bude muryarshi sosai ba,maryam dake kallon kofar shigowa ta dago fararen idanunta suka sauka cikin nashi sanda yake takowa cikin falon mami na masa duban mamakin dawowarsa adaidai lokacin sosai ya dauki hankalin maryam dan yayi wani fresh ya qara kyau kaman wani sabon matashi amma fa fuskar nan tashi tana nan kamar koda yaushe babu annuri a hade da miskilancin wanda na yanzu ya qaru "


Kallo daya yayi mata tai saurin janye idanuta akan shi shima ya maida kallonsa kan mami fuskarshi babu yabo babu fallasa"Lafiya dai ko adamcy Nah naga ka dawo by this time ?"Lafiya qalau sweetheart ..." Ya fadi alokacin da yake qoqarin zama a saman daya daga cikin kujerun falon idanunshi na kallon sama suka hada baki suka gaisa ya amsa da "Lfy !
kawai "Adamcy yanzu me ake ciki akan halimatu ne ? ni kaina yanzu bazance komai ba sai abinda hukuma suka ce " ya fad'a yana furzar da iska yanayin yadda yay mgnr kamar yana cikin damuwa."


"Me za'a kawo maka? "coffe " to maza mrym tashi ki kawo masa" badan ranshi yaso ba yayi shiru dan ko yace zai yi mgn damuwa kawai zai qarawa kanshi."ranar da nuzla ta cika kwana biyar aka kira ATA daga police station bayan yaje aka tabbatar masa an kammala duk wani bincike kuma ansamu bambamci a wajen gwajin zanen hannu ,dan nuzla da hannun dama take amfani yayinda mai kisan da hannun hagu, bugu da qari ba zanen hannunsu daya ba dan haka zai iya tafiya daita "to shikenan a fito daita ya fad'a lokacin daaka fito daita shi kansa ya tausaya mata tana ganinsa ta durkushe a gabansa ta kamkame kafafuwansa ajikinta saurin dauke numfashi yayi sai dai tausayinta ya hanashi zareta kafafuwansa ajikinta duk da dottin da jikinta yayi ."


Murya cikin kuka ta soma mgn "yaya na fad'a maka ban aikata komai ba wallahi bani bace kasa aka kawo ni nan kalli jikina yaya ni kaina bana son ganin kaina haka dan allah karka barni anan ka tafi dani gida ka tausaya min kafin na mutu da kyar ya samu ya zare kafafuwansa yana sauke numfashi ya mike tsaye yana mikewa dpo hannu "na gode sosai idan na koma gida zan kira akwai maganar da zamuyi "okay yalla'bai sai najika zumbur nuzla ta mike tsaye tana kuka "dan allah yaya karka barni wallahi bani bace dpo yayi murmushi yana cewa "ai ki kwatar da hankalinki yau a gida zaki kwana wani irin naunayen ajiyar zuciya ta sauke tana masa godiya ATA yayi gaba ta biyosa da sauri ."


Suna shiga cikin estate dinsu kai tsaye hanyar gidansu suka nufa sukai parking masu tsaronsa suka firfito shima ya fito suka nufi cikin gidan a parlour'n suka iske hjy salema da wasu yanuwanta mutun biyu da gudu nuzla ta qarasa ta fad'a jikinta tana kuka itama tana kuka ta rungume diyarta tana shafa bayanta ganin irin kukan da suke yasa ATA ya juya ya kama gabansa alkwari ne kuma ya cika ranar kam murna wajen hjy salema da yanuwanta baa magana sai da kira doctor domin lafiyar nuzla tare da allurar."




Kwanci tashi babu wuya a wajen Allah kullum kwanakin bikin ATA da maryam qara matsowa yake har yau ya rage sauran kwana bakwai kuma har lokacin zuciyar ATA bata rusuna ba salim da mb har ma da hisham ango suke yin duk abinda ya dace dan shi dai ATA yace bazai bata kudinsa akan auren maryam ba kuma babu abinda zai yi na event duk kuma wanda ya kashe kudinsa kar yace dan shi yayi ,dan bai aike kowa ba duk sun jisa amman babu wanda ya tankasa mb da hisham sunyi rabon iv sun kai duk inda ya kamata ace sun kai sosai shirye shirye yayi nisa amman babu ruwan ango dan ko tautaunawa baya yarda suyi dashi da zarar sun soma mgn zai bar wajen ."




