Showing 57001 words to 60000 words out of 185716 words
Chapter 20 - MAR'ADAM'S book Complete BY AYSHA A BAGUDO.txt
ita din ba marainiya bace ta daura hannunta daya a saman kanta ko zataji saukin zafin da zuciyarta take mata ."
tana cikin wannan halin taji an turo kofar dakinta da sauri ta dago tare dawowa haiyacinta tana mai goge hawayen idanunta da hannuwanta duka habib ne ya shigo wanda sakamakon sheshekan kukanta ya shigo dashi sai daya mata kallon tsanake sannan yace "me ye damuwarki male? dake shi kuma haka yake kiranta dashi ta sake sanyawa jikinta jarumta tana girgiza masa kai " alamun babu komai."
"karki fad'a min haka byn kukanki ne ya shigo dani ya fad'a yana kafeta da fararen idanunshi qara maimaita tmbyrta yayi tayi kasa da kanta sakamakon hawayen daya sake cika mata ido domin kwalkwaluwarta ta toshe ta kasa fad'a masa dalili "ya sake matsota sosai male ki fad'a min damuwarki domin bazan bar dakin nan ba muddin baki fad'a min ba domin dai damuwa Ke saka mutun kuka irin wannna kuma tunda nake ban ta'ba ganin kukanki irin haka ba kuka mai fitowa daga kasan zuciya ."
Ya kai hannu ya dago habarta yana kallon hawayenta dake zuba yabi hawayen da kallon hankalinsa na sake tashi cikin tsananin tashin hankali yace "wanene ya bata miki ranki haka? ta girgiza masa kai kawai "wai meye haka ne male kina son zuciyata ta kasa sukuni ne ko me ?ta sake girgiza masa kai ya juya a fusace zai bar dakin "bari naje na taso heartbeat.."
ta riko hannusa da sauri "karka tashe ta bacci dan baccinta yayi nisa gashi gobe tana da exam's "to ki fad'a min damuwarki kamoshi tayi ta zaunar dashi a gefenta ya zauna yana sauraronta kusan second goma sannan ta zayyane masa komai sai daya numfasa kana ya soma mgn "male duk abinda heartbeat ta fad'a is right and it good dan daman nima ina neman hanyar da zan miki wannan tmbyr domin abu ne daya dade cikin kwakwaluwata har ya Kan hanani kwanciyar hankali Kiyi tunani male
gsky heartbeat ta fad'a miki ya kamata kije ga danginki ko mu ki fad'a mana inda suke muje domin muna bukatarsu "
Jin haka yasa ta barke da wani sabon kuka "baku san me suka min ba baku san irin wahalar dana sha a hannunsu ba ,na sha wahala kuma duk akan mahaifinku ne bana tunanin zasu qaunaceku shiru yayi yana dubanta cike da mamaki "me dady yayi masu haka ?sannan wani irin wahala kika sha a hannunsu ?yayi mata tmbyr a jere cikin tsananin tashin hankali kafin a hankali ya kai hannu yana goge mata hawaye shiru tayi ita kanta tana son ta basu labarinta amman bata san yadda zata dauki abun ba "tana son mahaifiyarta tana tausaya mata tana gudun bacin ranta ,bata son ganinta cikin damuwa amman a karshe itace abar kyama itace abar wulakantawa, itace mara mutunci a idanunta
har tana cewa allah yasa mijinta ya wulakantata Allah ya hanata haihuwa Allah yasa ya saketa mijin da take tsananin so duk akan ta zabeshi a matsayin jikin aurenta ."
Kuka sosai take tmkr ranta zai fita tana furta "na yafesu har abada zan zauna na qarasa rayuwata ni kadai "yayinda habib Ke share mata hawaye yana kuka yana bata hakuri domin yasa duk abinda yasata kuka irin haka mai girma ne muryarsa a sanyaye yace "kiyi hakuri male ki daina kuka kukanki na balain daga min hankali na hakura da son jin komai domin jinsa bazai zame min alkhairi ba amman kema kiyi qoqarin ki manta abinda ya rigada ya
wuce amman iyaye da yanuwa duk abinda sukayi baa yafesu ."yana gama fadar haka ya juya har ya fita ya rufe mata kofar dakin hawaye ne yake fita dga idanunta "yaya suke son tayi da rayuwarta duk abinda suka fad'a mata tasan gsky ne amamn har yanzu zuciyarta ta saka mantuwa akwai wani abu da yake tsaye acikin zuciyarta ta rufe idanunta ta sake jingina jikinta da pillow daya saka mata a bayanta tana jujjuya maganganun yaranta tana yin filla filla dasu tana son kawar da bukatarsu amman tasan gsky suka fad'a mata bata taba daukar ya'yanta zasu girma da son danginta irin haka ba kasancewar suna cikin dangin mahaifinsu."
