Showing 108001 words to 111000 words out of 185716 words
Chapter 37 - MAR'ADAM'S book Complete BY AYSHA A BAGUDO.txt
kuskura ki bamu hakuri , shegiya yarinyar munafukar Allah taala kin wani marairaice fuska kamar ta kirki zaki bawa mutane hakurin gulma wallahi yau shine zamanku na karshe acikin gidan nan sai kun bar mana gidanmu ,gara ma tunda wuri Ki san yadda zaki d'auke wnn uwar taki da wannan shegen kannin naki mai falla fallan kunnuwa Kmr na fir'una ku bar mana gidanmu mu huta da jaraba sanda ussein yana raye bai barmu mun huta ba sannan bai tsinana mana komai ba sai ruwan shaye shaye da d'auko mana magana wanda sanadiyyar haka ya kwaso mana wannan munafukar uwar taku gashi ya mutu ya barmu da mugun iri ."
"Kuka maryama ta fashe dashi hade da sake durkusawa a wajen batare da tasan abinda zata fada ba, tana mai bakincikin irin kalar rayuwar da mahaifinta yayi a sanda yake raye, gashi ya bar duniyar amma basu huta ba , wannan wace irin rayuwa ce ? me yasa wasu yanuwa suke yin haka ? "tasani da ubansu mai arziki ne da duk abinda yayi babu mai tuna masu bare har a zagesu dashi ."
tsaki baba gali yaja yana cewa " Munafukar banxa sai anyi magana kisa mutane a gaba kina kuka, da ubannaku bai shaye shaye ba zaa fada? daya zauna da mutane lpy zaa ki fada ?kullum yana cikin d'auko mana magana gashi ya mutu ya bar iri an iya tujara iya tujara sauran shaye shaye .."
"Allah bazai sa ba ,baba ka daina masa mugun fata "me ya saura yaro ya zama dan daba ai sauran shaye shaye, habib zai yi magana maryama tayi saurin dakatar dashi tana cewa "walalhi karka sake cewa komai ai ga irin abinda ka haifar ko ?"ni dai na fada maku maza ku san ynd zaku yi ku bar mana gidanmu tunda gdn bana ubanku bane,"
maryama da tarin qunar zuciya da qunar rai take zubar da hawaye tafi karfin minti goma a durkushe sai daga baya ta koma inda tabar aunty ta durkusa kusa daita hawaye na zuba a idanunta Itama aunty hawayene take zubarwa a nata idanun tana jin ciwon abinda habib yake duk da tasan gsky yake fad'a masu amman bata só yana fadar duk abinda yazo bakinsu dan kome zai faru bazasu ta'ba sonta ba har yau tarasa me tayi masu mai zafi a duniya da suka kasa yafe mata sannan suka kasa danne tsanarsu akanta da yaranta ."
Habib ya kalli aunty ya kalli maryama itama duk kuka suke maryama kam har da shesheka tana rarrashin aunty " ku sani ku daina wulakantamu na kyale , kusani nadamarku ta kusan zuwa a nan kusa kuma munafurcinku ya kusan qarewa domin bazan sake yarda da iskancinku dan kuwa kun bari d'an zaki ya girma yayi girman da zai iya kasheku d'aya byn d'aya ,gidan nan kuma babu mai korarmu acikinsa sai dai a d'aga sa d'ungurungun dinsa a sakashi a kasuwa a siyar a bawa kowa hakinsa kowa ya kama gabansa"
"Ai kuwa baka isa ba wannan gidan ubanmu ne kai har ubanka ya gama iskancinsa ya koma ga Allah cima kwance ne bai da gidan da zaka yi wannan taqamar da kake yi "kai da ba cima kwance bane sannan bakayi iskancin ba ina naka gidan daka gida yake ? "sannan .."
"habib dan girman Allah .." saurin d'aga wa maryama hannu yayi ta hanyar dakatar daita " ki barni dasu heartbeat wallahi kowa sai na bashi size dinsa yau idan sunce basu da mutunci zan nuna masu ni d'an zamani ne , ya d'an tsaya yana kallonsu d'aya byn d'aya ,nan take ya hango tsananin tsoronsa da shakkarsa acikin kwayar idanunsu "oya kuna iya wucewa ku bar mu cigaba da rayuwarmu ko sai na fitar daku d'aya byn d'aya?".
