Showing 72001 words to 75000 words out of 110841 words

Chapter 25 - BAKIN CIKI BOOK COMPLETE BY ESHAT.txt

12 Sep 2025

64

haihu xa a daura
musu aure, su tare da yaronsu! Su karata can da
abin kunyarsu! Ya abdul rahman ya kara sanyaya
muryarsa mai taushi, yace wannan dole ne,
amma abu na farko shine, ina xata xauna? Ta
kula da kanta? Umma dai ba xata jure ganinta a
wannan yanayin ba, ya soja ya gyara zama yace,
gaskiya ne, kuma waje na ya kamata ta xauna,
sai dai ba xan iya daukarta ba saboda xan iya yi
mata dukan mutuwa yadda nake jin na tsani
ganinya. So a cikinku, wanda yake ganin xai iya
hkr da ita, yana iya tafiya da ita Allah ya
shiryeta, mu kuma kullum addu'a muke mata,
idan ta dauki wannan mtsayin darasi a gareta,
xamu fi kowa farin ciki. Ya Abdulrahman, yace ni
xan tafi da ita, no ka bari ni in wuce da ita
Minna. In ji Ya abdulkrm. Abba yace ba xata biki
ba nan da xata xauna... ban ce mata yin ku za
su yadda ta ba amman yau da gobe sai Allah.
gara ta zauna anan, domin anan ne suke aikata
abin kunyar u kun ga ganinta da juna biyu ba zai
girgiza kowa ba sanin cewar daman can
sakamkon da zai biyo baya kenan. in ba wani
gyaran Allah ba. saboda haka ku kwantar da
hankalinku kuci gaba da yi mata addua sannan
ku kwantar da hankalinku ku tallafa wa
mahaifiyar ku ta kowace fuska don ganin ciwon
BAKIN CIKIN bai tagayyara ta ba, dukkan su
suka jinjina kai alaman uban dawaki gaskia ne.
yaya soja yace da yardar Allah umma ba za ta
tagayyara ba, idan mama bata son ki mu bamu
da wacce ta fi ki. bamu da wani buri. da ya wuce
mu rayu tare da ke. kar bacin ran mama yasa
mu dakatar da dukkan farin cikin mu. mu ukkun
nan mun ishe ki kallo ki samu sanyi a ranki ko
umma? hawaye na suka malalo mata yaya abdul
yayi maza ya rungumota ya na share mata
hawayen ki daina kuka umma in kina kuka
mama ba zata taba ganin haske ba, duk adduar
da zamu mata tace ba komai wallahi bana
jayayya da ikon Allah amman ku sani BAKIN
CIKIN ba zai goge cikin raina ba, domin FARin
ciki da bakin ciki duk halitta ce cdaga Allah fata
na kawai Allah ya bamu ikon cinye jarabawarnan
Allah yayi maku albarka Kowa ya numfasa, yace
amin, abba ya dubi mama da hawayenta yaki
yankewa yace, ina fatan kin ji abubuwan da 'yan
uwanki suka fadi, idan kinyi anfani da su, ki ga
daidai, idan kuma kin ce ba haka ba, mu babu
abinda xamu iya yi, sai mu kyale ki, ki ci gaba
da rayuwar da kika xaba. Ko dama kin riga kin
ruguza ta, karashe ne kawai. Allah ya shiryeki,
ki na iya bamu wuri mu sha iska, ki jira dawowar
Danliti, amma ki sani auran ku ba shi yuwuwa,
sai bayan kin haihu. Tashi ki bamu wuri. Ta kara
makurewa, kukanta ya karu, duk suka xubo mata
ido. Ya soja yace wa yace kiyi kuka? Cewa akayi
mun gaji da ganinki, ki koma dakinki. Ta
yunkura kamar xata tashi, amma ta kasa, da
sauri ta rarrafa jikin Ya abdulrahman, ta
kudundune ta rushe da kuka. Nan da nan ta
karya masa xuciya, ko dama shi akwai sanyi da
saurin jin tausayin mutum. Idanuwansa suka cika
taf da kwalla, tun baya son kulata har ya kai
hannunsa, bisa knta muryarsa na rawa yake
fadin, imani kawai xai sa akalleki Mama, amma
ke ba abar tausayi bace, tunda baki tausaywa
kanki ba...... Ya soja ya katse shi, pls
abdulrahman, fita da ita, Umma tace sai ma ya
fita da ita? Gata kenan, ya kyaleta, ta tashi da
kanta ta wuce. Ya tarairayo ta suka mike tare,
ya janyo ta xuwa dakinta ya xaunar da ita bakin
gado. Ya tsugunna gabanta yace, dube ni Mama.
