Showing 75001 words to 78000 words out of 110841 words

Chapter 26 - BAKIN CIKI BOOK COMPLETE BY ESHAT.txt

12 Sep 2025

73

wannan marin mai tsanannin xafi ba. Sai
dai taji muryar Abba na fadin wannan shine
gargadi na karshe da xanyi miki, shi ya sa na
tara kowa su xama shaida! Idan har ba xaki bi
umarni na, ki xauna a gida ba, to wlh sai dai ki
xaba, ko mu ko Danliti! BAKIN CIKIn nan ya ishe
mu mama. Gara in sallama ki, in tabbatar da
kinfi karfina xaman kanki kikeyi. Saboda haka
daga yau kika kara sa kafarki kika fita kikaje
gun yaron nan, to kar ki dawo, ki yi zaman ki
can wajensa ku sha shagalinku yadda kuke so.
Duniya ce Mama, mai dauke da axuxuwa babu
adadi! Ina fatan kinji kuma kowa ya shaida! Alh.
Basir ya karbe karuwa kike so ki xama ko? To
Allah ya baki sa'a, mu dai ba xa mu hana shi
ba, duk ranar da koreki. Alh. Adamu yace dama
saboda me xamu hana shi? Cikin shege ne fah
ajikinki, amma bai sa kinyi nadama ba, to me
xai sanya ki kuwa? Karkiji da wai, mun tsame
hannun a kanki, haka xuri'ar gidan nan kaf! Kar
ki ce kin san daya daga cikinsu, duk ranar da
wuya ta koro ki! Ta shi ki bace mana da gani
shashasha sakarya. Ta mike da gudu ta fada
dakinta, ta dasa kukanta, a fusace abba ya bar
wajen kowa ya kama gabanmsa, suka cigaba da
yada xancan a sasan su. Daren nan su ma Umma
basuyi barci ba, musamman Umma da tabbatar
wa kanta ciwon xuciya ya kamata. Da safe ta
atashi xuru-xuru baki daya idanuwanta sun
xurma, shi kansa Abba ya rame ta maxa kawai
yakeyi yana wa Umma fada kar ta salwantar da
rayuwarta akan Mama. Ita Mama ba wannan ta
aje ranta ba, kawau burinta kasance tare da
Danliti, don haka take ganin kowa ya tsangwame
ta saboda kiyayya. Kafin safiya ma ta mance
duk kalaman su Abba da kawunninta. Allah Allah
takyi ta sami saukin laulayin safe dake damunta
ta lababa taje ta gano Danlitin ta. Xuwa 12noon
ta iya shiga kicin, ta dan tsiyayi ruwan lipton, ta
dawo ta shanye. Xufa ta keto mata, danji dadi
ajikinta, kana ta shiga bayi tayi wanka da
sabulun wanki maras kamshi. Ta kimtsa, tsaf,
duk da tayi haske sosai, ta kuma rame kwarai,
kana iya gane kyanta na asali mai daukar
hankali. Ta koma ta kwanta yana kllon agogo
1:00 ta tashi tayo alwala tayi sallah, ta dauko
gyalemnta ta xura takalma ta leko falo bataji
motsin kowa ba, ta kwahi sauri ta fice abinta.
Yara suna ce mata sai kin dawo aunty Mama!
