Showing 69001 words to 72000 words out of 110841 words
a falon, inna saude
tace, tun jiya naso fitowa, wani axababben ciwon
kai ya addabeni. Tace ayya ina fatan yayi sauki.
A'a da sauki, ina maman? Tana ciki ta shiga
wanka.... Wai dama saboda ita kika zo? Ai da
kin yi kwanciyar ki kin huta, domin al'amarin
Mama ya zama jiki. Tace, ya xama dole in taso
yaya. BAKIN CIKI kuwa baya taba zama jiki sai
dai imani. Allah dai ya bamu ikon cinye
jarabawar, ta nisa tace amin. Tace, yanxun me
kuke ciki? Ta fada mata yadda al-amarin yake,
ta cire tagumi. Tace haka shi yafi dacewa, in ma
banda sakarci ba ita xata taimaka mana ya turo
da wurin a huta ba. Tace ina fa, ai ina mai
tabbatar miki tafi son shi akan mu. Allah dai shi
kyauta. Ta amsa da amin. Suka ci gaba da hira
har suka ji motsin fitowar Baraka ta tashi ta
shige dakin. Ba suyi wata hirar kirki ba, domin
ra'ayinsu yasha bambam yanxun. Duk mai zagin
Danliti Mama bata ganinsa da kima haka ta fada
ma baraka, shiyasa ta shiga taitayinta, tafito
daga dakin tace xata ganin amare. Mama dataga
shirinta can ta sameta dakin amaryar Ya Ali, nan
suka shantake, sama da 2hrs sai da Inna saude
ta shiryo tafiya tasameta can, ita ma bata yi ma
Mama maganar komai ba akan abinda ta aikata.
Domin a tunaninta babu wata bakuwar kalmar da
xa agaya mata wacce bata sani ba. A wannan
daren mama tasa ido taga xuwan Danliti shiru
kakeji yasa ta jin haushin rashin dawowar abba.
Al- amarin nata cizon ta taga ba xata daure ba,
karfe goma harta goa, ta fito ta bude kofar ta
fice abinta. Ko kafin Umma ta fito taga wanda
ya bude kofar mama har ta kai kofar gidan,
ganin bata a dakin ya tabbatarma da Umma ita
ta fita. Ta nemi kujera ta xauna hannunta a
kunci BAKIN CIKI ykamar ya kasheta. Take nan
taji xuciyarta na ciwo, wani abu dum! Cikin
kanta kamar xai makantar da ita, tasbihi ta
shiga jerawa ko ta samu saukin kan. Ita kuwa
mama Tunda ta kwashi sauri bata sausauta ba
sai da taje shagon mutumin nata ta ja birki.
Ayuba na xaune daga ciki, taga kanta ta shiga
tare da sallama. Ya amsa mata ta wuce tana
fadin sweetyna naciki ne? Da sauri ya amsa
mata ai bayana nan bai gaya miki bane? Ta
tsaya cak dauke mamaki, ina yaje? Ya amsa
gaskiya bai gaya min ba, cewa yayi xaiyi tafiya
kawai. Na xaci ya gaya miki daxun. Ta kada kai,
bai gaya min ba wlh, amma xai dawo gobe ko?
Yace watakila, ta danyi shiru sannan tace to
shikenan sai goben. Allah ya kaimu. Taga kanta
ta fice, ya bita da kallo. Duk tasuayinta ya lullbe
shi, aransa yace Allah ya kubutar dake daga
sharrin Danliti. To nima nace AMEEN! Da babbar
murya. Tana tafe tana sakar xuci, wai duk fushin
ne yasa Danliti yatfi ba sallama? Ina xansa
kaina idan kalaman Abba suka korar min
Danliti? Bata samo amsa ba taji ann fige
mayafinta, 'yammata ji mana! Firgigi ta waigo
hankalinta ta dubi gungun samarin da suka kai
kusan shida, kowanne su dauke yake da tabar
wiwi. Ta dora hannu bisa kai wayyo nashiga uku,
duk suka fashe da dariya, ina kika nufa mu
rakaki? Ta durkusa kuyi hkr dan Allah, dariya
kwai suke kyakyatawa, 2 daga cikinsu suka
kawo mata cafka. Ta xabura ta mike, Allah ya
taimaketa ta kutsa ta cikinsu ta xura aguje,
dawa Allah ya hada su ba da ita ba, ta watsar da
takalma, ko daman gyalen yana hannunsu, taci
gudun fitar rai, ta rufta cikin gida, yayin da alh.