Da kyar ta dube shi, hawayen ta na xuba, yace
kukanki bai da wani anfani, muddin ba nayin
nadama bane. Nadamar ma ta gaskiyya, tsakani
da Allah. Saboda haka ina shwaratar ki da ki
kama kanki, wannan ya xama na farko kuma na
karshe. Ba soyyaya vace wannan, ki dauki jikinki
ki ba da ga namiji, daga ranar da ya sanki a
waje. Wlh kin gama yawo, duk wulaknci da ya ga
dama xaiyi miki, ko da kinyi sa'a ya aureki,
abanxa xai rika kallonki, sannan wulakanci ba
xai daina shi ba, a karshe ki ga auran ya
bantale, tun ba aje koina ba. Kuskure ne, kin
riga kin yi Mama, irin wanda bamu taba xato ba,
babu yadda xa muyi mu gyara shi, sai dai kiyi
tuba wajen Allah, sannan ki nemi afuwarsu Abba,
kin jini? Ta xura masa ido, hawaye na ta bulbula
ta kasa fadin komai, domin ita kanta bata san
ainihin abinda ke damunta ba, cikin ranta agame
da samun ciki ba tare da aure ba. Saboda haka,
sake fado masa tayi, ta kankame shi, kukan ta
kamar xai fasa xuciyarta. Ba karamin rikita shi
tayi ba, domin nan take ya goce da kukan shi
ma. Da kyar ya banbare ta ya mike da sauri ya
bar dakin, ya dawo falo ya cigaba da gugar
kwalla, xuciyarsa na masa ciwo. Kai! Sun
dandani BAKINCIKI, da akwai yadda xasuyi su
goge wa Mama wannan bakin fentin da sun goge
mata shi, ko da shi xasu rasa komai nasu. Sai
dai kash! Babu hali, shi ya sa ko abinci
tsakurarsa sukayi suka ci, ba don yayi musu dadi
a baki ba. Haka suka juya bayan sallar la'asar
makare da BAKIN CIKIN da baya misaltuwa.
Haka zalika sun bar Mama cikin wani yanayi na
kunci rayuwa, wanda ya wanxar mata da
cututtuka masu dama ajikinta. Kafin yamma ta
fadi, kamar ba ita ta dawo Legos dambasheshiya
ba. Sati 2 kenan yau babu labarin Danliti, yayin
da rashin lfyar mama ke cigaba da yaduwa
tamkar yadda labarin samun cikinta ya gama
baza gari, ta bakin Hajiya Gaje. Amma don
tsabar yaudara su suka matsawa Mazajensu su
akan su kai ta asibiti ko ta sami dan taimakon
da xai rage mata larurar jikinta. Da kyar abba ya
amince. Alh. Basir ya kaita babban asibiti da
garin Kagara. Suka ga likita, yayi gwaje gwajen
sa ya gano, lalurar shigar ciki ne ke wahalar da
ita. Saboda haka ya bata 'yan taimakon da xasu
rage abubuwan da take ji a jikinta, sauka dawo
gida. Sun wuce kofar shagon Danliti shi kuma
yana karasowa wajen. Yayi fakin ya fito tare da
yin daguwar mika mai isar da sakon gajiya.
