Showing 51001 words to 54000 words out of 110841 words

Chapter 18 - BAKIN CIKI BOOK COMPLETE BY ESHAT.txt

12 Sep 2025

61

idanuwa
na suka nuna min Al-ameen a tsaye ya cusa
hannu gaban riga ya zaro kudi ya mikawa
direban, yace, ka rike chanji. Ya sunkuci jakarsa
ya wuce. Direba na xuba gdoiya. Ya tura karamin
gate ya shiga, bakin mai gida har kunne ya taso
da gudu ya amshi jakar yana fadin Maraba da
oga! Fuskarsa babu walwala sosai, yace ya
kuke? Lafiya lau oga. Ya shige masa da kaya
falo. Al-ameen yayi sallama, muryar sa ta dauki
hankalin duk wanda ke cikin gidan. Iya ta riga
kowa fitowa, wa nakehi kamar dan Iya? Ya nufo
ta fuska sake, ni ne iya, surprise ko? Ya dan
rungumo tana fadin, ai kaki koya min turancin
nan, da yanxun na gane nufinka. Yana murmushi
ya rabu da jikinta, ya dubi Ladi, Hajiya Ladi ina
fatan kunje kun duba min jikin sakeena ta? Tace
muna dai shirin tafiya da hada tsaraba. Ya ce,
baku da tsraaba? Gaskiyya kunyi min babban
laifi. Tace, mun san hakan amma tuba muke. Ta
ya kuke? Ta amsa lfya lau ya hanya? Yace,
Alhmdlh. Yana juyo wa sukayi ido hudu da mami
tana masa kallon mamaki. Ya nufe ta da sauri
ya rungumeta, Mami na! Idanuwanta suka tara
kwalla, ta kasa cewa komai har ya dago ya
dubeta, yayi dan murmushi. Yace, nayi muku
laifi Mami, kuyi min hkr na kasa daurewa ne.
Tace nagode Allah da ya kawo ka lfya. Amma
banji dadin xuwanka ba Al-ameen. Yace, na tuba
Mami, ki duba halin da nake ciki, kiyi min uzuri.
Ta dan kada kai. Tace, muje ciki ka sha ruwa ka
yi sallah. Suka wuce yana tambayar Dadinda.
Tace, xai dawo anjima daga kd. Yana xama Ladi
ta shigo masa da ababen sha masu sanyi. Bayan
ya jika makoshi, ya dubi Mami yace, ya jikin
sakeena? Na daina kiran waya, don kunnuwa na
ba za su jure jin mummunan labari ba, koda
yaushe. Dalilin da yasa kenan, nace ya xama
wajibi in xo inga halin da take ciki da idanuwa
na. Dan hutu muka samu na sati daya, shine na
yi anfani da wannan damar. Yaya yanayin jikin
nata yake? Ta numfasa sosai kafin tace, jikin ta
har yanxun a rikice yake, xan so ace Allah ya
saka maka hkr, da dangana akan sakeena,
domin kwakwalwarta ta jirkita Al-ameen.....
Hauka Mami? Kina nufin sakeena ta haukace?
Inna- lillahi wa Inna-illaihiri Raji-un!
Idanuwansa suka tara kwalla, ba xan iya hkr da
ita ba Mami, ko ba zata taba warkewa ba, sai na
aureya. Alkawari ne wannan Insha Allahu ba xan
karya wa sakeena ba. Tana ina ne yanxu? Ita ma
nata idanuwan suka kawo kwalla. Ta ce, tana
Fandagori, kuma ni ma xan so hakan Al-ameen,
domin duk abinda kake so, nima shi xuciyata
take matukat so da kauna. Amma al-amarin ya
sauya salo, ka dauki kaddara kayi hkr da ita,
hankalina zaifi kwanciya Al-ameen. Da gudu
hawayen sa suka wuce bisa kyakkyawar
fuskarsa, ya matso ta a hankali, ya dauko
hannayenta biyu ya matse, ya dubeta ido cikin
ido. Yace, har abada bana fatan in saba umarnin
ku mama, amma ina rokon alfarma ki ban izini
in cikawa sakeena alkawarin da daukar mata.
