Showing 33001 words to 36000 words out of 110841 words
kallo ganin yanayim
fuskarta yasa ta kama bakicike da mamaki. Ta
jima zaunesannan ta tashi tarufe ko ina ta kashe
fitulu ta samiabba a daki. Waikasan yarinyar nan
sai yanxun tashigo? Ni fah ban gane
sauyinyanayin ta ba, ina mata fada tanabatarai,
yace ai na leka ta falon bakina hango su
sunawasu dararraku, ni ban ganewanene ba,
amma yayishigarsa tsaf harda motarsa. Kajiba?
Allah ya sagobe da kanka zaka fita ka
bashilabarinta. Ai kamarkin shiga raina,
kwanciyar nan danayi abinda nake ta tunani
kenan,karta hadu da romon baka, yajikirtatunani
nta. Ya kamata ka hanzartayin wani abu.
Yazama dole kar girma na ya fadi.Haka suka
kwan daabin cikin xukatansu. Ita kuwaMama ba
nantunaninta yake ba, hankalintakwance tayi
barci cikinshaukin son dan Liti. Da safe Abbaya
xaunar da ita yayi matanasihohi tare da jan
hankali, akankuskuranda take neman aikatawa.
Har yayi,ya gama batacekala ba. Abinda bai sani
ba, shinebabu kalma dayada ta shga kanta,
domin kuwa tananan akan bakanta,duk ta inda
za'a bullo mata. Danliti ne, ba sauyi.Bayan sun
gama ayyunkan su, tayiwanka Umma tayi barci
ta sadadata fice kamar jiya. A shago ta
samiDanliti, koda ganinta, sai yai tsayea kofa,
bakinsahar kunne ya mike, ah! Sanyinraina
kamar kinsantsundum nake cikin tunaninki.
Tatsaya rungume dahannaye ta zuba masa ido.
Tace,hum! Haka naji.Baki yarda ba kenan? Dubi
lissafinda nakeyi dole na aje shi don
banafahimta. Tayi dan murmushi, to yaka
kwana? Ya amsa barcin nan baiyidadi
basakeena, ko'ina najefa ido ke nakegani, kamar
zanzautu nake gaya miki. Tayi dariyafasa min
kai. Saiga Ayuba ya shigo, manya manyainji
kanana! Tadubi Danliti tace, ka yarda mugaisa?
Ku gaisa sanyin raina badamuwa. Ayuba ya saki
baki au saima kayarda zamu gaisa? To matar
kace?Ya kada kai,wane ni? Tafara dariya tana
fadinkadai ina kwana?Yace baxan amsa ba. Dan
liti yaceto idan bazakaamsa ba, ka fita ka bamu
guri,yace ai ko baka ce ba.Ya juya ya fice mama
na dariya,tace wlh baka da dama korarsa
makayi? Ah to yadawo ne? Ta kadakai a'a, yace
to shigo daga cikimana kya ta tsayuwaanan, tace
wlh karka damu datsayuwata. Yadan batarai me
yasa? Tace dan Allah karkabata ranka, yasaki
fuska nima na hkr banso natakura ki. Ammadole
kici wani cikin shagon nan,me xan miko miki?
Ta kada kaidon girman Allah ka barshi.
Yaceanan nezamuyi fada idan har baki sa
minalbarka ba. Me zanbaki? Ta sa hannu cikin
wani katontire ya dauki mintguda daya tace, na
dauka Allah yakawo kasuwa. Yazura mata ido
kawai, bai ce kalaba. Tayi murmushi tabare mint
din ta ajefa baki, kaganinama sha. Yace yanxun
duk girmanshagon nan ki rasa abinda zakidauka,
sai banzan sweet. Ta rufebaki tana dariyakafin
tace, baka gane manufa ta bakenan. Na
daukisweet ne saboda mahimmancinkalmar, kai
sweetheart dina ne, dole in sweet ashagonka.
Yayi 'yardariya yace, shagon mu zakice.
Toshagon mu. Yauwa yanxu najimagana. To ki
kara sweet dinmana, tunda ita kika fiso, zan
karabari sai zan tafi.Yace nabari sakeena ta. Sun
jimasuna hira, sai datakin taci tashin mama
daga barci,sannan tace masazata koma gida. Ya
dauki leda yacika mata da kayanzaki, ya bata.
