Showing 36001 words to 39000 words out of 110841 words

Chapter 13 - BAKIN CIKI BOOK COMPLETE BY ESHAT.txt

12 Sep 2025

87

ba sai tsabar tunani.Muryar
mahaifiyarsa yaji a kansa tana fadin,"kai kuma
yaushe ka shigo garin?"Firgigi ya dube ta
na'am!"Ta zura masa ido,nace yaushe kazo?Ya
sauke gwauron numfashi yace,"zuwa na kenan
inna".ciwon daya sami mama,ai ya same ni
domin jinin mu daya......"Gafara can sakarai kai
ka san wannan,da su ma sun san cewa jinin ku
daya ba'a hana ka auranta ba ai sbda haka ban
ga dalilin dogon tunanin da kake yi ba,don daga
ita har iyayenta basu san ka na yi ba!Gara tun
wuri ka halkantu ka gane cewar alhakinku ne ya
kamasu!Idan ba haka ba,ina mama,ina danliti?
Marasa asali da tushe ga tarin abin gori da na
kunya a jikin sa?"Ya dafe goshi idanuwansa suka
kara kadawa,yayi hucin zafi ya dubeta,"duk
wannan maganar bata taso ba inna abinda nake
so ki gane shine muddin mutuncin mama ya
zube,to martabar gidan nan gaba daya ta
fadi,ashe kuwa dole in damu tnda nima dan
gidan nan ne,ga shi kuma mama ta dauko
hanyar bada mana kasa a ido. Tace can dai zata
badawa iyayenta masu kwadayi,ban sa aka ba
balle ya dameni wahalar banza kake yi dama
ruwa da abinci ka samu ka ci,daya fiye maka
wannan sakarcin!Ya sake dafe goshi yana kada
kai,me yasa innar sa baza ta gane ba?Takaici ya
kara kama shi ya sunkuci jakarsa ya koma
dakinsu.Haj Gaje ta shigo saboda gulma ta
cigaba,sharri kala kala suka yi ta jifar uban
dawaki da su.La'asar sakaliya abba ya dawo
gida ya iske idanuwan umma sun jirkita jajur!Ga
kumburi sun yi,ko bai tambaya ba ya tabbatar
akwai abinda ke damun ta,don haka ya kasa cin
abincin data kawo masa,ya zura mata ido yace
kamar akwai abinda ke damunki sadiya? Tace
akwai matsala alhaji amma ka ci abincin sai mu
san abin yi."Fuska ki ta bayyana tashin hankali
dake tare da ke ban jin abincin nan zai iya wuce
min ba tare da naji damuwae ki ba.Gaya min
uwargida,ni kadai gareki wanda zai saurari
kukan ki."Ta dan yi murmushi karfin hali tace
mama zata siyar da mutuncin mu a garin nan
gara ka dauketa ka maida minna ko abj ta zauna
can har zuwa lokacin bikinta."Gaban sa ya fadi
yace,me tayi?Bata daina zuwa shagon yaron nan
ba,yau ali da kan sa ya koro ta tana zaune bisa
benci suna hira,benci fa a kofar shagon bakin
titi?Kamar mama yadda muke a garin nan take
zama tare da danliti?Ta goge kwalla,ina zan sa
BAKIN CIKI Alh,anya kuwa mama ce ke aikata
wannan abu?Hankalin alh yayi mummunan tashi
ya fuskanci umma da kyau ya sanyaya murya
yace,ki daina zubda mata hawaye halima ke
mahaifyarta ce,sai abin ya kara wargaje
mata......" "Ba yin kai na bane alhaji,hawayen ke
tilasta wa kansa zubowa."Yace duk da haka ki
rinka daurewa kina mata addu'a,insha Allahu
gobe zan maidata minna ko ta ki ko ta so dole
ta zauna.Ni abinda ban gane ba shine,tana nufin
ta fasa auran Al-ameen ne?Idan wani abu yayi
mata ai sai tayi bayani,ba wai ta nemi ta maida
mutane sakarkaru ba!Ina take ne?"Tace tana
daki a kulle tun safe daya koro ta,haushi yasa