Zan tafi samun nutsuwa, idan ina kallonta a
matsayin mata ta kowane irin yanayin take. Ina
rokon ki Mami ki taimaka min. Ya jingina
goshinsa bisa kafadar ta, ya matse hawayensa
tare da ajiyar zuciya mai karfin gaske. Haka
maminsa ke cikin irin wannan yanain. Ta jima
shiru tana tunanin zuci, tana son gaya masa
gaskiyya, amma bakinta ba xai iya furtawa ba,
saboda tausayin dan tilon dan ta. Ta yi ajiyar
zuciya. Tace, nayi maka Umarni akan duk
abinda yafi xama alkhairi Al-ameen. Mike ka je
kayi sallah kaci abinci. Ya dubeta yana share
kwalla. Yace, nagode Mami. Ta danyi murmushin
dole. Jeka yi sallah. Ya tashi da sauri ya dauki
jakarsa, ya fice. Mami ta raka shi da kallo,
hannunta a kunci. Ta nunfasa kafin tace, Allah
gamu gareka. Yana shiga, bangarensa ya isa ya
yar da jakar hannunsa ya xauna gefen gado Ya
kama kai hannayensa 2 yana yiwa Allah tasbihi.
Jim kdan ya tura hannu aljihunsa, ya xao wallet
dinsa ya bude ya xurawa dan karamin hoton
Mama ido, nan da nan hwaye suka goce masa,
bai ma san tsaninin kukan da yake ba har da
shassheka, kamar xuciyarsa zata tsago kirjinsa.
Allah da ikonsa, tamkar mami na da masaniya ta
taso ta biyo shi dakin, don ganin a wane yanayin
yake? Da sauri ta karaso ta zauna kusa ta shi ta
rungumo abinta, idanuwan na tara kwalla. Komai
ya sami bawa daga Allah ne Al- ameen, bai
kamata ka xauna ka rinka kuka ba! Jin muryarta
yasa hankalinsa ya dawo jikinsa, sannu-sannu
hawayensa ya tsane. Ya dago ido jajur! Ya dubi
Mami, yace mami ki amince min inje in dubo
sakeena Yanxun. Ta goge masa guntun kwallan
dake bisa kuncinsa. Tace, na baka izini Al-
ameen, fargaba na kawai dare. Yace, kar ki
damu Mami. Allah xai tsare. Shikenan, Ubangiji
Allah ya sa ganinka ya xama waraka gareta,
hankalin kowa yakwanta. Yace, Ameen Mami.
Tace , To kayi sallah Maza-maza, don Allah kar
ka zauna dogon tunani. Yanxun xan fito Insha
Allahu. Ta mike ta bar dakin. Al-ameen Ya
sauke numfashi, shima ya mike ya fada bayi,
nan da nan ya watso ruwa ya dauro alwala ya
fito. Bayan yayi sallah ya kimtsa, ya fito Mama
ta matsa yaci wani abu, amma bai iya zama ba,
gaba daya hankalimsa ya koma Fandogari. Sai
dai ya sha Mamaki daya ga Mami ta nace dole
ya tafi da direbanya, bai yi musu ba. Kai tsaye
ya shiga mota direba ya ja shi suka dauki hanya
suka bar Mami cike da damuwa tare da tunanin
yaya al'amarin zai kasance idan Mama ta juya
wa Al-ameen Baya?
BAKIN CIKI 2*** 8 Ba su ido Fandogari ba, sai
karfe 8pm, babu bata tym gidan Uban dawaki
suka dosa. Ya shige sassan sa tare da sallama.
Umma ta amsa ba tare da ankara da mai muryar
ba. Sannu Umma. Ta dube shi da kyau, gaban ta
yayi mugun faduwa, ta mike tsaye tana fadin,
Al- ameen! Saukar yaushe? Yace, yau din nan
Umma. Ikon Allah. Sannu da xuwa! Zauna mana,
ya zauna yana amsawa. Kafin yace, ina yini
Umma? Ta amsa, lfya lau ya karatu? Mun gode
Allah, ya jikin sakeena? Tayi dan shiru, kafin
tace wani abu. Abba yayi sallama ya shigo, duk
suka amsa amsa Abba! Yace, ah! Al-ameen!