*****
mrym zaune a d'akin hjy zulaiheart tana shirya mata kayanta da mai gugansu ya kawo tana tsaka da aikin aunty shahida ta shigo bakinta d'auke da sallama ta amsa tana gaisheta fuskarta d'auke da murmushi "aiki kike yi ne haka amaryar ATA tayi mgnr cike da zolaya " sannu da zuwa auntynmu me kika zo mana dashi ta fadi haka dan kawar da maganarta ,cikin dariya aunty shahida ta zauna akan sofa tana cewa "kayan dadi da bazasu fad'u ba maryam tayi murmushi yasu madina kwana biyu shiru kmr anyi ruwa an dauke "ke dai bari madina exam ne ya sakata gaba Amman Ina ganin ma zuwa wani sati zasu kammala ".
"okay to Allah Bada sa'a "Ameen ta amsa tana cewa "wata shawara nazo miki dashi a tsakaninki da ATA jin haka yasa ta dan tsaya ta kasa cigaba da abinda take hankalinta gbdy ta tattara shi kan aunty shahida " Ina sauraron shawara daga bakin aunty nah maganin kukana " Marym please ki sanya kunnen baseera akan abinda zan fada miki "ta sake mika mata hankalinta sosai " kin dai san halin wanda zaki aura yana da kyau ki dan rage wasu abubuwa sannan ki koyi wasu abubuwa nasan kin fahimci abinda nake nufi ki zamo mai kwantar da kai da iya girke girke dan bazance girki ba ,daga ke har nana na fuskanci Kuna da matsala ta wannan bangaren dan haka ki dage ki koyi kowani irin girki da tsafta duk Inda zaki kasance acikin gidanki the next thing shine kamshi domin shi din ma'aboci son dadd'adan girki ne da son kamshi ki zamo mai hakuri da lallabashi domin ta haka zaki yi saurin dakusar da duk wani taurin Kansa abubuwan social media Shima ki rage "dan kinsan bazai yarda dashi ba wasu daukar hoto kullum ana d'aurawa a duniya Shima bazai yarda ba ".
"shikenan naji aunty inshallahu Kuma duk zan d'auki shawararki ki dai tayani da addua biyyaya zanyi a aurena da ya Adam Allah yasa ya zamemin alkhairi "Ameen byn biyyaya har da soyayya sai kunyi aure zaki fahimci hk "Kai aunty babu wata soyayya " ki rubuta ki ajiye a Inda bazai goge ba ko na mutu sai kin fada "Kai aunty shahida bana tunanin yaya zai soni a yadda yake nunawa ni dai zanyi iya yina kawai "karki tsaya iya yinki kiyi kokari ki canzasa gbdy ta yadda zai manta da mafar.."
"wannan Kuma impossible aunty bazata iya ba " suka ji sautin muryarsa acikin dodon kunnensu a tare suka juyo a firgice suka Kalli Inda yake tsaye sanye da farar jallabiyya mai gajeren hannu ajikinsa gashi kan nan nashi sai sheki yake zubawa tamkar balarabe kallon second biyar mrym tayi masa tayi saurin d'auke kanta sakamakon mugun kallo da yake jifanta dashi .matsowa kusa da aunty shahida yayi sosai fuskarsa a hade babu alamun murmushi "babu abinda za'a ta iyayi wanda zai dakusa wannan soyayyar dake dawainiyya da zuciyata da gangar jikina Ina son princess so mai girma sannan gara ki fad'a mata babu iskanci da sakarci a gidana dan bazan dauka ba ."
Take kwakwaluwar mrym ya shiga ceculating abinda mgnrsa take nufi kenan akwai wacce yake so aka takura masa aurenta ?take jikinta ya kama kyarma ya ware hannuwansa duka cikin jin dadi "okay a she fa bata san da wannan zance ba fa ?"gsky ya kama ta san cewar akwai wata acikin zuciyar Adamcy Kuma ko ba dade ko bajima muddin na ganta zata kasance cikin rayuwata bukatata na ganta domin nafi bukatarta fiyye da komai ."
gbdy mrym dake zaune taji babu dadi acikin ranta "tabbas wannan shine dalilin dayasa bai maraba da aurenta wani bakinci ya ziyarci qirjinta ta mike tsam zuciyarta cunkushe ta nufi kofar fita tana fita aunty shahida ta soma magana cikin fushi "wai me yasa kake yin hk ne sam bai dace ba? "me Kuma nayi byn gskyr dake cikin Raina na fada gara tasani ? ''idan kana yiwa mrym hakan bazamu ji dadi ba , rainmu zai dinga baci fiye da bacin ran daka gani yanzu acikin kwayar idanuna ,dan bazamu yarda ka fifita wata banza can akanta ba banzar ma da ba gskiya bace .