Adamu, ke kokarin rufe gidan, bakara min figita
yayi ba, amma yayi axama ya maida kofar ya
jefa sakata. Mama kuwa tuni tana sassansu, ta
fadi warwas! Tana maida numfashi tamkar xata
mutu, Alh. Adamu ya biyota, ya isketa daidai
kasa, ya xura mata ido kafin yace, wai daman
mama ce kartin Maxan nan suka biyota? Me kike
a waje har 11pm? Umma tayo waje tana sallami,
ganin mama a kasa yasa ta dafe kirji lfy? Ya
dubeta ido waje, yace, yanxun saboda Allah me
yarinyar nan take a waje cikn duhu? Kinga kartin
da suka biyo sunyi su 10, wannan ai diban
albarka ne da iskanci. Jiri ya soma dibar Umma
tana fadin me? Innalillahi Wainna ilaihir raju'un
kasan Allah, Alh. Adamu har na rufe kofa naji
motsin fitarta, xaune nake kawai narasa inda
xansa kaina dan BAKIN CIKI! Ban san yadda
mama ta maida rayuwarta ba......... Tana rufe
baki, tayi kasa da dafe kirji, saboda ciwon da
yake tsananin yi mata. A hankali hawayenta ke
fita tana fadin, BAKIN CIKIN ki zai kashe ni
Mama.... Alh. Adamu ya daga murya yana
masifa, kin shiga 3 mama! Kin maida kanki 'yar
iska da karfi da yaji, to ki bi a hankali, muddin
kika bari BAKIN CIKI ya kashe mahaifanki, kin
buga babbar asara, tashi ki ba mutane wuri,
kafin in taka ruwan cikinki. Ta yunkura ta tashi
da kyar, amma ta kasa mikewa tsaye, a
duddauke ta shige falo a tym din har mutanen
gidan sun fara taruwa, don ji me ya faru, Alh
Adamu ke daga murya cikin dare? Nan take ya
maida yadda akayi har ya dora karya, wai kartin
har sun turmusheta, tsawat da yayi masu, yasa
suka gudu. Kowa tafa hannu yakeyi yana salati,
kusan 12am suna xuba magana. Sannan kowa ya
koma sasansu, aka bar Umma kwance da ciwon
abubuwa barkatai. Ya ali ne kadai bai tanka ba,
don BAKIN CIKIN sa na gaske ne, tamkar yadda
UMMa takeji cikin xuciyarta. Dakin amaryarsa ya
koma yana kuka da hawayensa. Amina tayi
rarrashinsa tana nuna masa addu'a Mama tafi
bukata ba kuka ba. Mts!.... Amina ba zata gane
ba, BAKIN CIKIN dake cin angonta ba xai iya
jurewa ba, tilas sai ya matse shi. Hasalima ba
zai iya zama yana kallon irin wadannan
abubuwan ba, gara ya koma bakin aiki ko ya
kauracewa idanuwansa ganin abinda ya fi komai
daga masa ciwon xuciya. Saboda haka yacewa
amina ta shirya kayansu gobe zasu koma birnin
gwari da yardar Allah. Al'amarin ya daure mata
kai, kuma tayi tambayoyin da bata sami
amsarsu ba. Washe gari da suke shirin tafiya,
taji fashin baki na bakin Haj. Hajjo. Eh lallai biri
yayi kama da mutum. Nan take kumallon mata
ya taso mata, ya dasa mata kyamar Mama cikin
ranta har tafi Ya ali kosawa su bar garin. 12pm
kuwa ya samo shatan mota suka damki hanya.