Saukan yaushe? Yace daxun da la'asar Abba. Ya
xauna suka gaisa, sannan ya sake tambayar jikin
mama. Abba yace ciwo na nan Al-ameen. Halima
kawo masa abinci ya ci, kafin muyi magana.
Abba bana jin yunwa, domin na riga na saba da
ita, tun tym din na sami labarin tashin hankalin
da kuke ciki. Abin daya hana ni jurewa kenan,
nace dole in xo inga halin da Mama take ciki.
Abba yace, gaskiyya ne. Mama na nan cikin
lularar da ta sameta sai dai al'amuran zai ba ka
mamaki idan na gaya maka alabari ya sha
bambam Al-ameen, nasan an boye maka komai
coz of karatunka, amma yanxun dole ka sani,
tunda ka zo. Jikinsa ya kara sanyi, yayi xuru
yana sauraron abba, al-ameen rayuwa ta
sauyawa mama, wanda muke ganin sa tamkar a
mafarki, daga ni har 'yan uwanta kaf! Babu
wanda ba shi ckin alhinin wannan abu. Balle
kuma kai da soyayyah ta hada ka Mama, kuma
ita da kanta takwo mana kai cikin gidan nan. Shi
yasa nayi rantsuwa, idan mama xata mutu, sai
dai ta mutu a dakin ka tunda tun farko ita ta
kawo ka. Ashe kuwa babu wani dalili ko uzuuri
da xata kawo mana mu saurare ta. Nasan har
yanxun kana jina a hagunce ne, baka gane inda
na dosa ba. To bari na fito maka a mutum kada
ka wahalar da kanka, Magana daya ce, mama ta
gano wani kuma idanuwanta sun rufe ta manta
cewar tayi xafin farko kuma na karshe a
swajena. Ka fahimce ni? Gaba daya kansa ya
kunce, daga yadda yayi kuri idanuwan sa kafe
yana kallon Abba, suka gane bai fahimci su ba.
Saboda haka yace, dole ka shiga rudu fiye da
wanda ka shuga a baya, amma ina so ka sani,
mu muna tare da kai, ba mu san kowa ba face
kai, ba don komai ba sai don tun farko kai tafara
kawo mana. Abinda nake son ka gane shi ne,
xuwanka ya sanya ni farin ciki. Domin kai kadai
nake jira in tabbatar wa Mama cewa lallai ni ba
tsohon banxa bane, kuma bana magana 2. Ina
mai tabbatar maka ba xaka koma ba sai na
daura auranka da sakeena da yardan Allah. Na
gama magana ta, ka tashi hankalinka kwance,
kashiga wajenta tana nan cikin dakinta. Ya mike
ya bar falon. Umma ta dube shi tace, Al-ameen!
Murya dishe ya amsa, na'am Umma tace kayi
hkr, ka kwantar da hankalinka. Mama bata isa ta
xubar mana da mtunci ba. Kai zata aura da
yardar Allah, domin da kai ne akayi mata baiko.
Tashi ka shiga wajenta ku fahimci juna. Ta mike
tabashi guri, don yaji dadin tashi......... Me
kunnuwan Al-ameen ke ji yau? Ya runtse ido
tamau! Ya girgiza kai wai ko barci yakeyi ne?
Abba ya xo masa a mafarki. Ya bude idanuwan
ya ware su sosai, tabbas zaune yake cikin falon
su Mama. Kenan dagaske ne maganganun da
Abba ya gaya masa? Kirjinsa ya soma bugawa ji
yake kiris! Yarage ya zare masa rai, saboda wani
gagarumin ciwo da yaji cikin xuciyarsa, nan take
ya kama shi. Motsin kirki ya kasa yi har Umma
ta sake fitowa da nufin dauko wa Abba
abincinsa. Ta danyi jim, tana masa kallon
tausayi, sannan ta matso tayi kiransa, ya dubeta
firgigi idanuwa sun juye jajur! Tace, ka na xaune,
baka shiga ba? Tashi ka shiga mana, ka kwantar
da hankalinka, komai xai wuce Insha Allah, ya
mike a kasale, ya nufi dakin ba tare da yasan me
xai je yayi ba. Tana zaune tsakar daki ba ta hade
kai da guiwa, tsiyayar hawaye kawai takeyi,
domin tana jin duk kalaman da Abba ke fadi.