nayi mata duka har ynzu bata fito ba."Ya mike
cikin fushi ya nufi dakin ya buga da karfi yana
fadin,"tashi ki bude kofar nan!"Tana budewa ya
cafko hannunta ya jawo ta zuwa falonsa,hakan
ya sanya mama cigaba da tsiyayar hawaye,ya
cillata tsakar dakin ta zube gefen ummanta.Ya
zura mata ido yace,"ashe wani lokaci zai zo da
zamu ce ki bar abu ki ki bari mama?Kin dai san
maganara auren ki da al-ameen ko?To ynzu nake
so ki gaya min manufarki ta bin danliti
shagonsa.Gaya min inji tun kafin mu tara 'yan
kallo!Tayi kasa da kai kukan ta ya karu.Abba ya
daka mata tsawa,"kuka na tambaye ki? Ki gaya
min dalilin bin sakaran yaron nan nace?Ta
cigaba da share kwalla tana mutsu mutsun rashin
gaskia,leben ta na makyarkyata tace,"shi....shi
na ke......na..na...ke so ab...."Umma ce ra doke
ta da bayan hannu tace rufe mana baki mara
kunya!"Ta dubi abba dake tsaye sake da baki
tace,"ka ji ko?Ni na san take-taken ta kenan!"Ya
matso ya cafki kunnenta cikin tsawa yake
magana."Idan barci kike yi to ki farka ki bude
kunnuwanki da kyau ki saurare ni! Ni ba tsohon
banza bane,in har kin ga ki auri yaron
nan,tabbaci hakika ni uwaisu na mutu an binne
ni cikin kabari na! Ya girgiza kunnen kamar zai
tuge shi,kin ji ni! Wannan itace magana ta
karshe da zanyi akan danliti kuma gobe ki shirya
kayanki zan maida ki minna!"Ya shirga mata
dundu tare da fadin,"tashi ki bani wuri!Ai bata
iya tashi ba nan ta baje ruf da ciki sbda tsananin
zafin dundun da yayi mata abnda bata saba
ba,sai ta ji shi har cikin kayan cikinta sun dau
zafi ba kadan ba,Ta fasa kara mai shiga zuciya
tace wayyo Allah na shiga uku! Na shiga uku!
Yaya ali ya mike a firgice,gabansa ya yanke ya
fadi ya fito da sauri yana tsinkayar kukan
mama,ya nufi sasa.Umman ke fadin,'ba ki shiga
uku ba mama sai nan gaba muddin baki dauki
nashihar da muke yi miki ba!"Hannu biyu yaya
ali yasa ya ciccibe ta ya mikar da ita,zafin duka
da tsananin BAKIN CIKI dake dankare cikin ran
ta yasa ta kwakume.Yaya ali bakin gado ya
zaunar da ita ya dago fuskar ta hannu biyu yake
share hawayenta,yayin da nasa kwallan ke
neman sauka,yace "haba mama ki yiwa kan ki
fada mana!"Murya na rawa tace,me nayi masu
yaya ali!Sbda Allah me nayi?"Me kika yi? ynzu a
wajen ki wannan ba laifi bane?Haba mama!Ba
haka kike ba,kin sauya da yawa kar dadin bakin
danliti yasa hankalin ki ya gushe,laifin me al-
ameen yayi miki kike so ki yi masa wannan
sakayyar?A zato na koda babu Al-ameen nine
mutum na farko daya kamata ki fara kawowa ran
ki don na dade ina yawo da ciwon son ki
mama.Ki tausaya mana me zai sa ki canza
kyawawan halayen ki? Ya Girgiza kunnen kamar
zai tuge shi. Kin ji ni! Wannan itace maagana ta
karshe da xanyi akan Dan-liti, kuma gobe ki
shirya kayan ki, zan maida ki bani wuri. Ai bata
iya tashi ba, nan ta baje ruf da ciki, saboda
tsanannin xafin dundun da yayi mata. Abinda
bata saba ba, sai taji shi cikin kayan cikinta sun
dau xafi ba kadan ba. Ta fasa kara mai shiga
xuciya. Tace wayyo Allah na shiga uku! Na shiga
Uku! Yaya Ali ya mike a afirgice, gabansa ya