Ta sa hannu ta amsatana ta xuba godiya. Ya
dago kantaya fito, barin in dan taka miki.Tace ka
barwa shagon wa? Bayanka kori Ayuba? Aiko
bakin kwata na rakaki ko? Ta fito waje tana
dariya, kawai saiga Barakata tsallako titi. Ido
sukayi da junabakinta har kunne,ta bar Dan liti
tsaye tayi gunta,kawata! Ta tsaya tanamata
duban da yafi gaban mamaki? Tace ban ganeba?
Kamar yaya? Daga shagonDanliti naga kin
fito,eh menene? A tunani na kodasiyayya ce,
ajinki ya wuce ki yi ta ashagon Danliti. Amma
sai nagakamarkun fito tare kina dariya. Ko
idonane? Tace kemuguwar 'yar sa ido ce wlh,
bamaganar sa ido bane,wai da gaske daga
shagon kika fito?Daga can nake.Amma dai
siyayya kikayi? Barakake kika haifeni ne?
Wannan irin tambayoyi, me yadame kine? Ta
fizge ledarhannunta, ta duba idan sweet kikeso
ai gara kitsallaka shagon Okundiri ki siya, yafiye
miki mutunci.Arnan? A waje na Okundiri ya
fiDanliti mutunci. Tagyara fuska tace, ni kuma
wajenabai fishi ba. Fadazamuyi Mama? Yaushe
kika faragood time daDanliti? Ban sani ba, ta
nuna tace,kina nufin yayi nasara kanki?
Baikamata ba, domin a iya sanina, bayaudara Dr.
Kike ba. Yaushe kikacanza? Ban sani baBaraka.
Haba mama, ai ko laifi Dr.Yayi miki bagirmanki
bane ki huce haushinkiwajen Danliti. Kigayawa
manya mana ayi masafada. To Ummamtsw.....
Ta fige ledar ta, ta dawotana kara zuba tsaki.
Baraka kuwatsaki tayi musamman da tagaMama
ta sake komawa wajen Danliti. Allah kadaiyasan
me sukace. Ta dai ga Mamata wuce, tanadariya.
Gabanta ya kara faduwa, tadafe kirji
tanaInnalillahi wa Inna ilaihi raju'un!Wlh sai
Umma tajimaganar nan...... KARSHE SAI MUN
HADU A NA BIYU
So Ko Kauna?
Go to Home
BAKIN CIKI (TRUE LIFE STORY) 2***1 Ta wuce
inda aka aiketa kamar zata tashi sama sbda
saurin ta dawo gida.Ta zube wa inna cefane,ko
zama bata yi ba ta fara fadin "inna mama na
cikin hankalinta kuwa? Tace,me tayi? "Kin san
danliti ya dawo....""Danliti?" Waye shi? Dan
gidan buzu mai shayi fa inna."Oho ,ina jin ki me
yayi? Lokacin da aka yi bikin yaya Abdulrahman
danliti yaga mama ya nuna yana son ta wlh a
lokacin ko kallonsa bata yi amma ban san yadda
aka yi ya shawo kanta ba,ynzun nan na gamu da
ita Ta fito shagonsa leda cike da kayan sweet."
Inna ta dafe kirji ido waje,mama fa kika ce? Wlh
inna ni kaina mamaki ya kusa kashe ni.Danliti
dan iska!"Inna tace,mun shiga uku ni saude wai!
Ban ga ta zama ba dole in bincika na tabbata
gidansu ba'a sa ni ba! Kai mama kamar mai
hankali,me zai tsone mata ido a wajen yaron
nan?Kai Allah ka shirya mana yara.Bari babanki
ya shigo Insha Allahu yau din nan za ni gidan
gara a yiwa tufkar hanci,kar ya kai mu ya baro!"
Ya kamata inna,ni ina ganin ma kamar fada
suka yi da Al-ameen don tun dawowar ta bata so
ayi maganar sa."To ba sai ta fadi ba,ko yayyinta
sun isa su kira shi su sasanta su balle ga
iyayensa a gari."Ni ma dai hakan na gaya mata.