A yadda suke kallonsa sun fahimci zai iya jansu ya fitar dasu kmr yadda ya fad'a dan haka aunty hassana ta kalli aunty "sai ki daina kukan munafurci tunda burinki ya cika kin haifa mana maseefa amman in sha allahu maseefar akanki zai qare tunda ya fara zama d'an daba tana gama fadar haka ta fice daga d'akin tana zage zage
aunty tayi saurin runtse idanunta tana jin zafin kalmar data danganta mata d'a dashi , itama aunty salma tace "shegu a haka zaku qare jiya iya yau babu cigaba ta nufi hanyar fita " da sauri habib yace "Ke ina naki cigaban da kika samu yake ? "Ke da ko sallah bakya yi , qazama mara sallah mai dotti kawai kije ki gyara tsakaninki da ubangijinki zai fiyye miki sauki akan shiga rayuwar wasu ."
shi kam baba gali cewa yayi "bilkisu Ina tarbiyar taki ?yau a gaban idanunki d'anki yake nuna min iyakata "to sai me dan na nuna maka iyakarka a gaban idanunta ? "kai da bakaji tsoron gaban idanunmu kake nuna rashin qaunar mahaifiyarta ba kiri kiri kake zaginta agaban idanunmu akwai abinda yafi wannan ciwo ? wallahi idan bakasani ba kasani yanzu abinda kukayi mata a da tayi hakuri ta shanye yanzu ta haifi d'an da zai kwatar mata 'yanci zan goge wannan tarihin idan ka cigaba da tsayuwa zafin jinina zai iya sa na d'auki takobin can na file maka kai dashi ko na raba katon kan nan naka gida hud'u idan yaso nima akasheni salin alin baba gali ya fice batare da ya sake cewa uffan ba."
Yana fita habib ya qaraso inda aunty da maryama suke durkushe suna kuka "cike da girmamawa yace "ku daina kuka in sha allahu ku daina kuka acikin gidan nan , kun daina damuwa matsawar ina raye zan tsaya maku , zan kula daku da zarar na gama karatu zan ...."bana son jin komai daga bakinka habib na fahimci kana bukatar na bar muku gidan nan shiyasa ka kirkiro abinda za'a koreni daga cikinsa tana gama fad'ar haka bata tsaya jin abinda zai ce ba ta mike ta shiga d'akinta ta d'auko mayafinta kawai ta fito zata fice ta bar masu gidan ."
Atare maryamah da habib suka sha gabanta cikin tsananin tashin hankali "haba aunty ya zaki mana haka ?kiyi hakuri aunty hakika habib bai kyauta ba amman karki tafi ki barmu ."maryama dan'uwanki baya bukatata acikin gidan nan yana bukatar na tafi na bar masa filin gidan nan ya cigaba da rayuwa ta qarasa maganar tana zubar da hawaye ta tabi gefen maryama zata raba ta wuce ."
habib ya riko mata hannu "kiyi hakuri aunty ki fad'a min abinda kike bukata nayi miki alkwarin wallahi zanyi kisani idan kika bar gidan nan bashi da wani amfani a wajenmu "yana da amfani mana tunda gashi kayi son ranka kasa an zageni anci mutuncina anci na iyayena ai gara na kama gabana tunda zamana acikinsa babu abinda yake haifa min sai damuwa da bacin rai ".
Kuka ya kufce ma maryama ta d'an rufe fuskarta da tafukan hannuwanta saboda tuttukin da zuciyarta Ke yi "kai ma kasan abinda kayi ba daidai bane har ka iya cire hannu zaka doki baba gali wallahi baka kyauta ba tunda kasan halinsu to meye amfani tsayawa kana fad'a yana fad'a "ki fahimci wani abu heartbeat wad'an nan mutane basa qaunarmu ,babu abinda Ke cikin zukatansu sai tsanar mu " tunda mun san halinsu sai mu kiyaye abinda zai kawo sa'bani dasu shima kukan yake yi "suna nuna mana bambamci akan ya'yansu ,suna quntata mana suna da fuskar gazawa garemu musaman akan ya'yansu yanzu laifin me kikayi ma aunty salma ta shigo tana zaginki ?"maryama bata sake cewa komai ba illa ta cigaba da kukanta haka ma aunty batayi magana ba illa qoqarin zare hannunta da take cikin nashi ."