Mama bata ma san anayi ba, tana can tana
murkususun ciwon ciki ita kadai a daki. Don ko
daya shigo yin sallama da umma bai shiga
wajenta ba. Sai wajen azahar barci mai nauyi
gaske ya dauke ta. Haka ita ma Umma ke ta
gyangyadin takaici bisa kujera. Rabonta da
abincin kirki tun jiya da daddare motsi taji a falo
ana shigowa da kaya, ta taso da sauri ta leko
falon. Kalla ta gani da tsirin kwalaye ya aje gefe
yana gaisheta. Ta amsa da fara'a ta karfin hali.
Bai karasa ficewa ba, abba ya kawo ka falon
tilas ya rabe gefe ya bashi wuri ya shigo, sannan
ya fice. Alhajin yana fadin, agaida Iyali, yace
xasu ji. Kallo daya yayi wa Umma gabansa ya
fadi, ya amsa sannu da xuwan da tayi masa. Ya
xauna falo. Yayi da ta shiga kitchen dauko masa
ruwa ta kawo masa ta xauna gefe tana kara
masa sannu da xuwa. Bayan yasha ruwa ya
numfasa. Tace an dawo lfy? Ya amsa lfya lau,
duk suna gaisheki, ni ne har abuja, daga can na
xarce kd yau da safe. Tace, wai kunsha hanya,
ina fatan duk lfya ka baro su? Yace kalau,
amma sai naga kamar kin rame, ina fatan ba
ciwo ne ya tashi ba? Ta kada kai. Kai dai bari
Alhaji, ciwo na ba zai taba warkewa ba, idan ban
ga yarinyar nan dakin miji ba. Kaci abinci
tukunna, kaji abinda ya faru jiya. Yayi dan shiru
har ta mike xata dauko abinci kafi, yace ki gaya
min kawai Halima, nasan babu bacin ran da
xanji wanda ya wuce na baya. Ta dawo ta xauna
ta fede masa abinda ya faru. Ya kada kai. Yace
ya rage nata, ba burinta ta fita duk tym da ta ga
dama ba? Jikinta xai gaya mata, xata gane
akwai wadanda suka fita iskannci. Yanxun tana
ina? Tana daki, ni yau ko kalarta ban gani ba.
Bata xo ta gaisheki ba ke nan? Tace ni a suwa?
Bana ma bukatar gaisuwarta, amma tun jiyan na
gaya mata idan na mutu, ta sani BAKIN CIKIN
tane ya kasheni. Yace, ba xaki mutu ba Halima
da Yarda Allah mama ba zata salwantar min da
rayuwarki ba. Karki manta, su hudu kika haifa,
kuma Allah ya albarkace su dubi tsibin kwalayen
nan, duk sakonki ne, kowa na da sa nau'in
tsarabar, zabi kalar abubuwan da kika fiso.
Bayan haka, jibi asabar duk zasu hadu anan,
don su share mana hawayen kukan da Mama ta
samu. Don kuwa zau tsaya tsayin daka dole
Danliti ya turo wakilnsa a daura masu aure a
cikin satin nan. Saboda haka ki kwantar da
hankalinki, ki na dasauran 'yal3an da suke
bukatar ki kusa da su a koda yaushe. Kinji ni da
kyau? Ta goge 'yar kwallan da suka xubo mata,
tace naji alhji, Allah yayi musu albarka baki
dayansu. Yayi murmushi yana fadin, amin kina
iya dauko abincin yanxun. Ta tashi da saurinta,
ta wuce, ya raka da ido tausayinta ya kwarara
cikn ransa. Ya numfasa yace, mun gode maka
Allah da wannan jarabci. Ta fito masa da abin,
ya gaugauta ci, domin gab ake da kiran la'asar.
Ya kammalawa kuwa tym yayi, ya mike yana
fadin, ki shiga ki tasheta tayi sallah. Ta amsa da
to, ya wuce dakinsa. Umma ta kwashe kayan ta
maida kicin, sannan ta nufi dakin Mama, don
tashinta. Tana kife ruf da ciki, Umma ta dada
mata duka ta tashi a firgice. Umma ta xura mata
ido, tace, in kin ga dama ki tashi kiyi sallah!
