Showing 42001 words to 45000 words out of 110841 words
addu'a
yana tafe addu'a, haka acikin aji, hankalinsa
yafi rinjayea ga addu'o'in da yakewa mama cikin
ransa. 12pm washegari lokacin ne motar Mami
ke fakin kofar gidan Uban dawaki. Yayin da
mama ke kwance rankas ciwon jiki, sakamakon
fadowar da tayi daga mota. Can da nan bata iya
motsawa, Baraka ke tare da ita tana zazzaga
mata nasihohi, duk da ta san bata sauraron ta,
sai dai ya zama wajibi gareta, ta kara gaya mata
gaskiyya. Mami tayo sallama falon ta shigo,
gaban Umma ya yanke ya fadi. Ta amsa tana
fitowa daga dakinta. Yake baki kawai takeyi,
amma zuciyarta ta shake take da takaici tare da
BAKIN CIKI mai tarin yawa. Ga wata kunya da ta
yo wa idanuwanta dirar mikiya, mai alaka da
ciwon dundumi. Sannu da xuwa Hajiya! Ta amsa
mata da fara'ar karfin hali. Ta nuna mata kujera
ta xauna, tana kara yi mata sannu da xuwa.
Sannan ta debo mata abubuwan sanyi masu
ruwa. Ruwan ta fara xuba mata, ta mika mata ta
sha. Suka gaisa cikin girmama juna. Ta kara
gyara xama, tace, sai kika ganni da rana tsaka
ko? Fuska kunshe da tashin hankali. Tace ke dai
bari, nasan kin sami sako maras dadin ji. Ta
kada kai dauke da damuwa. Tace naji sakon da
ya hani barci jiya, wanda ya sanya ni rama kafin
safiya. Ina jajantawa shi kansa Al-ameen da ya
sallama rayuwarsa kaf kan sakeena. Nayi kuka
da wadannan idanuwan nawa, don na tabbatar da
amsata ba alkhairi bace a gareni, domin komai
zai iya faruwa ga tilon da na, farin ciki na kuma
sanyi idona. Shi ya sa nace xama bai ganni ba,
tilas inxo in rarrashi sakeena, ta tausaya min kar
in rasa Al-ameen. Wadannan kalami sosai suka
sanya hawayen Umma suka tsinke nan take, ta
rasa me zata ce wa Mami ta sanyaya mata rai?
Dole tayi kuma domin dai bata da kwakkwarar
mafada, mama na nan akan bakanta babu sauyi.
Da kunnunwata ta, taji lokacin da take gaywa
Baraka tabbas zata iya kashe kanta, saboda
Danliti. Mami ta cigaba da fadin ki daina kuka
Hajiya, Baban ameer ya gaya min tashin
hankalin da kuke ciki, kukan bashi da
alfanu.......
HAUSA
BAKIN CIKI 2***4(TRUE LIFE STORY) umma ta
hare kwalla ta katse ta Tabbas mama bata da
lafia ciwon daya kamata mai tsanani ne maganin
Allah, dole kuwa in yi kuka , don mama ta dasa
mana BAKIN CIKIN da ban taba tunani ko
mafarkin irinsa ba daga ni har Abban ta mu na
cikin rudu tare da mamakin yadda wannan
alamari ya kasanze haka, hakuri zakuyi hajia
sannan ku taya mu addua mama kam ko ta so
ko taki doke ta auri Alamin, tunda zabin ta ne na
farko bamu muka cusa mata shi ba. Hasali ma
bamu san lokacin da suka hadu ba. tsabat rashin
kunya ce irin t yayan zamani da rashin sanin
mutuncin mutane. saboda. haja hajia karki damu
kuma dabarar da kikayi wa alamin tayi daidai
sai dai akwai sauran rina akaba domin fadar
kalmar ciwon ma ba zai bar shi yayi sukuni ba.