yanke ya fadi, ya fito da sauri yana tsinkayar
kukan mama, ya nufi sasan. Umma ke fadin baki
shiga uku ba Mama, sai nan gaba muddin baki
dauki nasihar da mukeyi ba miki ba! Hannu biyu
Ya Ali ya sa ya ciccibeta ya mikar da ita, xafin
duka da tsananin BAKIN CIKI da ke dankare cikin
ranta ya sa ta kwakume Ya Ali. Bakin gado ya
xaunar da ita ya dago fuskar ta hannu biyu yake
share hawayen ta, yayin da nasa kwallan ke
neman sauka. Yace, haba mama kiyi wa kanki
fada mna! Murya na rawa tace, me nayi musu Ya
Ali? Saboda Allah me na yi? Me kikayi? Yanxu a
wajenki wannan ba laifi bane? Haba mama! Ba
haka kike ba, kin sauya da yawa kar dadin bakin
Danliti ysa hankalinki ya gushe. Laifin me Al-
ameen yayi miki, kike son ki masa wannan
sakayyar? A xato na koda babu a alameen, ni ne
mutum na farko daya kamata ki fara dawowa
ranki, don na dade ina yawo da ciwon sonki
Mama, ki tausaya mana, zai sa ki canja
halayenki? Ta xuba masa kwala- kwalan
idanuwanta da suka kara fitowa waje jajur! Tace,
Yaya Ali ina ganin girman ka, ka kyale ni da
wadannan surutan, don ba xa suyi tasiri ba. Ni
nace ina so Al-ameen, yanxun kuma bana son
shi Danlilti nake so. Ra'aryi nane, ba sai a kyale
ni ba, ko akwai wanda zai zauna min da shi? Ya
bita da kallo, ta sa aya kafin yace, ki daina
tunanin wannan ra'ayin na ki mai yuwuwa ne,
kin dauko katon aikin da xai rushe martabar
gidan nan a idon jama'a. Idan baki son Al-
ameen, ki musanya da ni Mama, zai fi miki kyau
a bisa shirmen da kie sonyi. Ta runtse ido tace,
yaya Ali je ka kawai! Ba ki son gaskiyya? Ta
kauda kai kwalla na tsiyaya. Ya sanya murya
yace, xan bar ki ki kwanta kiyi tunani sosai,
cikin kan ki. Ina rokon ki girma da Allah, ki
manta da kudirin da kika dauko. Bata tanka ba,
haka bata dube shi ba yace, A bakin tofa ya
tsaya ya kare mata kallo kafin ya sake fadin,
bana so ana taba jikin ki mama, tamkar ni ake
tabawa nakeji. Pls ki sauya tunaninki. Haushi ya
kara kuma ta, ta juya masa baya. Ya fice yana
kara waigen ta. A daren nan daga ita har Yaya
Ali babu wanda ya iya cin abincin balle barci.
Tunanin Mama shine xata ga yadda za'ayi a raba
ta da garin nan. Cikn xuciyar ta tasha alwashin
ko sun maida ta, zata dawo, dole su gaji su
kyale ta da wanda take so. Dalilin da yasa ke
nan, yau kwata-kwata taki bude kofar ta, kowa
yayi bugu, iyayinsa har kawunninta, sai dai
kalaman bakin su suka kare. Amma mama taki
bude kofarta. Duk wanda ka duba ransa bace
yake, musamman Abba, fuska kamar gobara ya
dubi Umma yace, dauko min tabarya! Ta mike a
salube ta shiga kicin ta dauko masa tabarya, ta
mika masa. Alh basiru yayi caraf! Ya karba.
Yace karka balle kofar nan yaya, asara biyu
xa'ayi..... Yace yarinyar nan dole ta bar garin
nan, ba xata xauna tana jawo min xagi ba, ana
kallo na tsahon banza, bansan abinda nake yi
ba! Buge min kofar nan, ko ka ba ni da kaina, in
sauketa! Kowa yayi cirko-cirko. Alh. Basiru ya
kai wa kofa duka da tabarya, sai ga sallamar
Yaya abdul- kareem. Basu gama amswa ba, yaci
gaba da tambaya, lfya? Me ya faru da kofar?