Ayuba ya fito ya tarbe shi, sai dai fuskar sa
babu fara'a ko alama. Yaya dai mutumina? Naga
kamar kana ciwo? Ya numfasa, amma bai tanka
ba har suka shige shagon. Ya dube shi da kyau,
yace ina magana ka kyaleni, lfya nace? Ya kara
sauke numfashi. Yace ina fa lfya, magana ta
cika gari..... Ya katseshi Mama na da ciki ko?
Gabansa ya fadi ya saki baki yana masa kallon
Mamaki, Dan liti ya kece da dariya, kwalla na
gangara bisa kuncinsa kafin yace, shiege ni, dan
buzu mai shayi. Raina kama gaiyya, ka tabani ka
ga tsiya. Watau labari har ya bazu ko? Kaga
burina na farko ya cika, amma har yanxun akwai
saura, don na san dan xagin kalilan za'ayi mata.
Ido jajur! Ayuba yace, kaji tsoron Allah Danliti,
ka kyale yarinyar nan haka. Tunda ba xaka
aureta ba, ka barta taji da wannan bala'in! Ai ka
gama ruguzamata rayuwa, babu sauran
wulakanci da yafi wannan..... Ya ja Kujera ya
xauna, yace haka kake gani, nasan akwai saura,
sai dai ba xan shanye maka dadin labarin ba,
idon ka nake son ka gani kamar yadda ka ga
wannnan. Ya bishi da kallo, yana kada kai.
Murmushin keta Danliti yayi, ya sake fadin, babu
wani abu mutumina, kai kanka kasa ramuwar
gayya, tafi gayya xafi. Dadin abin a gabanka
mama ta xageni, ta xagi Mahaifina, ka manta
kawai! Yace wannan ba hujja bace Danliti, ina
gaya maka barnar da kakeyi tayi yawa. Allah ba
xai kyaleka ba. Ya ja dogon tsaki ya mike tsaye,
kai wannan ya dameka, ni yanxun gidan ma xani
kuma lfy lau xaka ga na dawo, see you! Ya juya
ya daga kanta ya fice abinsa, ayuba ya koma a
hankali, ya xauna ya dora tagumin mamaki da
takaici. Danliti ya sake gani ya dire masa bakar
leda tare da kwalin juice kato bisa kanta. Yace
ga sauran kazar da na ci a mota nan, idan ka
gama laulayin, ka ci. Ya juya ya wuce mota, yayi
tafiya sa ya bar shi da tagumi. Kansa tsaye yayi
fakin kofar gidan Uban dawaki, akwai yara gidan
suna wasa, don haka bai yi wahalat neman yaro
ba, take nan ya aika yana kiran Mama. Yarinyar
ta shiga, jim kadan ta fito ta gaya masa tana
xuwa. Yana nan jingine da mota yana kada
makullai. Abba ya fito. Nan da nan ya tsuguna
kai sunkuye, mummunin kare kenan. Yace, ah!
Sannu abba, ina yini? Abba ya bishi da kallo,
amma kash, ya kasa ganin bakinsa balle ya gaya
masa bakaken maganganu. Ya amsa gaisuwasa,
sannan yace mike ka biyoni. Ya wuce kofar falon
bakinsa, ya murda ta bude suka shiga, xauna, ya
nemi waje ya tankwashe kafafuwa. Abba ya
xauna ya dube shi da kyau yace, yanxun saboda
Allah Danliti abinda kayi, ka kyauta kenan? Me
ya sa duk abinda xakuyi baku sa tsoron Allah a
xukatanku? Ya xa kace kana son yarinya da
aure, sannan ka aikata mata abinda ba shine ba?
Danliti ya kara sunkuyar da kai, kamar xai tsaga
kafet din falon ya shige don gulma, abba ya ciga
da cewa, to ta faru takare, ahalin Yanuxn Mama
juna 2 gareta, kaga xancen auranku ya rushe
kenan dole tayi zaman istibra'i xuwa tym da xata
haihu. Wannan abu ya bani kunya kuma kun
xubar min da mutunci da kima a garin nan.