Daf! Da ita ya tsugnna, bai san lokacin da yasa
hannu ya dago fuskarta ba. Sukayi wa juna xuru
tsawon lokaci kafin yace, kin ganeni sakeena?
Al-ameen ne, kin gane ni? Ta kau da kai abinta.
Da sauri ya kara juyo da ita, kiyi min magana
sakeena ko na sami nutsuwa saboda ke na dawo
kasar nan, don na duba jikin ki. Ina can tunani
da xulimmi sun addabe ni, idan kin gane ni, ki
amsa min, ya jikin ki? Ta watso masa harara,
hawaye na kwarara. Tace waya gaya maka banda
lfya? Yace, haka kowa ke gaya min tun tym din
da na daina jin muryarki a waya, komai nawa ya
tsaya sakeena, radadin ciwon daya sameki, ya
hanani sukuni. Ina fatan gani na ya zama
sanadin samun saukin ki. Ta goge kwalla. Tace
duk wanda ya gaya maka banda lfya, ya maka
karya, kalau nake, gani kuma kana kallo na
xaune, sai dai na tabbata dawowar ka zata iya
zame min cuta! Ya kara xura mata ido , kina
nufin abinda Abba ya gaya min yanxun gaskiyya
ne? Tace ka daina kokwanto. Ya langwabe kai
gwanin ban tausayi. Yace dole nai kokwanto
sakeena, don nasan akwai alkawarin a tsakanin
mu, kuma bana tunanin zaki yaudare ni, wannan
ya tabbatar min da tsantsan son da kike min.
Ban taba kallonki da xuciya 2 ba sakeena.
Shiyasa har halin yanxun da nake magana dake
ban yarda kin karya alkawarin mu ba. Ta kalle
shi a dage, ta watsar tace, ya kamata ka amince,
tunda gashi da bakina ina gaya maka, tsutsun
soyayyarka yayi fiffike yayi dogon tashi. Ya dafe
kirjinsa a natse idanuwansa tam! Da wahaye,
yace, bai tashi ba sakeena, nayi rantsuwa kina
so na. Akwai miskhila dai a wani wuri, ki gaya
min laifin da nayi miki. Wlh da kaina xan
hukunta kaina, koda da jinin jikina ne xuba, idan
har zai zama fansar tarin laifin da nayi miki.
Gaya min da sauri inji. Ta ya mutsa fuska,
hawayen ta ya bushe tace, Al-ameen ka farka
daga barcin da kakeyi ka saurareni, ni sakeena
na gaya maka a da naso ka, amma yanxun ban
son ka, ba kuma zan aure ka ba, idan sama da
kasa za su hade! Kaji ni ko? Sai na maimaita?
Ya matse ido, kwalla masu zafi suka yo waje da
gudu, ya dan kada kai murya shke yace, kin
xuba min dafi, kin xuba min dafi sakeena. Baki
tunanin amana? Yasa hannu ya kamo yatsunta,
ya kura wa zobensa ido, ya ciga, baki kallon
zoben alkawarin mu? Me yasa kika mance da
dimbin kalaman da kika sha gaya min? Wadanda
suka jaddada imani na akan son da kike min? Ta
kwace yatsunta a hankali ta zare xoben, ta jefa
masa, ga tsiyarka nan, idan shi kake kallo a
matsayin alkawari, ni ma cire min nawa ka bani.
Yaci gaba da kallonta, kafin ya dauko zoben
yace, kiyiwa Girman Allah ki maida zoben nan
sakeena.... Bazan karba ba! Idan ma ka aje shi,
zan jefa shi masai! Kuma nima dole ka ban
nawa! Yace sai dai ki kashe ni, sannan ki zare
shi, wannan din ma zan ciga da boye shi, har
xuwa tym din zaki sami nutsuwa dakin auranmu.