Abba yace, nayi farin cikin xuwanka, don ni ma a
yau nayi niyyar tafiya gunka. Me ya faru abba?
Umma ya naga kamar kina kuka? Yace, mama
ce.... Me ya sameta? Ya kwashe kaf halin da
suke ciki ya gaya masa. Kai! Bai gaskanta
kunnuwansa ba, shi yasa yace, abba ban yarda
da wannan maganar ba, ya kamata asake
bincikawa. Abba ya xuba masa ido jajur! Yace,
wannan maganar ni Uwaisu nake gaya maka ita.
Abdul kareem kasan kuwa ba za ayiwa mama
kage ba, domin ni na haifeta. Saboda haka gidan
ka xata xauna can har xuwa lokacin bikinta!
Yace, ya xama wajibi, don ganin nan da kuka yi
min xuwa nayi in tafi da ita dama. Al'ameen ya
damu kwarai har yana ganin kamar wani abu ne
ya faru da ita ake boye masa. Wlh jiya ya turo
mahaifiyarsa da yamma wai ta zo ta bincika
masa lfiyar mama, shine nace shi kwantar da
hankalinsu Insha Allah da kaina xanje in dawo
da ita. Wannan al'amari ya daure min kai.
Yaushe mama ta canza haka? Kawu Basiru yave
xancan banza takeyi, tunda ita ta kawo Al'ameen
har aka sanya musu rana, bata isa tace ta canza
shi ba! Wannan karya take yi. Haushi ya kara
kure yayanta, ya mike ya suer tabarya ya kaiwwa
kofar duka sau biyu kofar ta balle, bata a dakin.
Ya nufi kofar bayi ya murda can ma garkamen
yake, bai tsaya wata-wata ba, ya maka mata
tabarya. Bugu daya kofar ta wangem, sai ga
mama jikin bango ta fita hayyacinta saboda
tsabar kuka. Al'amarin tamakar mafarki yayana
yake gani. Ya xura mata ido, yace hauka kikayi
mama! Me Al-ameem yayi miki? Iye? Yayi miki
laifi ne da ba zaki fada ba! Sannan ki rasa
wanda zaki bi, sai dan liti! Kinji abinda nace?
Kin yi karya ki xuabar mana da mutunci a garin
nan! Zo mu wuce, ban son jin komai daga gareki!
Ta sulale kasa hannaye biyu bisa kanta, ta kara
fasa kuka mai tsananin gaske. Matan gidan suka
kutso kai cikin bayain suka tarairayo ta, suka
fito da ita dakin. Yaya yana fadin ko mutuwa
zakiyi yau, sai na tafi dake mu je can idan Al-
ameen ya kira waya, in tambayehsi a gabanki,
muji abinda ya hadaku! Amma yaro na sonki
yana tattalinki. Iyayeynsa na ririta ki, tashi guda
kice ba kiyi da shi, aikin san wannan karya
kikeyi. Ina kayan ta suke umma? Hada mata si
don baxan bata lokaci ba! Gaba daya suka
yanyame ta da fada kowa na fadin albarkacin
bakinsa, su Umma na hada mata kaya. Su
Hajiya Hajjo na rarrashi ta suna bata baki tare
da gyara mata jiki da fuska. Yaya Ali kuwa yana
xaune gefe rayuwa tayi masa bakikkirin! Ana
janta, tana togewa suka saka ta gabn motar
yayanta. Ya jefa jakar ta gidan baya, daga nan
yayi sallama ransa bace, ya ja motar yayi gaba
da mama. Dole ne ya saurar daidai shagon
Danliti, domin akan mahada shagon yake.
Tsayuwar su wajen, ya jawo hankalin Danliti
xuwa garesu. Ya xuba wa Mama idanuwan sa
suka sha kwalli rangadau! Haka ita take kallonsa
kwalla fal! Suna neman sauka. Ya daga kanka ta
fito kofar shagon, irin duban da yake mata ya
bayyanar da damuwarsa karara bisa fuskarsa.