Jin haka yasa Umma yanke sallah, ta fito da
sauri ta tambayi yaran ina maman? Sukace
yanxun ta fita. Tabi xauran, yaran suka biyota ta
tura su tace, ku kira min ita. Yara suka fice da
gudu suna kwala mata kira, Aunty Mama, ki zo
Umma na kira! Haka suke ta gudu suna fadi har
suka isketa, ta dube su tace, sai na ci ubanku in
kuna kwala min kira haka! Ni sa'ar kuce don
Ubanku? Ku tafi ku ban wuri kafin in fallawa
yaro mari! Mts..... Taja tsaki, ta wuce abinta,
yara suka dawo a guje suka iske Umma a xaure
sukace, wai sai ta ci ubanmu idan muka sake
kiranta! Ta dafe kirji tace, ta kyauta, kuje wasan
ku. Ta dawo cikin gida a salube tare da mamakin
taurin kai irin na Mama, me take nufi kenan? Ta
xauna a falo tana juyayi. Da kyar ta sake mikewa
ta shiga dakin Abba, ta tashe shi barcin ramakon
da yakeyi. Ya farka yana kallonta...... Yace,
azahar tayi ko? Tace tayi alhaji. Ya yankura ya
tashi yace menene na ganki a salube? Tace
tasake fita, wa? Mama mana. Cike da mamaki
yace ta fita? Yanxun nan kuwa, kamar fako na
takeyi, har yaran nasa su kirata, ta dinga
kunduma musu xagi, taki dawowa. Ita Maman ta
zage su? Tayi murmushin takaici, tace kana
mamaki ne? Bai kamata kayi ba alhji. Ta kuwa
tafi kenan, kinsa Allah ba zata dawo ckin gidan
nan ba. Kiyi hkr, duk abinda ke ranki na so da
kaunar Mama, ki cire ki dangana da ita, nima na
hkr da ita. Umma ta fasa kuka, ta tashi da
asauri ta bar dakin. Hankalin Abba ya kara
tashi, ya taso ya biyota dakinta, tana xaune
bakin gado kukan kawai takeyi. Ya tsaya kanta,
yace saboda Allah ya kike so nayi Halima? Ta
cira kai murya na rawa. Tace har ga Allah ba
korar Mama ke sanya ni kuka ba, tausayin
rayuwarta ke bani, yadda ta ka sa gane cewar
mu ba tsangwamarta mukeyi ba, saboda tana son
Danliti. Yanxun shikenan ba xata gane cewar
alabarkar mu itace kwanciyar hankalinta ba, duk
tsananin son da Danliti ke mata, shikenan ta
xabi cigaba da xaman shashanci akan ta nutsu,
dn tym kankani a daura masu aure? Wannan
rayuawar tana cike da tausayi da ban Mamaki,
kamar Ya asirce Mama? Ta kada kai ta ciga, ba
haka Mamar mu take ba alhji, ta sauya saboda
soyayya, kenan ta fi son shi a kanmu? Ina xan
samo amsoshin nan Alhji? Ina xan..... Ya rufe
bakin da sauri, ya ace ya isa haka! Kar ki jefa
kanki damuwar da xata tada miki ciwo, ki kauda
kanki ki akan komai, sannan ki nisanta xuciyarki
ga irin wadannan tambayoyin da kike wa kanki.
Xaki xautu saboda yarinyar da bata damu da
lfyarki ba, xamani ne Allah ya kawo mu da yara
ke rufe idanuwan su akan abinda suke so. Suyi
ta fada da iyeyensu har xuciyoyin iyayen su fara
xargin asirce su akayi. Xan ji dadi da farin ciki
idan xa'a ce, duk wannan abubuwan da suke
faruwa, ki dauke shi amatsayin mafarki mai
wucewa, tamkar baki taba haihuwar wata mai
suna sakeena ba. Ta dube shi xai yuwu ko? Mai
hana? Idan har zaki dage da adduoi, ubangiji ba
xai barki haka ba, ta goge hawayenta ta sauke
gwauran numfashi tace, xan yi iya kokarina Alhji.
Ya jinjina kai. Yace haka nafiso sadiya, kin san
ina jin dadin xama dake, kuma tun ina saurayi
ban taba son wat 'ya mace ba sai ke. Ban fatan
abinda xai salwantar min da rayuwarki, ya
kasance wata kaddara tasa kin fara barina cikin
duniyar nan. Kullum nayi sallah, sai na roki Allah
ya fara daukar raina saboda ba xan iya ganin
gawarki ba halima. Idanuwanta suka kara tara
hawaye. Tace ka daina fadar maganar nan
Alhji..... Ya katse ta, ni ma ba ason raina na fadi
ba, domin sirri nane wanda nake xaton shi kdai
ne ban taba gaya miki ba, sai yau, dole ce ta
sanyani, don ina son ki sami nutsuwa sadiya. Ta
matse ido kwallatana suka kwararo ya mika
hannu ya goge mata yace, sha kurkuminki
Maman abdul 3, gwarazan samarin nan masu
takama da baiwar Allah. Ta numfasa tace, Allah
yayi masu albarka baki dayansu. Kina nufin har
da sakeena ko? Ta amsa da kai, kafin tace, ai
mu na mata fatan shiriya ko? Yace haka ne, toh
Allah ya shiryta. Amin ta amsa. Haka yayi ta
rarrashinta, ta samu nutsuwa, sannan sukayi
sallah suma mika kukan su ga Allah. Na san
kilan kuyi musu ko mamaki idan nagaya muku
Mama bata dawo gida ba, sai bayan sallar
magriba. Abu na farko da ta fara cin karo da shi
a kofar sasansu dake kulle, shine akwatin
kayanta. Taja cak! Ta tsya ta xura masa ido
tsawon tym, kana ta matsa ta tura kofar taji ga,!