Ta kwada masa harara, sannan tayi wani dan
murmushi na kaico, ta kauda fuska, y mika
hannu ya kamo habarta, ta sa nata da karfi ta
doke nasa, kafin tace, karka sake tabani, idan ba
haka ba kuma sai na kurma maka ihun dan iska!
Ta mike da sauri ta bar wajen, kai tsaye bayi ta
shige, ta maida mukulli ta kulle. Yayin da Al-
ameen ke cigaba da kiranta. Ya tashi ya tsaya
kofar bayin yana fadin, ki fito ki saurare ni
sakeena, ya kamata mu fuskanci juna, mu gane
inda matsalar mu take. A zatona har duniya ta
nade ba zaki taba juya min baya ba! Tana daga
ciki ta amsa, bazan fito ba. Daman kasan inda
dare yayi maka, yace ki tuna alkawari sakeena,
don Allah karki bari ayi min dariya. Idan na
rasaki zan iya rasa komai nawa, ki tausaya min
sakeena, kar damuwa ta kasheni. Tace, kan ka
akeji! Ni na gama magana da kai. Ko za'a kashe
ni ba xan sauya ba, dama ka kama gabanka zai
fiye maka alkhairi. Ya tsaya jim, shiru goshin sa
jingine da kofar ya rasa inda zai tsoma ransa
yaji dadi. A hankali ya soma karannto Innalillahi
Wa inna ilaihir Rajiu'un. Ya fi 10mins tsaye.
Sannan ya juyo da sauri ya fito yana share fuska
da hankaci. Kawai arba yayi da su Abba zaune
falon. Ya rage sauri ya nufi gunsu ya tsugunna,
abba zan koma. Gab dayan su ido suka xuba
masa, jim Abba yace, amma dai ba minna zaka
nufa ba yanxu ko? Ya dan kada yace, kuma ka
kwantar da hankalinka Insha Allahu Mama matar
kace. Kar ma ka bata tym din wajen xuwa goben,
kai tsaye ka wuce gida, ka gayawa Marafa ina
tafe da kaina, muyi magana. Yace to, Abba na
barku lfya. Ya mike ya fice suka raka shi da
kallo. Ummma kam bata sami cewa komai ba,
saboda tsabar tausayinsa. Yana fitowa Gambo
direba ya balle murfin mota ya fito, ya tarbe shi
ganin ogansa na ta share fuska, yaya jikin nata?
Ya dube shi ido jajur yace ba sauki Gambo. Mu
shiga mota, ka maidani gida. Yace yallabai ai
dare yayi sosai, nayi zaton gidan gwaggo xamu
kwana. Ya miko hannu yace bani keys, kai ka
wuce gidan Gwaggon ka kwana! Ya dan sunkuyar
da kai, yace yi hkr yallabai Allah ya sauke mu
lfya. Shi tuni ya bude gidan gaba ya fada.
Gambo ya xauna mazauninsa da sunan Allah ya
murza mukulli yaja suka wuce, a tym din agogon
motar yana nuna 09:45pm. A daren nan nake son
ganin Dady na. Gambo yace Allah ya yarda
mana, ita kuma Allah ya bata lfya. Ya kama kai
ya runtse ido, ya jingina sosai da kujera yana
fadin amin Gambo. Direba na ta tsula gudu cikin
dare. Shi kuwa Al-ameen kurwarsa na can cikin
tunanin baya. Itin tsantsan son da Mama ke
masa, shi yake gani cikin idanuwansa, har xuwa
ranar da ya xo sallama da ita a sch, kawai
gambo ji yayi Al-ameen na sambatu, sosai
kikace kina sona sakeena, dama yaudara ce? Me
yasa sakeena? Me yasa? Hnkalin Gambo ya
koma gunsa yayi kiransa sau uku, kafin yaji
kiran. Ya xuba masa ido yayi da direba ke fadin,
kayi hkr yallabai, yace sakeena ta yaudareni
Gambo, ta xuba min dafin da xai wuya na sami
maganinsa. Xan iya mutuwa Gambo, domin gaba
daya na sallama kaina gareta. Ko kasan inda
nake da mishkila ka gaya min in gyara? Gaba
daya tausayin sa ya lullube gambo, ya kada kai
da sauri, yace babu inda kake da mishkila