Tace zaifi sauki akan a gaya masa gaskiar
magana ni na dauki dawainiyar kwantar masa da
hankali kullun ya kira waya. Tace to shikenan
Allah yasa mu dace ta ce ina sakinar take mu
gaisa Ta mike tana fadin Taso muje in kaiki
kwance ma take bata iya tashi. Ah me ya faru?
ina fatan ba dukanta kukayi ba, ta ce Baban
Amira bai gaya maki bude mota tayi ta diro kasa
ba? ido waje ta dafe kirji ta diro daga mota?
tace ya wuce wai! zo muje ki ganta ta tashi
dauke da mamakin tana fadin naga abinda ya
ishe ni ni yasu, sakina da gaske take bata son
Alamin. suka cusa kai dakin, baraka dake zaune
bakin gado ta mike tana gaishe su. umma ta
nuna wa mami wurin zama a bakin gadon tace
zauyna hajia kinga idanuwan maras kunya ta
juya kan mama taci gaba ga hajia nan tazo da
kanta inkinga dama ki bude ido ta kudundune
kai cikin pilli mami ta dube su tace ku bamu
wuri hajia ita baraka suka bar dakin mami ta
karasa matsowa tasa hannu ta birkito ta kuka
taga tanayi tasa hannu biyu ta tallafo kuncin ta
ta sanyaya murya tace sakina dan dubeni kinji?
ta dago idanuwa jajur ta dube ta hawaye suka
wuce bisa kuncinta. mami ta kara goge su . ta ce
na san ba'a siyan so mama da yau nayi cinikin
sa ko nawa ne na siya wa alamin, koda zai
kasance zani daya zai rage min a fadin duniya.
amma kash hakan ba zai taba yuwuwa ba, sai
nayi imanin ko dan yaya ne kin san mahimamcin
rike alqawari me yasa kika dauki alqawarin da
ba zaki iya cikawa ba? me yasa kika yaudari shi
kika bari tsananin son ki ya zauna a zuciyarsa?
kina so ki kashe shi ne sakina? ki tausaya min
ana gaya masa sakon nan zuciyar sa zata iya
bugawa ya mutu mama. shi kenan na rasa shi
kuma ban da wani alamin na sonki mama sai dai
ayi zancen dan adam ssaboda haka ki gaya mani
abubuwan da yake miki wadanda baki so har
suka sanya ki tunanin fasa aurensa. wallahi nayi
maki alqawarin zan masa fada tare da lallashi in
kuma. gargade shi kinji? gaya man matsalarki da
alamin. hawaye suka ci gaba da ambaliya bisa
fuskar mama domin ko sunan alamin bata son
ana ambatowa tsawon lokaci bata tanka ba sai
kwarara ruwan idonta kamar zai kare mami ta
sake fadin da alama alamin dai bai maki komai
ba sakina tsuntsun son sa ne kawai ya tashi
daga kansa ya koma wa wani ko? ta kara aje ido
kasa mami tai wawan ajiyar zuciya idanuwanta
suka kawo kwalla baki man halacci ba sakina a
iya tunani na mutuwa ce kawai zata raba ki da
alamin shi yasa gaba dayan mu muka dora burin
mu a kanki. bamu da wami buri face Allah ya
nuna mana ranar da zki zama mata danmu sai
gashi dare daya kin juya mana baya. A tunani ki
kinyi daidai? baki gudun kar amana ta ci ki
sakina? kiyi tinani cikin natsuwa duk wanda ya
ha'inci wani Allah ba zai kyale shi ba. zan barki
kiyi tunani kan magana ta. idan kin canza ra'ayi
ki koma minna zuwa gobe Alamin yaji ki
hankalinsa ya kwanta kinji? yace in gaishe ki
kuma yace inyi maki addu'a. Ta taimaka mata ta
kwanta a hankali idanuwanta rufe suke yayin da
mami ta dafa kanta tayi mata addu'oi da alamin
yace tayi sannan ta kirata ta bude ido. nizan
koma sai najiki a minna karki bari shaidan ya
rinjayeki ki bar mai tsananin sonki cikin kunan
zuciya nakasa zaiyi kinji? ta lumshe idon a natse
mami ta wuce ta bar dakin umma ta shiga tare
da sallama ta nemi wuri ta zauna yayin da
baraka ta fice. ta basu wuri ta saurareki? tace
to! bata dai tanka ba sai kuka da zan fito. ma
nayi mata addua' kallo na ta dinga yi. da alamun
za'a dace tace kwarai da gaske bari in lallaba
hajia zan shiga wajen gwaggo sannan mu wuce .