"duk son da nake maka zan iya ajjiyeshi gefe na hukuntaka hukunci mai tsanani akan mryam ,kada ka sake makamancin wannan maganar a gabanta wannan ya zamo Karo na karshe ya jiyo sautin mahaifiyarsa wacce ta shigo byn fitar mrym nunfashi ya fesar yana cewa ''relax sweetheart insha Allahu an gama ya fice ya barsu "Allah ka shirya Adamcy na rasa meke damunsa " meke damunsa kuwa ban da iskanci aunty shahida ta katse hjy zulaiheart , nifa wani lokacin sai naji kmr Abar had'in nan kar yazo ya bata zumunci ."babu wani zumunci da zai bata wannan auren Allah ya rigada ya hadashi tunda gashi har ya amince ayi ,da yarda Allah rayuwar gaba zatai dadi "Allah yasa inji cewar aunty shahida.
Da fari baba qarami hjy zulaiheart taso ta kira ta sanarwa hukuncin data yanke kasancewar shi yana bangaren baya inda mallakinsa yake sai dai tayi tunanin ta fara sanarwa baba Babba kasancewarsa babba a tsakaninsu a yanzu saji daga bakinsa
tayi murmushin Jin dadi dan tasan baba qarami zai ji dadi sosai idan labarin auren adamcy dan kusan kullum sai yayi mata maganar ."
*****
a natse ta fara neman layin qanwarta hjy nuriyya wacce ta kasance abokiyar wasanta iyayensu uwa d'aya Uba d'aya Kuma akwai shakuwa sosai a tsakaninsu tana zaune a kasar london tun aurenta har zuwa wannan lokacin acan ta haifi yaranta duka iyakarta da naija ziyara ko wani sha'ani mai mahimmam. suka gaisa cike da farinciki Inda hjy zulaiheart take sanar mata batun hada Adamcy aure da maryam " Kai alhamdulillah masha Allah gsky abu yayi kyau sosai Allah ya sanya alkhairi ya nuna mana lokaci ,wannan karon zanyi k'okari na shigo kasar kafin lokacin domin ayi biki dani ".
Hjy zulaiheart tace "gsky kam anyi bukukuwa duk baki samu damar shigowa naija ba "haka ne kam amman inshallahu zan shigo wannan bikin nayi ne no any excuse ta k'arasa maganar tana murmushi suna cikin hirar hjy zulaiheart tace "nuriyya wai kuwa kina jin labarin bilkisu ?dip hjy nuriyya tai tmkr an d'auke wuta nepa tana jin wani irin daci acikin ranta sai data yi kusan minti biyar sannan tace "bana Jin labarinta Kuma bana son na ji labarin Inda take , kuma Ina son ku shareta ku cireta acikin zuciyarku har abada Kmr yadda mukayi yarinyar data nuna mana bamu Isa daita ba ,sannan bata sonmu ta zabi rayuwa ko babu mu me yasa zamu damu daita ?
"ni dai duk wanda zai nemata acikinku yaje amman ni nuriyya bana ciki kuma babu hannuna babu kafa ta ciki "naunayen ajiyar zuciya hjy zulaiheart ta sauke tana cewa " dan Allah nuriyya kiyi hakuri ko babu komai rayuwarta qaddara ce Allah ne ya d'aura mata wannan rayuwar babu yadda zata gujewa qaddararta ,wallahi duk sanda ta fado min sai na zubar da hawayen tausayinta , da nasan Inda zanganta wallahi zan nemota .
"Kune fa kuka damu daita ko nace ke dan duk cikinmu babu me zanceta wallahi sai ke ,bata ga wuya bane shiyasa bata dawo ba, wallahi nafi son rayuwa ta juya mata baya ta dawo tana kuka tana rokonmu kullum mummunar adduar da nake mata kenan sannan Ina adduar duk tsanani karta dawo mana da zuria Kmr yadda hhyrmu take addua ."
"wannan addua ta rashin haihuwa a tsakaninsu batayi ba ku daina mata mummunar addua gskiya "ai babu abinda ya kamaceta da wuce mummanar addua " yanzu dai kiyi hakuri muyita mata addua da fatan alkhairi a duk Inda take lokaci nata tafiya a lisafinsa shekaru ashirin kenan rabonmu daita , kiyi hakuri dan mu barwa Allah komai sannan muyi mata adduar Allah yasa ta waiwayo mu cikin koshin lafiya naunayen ajiyar zuciya hjy nuriyya tayi sannan tace "shikenan big sister ai abinda kikace shi zamuyi cike da qauna yar'uwarta hjy zulaiheart sukayi sallama da yaruwanta suna gama wayar uncle Umar ta kira ta sheida masa tana son ganinsa ."