Tace min babu ruwa na" "ita mama din ta fadi
hakan? "Ko yanzu ta maimaita min kiris ya rage
mu yi fada a titi,inna ta kuta,ta numfasa,kai
jama'a yara halin su sai su,Ita fa ta kawo shi ba
dole aka yi mata ba?Ta zabga tagumi bakin tana
maimaita salatin Manzo,Da azahar mahaifin
baraka ya shigo gida,inna saude ta maida masa
halin da ake ciki.Nan da nan ya bata umarnin
taje ta bincika,ai bata bata lokaci ba,cikin
tsakar ranar nan ta kama hanya ta nufi gidan
uban dawaki.Umma na daki tare da abban shi
ma shigowarsa kenan gidan aka gabatar masa
da abincin sa yana ci.-Inna ta shiga suka gaisa
sannan suka koma dakin umman.Bayan sun
gaisa da en hirarrakin zumunci kafin
tace.magana ce tafe dani yaya amma ki duba ko
alhaji ya gama cin abincinsa zan so in fade ta a
gabansa."Nan take jikinta ya mutu,tace me ya
faru saude?"To magana ce data shafi mama na
rashin jindadi shiayasa nace ba zan bari ta
kwana ba dole in zo in bincika,sai dai alhaji shi
yafi dacewa ya sani,tunda nayi sa'a yana
nan.Tayi dan tagumi......Subhanalillahi!Bari in yi
masa magana.Ta mike jiki a salube ta shiga
dakin abba ta iske ya kammala tace,wai magana
ce tafe da saude idan ka gama ka taso muje,To
muje gani nan".Ta gyara zama ta maida musu
abinda baraka ta gaya mata umma ta shiga tafa
hannu,abba kuwa sai daya mike."Kar dai ace shi
ne yazo jiya da daddare?Lallai biri yayi kama da
mutum,ina maman take? Umma ta dube shi ido
taf da kwalla,tana daki. Kira min ita!Ta mike ta
fita,har suka dawo tare babu wanda ya tanka
sbda tsabar mutuwar jinin jikinta,a darare ta
karaso dakin tana fadin,inna sannu da zuwa."Ta
zuba mata ido,ke ma sannu."Ta gaishe da abba
da umma na mata kallon mamaki,ta dube shi
suka hada ido,tace abba ga-ni" yace,wanene
yazo gun ki jiya?Ta sunkuyar da kai,tayi
shiru,ya daka mata tsawa,ko baki ji ne?Nace
waya zo gun ki jiya? Tana rawar lebe tace dan-
liti?"Kin kuwa san ko waye danliti a garin nan?
Tayi shiru,mama ni kike so ki mayar tsohon
bnza,ki tozarta?jiya me na gaya miki?To ni ba
hayaniya na kira ki mu yi ba domin a iya sani na
ke mai hankali ce,kin san abinda ya dace,kin fi
kowa sanin cewa saura 'yan watanni suka rage
bikin ki.Sannan idan kika nutsu kika yi tunani ba
mutuncin mu bane daga ke har mu ace an gan
ki,kina karakaina a shagon wani ma,balle danliti
sbda haka nake umurtar ki daga rana mai kamar
ta yau,bana son in sake jin wani labari
makamancin wannan!Ina fatan kin fahimce ni?Ta
kara sunkuyar da kai yayin da idanuwanta suka
fara tsiyayar ruwan hawaye,umma ta muskuta ta
karbe "kin bani mamaki ba kadan ba mama,wai
ma in tambaye ki,me kike nufi da bin sa har
shagonsa? Shiru babu amasa,umma ta
cigaba,wannan katon sakarci da me yayi kama?
A zaton ki abin birgewa ne yadda 'yan mata ke
tsayuwa kofar shagon samari suna amsar abin
hannun su?Ban taba zaton hakan zai fito daga
gareki ba mama kuma mun saurara miki ne
kawai sbda wannan shine karo na farko da irin
haka ta faru!" Inna tace,kin ga gidan nan da
dukkan jama'ar gidan dake cikin sa ana ganin
girma da mutuncin su musamman mahaifnki,don
girman Allah kar ki bari wani ya rusa wannan
ginin,ya hure miki kunne ya kai ki ya baro,kin ji
mam? Ta goge kwalla bata ce uffan ba,abba
yace,to mun ci mun rufe anan bana son ki sake