Tayi waje ta bata wuri. Da kyar ta mike zaune,
kanta ya sara mata, ta dafe shi hannu biyu, gaba
daya miyan bakinta ya kafe. Makoshin ta ya
bushe. Tana daga xaune, amma jiri ne ke dibar
ta.... Idanuwanta na ganin duhu, don haka ta
runtse su tamau! Tana maida numfashi, ta wuce
minti sama da goma ahaka, sannan ta iya tashi
a daddafe ta shiga bayin. Tunaninta kawai tayi
wanka ko tafi jin dadin jikinta. Nan da nan ta
kwashi ruwa a bokiti ta fara wanka. Kamshin
sabulun( Joy) Ya gauraye bayin, ba xato ba
tsammani taji xuciyarta ta tsani kamshin, kan ka
ce kwabo ta goce da amai. Ta kwarara mai
isarta, wai don ma babu komi cikin nata. Tana
gamawa ta dauki bojitin ta juye ruwan ajikinta,
tun daga kai. Ta jefar da shi ta yayo xani ta
daura, ta banko kofa ta dawo daki, ta bar bayin
face face da amai. Ruf da ciki ta sake fadwa
gado fadi take, wash! Wayyo Allah xan mutu! Tun
daga tym din al'amura suka kwance mata, ta
rasa kanta ta rasa meke damunta tana rashin
son abinci da yawan tashin xuciya, ga wani cikin
safe da jiri wani tym din jikinta yayi xafi, don
kansa kuma ya sauka ba tare da tasha magani
ba. Duk ba wannan bace babbar Matsalarta ba,
Ina Danliti ya shiga kwana 2 babu labarinsa? Me
kuma yake nufi da tafiyarsa? Duk da cewar tasan
dole ya dawo, idanuwanta da xuciyarta sun gaza
jure rashin sa na 'yan kwanakin 2. Shi yasa koda
yaushe tana kunshe a dakin matsalolinta masu
yawa na neman xautar da ita. Umma da kanta
bata gane kanta ba, musamman rashin xuwanta
neman abinda xat ci. Amma yawan xaman daki
umma ta jingina da rashin ganin Danliti da ta
rataywa xuciyarta, balle ayi maganar jingina shi
da wanccan Matsalar. Ta kan kada kai, tace,
kaico! Abincin wani, gubar wani! Allah ka raba
mu da muguwar kaddara... A yau asabar ake sa
ran xuwan yayyin Mamma, ga shi babu magana
mai kwari ko kuma muce uban gayyar baya gari,
shi da kansa abba xaune yake shiru dakin ta
same shi, ta xauna gefensa tace, kana xaune
baka shiga wanka ba? Yayi gajeran tsaki, yace
maganar nan ke damuna, da yarinyar nan xata
gane da ta amince cewar Dalinti ba xai turo kowa
ba. Banda aikin rashin gaskiyya, menene na
kama hanya kabar gari, kai da aka ba damar ka
aiko a baka mallakar abinda kake so. Wane bata
tym xakayi saboda Allah? Ta numfasa, tace
yaushe xata fusknaci hakan yadda ta makance
gaba daya, bata ganin kowa sai shi? Ai na gaya
maka ko abinci bata ci, duk ta fige saboda
bala'i, ni yaran nan ma dasu wahala suke nake
tausayawa ba su gama warware gajiyar biki ba,
ga aikinsa mai dan banxan wahala, da da halin
da xa'a ce da su dakata, wlh da ance suyi
xamansu. Ya gyara xama kyale su suzo ko hira
mukayi, ai maji dadi, ko ba haka ba? Haka ne,
Allah ya kawo su lfya. Amin ke ki kira min
Mama ta zo yaushe, dan liti xai dawo? Ta mike
ta nufi daki Mama ta tura kofa kakarin amai ya
fara dibar hankalinta, cikin fargaba ta nufi kofar
bayin ta murda ta bude, Mama! Tana durkushe
kame da ciki, kamar xata mutu. Kan Umma ya
kara daurewa, domin bata taba ganin Mama na
kwarara amai haka ba. Ko rashin lfya takeyi,
bata amai, sai dai xafin xaxxabi. Don haka ta
nufe da sauri ta dafe ta, me xan gani haka
Mama, baki da lfya ne ko yaya ne? Bata iya
amsa mata ba, tana tsaye kame da haba, tagama
kakarinta, ta kuskure baki hade da fuska, tayo
waje abinta, ba tare da kula Umma ba. Bisa gado
ta fada ta datse ciki tana numfarfashi. Umma ta
biyo a fusace tasa hannu ta birkito ta, ba kyajin
ina magana ne? Nace lfya kike sheka amai? Ido
jajur! Cike da kwalla tace, cikina ke min ciwo,
tun yaushe? Yau 3days. Ta jawo ta waje cikin
haske sosai, ta kama hannayenta ta dudduba,
sannan ta gwale idanuwanta, ta duba cikinsu, a
tsorace ta tambayeta ke, kina yi al'ada kuwa?