to a gaishe ta da kyau Allah ya kiyaye hanya
Suka wuce suna fadin"Amin"har kofar gida tayi
mata rakiya,motarsu ta daga ita kuma ta dawo
gida dakin mama a koma suka taru da baraka
suka ci gaba da yi mata nasihohi tana
kudundune bata tanka ba,balle su gane me take
nufi,Awa guda bayan tafiya mami yaya. Abdul-
kadeer ya iso gidan daidai lokacin kuwa Abba ya
dawo gidan,yayan tare yake da dakarun sojoji
guda uku,duk suka fito,suka toge suna sarawa
abba,sannan suka gaishe shi tare da yayan suka
rankayo yana ruwan masifa, maganar banza
yarinyar nan take yi,mu makace ta kawo shi ko
mu muka hadasu wannan ai iskanci ne yanzun
nan zan wuce da ita shiya na dauko kuratan nan
su yi min gadinta a mota na ga ta inda zata
fito,Nonsense kawai" Abba yace kayi daidai
domin ni mama ta ginsheni ko ganinta bana
sonyi cikin gidan nan,saboda "BAKIN CIKI",abu
kamar al'mara yana so ya zama gaske yarinya
ta bamu kunya ta zubar mana da mutunci basu
ma san sun shigo falon ba sai da umma tace
maraba da babban yaya yace sannu umma
bamuyi sallama ba ko?raina bace yake ina
mama?tana daki ina fatan tafiya kazo yi da ita
sosai kuwa umma akwai kurata uku nazo dasu
wadanda zasu gyara mata zama muddin tayi
yunkurin bata mana lokaci tace yayi kyau wallhi
yanzu ma hajiyar al-amin ta bar gidan nan
bakaga uwar kunyar da ta lullubeniba na rasa
inda zansa kaina Abba yace tazo kikace"tana ma
cikin garin nan bata wuce ba"Abba ya nemi waje
ya zauna ya kama kai,shi kuwa yaya babba
dakin ya nufa kina jina baza ki fito ba"umma
tace da wace kafar zata fito bayan ta kusan
kashe kanta,yace kadan ta gani amma yau sai
kin bar garin nan ko za ki mutu!Useless girl!kina
nufin ki zubar mana da mutunci ko,baki. Kai
wannan matsayinba,I swear,kin ji na rantse"yasa
hannu ya fisgo ta da karfin sa yana fadin"stand
up my friend"ta tsandara kara mai garfin gaske
saboda gaba gabobain ta suka amsa suka kaiwa
kwakwalwar ta zuwa falon dole gabobin suka
loma aiki ashe dama wuri suka samu. Ya
dankwafar da ita bisa kujera tace wayyo na shiga
uku yace"No lokacin bai zoba tukuna sai kin ci
gaba da bijire wasu umma I'am telling you! yau
abuja zamu wuce ki zauna can, sai lazy doktan
ki ya dawo ai ke ki ka zabe shi tun farko so now
you have no reason ki ce kin fasa bayan kun
kusa aure ya dubi umma yaci gaba karki ji
tausayinta ta umma ki fidda ta a ranki har sai
tayi biyayya a gareku, Ta kada kai tace tuni
mama ta fice min a rai balle tausayinta ko alama
babashi cikin raina ka tafi da ita duk abinda ya
dace kuyi mata don ta gane kuskuranta yace
wannan dole ne Abba bari mu wuce umma ta
fara magana bari in hado mata kaya yayin da
abba da babban yaya kamar zasu cinye mama a
falo kuka take tamkar za a zare mata rayuwa
umma ta fito da jakar kayan ta wurga mata gyale