Yallabai, sai dai ko ajizanci na dan adam. Ni
kaina ban yarda sakeena bata sonka ba,
watakila ciwo ne rudata yace, kai ma ka yarda
bata da lfya ko? Amma kowa yace kalau take, ni
nasan sakeena bazata ki ni haka kawai ba,
zuciya na wasi-wasi. Gambo yace , kar ka damu
Yallabai, Allah zai warware komai, sakeena zata
zama matarka. Ya sauke numfashi mai karfi
yace, wannan shine babban burina a duniya,
komai Allah ya bani na gode masa, saura
wannan burin ya rage min. Shima zaka sameshi
Insha Allahu. Yayi dan shiru, sannan ya kada kai
yace, laifi nane, rashin kasancewa ta kusa da
sakeena, shi ya jawo shaidani ya shiga tsakanin
mu. Lallai mata na da rauni Gambo, ba taba
tunanin sakeena zata iya hango wani har ya
rikita ta amince dukkan amanar da muka damka
ma juna. Al'amarin na daure min kai, na rasa
yadda xan fassara shi. Yace, haka ne yallabai,
amma idan ka barwa Allah komi na tabbata xai
maka zabin alkhairi. Ka sani ko wata jarabawa
ce Ubangiji yake yi ma don ya gwada imanin ka.
Kar ka damu Yallabai, Allah ba zai hana ka
sakeena ba, idan har kayi imani shine mai
hanawa da badawa. Ya sake jingina da kujera,
ya runtse ido ka fadi gaskiyya Gambo, na gode.
Bai sake tankaea ba haka kuma bai daina
tunanin xuci ba, ma'ana sakeena bata daina
xuwa cikin idanuwan sa dauke da lallausan
murmushinta mai sanyaya masa rai, tana tura
hularasa gaban goshi bakinta na fadin, so much!
Shi ya sa baya aikin komai face ajiya xuciya.
Gambo na jinsa tausayinsa nakara zama cikin
ransa. Karfe daya dai-dai na dare motarsu na
tsayuwa kofar gate din gidansu. Gambo yayi
hon, nan da nan Mai gadi ya shaida hon din
motar mami ne, ya taso a guje ya bude kofar,
motar ta shige kai tsaye kofar shiga ya tsaya.
Al-ameen ya fito, sannan ya wuce ma'ajiya
motaci. Tun kafin ya kwankwasa, yaji ana
kokarin budewa, don haka ya dakata hannayensa
biyu cikin aljihu. Marafa ne da kansa ya bude
kofar, suka zuba juna ido, daga bisani ne mami
ta bayyana wajen har ta riga marafa magana, Al-
ameen . Idanuwansa suka yi tam da kwalla, ta yi
azama ta jawo shi ciki, daddynsa ya maida kofar
ya rufe. Don me ka iyo daren nan Al-ameen? Sai
kace babu inda zaka raba ka kwana! Ya zauna
dabas! Ya kama hannaye biyu, Marafa ya xauna
kusa shi. Ya rungumo kafadunsa, yace baka
kyauta min ba Al-ameen, da ka dauko hanya
cikin daren nan dan kuskure kadan za'asamu,
shikenan ka ajwo mana tashin hankali, karfa ka
manta, kai ke nan guda daya muke kallo zukatan
mu na wankewa daga radadin rashin da. Ya dube
shi ido jajur! Yayin da Mami itama ta xauna daya
gefen suka sanya shi tsakiya. Yace, na kosa in
ganka Dady, sakon Abba xan gaya maka, yace
gobe yana nan tafe maganar aure na sakeena,
kafin in koma yake so a daura shi. Mami tace,
kun daidaita da sakeenar ne? Ya dan kada kai
yace, sakeena ba warke ba Mami, hasalima bata
gane ni ba, shiyasa tun farko nace a kaita
asibiti, kowa yaki amincea da ni, ga shi nan
kwakwalwarta ta tabu. Sakeena ta kasa ganeni
Mami, ni kuma bazan fasa auran ta ba, domin
shine babban buri na a duniya. Su abba sun goya
min baya, kuma ku taimaka min buri na ya cika
don girman Allah. Gaba daya ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login