A kulle. Ta tabe baki tare da jan tsaki, ta figi
akwatin ta juya tana fadin a ranta, sai aga na
kwana a titi. Kai tsaye Danliti ta dosa, yana
xaune kofar shagonsa, inda ta basa. Yana
hangota da akwati, ya mike ya shige daga ciki
yana gayawa Ayuba ga mutuniyar can tafe da
akwati, ko maganarta tace ta tabbata? Ayuba ya
murtuke fuska yace ni xaka tambaya? Au haushi
kaji? Amma dai kana ji na gaya mata kar ta
kuskura ta bari su koreta, don bani da wurin
ajeta, ko ban gaya mata ba? Yace oho! Wai kai
wani irin banxa ne? Yace Ni banxa bane, ai
rainin wayau yasa ka gaya mata hakan. Wa ke
jan ragamar rayuawarta, in ba kai ba? Ai sanin
bata da xabi shi yasa ka raina mata hankali. To
ya isa malam, sai gata tsaye gaban kanta, tana
kokarin dagawa, duk suka xubo mata ido, ta
karasa shigowa, ido waje ya dubi shirgegen
akwatin, ya ce ya dai? Bata saurare shi ba, kofar
dakin ta tasarmawa xata shige. Yayi azama ya
shawo gabanta, magana fa nake yi, kona kokarin
shigewa kamar gidanku? Ta xubo masa ido a
marairaice tace, me na gaya maka? Ni kuma me
na gaya miki? To yaya xanyi? Ina komawa na
iske akwatina akofar gida sun kulle gidansu. Ya
gayara tsayuwa, da yake kuma ke sakarya ce sai
kaka kamo hanya kika taho baki tsaya kika nemi
sulhu ba! Yanxun menene nufinki? Anan xaki
xauna? Cikin shago? Lallai kin cika dakikiya,
Jaka! Kuka sosai ya kwace mata, ta tsugunna ta
rungumi kafafwansa, murya na rawa tana fadin,
karkayi min Haka Danliti! Saboda kai suka
koreni, ina kake so naje, idan ba nan ba?
BAKIN CIKI 2***15 Ayuba ya daga kanta, ya fice
hankalinsa tashe, shi kuwa ko gezau beji ba
ajikinsa, a dage yake kallonta, tsawan tym
sannan ya fizge kafarsa ya kama hanya xai fita,
da sauri ta mike ta cukuikuyo rigarsa, fadi take,
kayi hrk don girman Allah. Wasu samari 2 suka
iso wajen siyen taba sigari, ai sai suka buge da
shari'a, kaya-kaya hayaniya har waje Danliti na
daga murya shi ba xai aje ta cikin shagonwa ba,
ta koma ta nemi sulhu da iayeynta. Kan ka ce
kwabo jama'a sun cika makil a gun. Kai Mama
ta sha zagi da la'anta, Allah shi kara kwando-
kwando. Kalilan ke cewa Allah ya shiryeta, Dan
liti ya gacciye banci kofar shagoin ya xauna yace
yaga uban da ya tsaya mata agarin nan, wnada
xai sashi ya ajeta. Baiwar Allah kuwa na tsugene
gaban akwatinta, tana ruasar kuka har karfe
10pm. 'yan ganin kwakwaf suka gaji suka koma
gidajen su dauke da labari mai ban al'ajabi.