aikata wani abinda zai sa ayi miki zama irin
wannan,kin ji ni? Ta amsa da kai tana goge
kwalla.umma tace tashi maza muje ki dauko min
ledar kayan da aka ce ya baki,a iya sani na dai
baki da yunwar su,maza tashi muje!Ta mike da
kyar umma ta tasa ta suka je dakin ta dauko
ledar.Umma ta fizge cikin zafi tace,Allah yasa in
sake gani ko ji sai kin sha mamaki!" Ta fice ta
bar dakin,ta bar mama cikin tashin hankalin da
bata taba jin irinsa ba,har inna ta gama zamanta
ta bar gidan mama na aikin kuka a daki domin
dai tamkar sun kara debo soyayyar danliti ne sun
kara antayawa cikin zuciyarta.Ita wannan ranar
da suke kwakwazon an sanya mata ta jima da
manta saurayin ma balle ranar,ba shi a idon ta
ko birnin zuciyarta.Al'amarin ya daurewa
iyayenta kai,shin wai me mama take nufi da
kukan ta? Tambayar zukatan su kawai suke yi
amma basu da tabbacin amsa.Karfe takwas da
rabi cif! Lokaci ne da motar danliti ke fakin a
kofar gidan uban dawaki,kai tsaya ya aiko yaro
a kira masa mama,abba na nan a falo yana
gadin zuwansa don haka yace da yaron yaje yace
tana zuwa. Umma ta fito masa da kullin ledar
kayan kwalamar da ya ba mama Abba ya karba
ya bi bayan yaro kamar jiya,yau ma yana harde
jikin motarsa yana kada mukullai sai dai yau
kananan kaya ke jikinsa,gaba daya ya firgita
kofar gidan da kamshin turare.Yana hango uban
dawaki tilasa ya gyara tsayuwa yana 'yan kame
kamen gulma ko kafin ya karaso ya tsugunna
yana fadin,sannu alhaji,yace yauwa sannu,ya
sake fadin ina wuni? Lafiya kalau,mike abin
ka,magana zamu yi,ya mike a hankali yana
sunkuyar da kai kamar muminin gaske.Abba
yace magana guda daya ce nake so zan gaya
maka danliti,'ya ta sakeena na riga nayi mata
miji,tuni aka sa musu rana har ma lokacin ya
kusan zuwa da yardar Allah sbda haka ina rokon
ka da girman Allah kayi hakuri ka nemi
wata,daga yau kar ka sake zuwa gun mama don
tana da miji,ina fatan ka ji ni? Ya dan yi shiru
jim kafin yace naji alhaji amma nima ina roqon
arziki ka bar ni in rinka zuwa muna gaisawa,tnda
ba'a daura ba.Wlh..."Abba ya katse shi,ba zai
yiwu ba danliti domin koda babu alkawarin wani
akan mama kai kanka ka sani zai yi wuya ka
sami auranta,sanin kanka ne kaf garin nan babu
wanda ya san tushenka,kaje kayi tunani
mana.Ya saki baki yana kallon abba ran sa a
bace,abba ya mika masa keda yace ungo
nan,yasa hannu ya karba kafin ya cigaba da
fadin,abubuwan daka bata ne dazu tunda ba
auranka zata yi ba bai kamata ta amshi kayan
ka ba.Don Allah kayi hakuri ka nemi daidai
kai,sai da safe.Ya juya ya shige gida abinsa ya
bar danliti a tsaye. )Ya kara harde kafafuwansa
yana irin murmushin mugunta,sannan yace ko
banzo ba ita zata zo wajena,koda kuwa kasheta
zaku yi ta dawo.Dama ai zuwan nawa na hure
kunne ne ba wai neman nake da gaske ba."Yayi
er budurwar dariya ya bude motar sa ya shiga ya
sake fadin,sai ni dan gidan buzu mai shayi taba
ni kaga tsiya da bala'I!Ya ba mota wuta yaja ya
bar harabar gidan hankalinsa kwance.Sabanin
mama da take ji kamar ta saci jiki cikin daren
nan taje wajen danliti shiyasa tayi ta leken
falo,amma kash!Abba da umma sun ki tashi har
dare yayi sosai suna tattauna zancenta.Daren
nan bata yi barcin kirki ba sbda bakin cikin an
hana ta fita ganin danliti.Gari ya waye ko alama
umma ta ki sakar mata fuska,sam abin bai