"na tuba aunty bazan sake ba ki fad'a min abinda kike so ,nayi miki alkwarin bazan sake ba ya fad'a yana zubar da hawaye itama ta goge hawayen dake zuba akan kuncinta ta cigaba da mgn "daga yau babu ruwanka da kowa acikin gidan nan duk abinda zasuyi ko zasu fad'a akanmu ka kawo ido kasa masu , kai ba zagi ko dukana zasuyi babu ruwanka a rashin yace ba dai duka ba amman a zahiri yace "to aunty an gama ."wallahi abinda kayi yau din nan ba irin tarbiyar daaka bamu bace "in sha allahu bazan sake ba heartbeat ki bata hakuri bazan sake ba kamo hannun aunty maryama tayi suka koma kan kujera mai zaman mutun uku da duk ashon jiki ya batattake suka zaunar daita tare da sakata a tsakiyarsu suna bata hakuri ."
Kamar yadda mlm yahuza ya sanarwa nafisa byn sallahr ishai zai zo sai ga yaro yana sallama da maryama lokacin suna zaune a falon aunty ta dubeta amman ita ko ajikinta sakon da yaro ya fad'a aunty tace "maryama bakiji bane ?ta d'an dubeta ta share yaron ya tsaya yana jiran abinda zaace "to sai ki tashi kije "ina kenan aunty?"bakaji ana sallama daita bane "gsky babu inda zata ban san dalilin da yasa da mutun yazo nemanta ba sai ki bata damar fita baki san ko waye ba mazan da duk 'yan iska ne da zarar sun fara zuwa kamar abun arziki da zance aure ya shigo sai su gudu su barta ni gsky babu wanda zai sake zuwa ta fita ."
"Maryama tashi Kiyi maza kije ki dawo saboda ki samu ki d'an huta karki dade duk da nasan ba dad'ewar zakiyi ba ,ina dalili da zakace bazata ba kai zaka aureta ?ya marairaice murya "bani zan aureta ba amman at least aunty ki duba lamarin nan kawai suzo suna 'bata mata lokaci da dagula mata lissafi "Babu wani dagula lissafi a haka allah zai kawo mata wanda zai aureta ,ina son kasan wani abu habib duk cikin masu zuwa neman auren maryama babu mijinta acikinsu , duk lokacin da mijin yazo to babu makawa sai anyi domin babu mai aurenta matar wani kai yaro je kace gata nan zuwa yaron ya juya da sauri dan daman amsar da yake jira kenan zata fito ko kuwa bazata fito ba ."
maryama ta tashi ta shiga d'aki dan tasan ko waye yazo ta d'auki hijab dinta ta fito "amman dai ni aunty a wajena ba daidai bane ,ni fa kamar mahaifinta ne a matsayina na namiji acikin gidan nan amman me yasa sai a dinga nuna min iyakata acikin gidan nan , na fiku sanin halin mazan wannan zamani babu komai acikinsu sai tsabar yaudara ".
Aunty ta kallesa saboda yadda yake maganar tamkar wani babban mutun tace "wai har guda nawa kake habib ?" duka shabakwai gare fa kawai dan allah ya baka jikin girma "ni dai gsky ban yarda ta fita koina ba girgiza kai aunty tayi tana kallon yadda yake kamaninsa yake canzawa a kullum yana komawa na mahaifinsa tun ba yau ba kusan kowa yana fad'in kamanin nasu "gaskiya habib kar ka zama mai hana neman auren ."
tsayawa maryama tayi tana kallon fuskar habib daya had'eta tmkr ance masa idan ta fita guduwa zaa yi daita ,ahankali ta kira sunansa "after dad "
"Karki wani kirani da wannan sunan dan dani din ina da wannan matsayin da za'a dinga bin umarnina " ta qaraso ta zauna kusa dashi ta riko tafin hannunsa cikin nata tana kallonsa da idanuwanta da suka canza kalla "after dad me kake so dani ?"ta fad'a tana kallon yadda shima ya zuba mata ido yana kallonta ."
"Abinda nake so duk wanda yazo karki qara fita koina idan abinda ake miki acikin gidan nan baya damunki ni