Wasu suna ganin bai kamata Uban dawaki ya
koreta ba a matsayin sa na Uba, kuma babban
mutum mai sarauta, wasu kuwa suna ganin
hakan shine daidai, imna xai sa BAKIN CIKI?
Idan bai sallame ta ba, tunda ta tara masa, ya
cika masa xuciya, tana neman fashewa ta
hallakashi? Ai gara da ya sallamata duniya ta
koya mata hankali. Ga darasi na farko nan ta
fara gani, duk iskancin Danlitim yace baxai aje
taba. Alhalin saboda shi aka koreta. Wannnan ya
nuna a fili ita ta nace masa kamar sauran 'yan
mata marasa xuciya. Mutane na mamaki abinda
Danliti yake da shi wanda yake tsonewa 'yan
Mata ido. Su mutu cikin soyayyar sa. In bata ga
kyau me yake da shi? Shi babu hali babu
kwakkwaran asali. Amma duk wacce ta fada
tarkonsa sai gagari iyayenta. Ko don kudi da ya
ke kashe mus ne? Shiya sa suka dauki laifi
kacokan suka dorawa 'yan Matan masu biye
masa don kwadayi da kyalekyalen jikinsa. Wayyi,
kai bai san dawan garin ba, dai bai yi tunanin
kutsa kansa ciki ba. Tun ciki dare surutai kala-
kala suka fara baza gari. Shi kuwa gogan da ya
ga kowa ya watse sai ya matso ya xunguri Mama
da kafa, ta dago kai da sauri ta dube shi, matso
mana nan kiji, ta matsa gareshi, tana hawaye.
Ya dubeta da kyau yace, ke banxa ce wlh, shi ya
sa kika bani haushi. Nace ba xaki xauna anan
ba. In banda hauka irin naki, ya xa'ayi ki xauna
tare da mu cikin shago? To ina sane da abinda
nakeyi, kin gane? Saboda haka ki koma ki nemi
wani wurin ki xauna, ki bani nan da sati xan san
abinyi. Murya dushe tace, ni bansan inda xani
ba, a'a ko gidan 'yanwanku ba xaki je ba? Ko
baku da su ne? Sai dai inje gidan su Baraka,
yace ko gidan su Mubarak xaki, sai kinm dawo
matsalar kice. Amma ba xaki kwana shagon nan
ba. Yauwa, tashi ki sungumi akwatinki, ki wace
kar su kulle gidansu. Tace to nagode, sai da
safe, Allah ya kaimu 'ya bebine. Muyi fada mu
shirya ko? Kar ki damu xan ganki goben. Tayi
murmushi, dadi ya rufeta, ta mike tana kara
masa godiya, taja akwatinta ta nufi gidansu
Baraka. Ya mike janye da benci yana kyalkyala
dariya, ya shige shago. Kai mugu dan gidan buzu
mai shayi! Yayi wa kansa kirari ya shige daki.
Ayuba na kallonsa yana kada kai. Gidan su Bara
akulle yake, saboda sha dayan dare tayi ma. Ta
shiga bugawa har aka xo aka bude mahaifin
Baraka ke tsaye cikin xauran, ya dubeta da kyau
yace, Mama ce? Daga ina haka? Ta fara kuka
yace shigo shigo ciki! Ta wuce da uban akwati
ya maida kofa ya rufe. Tana gaba yana biye da
ita yana fadin, subhanalillahi! Dakin Inna saude
suka shiga tana tsaye tsakar daki, lfya? Ta xube
sharaf! Cikin kuka tace, abba ne ya koreni.....
Ina saude ta nemi waje ta xauna, yayin da
malam kasim ke fadin, me ya sa Uban dawaki
xaiyi hak? Inna saude tace BAKIN CIKIN ta ne ya
ishesu. Ace kamar Mama ta gagari kowa duk
abinda ya sameta da abinda ake gaya mata ba
su isheta nadama ba, idan ba su koreta ba me
kike so suyi miki? Ba shashanci kike sha'awar yi
ba? To sun baki hanya, meye kuma na kuka?