Ranar asabar da misalin karfe hud'u na yammaci baba bAbba yazo bisa Kiran da hjy zulaiheart tayi masa , byn sun gaisa hjy zulaiheart ta karanto masa hukumcinta akan ATA cike da farinciki uncle Umar yace "masha Allah wannan hukuncin yayi Kuma mun gamsu dari bisa dari dan burin mu bai wuce muga adam ya ajiye iyali ba ,bugu da Qari zaa sake karfafa zumunci a tsakanin inshallahu zan sheidawa sauran yan'uwana sai mu saka ranar da zamu ga alhj saidu dan zamu so a daura auren nan kusa". "wannan maganar tayi Kuma naji dadinta sosai dan haka a fara sheidawa baba qarami dan nasan murnarsa sai tafi ta kowa domin duk yafi mu d'auki son ganin Adamcy yayi aure ta k'arasa maganar tana murmushin jin dadi "ai kuwa daga nan ma bangarensa zan shiga na fara sheida masa Allah ya sanya alkhairi ya nuna mana lokaci "Ameen ya Allah,Allah kadai yasan murnar da zaiyi idan yaji ya sha lemu da kayan snaks din da'aka jera masa suka zarce da tautaunawa kafin daga bisani sukayi sallama ."
Baba qarami na zaune akan kujera me zaman mutun uku sai ga baba Babba wanda ya kasance yaya garesa Kuma Kani ga mahaifin ATA yana ganinsa ya saki fuska tare da farincikin ganinsa ya d'an mike tsaye cike da girmamawa ya bashi hannu suka gaisa sannan ya nuna masa mazauni atare suka zauna "sannu da zuwa yaya ! "ya gida da iyalin fatan suna lfy?"alhamdulillah kowa Lafiya yake ya naka iyalin ?"Suna lfy ya bashi amsa yana murmshi ya mike ya dauko masa abun sha "bazan sha komai ba daga bangaren hjy zulaiheart nake na sha " .
suka yi shiru na second biyu sannan baba babba ya fara magana a tsanake " kamar yadda na fad'a mk daga bangaren hjy zulaiheart nake tayi decide ta had'a Adam aure da diyar kaninta abdulrauf " what ?"when ?ya fada a matukar rude yana Jin wani irin abu ya caki kahon zuciyarsa , yayi saurin runtse idanuwanshi "zulaiheart na bukatar wannan labarin ya zamo Kaine ka fara jinsa bisa kokarinka na son ganin adam ya ajiye iyali dan haka nan da sati me zuwa zamu gana da yayan mahaifin yarinya alhj saidu ."
shiru baba qarami yayi har sanda yayansa ya dasa aya ya mike tsaye"to ni zan wuce duk abinda ake ciki zan kiraka a waya a fusace baba qarami ya mike Shima yana cewa "yaya wannan wace irin maganar banza ce kazo min dashi sannan kana k'okarin sa kai ka wuce ka barni ? yayi mgnr a fusace yana sa hannu ya daki center table din dake tsakiyar falonsa wanda ke d'auki da ruwan lemu kala dabam dabam ,nan take wasu glas cup suka tarwatse yana huci yake kallonsu "yanzu ni dana cin burin ya zabi daya daga cikin ya'yana ya aura shine dan munafurci zata hadashi da diyar kaninta saboda son Kai irin nata ?
"ya'yana yafi dacewa Adam ya aura ba wannan yarinyar ba ya sake dukan table wanda hakan yasa gbdy ahlin da ke numfashi a part din suka bayyana" burina bai wuce ya'yana ko jikokina su had'a iri da dashi ba yayi mgnr yana kallon cikin kwayar Idanu dan uwansa ."me yasa zaka fadi haka idris? "eh na fad'a yayi mgnr yana cakunar wuyan dan'uwansa da iyakacin karfinsa yana maxurai abinda bai taba faruwa ba a tsakankanisu ,hindatu wacce suke kira da hindu ta samu guri ta zauna tana kallonsu zuciyarta na rawa dan ta dade a tafkin qaunar ATA mahaifinta ne ya hana a fito da soyayyar a cewarsa yana jiran lokaci yau ga lokaci ya zo masu a wani iri .
sauran kuwa hankalinsu ne yayi kololuwar tashi ganin yadda mahaifinsu ke rike da wuyan dan'uwansa uwa d'aya Uba d'aya .Wallahi yaya Kai kare ne da bai san ciwon kanshi ba ! "shin ya'yana basu dace dashi bane ka bani answer ?uncle Umar yayi shiru kawai yana kallon hannun uncle idris dake rike da wuyansa batare daya ce uffan ba.
"me yasa kazo min da wannan banzar labarin mara dadin ji ?ya k'arasa maganar yana sakar masa wuya yana dubansa yana huci "saboda mu bamu Isa ta hada jini damu ba shiyasa ta za'ba masa acikin dangi ta ?"to me zai faru idan na hana auren ?"zan hana wannan auren ta karfin tsiya yayi