Hannaye 2 Danliti ysa ya rufe fuskarsa yayi
xugum, ko mtsi ba yayi. Abba ya numfasa ya
kada kai ya cigaba, ni bani da abinda da xan
iyayi, tunda kaddara ta riga fata, abinda kawai
nake soka sni, shari'a ce ta tsara haka, saboda
haka dole ku kauracewa juna, don gudun karku
kara maida hannun agogo baya. Ina fatan kaji?
Sai ka koma jira ranar da xata haifamaka danka,
kaga kun sami dan aike, ba sai kun nema ba.
Kana iya tfiya, mu jira abinda Allah xaiyi.
Shawara da xan baka kawai, ka nemi tuba wajen
Allah, domin ka saba masa, ka keta rigar
mutuncin yarainya. Shiru yayi ya kasa tashi,
abba yace tashi mana, ni nakare magana, ya
dago kai da kyar, amma bai kalli fuskar abba ba,
cikin sanyin murya yace, abba kayi hkr ka yafe
min? Wlh sharrin shaidan ne. Ya goge kwalla,
abba na kallonsa kafin yace, haka ne, amma
wani tym har da son xuciya. Si yasa nace ka
nemi tuba wajen Allah, don ta ni mai sauki ne.
Ya kara rankwafawa yace, je ka kawai. Ya tashi
simi simi ya fice babu ko waige. Abba ya raka
shi da ido, sannan ya numfasa ya kada kai, yace
Allah ya shirya mana. Shi kuwa Danliti yana fita
yayiwata 'yar girgiza ta jin dadi, ya wuce
motarsa cike da farin ciki ya koma shagonsa.
Ledar kazar da ya ajewa ayuba suna nan bisa
kantar bai taba ba. Wai don ya ba ayuba haushi
sai ya dage kantar kayan suka watse kasa.
Ayuba ya bishi da kallon kafin ya ce ni baka ban
haushi ba don ka xubar kudinka ne, ba nwa ba,
gaskiyya ce dai ba xan daina gaya maka ba,
watakila ma baiji shi ba, domin bai tsaya ya
saurare shi ba, cikin daki ya shigr. Yayi kwance
yana tunanin shirinsa na gaba akan mama. Abba
kuwa ys jima falon xaune yana tunani rayuwa
kawai. Sannan ya mike da kyar ya koma cikin
gida, ya maida wa Umma yadda sukayi da
Danliti ta kada kai tace , shikenan, Allah yasa ta
nutsu ta xauna gidan. Yace amin, amma ina mai
tabbatar miki muddin tace ba xata nutsu cikin
gida ba, xan bata mamaki, domin, dole ta xaba
ko mu ko shi. Umma tace gaskiyya ne, ace
wannan abu ya sameka, baka yi nadama, ai
kuwa sai a sallama mutum asa masa ido. Allah
yasa mu dace. Ya amsa da amin. Tunanin uwar
gayyar ba anan yake ba, domin kuwa jin ga
Danliti yana kiranta, ya tabbatar mata da cewar
ya dawo kuma taso ta ganshi, su Abba suka
taka mata birki. Duk da haka taji karfi a jikinta
kwarai da gaske, har wasu daga cikin
cuttuttukan da ke damunta suka yaye nan take.
Sai dai tana ganin babu adalci a hukuncin dasu
abba suka yanke. A zaton su zan iya zama
tsahon tym banga masoyina ba???????? Ta tabe
baki tana daga kwancw tace, ba xan iya ba
gaskiyya, sai dai suyi hkr wlh. Ai dai maga juna,
ya san halin da nake ciki, ya tausaya min. Ta
goge kwalla ta cigaba da sakar xuci. Ana ta
sallar magriba, tym ne da ita mama ta sami
damar satar jiki ta sulale ta isa shagon danliti.