Mal. Kasim yace hakan ba hujja bace, duk
abinda xatayi, gara tana gabansu suna tsawata
mata, yau da gobe ana hada mata da addu'a, sai
Allah ya taimaketa ta gane illar abinda take
aikatawa. Saboda haka ta xauna, gobe Allah ya
kaimu lfya, xanje in ganshi. Ke kuma je ki
kwanta kiyi tunani, meye amfanin lalata
rayuwarki da kikeyi? Har jikokinki sai an yi musu
gori, wannnan abinda kika aikata! Kina da
babban laifi mama, sai kin tuba kin bi Allah kin
bi iyayenki sannnan xaki ga daidai a rayuwarki,
kinji ni? Ta amsa da kai, yace ta shi ki shiga
wajen 'yar uwarji kafin Allah ya kaimu goben. Ta
mike simi-simi ta ja akwatinta, inna saude ta
xuba mata ido tana mamakinta. Ta kada kai,
taca baka ce xata aikata ba, yarinya kyakkyawa,
ta lalata rayuwarta. Allah ya shirya mana, yace
amin albarkar annabi. Atsakar gida taga Baraka
tsaye tana share hwaye, ta matso ta kama mata
akwatin suka shiga dakin, kowacce ta nemi wuri
ta xauna bakin katifa. Baraka ta dubeta.........
Tace anya mama abubuwa da kike yi kanki
kalau? Ke bakijin kinya? Baki tunanin gaba daya
idanuwan garin nan sun dawo bisa kanki? Baki
da martaba da darajar Abba agarin nan? Haba
Mama, kamar ba tare muka taso ba? Tarbiyarmu
iri daya, nutsuwa da kamun kai, kowa na yabon
mu. Mutane na rububin mu, da son hada xuri'a
tagari. Ta daga kai sama, idanuwa cike da
hawaye ta cigaba, Allah ya isa tsakaninmu da
Danliti! Ta dube ta sukayi ma juna xuru kafin
Mama tace kar ki sake xagin Danliti Baraka,
alhakin sa xai kamaki, laifin mune? Tun tym din
da mukace muna son juna, ya kamata su Abba
su rungume mu hannu 2 amma suka ki, suka
gwammace in kwashe kayana in bishi. A tunanin
ki wane sakamako ya kamata su gani? Bayan
wannan dake jikina? Baki sake take kallonta,
kafin tace, maganar Banza ce, idan duka jina
kunnuwa ne xai taba sauraronki ba, wa kika
burge don kin aikiata wannnan sakarcin? Shi
kansa Danlitin adage yke kallonki. Kin dawo an
yi miki afuwa, cikin nman ya bayyana, duk sun
hkr, sun shanye, amma ki ntsu xuwa tym din da
xaki haihu, a daura maki aure, kar fa ki manta
xaman nan naki agida ibadane tunda Allah ya
shifida hakan, sai ki ga dalilin xaman, duk
xunubunku sun kankare, auran ku yayi karko tare
da xuria masu albarka. Ki kwanta kiyi tunani
mama, ko asiri Dan liti yayi miki, xakewar taki
tayi yawa. Ta sualala kafita ta kwanta, tace, na
kwanta shekiya Baraka, sai da safe ko? Ta bita
da kallo ta numfasa, tace Allah ya sa ki gane.
Amin, ta amsa da gatse ta juya baya abinta.
Baraka ta mike ta rufe daki ta dawo ta kwnta. Ta
jima bata sami barci ba, saboda juyayin halin da
'yar uwarta ta shiga. Da farar safiya M.kasim ya
usa gidan Ubban dawaki yasa aka yi masa
sallama da shi, jin cewa shine ke sallam ya sa
yace ya shigo cikin gida. Bayan su gaisa. Umma
ta fito suka gaisa. Sannan ya maida jawabinsa, a
karshe yace, alhaji kar bacin rai yasa ka yanke
wannan hukunci, ni ina ganin gara yarinyar nan
ta xauna agaban ku, kuna tsawata mata, sai
Allah ya taimakemu ya shiryar da ita. Don
girman Allah ka yafe mata dawo gida, tunda tayi
tunani taxo wajenmu, ta kawo mana kukanta.