dameta ba Allah- Allah take yi kowa ya kama
gabansa,itama ta samu ta sulale,ai kuwa abba
na fita karfe goma umma ta gama abnda take
yi,ta dare gado kamar yadda ta saba barcin
safe,mama ta gama caba kwalliyarta ta sadada
ta bar gidan.Ta kwarara sallama kofar shagon
danliti,ya taso cike da fara'a yana amsawa kafin
yace,a zatona ke ma zaki juya min baya ne,har
na fara shiga damuwa,jiya sam ban yi barci
ba.Ta dube shi cike da tausayi tace nima haka
danliti ko gyangyadi ban runtsa ba,me zai sa na
juya maka baya alhalin na san cewa nima zan
cutu? Ya zura mata ido a marairece yace,abbanki
ya nuna baya so na ban san yadda zanyi da
rayuwata ba sakeena,kar ki bari ciwon zuciya ya
kama ni.Kwalla suka taru cikin idanuwanta tace
ka daina fadar wannan maganar don Allah,in ka
ga na rabu da kai to sai dai su kashe ni in daina
numfashi,zuciya ta kai take so kuma bana
ra'ayin auran kowa face kai." Kwalla suka zubo
bisa kuncinta.Da sauri ya tauko sabuwar t鐭泂hu
kware ta ya yago ya miko mata,"share
hawayenki, ki daina kuka.Na yarda dake
sakeena,amma mece ce mafitar mu? Ta dan
kada kai tace, "zanyi tunani,ka ban dan lokaci
kadan,zan samo mana mafita.'ya daga kanta ya
fito ya gyara zaman benci.Yace zauna kiji Ta
zauna gefe shi ma ya zauna ya fuskanceta sosai
yace,me zai hana ba zaki gaya musu ni kike so
ynzu ba?Ta daga ido ta dube shi,jim,amma ba
tace komai ba,yace "kar kiji tsoron komai kai
tsaye ki gaya musu ke kin sauya ra'ayi ni kike
so,za'a yi miki tilas ne?Dole a baki wanda kike
so,don babu wanda zai zauna miki da shi,idan
kuma kina son in rasa raina ne shikke
nan........Ta kada kai tace,"nace ka daina fadar
rasa rai danliti idan ka mutu nima mutuwar zan
yi.Ka kwantar da hankalinka insha Allahu a yau
zan gaya musu na sami sauyi wanda hankalina
yafi kwanciya."Ya dafe kirji,ya lumshe ido
yace,kin sa naji sanyi cikin raina sakeena.Ya
bude ido ya bi ta da kallo ya cigaba,idan kika yi
min haka kin gama min komai sarauniya ta,ba
zan cika baki ba sai mun yi aure zaki ga tsantsar
son da nake miki,bana jin akwai wata 'ya mace a
fadin duniyar nana da zata sami irin gatan da
zan nuna miki." Tayi dan murmushi tace,Allah ya
nuna mana,yace amin.Ya dan gyara zama ya
sake gadin,"wai sakeena kin san cewa kin fi
kowa kyau a duniyar nan?Ta saki baki,ido waje
tace,duk duniya? Wlh duk duniya babu mace mai
kyau irin naki,ta kada kai tana murmushi
tace,"ka daina fasa min kai danliti,ni na san ban
kai ka ba,ya washe baki ya nuna kansa ya9e "ni
kuma? A'a ni dai kike son ki fasawa kan,ina ni
ina ke? kin gan ki kuwa?kin ga wannan dan
bakin naki dagwas ba karamin kashe min jiki
yake ba."Ta sunkuyar da kai tana 'yar dariya ya
bita da kallo yana shafo habarsa."Mama!"
Muryar kawai taji anyi mata wani gigitaccen
kira,gaba dayan su suka kalli mai magana,ta bi
shi da kallo babu tsoro ko wata fargaba tace,ah!
yaya ali! saukar yaushe?"Ya kara tsuke
fusk,yace me kike yi anan?"Tace me kuwa?Ba
komai,taso muje gida,kaje ina zuwa,"ina wasa
dake ne? nace ki taso mu wuce." "Ta dubi danliti
suka hada ido yace,tashi ku tafi sai wani lokaci
ko?Ta dan numfasa ta mike ta wuce,yaya alin
dake tsaye,ya bi ta da sauri ya
sameta,"mama,wai mafarki nake yi ko kuwa
gaske ne?Ta yamutsa fuska "da aka yi me?"