Tausayinsa ya lullubeta, nan da nan hawayen
suka fara bulbula. Yayanta bai kula ba, kokarin
sa, duk motocin da suka kawo, suka wuce shima
ya samu ya haura. Yawanci duk manyan motoci
ne, kamar yadda akansan babban titi ne, wanda
ya mike ya tafi har lagos. Suna tsagaitawa ya
cilla tasa motar ba tare da ya fahimci Danliti da
mama sun ruga sun gama magana da
idanuwansu ba. Kawai ji yayi ta kara gocewa da
kuka mai karfi. Ya dan dubeta, ya kada kai.
Yace, Al'amarin ki na bani mamaki, look kina
jina? Saurare ni muyi magana ta fahimta. In
tambayeki xaki bani amsa? Hankalinta sam ba
awajen sa yake ba, balle ta saurare shi. Fuskar
Danliti take gani, irin yadda ya shifa damuwa
yana neman xubar da hawayensa, shi ya kara
dagula mata lissafinta. Yace, saboda Allah zaki
gaya min Al- ameen yayi miki da zaki juya masa
baya? Tayi shiru, danliti na cigaba da yawo a
idonta. Yace, kin kuwa san tun ranar da kika
dawo garin nan. Al-ameen ya rasa nutsuwarsa?
Ban iya kirga yawon wayoyinsa ba, tunaninsa
kina cikin wani matsanancin hali ne aka boye
masa. Kar ki saki reshe ki kama ganye Mama,
domin kowa yasan Danliti lalata rayuwar ki
kawai zai yi, ya kai ki ya baro ki tashar
danasani. Ki ga ya min idan Al- ameen yayi miki
laifi ne, ni da kaina xan masa magana in ja
masa kunne. Kinji? Bai yi aune ba yaga ta balle
murfin motar ta dire waje. Ta mulmula cikin
ciyayi. Cikn tashin hankali ya take birki.... Allah
yasa ba babu mota a bayansa, yayi fakin gefen
titi, ya fito. Can ya hange ta tana kokarin tashi,
amma ta kasa, kafin ya gangara wajen 'yan
tsirarrun jama'ar wajen sunyi caa! Kanta. Suka
ciccibota, suna sallalami tare da mamakin yadda
aka yi abin ya faru. Gaba daya gwiwowin ta
sunyi mugun kurjewa ta xura da gudu amma bata
je ko'ina ba mutane suka cafke masa ita. BAKIN
CIKI yasa ya dauke da wani mahaukacin mari
daya tilasta mata xubewa kasa. Wani dan dattijo
cikinsu ya kama shi. Yace, haba malam yaya
haka kuma? Baka ganin kaddarar da ta sameta?
Da ta mutu fa? Ku rinka kulawa da murafen mota
mana don gudun irin hakan! Idanuwan sa ajuye
yake magana, kyaleni da yarinyar nan baba! Da
kanta ta bude murfin ta fito! Iskanci ne kawai,
dama kin mutu, mu huta da wannan BAKIN
CIKIN da kike son jefa mu! Saboda haka xan
koma in gayawa abba kin bude mota ki diro, ni
kuma ba xan tafi dake ba, ki xauna kiyi duk
abinda kika ga dama agarin nan, tunda lalacewa
kika xaba. Allah ya shirye ki! Ya shura
takalmansa ya koma mota ya tayar yayi kwana
ya koma gida ya bar Mama anan tana faman
kuka, jama'ar dake wajen suna mamakin wannan
abu har sun kasa fassara shi. Dan dattijon nan
shi ya riko ta hankali suna tafe tana bashi
labarin wai auran dole ake son yi mata. Kwarai
kansa ya daure jin cewar ita 'yar gidan Uban
dawaki ce, don haka ya tasa ta har gidan. Amma
me? Suna xuwa kofar shagon Danliti ta xarce can
tayi xamanta bisa benci. Dan liti ya fito aguje da
ayuba, mamaki ya rufe ayuba, shi kuwa dan
gogan munafuncin ne yasa gaba, sai yazo ya
narke a gabanta. Yace, saboda me sakina,
kinaso ki rasa ranki ne? Tace gara in mutu da su
raba ni da kai, ya dubi Ayuba a gigice. Yace,
kawo min mukullin mota ayuba! Ya shige shagon
da surinsa, shi kuma ya juyo gunta ya marairaice
yake fadin, aure na Allah ne sakeena, ina so ki
yarda da wannan. Duk iya son da muke juna idan
Allah bai nufi auran mu ba, babu yadda xamuyi.