bisa jiki,yaya soja ya mike tashi karki bata min
lokaci taki mikewa yasa hannu ya maketa
sannan ya cafko. ta yana fadin zan iya karya ki
u know dat! gara ki shiga hankalinki bai sake
taba har kofar gida ita kuwa umma cikin sasa ta
shiga ta gayo masu za a wuce da mama don
haka suka yo waje ganin yadda za a yi saboda
suji dadin karaars wa. A gaban su ya cilla wa
kuratan daya zo da su ya ce kusa min ita a
mota! kan kace kwabo mama na cikin mota,
suka sanya ta tsakiya yayanta na gaba sanda ya
jefa jakarta a but yaya ya juya da sauri ya zauna
matsayin driver babu bata lokaci ya murza
mukulli mota ta tashi ya bar wajen, idanuwan
baraka suka cika da kwalla nan da nan ta fasa
kuka ta koma cikin gida da gudu. sauran matan
na ta fadin Allah ya kiyaye hanya ubangiji yasa
a dace. umma ta juya ta shiga gida su suka biyo
bayanta . ganin hankalin umma yayi mummunan
tashi yasa hajia gaje ta janye hajia hajo cikin
gida ta mika hannu suka tafa sannan ta tallafe
haba ido waje tace Ashe abin har ya girman
haka? wanan sojoji kamar an zo kama
gagararren barawo? ta ce ai kamar hakan ne
tunda ta gagari iyayenta. zamuga ikon Allah
yarinya na neman tayi wa iyayenta bakin cikin
daula, sun ga samu zasu ga rashi ai kinga haj
halima kamar ranta zai fita sai kace dole suka
sake tafawa haj hajo tace Hakki ne nake gaya
miki kadan ma suka gani badai danliti ta jajibo
masu ba? Allah dai ya kiyaye lalacewa! ta tabe
baki Nayaushe kuma? wai ance wa kuturu Allah
ya laance ka! shagonsa fa take zuwa tsinancewa
ai ba sai an tambaya ba! hajia hajo tace Allah
shi kyauta haj gaje ta amsa na gaba domin dai
wannan ya riga ya faru anyi abin kunya maga
yadda za ayi! sun jima suna yada labaran banza
da karairayi kai duniya ina zaki da mu? rayuwa
kenan uban dawaki da umma suna kallon ikon
Allah suna fama da BAKIN CIKI sai fatan Allah
ya musanya masu alkhairi Mama kuwa tun
isowarsu Abuja take kudundune cikin daki duk
hargagin yaya soja baisa ta dauki lomar abinci
tasa wa bakinta ba,al'amari ya daure wa anti
amina kai ta zauna ta siga yayyafa mata
nasihohi da rarrashi ko Allah yasa ta gane amma
ina Alla bai nufa ba tukuna shi kuwa soja babu
abinda ya dame shi cewa yayi zai fi kyau da
zata bari yunwa ta kasheta a yau hakan kuma
shi zai tabbatar masa ta cika mai kunnen
kashi,yasa kai ya bar gidan amma kuratan
sojojinsa na nan tsare da gidan bayan masu gadi
mutun biyu ke nan yanzu sun zama su
biyar,kafin yamma mama taci kukan daya fidda
ta daga hayyacinta bama ta jin tarin yunwar da
ke cikin ta saboda tsananin tashin hankalin da
take ciki domin ita kanta ta san ta shigo kurkuku
zai yi wuya ta kara ganin dan liti sai dai tunanin
ta bai yanke ba duk tsananin da zata shiga baza
ta taba auren wani ba dan liti ba.