Zaune na gan ki kofar shago kina hira da
wani...." 'Wani? Ba ka ma san danliti ba?"Shut
up don Allah!waye danliti kike gaya min magana
ba dadin ji?Hauka kika yi?Ina mutunci ga'ya
mace tana hira da maza a kofar shago gaban
jama'a? Ban san ki da wannan ba,yaushe kika
canza mama? Ta ballo masa harara ta ja dogon
tsaki ta kwahsi sauri ta wuce shi,shi ma ya biyo
ta yana fadin,ban gane nufin ki ba?"Ta juyo ta
dube shi tace,wai menene yaya ali?"Shi kike
so?" 'Ai kaji,menene na sake tambaya? ya kara
cika da mamaki,'Ban fa gane shi ki ke so ba
mama.Ina Al-Ameen din?" Ido jajur! Ta dube
shi,"kai ka san wannan sunan,don girman Allah
ka kyale ni da tambayoyin nan." "Ba zan kyale ki
ba Mama,hasali ma sai na gaya wasu
Abba.Wannan ai zubar da mutunci ne da cin
amana!Me ya tsone miki ido a wajen Dan-Liti?Ke
ma kin shiga sahun 'yan matan da yake ruda da
kyan sa ne?Kai na ya daure Mama.Allah yasa
abinda na ke gani da ji ba gaskiya bane." Da
gaske ne yaya Ali! Kuma ko baka gayawa su
Abba ba,ni da kaina zan gaya musu."Ta zura da
gudu ta bar shi tsaye, shakare da
mamakinta.Kafin ya iso gida kansa,ya kusa
fashewa sbd tunani da al'ajabi.Rokon Allah
kawai yake yi Allah yasa mafarki yake yi. Kai
tsaye sasan su Mama ya zarce.Suna tsakar falo
umma ta tirke ta da tambaya,"Idan biki gaya min
inda kika je ba sai na sumar dake yau a gidan
nan!"Yayi sallama.Umma bata iya amsawa
ba,sbd bacin ran da take tare dashi.Ya-ce,'yanzu
na koro ta daga shagon Dan-Lati suna zaune
bisa benci suna hira Umma.Yaushe Mama ta
sauya haka? Tuni Umma ke sallallami,ta dafe
kirji ta-ce "shagon Dan-Lati ki ka koma Mama?
Mu kike so ki zubarwa mutunci a garin nan? Ai
kuwa baki isa ba,ba ki isa ba Mama!'Ji ka ke
tim! Ta rufe ta da duka ta ko'ina.kafin yaya Ali
ya kawo mata dauki,ta sha dan banzan
duka.Kukan ta ya watsu cikin sassa,matan gidan
da kananan yara suka sheko don ganin meke
faruwa?Al'amarin ya daure masu kai,ganin
Mama na birgima tsakar falo tana ture hannayen
Yaya Ali dake kokarin rarrashinta
BAKIN CIKI 2***2(TRUE LIFE STORY) Wa ya mutu
Ali? "suka tambaya,yayin da umma ta fito daga
daki dauke da wayar rediyo kafin su yi aune,ta
fara tsula mata.Haba gaba daya matan suka
cafke hannun Umma, 'Hajiya Halima! Lafiya
wannan abu haka?Me ta yi da zafi irin wannan
duka?" Umma na haki tace wai yarinyar nan ita
ce zata siyar mana da mutunci? Ta rasa wanda
zata tsaya da shi, sai Dan-Liti? "Dan-Liti? Waye
Dan- Liti?"Dan gidan Buzu mai shayi mana! Yau
kwana uku kenan muna fama da ita ta rabu da
yaron nan,ta ki! Jiya yazo kofar gidan nan.Alhaji
da kansa ya same shi ya gaya masa tana da rana
a kanta.shine don dibar albarka ta bi shi shagon
sa,yanzu Ali ya ganta ya koro ta! Wace irin tijara
ce wannan sbd Allah! Tuni suke kallon juna suna
tafa hannu,hajiya hajo tace "danliti kuma?Waye
bai san tarihin su ba a garin nan?Yaron da tun
tasowar sa garin nan basu da aiki sai bata
'ya'yan mutane koda baki da wayau sosai ai kin
yi dan hankalin da zaki gane buzu mai shayi
kasurgumin kwarto ne,shi kuwa danliti kananan
yara sau nawa ana kama shi dasu?Ko kin mance
ranar da dubu ta cika suka ci shegen
duka.Danliti ya sha da kyar shi kuwa buzu ya
shura barzahi?Me ya dawo da shi kike kwadayi
da har idon ki ya rufe kika kasa duban kazantar
dake tare dashi?Hajiya Gaje tace "duk ba ma
wannan ba kina nufin zaki fasa auran Al-ameen
ne?Umma tace,karya take yi sai dai bayan ran
mu,bari kuma alhajin ya dawo,yau din nan zai
maida ta minna tnda zaman naki anan abinda ya
haifar kenan!Ta tashi da gudu ta fada dakinta
har da danna sakata ta bar su nan suna maida
yadda aka yi. Shi dai yaya ali tunda ya sunkuci
jakar sa ya fada dakin mahaifiyarsa bai sake
kyakkyawan motsi