Abba ya gyara xama yace, a tunanin ka a kashin
kanta, ta yanke shawara taje wajen ku? To ba
haka xancen yake ba, kila ba xaka sani ba ne,
saboda kuan cikin lungu. Amma ni tun jiya na
sami labarin wulakancin da yaron nan yayi mata,
ya tara mata jama'a, ya tozarta ta, ya kuma ce
ba xata xauna masa a shago ba, kaji dalilin
nemanku, amma ba nadama tayi ba. Yace, duk
da haka ina son ka duba girman da martabar ka
agarin nan. Kayi hkri ka amshi rokona, ba don ni
ba, sai don girman Allah da darajar iyaye. Ya
sunkuar da kai yana kadawa, kafin yace,
M.kasim ban ki ta taka ba, amma ba xan iya
xama da yarinyar da ban isa in bata umarni ta bi
ba. Ta fita tayo shashancinta, ta dawo min gida
ta wanke najasa ta kwanta. Mts! Ban jin
idanuwana xa su iya jure gainin wannan kaxanta.
Gara ta tafu su cikashe. Wlh na hkr da ita, kuma
ina rokon Allah ya sanya mana dangani nida
Mahaifiyarta, ba kuma xamu gaza ba wajen yi
mata addu-ar shiriya. Watakila wata rana taga
uwar bari, ta dawo da kanta ta neme mu. Kaga a
tym din xan tabbatar da tayi nadama. M. Kasim
yayi shiru, jawabin Uban dawaki na cike da
tausayi, ya numfasa, yace, na yarda da kai Alh.
Sai dai har yanxun ina rokonka, da ka sake bata
dama ta karshe, mu gani.idan bata daina ba, to
muma sai mu tsame hannayen mu. M. Kasim ya
cikwa Abba ido kwarai da gaske, ya jima kafin
ya numfasa, yace, shikenan ba komai nagode.
Yace nima nagode, Hajiya akara hkr, a bata
damar karshe, tace babu komai M. Kasim, Allah
saka da alkhairi. Yace amin, barin in koma in
turo saude ta dawo ita. Tace to ka tsaya kaga
abin kari akawo maka mana, ya mike cike da
fara'a, yana fadin alhmdlh, kar ki damu nagode,
to nabr ku lfya, Allah ya shige mana gaba, suka
amsa amin. Yaka hanya fice. Bayan tafiyarsa
kamar da hadin baki, jama'a sukayi ta xuwa
suna ba uban dawaki hrk tare da rokonsa ya
daure ya maida 'yarda gabasa xai fi kyau
agareshi. A cikin su har da abokansa da yaron
gidansa, watau kalla. Duk ya karbi rokonsu,
kuma yaji dadin kulawar jama'a gareshi tare da
tausaya masa akan kaddarar da ta fada wa
iyalinsa. Karfe Tara saura, Inna saude ta taso
Mama xuwa gida. Bata ma biyo da ita ta shagon
Danliti ba, balle ya gansu, haka suka taru da
matan gidan kamar zasu cinye ta danya, sannan
matza suka shigo suka dasa nasu. A gaban kowa
suka tilasta, ta dauki alkawarin ba xata sake
xuwa ko ina ba, kidan kuwa ta saba, to a yanke
mata hkunci da yafi wannan. Kwana 2 hatsaniyar
nan ta kwnata, mama na xaune cikin gida bata
fita daidai da tsakar gidan sasansu. Muna iya
cewa Danliti bai murda kambunsa bane haka?
Saboda haka xuciyar Mama ta sami 'ya nutsuwa.
Bata ita kadai ba, su abba ma sun sami 'ya
nutsuwa har tana debo 'ya'yan itatuwan da Abba
ya ka siyo ta kawo mata, tace ta sha saboda
rashin cin abinci da take fama da shi.....
***************** A wannan asabar din ma
abdulkrm ya xo daiyalinsa duka. Su ameera nata
murnar ganin auntynsum domin sun jima basu
ganta ba. Dr. Na ta dabo, yana son ya taka, sai
'yar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login