BAKIN CIKI 2***5(TRUE LIFE STORY) Saboda
haka taci gaba da zama cikin kunci da yunwa
har bayan sallar isha'I yayanta ya shigo gida
kamar shi alamin ke kira wayar sa ta hau
bugawa falon kai tsaye kan wayar ya nufa ya
dauka yayain da malami ya sheko da gudu don
yi masa oyoyo.anti Amina ta biyo bayansa daga
jin muryar al'ameen kasa yana cikin farin ciki da
doki cike da zuciyarsa ina yini yaya,yace lazy
dokta ya karatu?"Yana yar dariya ya amsa
Alhamdulillahi ai na kira can minna don in
tambayi jikin mutunniyar sai aka ce min ta sami
sauki harma ka taho da ita, yace haka ne amma
kasan yana yin rashin lafiyar sai a hankali cikin
dan kankanin lokaci sai ta birkice bari in turo
maka ita,koda kaji sauyi daga gare ta kar ka
damu haka yanayinta ya sauya,jikin sa yayi
mugun sanyi duk a lokaci guda gabansa ya ci
gaba da faduwa murya dishe yace to yaya Allah
dai ya bata lfy,ya amsa da amin ya aje kan
wayar gefe ya amsa gaisuwar iyalinsa sannan ya
haye sama ya fada dakin mama yana shiga ta
kara kudundinewa cikin bargo yasa hannu ya
kwashe bargon ya watsar gefr yace tashi zaune
sai ga antin ta shigo ta matsa bisa shimfidar ta
birkito ta tana fadin yi mata a hankali ke mama
tashi kinji! Ta ciccibo ta ta tashi zaune kamar
wacce ta shekara tana ciwo saboda tsabar fita
hayyacin da tayi Tausayi ya lullube antyn a
hankali tace kinaji na? Ga alamin cen ya kira
waya don Allah ki fidda mu kunya ki tashi ki je
ki saurare shi badon mu ba sai don girman
Alkawarin da kika daukar masa kafin ya tafi
tashi kije kudinsa na bin iska kinji? Tamkar
antyn na magana da dutse don ko motsi batayi
ba sai idanuwa ta ke ambaliyar ruwan hawaye .
Haushi da takaici suka rufe yayanta ya daka
mata tsawa mai tsanani sai ta zabura bazaki
tashi ba? Alamarin ya kara kure su cikin
mamaki sukaji wannan kalmar ta fito bakinta
Nifa yaya ba zanyi magana da kowa ba Gaba
daya suka ware ido baki sake sai dai shi soja
baya tsayawa yana kallon raini don haka ya cira
hannu ya tsnke ta da wawan marin da yayi
sanadiyyar daukewar numfashinta karkaf,ta zube
sumammiya ya nuna cikin zafi yace ni zakiyi wa
rashin kunya ba na wasa da ke ni zan iya karya
ki wallhy anti amina da tuni take kwasar salati
tace ai maganar karyawa ta kare tafa suma
yallabai yanzu me za a cewa Al'ameen din Yace
ta mutu ni tayiwa rashin kunya bata isa ba
wallahi!Mtsw"ya ja dogon tsaki ya bar dakin
falon ya sauka ya dauki kan wayar ya kanga wa
kunnensa hello al'ameen naji na ya amsa ina
kinka yaya yace kayi hakuri da mama al'ameen
ya katse shi me ya faru yaya ina take yace ta
suma al'ameen kayi hakuri da ita domin mama
ta riga ta sami matsala....". Ya sauke salati ya
katse shi yaya bazan iya hakura da sakeena ba
kowane irin hali ta shi ina son ta haka koda
kuwa ciwon hauka ne ya kamata,Roko na gare
ku shine ku taimake ni ku kai ta asibiti don
Allah ko nawane zan kashe yaya please ku
taimake ni ya goge hawayen dake zuba bisa
kuncinsa yayin da jikin yaya soja yayi mugun la
a sar cikin taushin murya yace kar ka damu
al'ameen zamu kaita kar ka damu kaji sai da
safe. Ko kamin ya gama amsawa ya kife kan