Tayi shiru tana xaxxare ido, baki na rawa tace,
nima ban sani ba Umma. Ba ki sani ba? Ke xaki
gaya min ko sai na farfasa bakinki? Ta goce da
kuka, don ita ma ta kideme, ta mance rabonta
da a'alada. Umma ta xura mata ido, jinin ta na
kara hauhawa, da sauri ta wuce ta bar mama
tsaye. Dakin abba ta koma ta xauna, ta rike kai
tana maida salati. Me akayi? Tace alh. Magana
takare ka dauki mama ka kaita asibiti ayi mata
gwajegwaje! Gabansa ya fadi gwajegwaje? Name
kuma? Na komai Alh. Ina shiga na sameta tana
sheka amai a bayi, wai cikinta ke ciwo, amma
alamu a bayyane sun nuna Mama juna 2
gareta........ Tsaye ya mike tare da fadin me?
Hawaye suka kara tsunke mata, ya koma a
hankali ya xauna bakin sa na karanto salatin
Manxon rahma. Gaba dayansu tsit! Sukayi
tsawon lokaci sai Umma ke shatatar hawaye,
baiyi aune ba kawai ya ga ta dungura ta fadi a
sume. Ya xabura ya tarairayota, yana kiran
Halima! Halima!! Don girman Allah karki kara
min tsahin hankali akan wanda nake ciki, ya
jawo goran ruwa ya xuba a hannunsa, ya yarfa
mata, ya cigaba da shafa mata ruwan bisa
fuska, ahankali har ta dawo hayyacinta. Ta bude
ido, jim tana kallonsa, sannan ta sake fashewa
da kuka, nan take tausayinta, yasa kwallan
Ubandawaki suka fara sauka bisa kuncinsa.
BAKIN CIKI kamar ya aika shi barxahu. Kiyi hkr,
ki kwantar da hankalin ki Halima, wannan
jarabawa daga Allah Ubangiji take, babu wanda
ya isa ya kankare mana ita, bana son tsanin
damuwar nan da kikeyi, tana jefa ni mummunan
matsayi, ko dogara da Allah Halima shine xai
magance mana komai. Ta goge hawayenta tayi,
iyayinta don ta tashi xaune amma ta kasa. Yace
kar ki damu da sai kin tashi yanxu kiyi
kwanciyarki ki huta, bari in kwaso magungunan
ki in duba wanda ya dace kisha. Ya mike da
sauri wani duhu ya rufe masa idanuwansa, bai
ganin komai face wasu miliyoyin taurari kanana,
tilas ya dawo ya xauna ya fadin Hasbinallahu wa
nimal wakil. Yayi ta maxa ya sake mikewa.
Umma tace ka xauna Alhaji kar kaje ka fadi ka
nakasa. Bai tanka ba, ya fice. Jimawa kadan ya
dawo da kwanndon magungunan ta ya xauan
yana bincikawa, jikinsa na rawa saboda bacin
rai. Sallama sukayi daga falo kuma babu
tantama muryar Ya abdurahman ce, abba Ya
amsa, ya kara da fadin gamu nan, ku karaso
ciki. Ganinsu jugun2, Yaya take ya rasa
kuzarinsa. Yaya dai Abba? Jikin nata ne ya
tashi? Yace shine abdulrahman, nan da nan ya
xube gabanta, da dauko kanta ya dora bisa
cinyoyinsa, sannu Umma! Sannu! Ta matse
kwalla, ta dube shi, kaxo lfya? Ina safiyya? Ya
amsa lfya lau take, tace in gaisheki. Ina
amsawa, me yasa baka xo da ita ba? Ya goge
mata kwalla, tayi nauyi ne Umma bata jin dadi,
idan tayi doguwar tafiya, koda muka koma,
bayan daura aure sai da tayi xaxxabi. Ta dan
kada kai, tace Allah sarki, Allah ya raba su lfya.