Don me xaki nemi halaka kanki? Bata bashi
amsa ba. Ayuba ya mika masa mukulan. Bai jira
tace wani abu ba, ya kamo hanninta taso muje
asibiti asa miki magani. Dattijon nan ya bisu da
kallo, duk tausayi ya rufeshi. Rashin sani kenan,
ya fi dare duhu, domin shi gani yake irin haka ke
jefa yara yawon banza..
BAKIN CIKI 2***3 (TRUE LIFE STORY) Wasu
iyayeyn na da ra'ayin rikau, idan kuma ka
bibibya kwadayi ne, wata kila wancan yafi
wannan kudi ne? Sai dai kuma ai uban dawaki
mutumin kwarai ne, me xai sa ya aikata haka
akan yarsa? Duk da cewar dan dattijon nan
talaka ne, ya doshi gidan uban dawaki, don ya
bashi shawara. Fuskar Umma a sharkaf da
hawaye take muryar ta har rawa takeyi, bai
kamata ka baro ta can ba abdul... Yaya xanyi
umma? Kona cusata cikin, sake fitowa xatayi.
Mama ba zata mutu a hannu na ba, umma ta tafi
inda take son xuwa, kanta tayi mawa. Fatana
kwai Allah ya yaye mata abinda ke damunta.
Kuyi hkr ku kyaleta anan domin ina mai tabbatar
muku xata xauna can ba dawowa xatayi ba.
BAKIN CIKI ya hana abba magana, sai A. Adamu
ya iya fadin, gaskiya, gara ta xauna a cigaba da
yi mata nasiha watakila a dace. Kuyi hkr Yaya
mu dauki wannan a matsayi kaddara. Kai abdul
idan ka koma Al-ameen ya kira ka kwantar masa
da hankali ka... In ce masa me kawu? Gaskiyya
xan gaya masa shi ma ya hkr da ita tunda ba ita
kadai bace 'ya mace. Allah xai bashi wata. Ko
kuwa? Abba ya dube shi, sai yanxun ya iya cewa,
karka gaya masa haka abdul, da yardar Allah sai
inda karfina ya kare akan mama. Indai ni na
haifeta kuma ni ne xan daura mata aure Insha
Allahu shine xai aureta. Kawai ka bashi hkr kayi
masa wannan bayanin da naga ya maka yanxun.
Ya dafe goshi yayi huci zafi kafin ya dubi
Umma. Yace ki share hawayenki, umma ki yi
mata addu'a Allah ya shiryata. Ni xan koma sai
yadda ta kama. Basu amsa ba, ya mike kawu
Basir da Adamu suka yo masa rakiya kuma suna
gaya masa kalaman da suka dace ya gayawa Al-
ameen. Da dan dattijon nan sukayi kicibis yana
sallam cikin xaure suka amsa nan take. Yace
baka shaida ni ba ko yaro? Nine wanda yaga
lokacin da yarinyar gidan nan ta bude murfin
mota ta fito, tayi min bayani ita 'yar mai girma
Uban dawaki ce, shine nace ai mai martaba yana
da saukin kai xan xo in bashi shawara game da
auran dole, yayan ya dube shi da kyau. Yace
hakan ta gaya maka? Yace, kwarai hakan ta
fada. Yace to tayi maka karya, kawu ka na iya yi
masa bayani, don na tabbata abba baxai iya
fitowa ba ahalin da yake ciki. Alh. Basiru yace
yanxun ina take? Yace tana can ta tsaya wani
shago har sun tafi, zai kaita asibiti. Suka dubi
juna, yaya yace, kunji ko? Mama ta tafi, bata jin
kira saidai addu'ar Allah ya shiryata. Ni na tafi.
Ya fice ya barsu nan tsaye. Alh. Basiru ya dubi
tsoho yace mun gode baba, amma kayi hkr,
bazaka ji komai daga gareni ba, saboda ban
sami izinin yin hakan ba. Maganata gaskiyya da
nake so ka gane shine karya yarinyar ke maka,
tare da shegantaka irin ta yaran yanxun. Mun
gode da kulawarka. Tsoho yace,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login