wayar al'ameen sai da ya lalubi wuri don baya
gani yadda ya kamata sauran abinda ke zuciyar
sa kuwa biro na ba zai iya rubuce shi ba domin
al'amarin gagarumi ne maras misaltuwa sai dai
muce Allah ka kiyashemu sharrin masu sharri
amin summa amin Anti amina keta faman
neman ran mama shi kuwa yayanta bai sake
komawa ta kanta ba dakin sa ya shige don yin
abubuwan da yake ganin suna da muhimmanci a
gare shi ita kuwa mama zafin. Mari da tsananin
yunwa tare da tarin damuwa su suka taru suka
jefa ta cikin doguwar suma awa daya da rabi ta
kwashe babu motsin rai sannan ta dawo
duniya,ta fasa kuka tana fadin wayyo Allah na
zan mutu wayyo Allah! wayyo!" Nan da nan
hawaye suka tsunkewa anti amina saboda
tausayin da ya kamata murya na rawa ta
tarairayo ta tana fadin mama ki tausaya wa
kanki wannan mugun halin da kika jefa kanki
kin kuwa ga yadda kamannin ki suka sauya wane
irin masifar so ne wannan na bala'I. Akan da
namiji kike wahalar da kanki a banza a wofi ki
mutu ya nemi wata ya aura,wannan sakarci ne
mama kiyi wa kanki fada tun dare bai miki ba
sannan ki sani idan kika ci amanar al'ameen
Allah ba zai kyale ki ba,ta fizge jikin ta ta sake
faduwa bisa shimfida ta kara fasa kuka, malami
ya budo kofa ya shigo cikin sanyin jiki ya karasa
gun su yace mami uncle al'ameen ya bugo waya,
kafin anti amina tace wani abu tuni mama tayi
wuf ta tashi zaune cikin sababi take fadin ba za
a zo ba kaje ka gaya masa bazan dauki wayar ba
dole ne sai na aure shi nace. Ba zan aure shi ba
duk ku taru ku kashe ni kowa ya huta ta sake
komawa ta dase ciki anti amina da malami suka
saki baki suna kallon ikon Allah. Jimawa kadan
ta dube shi tace,Mu je falon." suka fice jiki babu
kwari,musamman Malami da sababin ya bashi
tsoro ba kadan ba.Anti Amina ta dauki wayar
tayi sallama,suka gaisa kafin yace, Ya jikin
sakeenar? Ta farfado kuwa? 'Ta farfado Al-
Ameen, har ta samu barci. Ya sauke
numfashi,'Allah ya kara mata lfy. To amin.yace
Anti,don Allah ki taimaka ki tuna wa yaya tafiya
asibitin.Ni ina ganin babu abinda zai gagari
asibiti koda matsalar junnu din ne, akwai ta su
irin gudumawar da zasu iya badawa. Please Anti
a kai ta asibitin a gwada." Idanuwan ta suka
kara tara kwalla,jin yadda muryar sa ke rawa,ta
tabbata hawaye ne ke zuba bisa kuncin sa.Ta
numfasa tace "karka damu Al-Ameen,duk wani
iya kokari ana yinsa.inshaAllahu Allah zai dube
mu ya yaye mata wannan lalura.ka kwantar da
hankalinka kaji? Ya amsa,Hankalina ba zai
kwanta ba Anti,har sai naji muryar sakeena da
bakinta ta gaya min tabbacin samun saukin.Ban
san halin da sakeena ke ciki ba Anti,kowa cewa
yake tana samun sauki,amma ni ban ji alamun
ba a jiki na.zuciya ta tana min sake-sake iri-iri
akan sakeena kuma tana nuna min ita acikin
mummunan hali.jin muryar ta ne kadai zata
warware min rudun dana fada.....Anti Amina ta
amshe,komai yayi zafi mgnin sa Allah Dokta.ka
tsaya wa addu'a kawai ita ce kadai zata taimake
mu.shi kenan Anti,ngd.Idan Allah ya kaimu gobe
zan sake kira ko na dace jin muryar ta.Tace To
Allah ya yasa a dace.ameen Sukayi sallama ta
aje waya ta koma bisa