Yau tun safe maryam ta tashi jikinta a sanyaye ji take kamar zata rasa rayuwarta komai take gabanta na faduwa abu na tashin hankali dana farinciki duk sai taji gabanta ya yanke ya fadi har kasan mararta take jin ga zuciyarta dake tsinkewa shiru kawai tayi kwance har zuwa lokacin da mami ta shigo "maryam bacci kike yi ne ?ta tmbyeta tana shigowa dakin sosai ta yunkura ta tashi daga kwanciyar datayi tana cewa "a'a mami ba bacci nake ba na dai dan kwanta ne ."akwai abinda zan miki ne ?mami tayi murmushi tana dubanta dan ta lura tunda aka shiga satin bikinsu take cikin damuwa ."


"akwai abinda ke damunki ne ?
Ta girgiza mata kai alamun a'a "ki sanar dani idan akwai abinda Ke damunki ni din tmkr mahaifiya ce agareki ? ta sake girgiza mata kai alamun a'a sai dai kallo daya zaka mata ka fahimci akwai damuwar dake damunta ,ki cire damuwa aranki kinji maryam babu abinda zai faru sai alkhairi ta lumshe mata idanunta alamun ta gamsu "maza tashi ga mukulin mota kije gidan shahida yanzu ta kira wai kije tana son ganinki anya kuwa zan iya tuki nan mami ? bana jin zan iya dan bani da kuzari ajikina ,to shikenan bari nayiwa nura direba mgn ya kai ki ."


"to mami amman bari naje nayi masa magana da kaina tare suka fito maryam ta fice ta bar mami da nana hauwa'u a parlour'n zuwa haraban gidan akan idanun hindu ta fito dan haka tayi adduar samun nasara da aiwatar da nufinta akanta domin kusan wata guda kenan tunda aka saka lokacin aurensu take neman hanyar da zasu samu kebewa ."


bayan maryam ta fad'a masa zai kaita gidan aunty shahida ta juya ta koma ciki domin ta qara shirya kanta a parlour ta tsaya kusa da nana hauwa'u "sister muje ki shirya ki rakani." a'a babu inda zani maganarku ta matan aure zakuyi ina ni ina rakiya kinga je ki kawai sai kin dawo allah ya tsare hanya" ganin mami zaune a wajen yasa maryam bata sake cewa komai ba ta shige ciki .yayinda hindu ta qaraso inda nura yake zaune tana cewa "mlm nura ina son na dan aike ka ko akwai abinda zakayi ne ?tayi masa tmbyr dan tasan me zai yi adaidai lokacin "hajiya mryma zan kai unguwa okay to shikenan karka damu allah ya tsare ta juya zata koma ciki ,kina bukatar wani abu ne ?




Ta tsaya cak ta dan juyo fuskarta a sake "daman abu nake son a karbo min anan bakin titi amman tunda fita zakayi karka damu ,aa baa yi haka ba kawo nayi sauri na karbo miki kafin ta fito ta mika masa kudi dan cake zaka amso min amman mai chocolate ya karba kudin ya nufi babban get din estate din da dan saurinta ita kuma ta shiga gidansu domin ta shirya ."akan idanunta still maryam ta fito kafadarta makale da jaka tana neman nura direba tayi sauri ta fito tana cewa "mrym amarya fita zakiyi ne ?ta waigo bayanta a hankali ganin hindu ta saki fuska sai dai mgnr datai mata yau din ya dan bata mamaki dan sam batayi tsammani ba dan ba abokiyar maganarta bace domin dai kusan duk kallon mai girman kai suke mata kasancewar ta girmesu km bata shiga cikinsu "


"Eh wallahi fita zanyi nura direba ne zai kai ni gashi na fito ban gansa ba ko ina ya shiga ,Allah sarki okay muje na saukeki mana nima fita zanyi ta fad'a tana qoqarin shiga motarta da kamar bazata shiga ba amman sai tayi tunanin karta ga Kmr tayi mata wulakanci dan haka ta yanke shawarar shiga idan yaso direban aunty shahida ya dawo daita ta bude dayan bangaren ta shiga ta zauna hindu ta tada mota suka fice daga gidan koda nura direba ya dawo kai tsaye gidansu hindu ya nufa ya bada sakonta ya dawo zaman jiran fitowar maryam ."


Ahankali suke tafiya hindu na jan mrym da hira "Maryam amarya adamcy kenan gashi yazo amman naga baki fara shirin komai na amare ba, wallahi ban fara ba dan bana cikin natsuwata "to me kuma Ke damun amarya ko fargaban kasancewa da angonki ne ? maryam tayi murmushi kawai "Ke kuwa me zasa kiyi fargaba alhalin auren soyayya zakuyi ?ko auren soyayya ne dole kaji wani iri dan aure ba wasa ba, kenan gskyr labarin danake ji daga bakin mutane daban daban na kina son adamcy gsky ne ? zuciyar maryam a dake tace "eh hk ne muna

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login