Amin. Ya amsa sannan ya dubi Abba suka gaisa.
Kafin su kama wata maganar, muryar Manyan
yayin ta gauraye cikin falonm. Abba ya gaya
musu suna ciki, kowa ya shigo da kuzarinsa, ya
ga Umma a kwance sai yayi turus! Bayan sun
gaisa tasha magani. Abba ya kwashe abinda ke
faruwa kaf, ya gaya musu, kowa yayi shiru,
kawunansu sunkuye tsawon tym kafin Ya soja,
yace, yanxun Ina Maman take? Oho inji Abba,
gaba daya sukace oho? Ta bar gidan nne, Umma
tace tsakar gida na barya tsaye, ban sani ba ko
ta koma daki ko ta fice don ba sani xamuyi ba.
Duk tym din ta so fitarta, ficewa ta takeyi.
AKIN CIKI 2***14 Ya soja ya dubi Ya
abdulrahman, yace je ka kawo mana ita nan! Ya
miki cikin hanxari, ya nufi dakinta, tana kife bisa
gado aikin kuka kawai takeyi. Ya sa hannu ya
fisgota, ba karamin tsoro ya bata ba, ta kwala
ihu, wani BAKIN CIKI ya kara turnuke shi, bai
san tymda yasa hannu ya doke bakinta ba, yace
rufe mana baki shashasha. Da sauri ta kame
baki, wanda take kyautata xaton hakoranta xasu
iya xaxxagow idan bata dafe shi ba. Ahaka ya
ciga da jan ta har dakin abba. Gaban babban ya
direta, ta xube har tana karo da guiwarsa. Ya
xuro mata ido kamar zasu fado kasa. Yace
matsa kdaga kusa dani, xan iya tokarinki, ki
mutu idan baki matsa ba. Ta janye jikinta baya,
ahankali hawaye na ambaliya, sunfi minti 5 babu
wanda tanka saboda takaici, kafin Ya abdulkrm
yace, gaba daya kin rusa rayuwarki Mama kin
lalata cikar asalinki da martabar iyayenmu.
Yanxu wa ya isa ya kankare bakin fetin da kika
shafawa kanki? Wa ai daura miki aure da ciki?
Wa kuma xai jagoranci kisan kai? Wannan cikin
dole ki haife shi, domin yunkurin xubda shi, ya fi
yinsa barna da tarin xunubi. Kin ga tun daga nan
idan kinyi tunani cikin hankalinki, xaki gane
babu soyayysa tsankaninki da Danliti. Burinsa
dama ya ruguxa rayuwarki, burinsa kuma ya cika
tare da hadin kanki. Saboda haka dabara ta rage
wa mai shiga rijiya, sannan karki xargi Danliti,
idan ya tsallake auranki, gaba daya abinda yake
bukata ya samu, abinda yai saura shine ki haife
masa wannan ckin, in ya ga dama ya karbi dan,
idan bai yarda ba ya kyaleki da shi, ku wulaknta.
Dama wannan shine karshen son xuciya. Babu
uwar kudi balle riba ga mai cinikin son xuciya.
Kuma duk wanda ya hau motar kwadayi da son
xuciya, babu tantama tashar kunya da nadama
xata kaishi ta aje. A koda yaushe karshen
danasani, ina fatan wannan xai xama darasi
gareki, ki gane cewa abinda Babba ya hango,
yaro ko ya hau gwauron dutse ba xai hango ba.
Ya goge 'ya kwallan da suka xubo bisa kuncinsa
sannan ya sauke numfashi ya dubi sauran, yace
yanxun mene abinyi? Abba yace abinyi babu shi
abdulkrm, tunda maganar aure ta rushe a halin
yanxun. Ya Soja yace duk da haka, dole ya san
tana dauke da cikinsa, bayan ta