Shi kuma kaida ke xaune cikin shagon. Ayuba ya
shiga sallah. Yana ganinta ya dafe kirji ya wani
lumshe ido. Yace wayyo Allah na gode maka! Ta
daga kanta ta shiga, ta nemi t barma ta zauna,
saboda bata jure tsayuwa. Tana xama ta hade
kai da guiwa ta fasa kuka ya kare mata kallo, a
dage yana dan murmushi, sannan ya taso ya
dawo gunta yace haba bebina! Meye abin kuka?
Ya xauna gefenta ya rungumota jikinsa, bana son
kukan hakan nan....... Ta cira kai da sauri ta
dube shi, ba xanyi kuka ba? Ciki fah gareni,
kowa ya tsaneni ana ta zagina. Shine xaka ce ba
xanyi kuka ba? Yayi dan murmushi yace, bebi
kenan, to don kowa ya tsaneki shine me?
Bayanni ina son ki kuma ina son ciki na! Kina so
yi kukan ne, wata kila kuma na dadi ne yayi
miki yawa. Ta mako masa harara tace, jin dadi?
A zageni, a tsaneni shine jin dadi? Son ka ne
kawai yake sawa bana damuwa, amma kai ina
ganin abin baya damunka, daya dame ka, da
baka wanke kafarka ka bar garin ba, tsawon sati
2, alhalin an ce ka turo a daura mana aure. Da
ka maida hankali ka turo din, ai da duk hakan
bata kasance ba, koda cikin xai bayyana
adakinka xai fito. Tunda ni ban ma taba nuna wa
akwai wani abu tskanin mu ba. Sannann.... Ya
da ka mata tsawa, ya ida don Allah! Haba!
Wannan maida xancen na menene? Ko kuwa turo
ki akayi ki zo ki batan rai? Ko dan kinga ina ta
rarrashinki? Babu fah dole, kin ganne? Abban ki
cewa yayi ba dole bane ya bani ke, ko bayan kin
haihu. So pls ki daina damu na da irin
wadannnan surutun banxan, ban son jinsu, idan
har kin son mu shirya! Kin gane? Ta xura masa
ido hawaye na xuba, ta ma rasa me zata ce?
Ayuba yayo sallama ya shigo ya riske su cikin
wannan halin. Shi ma yayi tsaye yana kallon su,
jim kadan Danliti ya buga tsaki ya tashi ya
shige daki ta goge hawayen itama ta tashi ta
bishi, ayuba yaa kada kai ya ja kujera ya xauna
yana fadin Allah ya kwaci yarinyar nan. Tana
shiga ido ya xubo mata. Yace au biyo ni kikayi?
To ranki xai baci kuwa, gara ki koma. Ta
marairaice tace, kayi hrk Danliti, ba don ranka
ya baci bane ya sa na gaya maka abinda ke
damuna. A xatona xaka tausaya min a halin da
nake ciki. Bani da wani gata wajen iyayena. Tun
ranar da na nuna kainake so Danliti, ka tausaya
min. Yayi lum da ido ya bude, ya cigaba da
kallonta tana tsiyayar hawaye kusan 3mins
sannnan ya yafito ta da hannu, yace xo nan! Da
sauri ta isa gunsa, ta fada jikinsa ta kara fashe
da kuka. A'a, kinga ni fa kukan ne bana so.
Yanxu menene damuwarki? Ta goge hawaye, tace
kullum in rinka samun kulawarka, hakan shi xai
tabbatar min da kana sona kana son abinda ke
cikina. Yayi dan murmushin nan nasa, ya kara
janyo ta jikinsa, yace, kin samu bebi, karewa ma
da kewarki na dawo. Kin ci abinci? Ta kada kai,
saboda me? Bana iyawa ne, jikina gaba daya ya
canza, sai amai kamar xai kasheni. Yace ayya
sorry ko? Amma duk da haka ba za a rasa
abinda kike sha-awa ba, gaya min in nemo shi,
na kosa in kore kishirwata. Ta mako masa
harara, ya kyalkyale da dariya, meye na harara
ta? Ko ke ma xaki min BAKIN CIKI ne, irin na
'yan sa ido? Masu shiga tsakanin masoya suna
son suga bayansu. Haushi su nake ji wlh. Tace ai
ko ni din ma haushin su nake ji, ah haba? Wlh
kaji na rantse. Ya cacume ta tana dariya tana
fadin, ban da lfya Danliti, bai saurare ta balle ya
tuna ya nemo mata abinda take son ci. Karfe 8
ya fito ya barta can kwance tana murkukusun
ciwon ciki, ya wuce waje wani mai suyan nama,
ya karbi danyan naman da yasa ya aje masa. Ya
dawo ya bade shi da magani, ya maida cikin leda
ya nade. Yana xaune bakin shgo bisa benci, yana
tunanin tafiya yayi wanka ko ya samu yayi
sallah. Mama ta fito tana yafa mayafinta, ya bita
da kallo yana murmushin keta, ya cikin? Tace
yayi sauki ni xan koma gida sai gobe. Haba haka
da wuri? Yanxun fa 8 ta wuce? Kar a neme ni ne.
Wa xai neme ki? Don Allah xaumna muyi hira, ba
wanda xai nemeki, bayan sun san kina nan. Bata
da xabi, don haka ta xauna kusa dashi, ya shiga
bata labaran banxa. Jimawa kadan wani kare ya
xo gilmawa nan take ya hau kiransa, tace me
xakayi da kare kake kiransa. Kasan karen
okundiri fada gareshi ko? Yace bai sami nama
bane don ubansa okundiiri, ya kece da dariya,
okundirin ne ubansa? Lallai ka samo shi. Yacee
to da waye ubansa? Kinga bude ledar nan nama
aciki dauko ki ba shi. Yana magana yana shafar
kan karen. Tace, taf ya cafke min hannu? Kai
dai ka bashi kai da ka siyo masa,don raka
asara. Yace karki bani kunya mana, me xai sa
ya cije ki, bayan yasan ke bebina ce, ko kare? Ai
ka santa ko? Sweetheart dina ce kar ka cije min
ita. Tuni kanta ya fasu, ya jawo leda ya bude ta
dauko katon yanka ta mika masa tana fadin,
abin har da yaji? Sangarta! Ya kwashe da dariya,
yace ina ruwanki? Ke dai mika masa gudan. Ta
dauko ta mika masa, ya cafke, Dan liti ya runtse
ido yace yes! Ya xarce da dairya. Ta xuba masa
ido tace, menene abin dariya har da wani cije
labe? Yace ji nayi kamar ya hade da hannunki ya
gartse. Takai masa bugu a kirji tace amma kai
mugu ne! Yace sosai ma ashe baki sani ba
yarinya, to tashi kije gida an gama hirar, kinga
karen yayi tafiyarsa. Ka gaida okundiri kaji? Ta
ci da kyakyata dariya. Yace, ah! Tashi karki sa
yarona ya fito yana fito yana kyakyatawa kamar
dolo. Ta shi kije gida sai safe. Don Allah kiyi
hkr, so nake nayi wanka inyi sallah. Ta fido lah
nima har ka tuna min banyi ko magriba ba. Ta
juya da sauri tana cewa, sai da safe! Yace Allah
ya kaimu. Ya bita da kallo, yace yarinya kin
gama yawo kin shiga 3 kin lalace, ya daga
murya ki fa sami abinci ki ci. Ta juyo ta amsa,
kar ka damu xanci. Suka ja hankalin mutane,
don haka yama didi ya biyo baya, masu tsinuwa
nayi, masu addu'ae shiriya nayi. A tsakar gida
ta iske su Abba na jiran dawowar ta, shi da su
Alh. Basiru. Tana shigowa tasha jinin jikinta, ta
shiga bin bango, tana so ta shige falo. Alh.
Basiru ya daka mata tsawa, ke dawo nan! Simi
simi ta matso gun su ta durkusa guiwa 2, batayi
aune ba, taji saukar wani wawan mari. Gaba
daya ya ratsa kanta, ya gigita ta, ta dunkule ta
fasa kuka. A cikin ba tace ga wanda ya xabga
mata

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login