Showing 48001 words to 51000 words out of 110841 words

Chapter 17 - BAKIN CIKI BOOK COMPLETE BY ESHAT.txt

12 Sep 2025

83

tayi ,halin da
idanuwansa suka gane masa mama a halin yanzu
kwarai tausayinta ya kwanta a zuciyar sa shi ne
ya fara kai hannu ya ciccubo ta suka taimaka
suka sauko da ita kasa kamat matacciya,da kyar
likita ya karbe ta sai da yan uwanta suka yita
rarrshinsa sannan ya bata gado yayi mata duk
abinda ya dace. Acan yaya abdul- kadeer ya
same su bayan sallar magariba kafin ayi issha'I
suka rankaya gida akabar anti amina tare da
ita,kusan kwana sukayi shawarwari akan
al'amarin,kwana daya da wuni mama na kwance
magashiyan ledar ruwa goma sha tara ta
shanye,ana shirin daura mata na ashirin sannan
idanuwanta suka fara washewa ta gane inda take
hada ido da abba tare da karkaf yan'uwanta bai
haifar mata da wata nadama ba illa kuka da ta
fasa wai don su tausaya mata babu wanda ya
tanka mata wannan itace shawarar da suka
yanke babu wanda zai sake bata bakinsa don yi
mata fada amma zata sha mamaki ranar da
Allah ya yasa al'ameen ya dawo kasar nan,babu
wanda yace cikanki har ta gaji da shashekar
kukanta. A zaton ta shirun na su alamma ce ta
saduda ma'ana sun rasa yadda zasuyi da ita dole
suu sa mata ido anti amina ta fara bata ruwan
lipton tana kurba da kyar take iya hadiye shi
gaba daya Makogwaronta ya farfashe kafin gari
ya sake wayewa mama ta samo kanta misalin
goma da rabi kawai ganin su tayi sun shigo suna
gaya wa anti amina an sallame ta zasu wuce
yanzu bata yi mamakin jin haka ba don haka ta
amsa da to,Allah kara lafiya ita kuwa yar gigalar
murna ce fal cikin ta jin za a wuce da ita
fandogari nan da nan suka kwashe kaya,yaya
abdul-kadeer ya dauki matarsa,mama kuma tabi
ayarin komawa gida a minna suka yada zango
suka ci abinci tare da yin sallolin azahar da
la'asr in banda su ameera babu wanda mama
tayi magana dashi domin anti rabi ma ta sauya
fuska al'ameen dintama bai sami kulawa ba
suna idar da la'asar yaya abdul-rahman ya jawo
matarsa daga inda ya aje ta aka maida jakar
mama ciki ita ma ta fito ta shige gidan baya
abba na tare da karamin yaya a gaba Shi ya jasu
a hankali xuwa fandagori. tun daga kan kwana
hankalin mama ya soma kwantawa, domin dai
idanuwan ta sun hango wanda take son gani.
yana zaune bisa benci a kofar shagonsa, yayi
murmushi itama ta sakar masa nata. har motar
ta wuce, ba su daina leken juna ba. sai da ta
daina hangensa, sannan ta zauna sosai kirjibta
nata bugawa, ji take kamar ta balle murfin motar
ta fice taje gunsa. ya mikawa ayuba hannu suka
tafa. yace baka da kyau! Yace karya kak don
ubanka, kalle ni sama da kasa! ba kyawun sura
ba, ina nufin.... ya kai masa naushi a kafada, shi
ya katse shi. zan ci..... kai! ka kiyaye ni fa wlh!
me na gaya maka? yadda suka dauke ya ahaka
za su dawo min da ita. wahalar banza sukeyi
sakeena mallaka tace. yace ranar da Allah kuma
zai kama. ayuba baya wajen, duk ka gama
iskancin ka. ya ballo masa harara yace, to ko ka
na wajen me zakyi? kai ma ka ji da naka, don
ubanka. Menayi? ni nakai ka iskanci a garin
nan? dama wane kai, amma sannu a habkali
xzaka biyo ni mujera hanya watakila ma ka xarta
ni. ya tabe baki yace Allah ya sawwake, kai din
ma so nake na janyo ka baya. ka auri yarinyara
nan, ka manta da kudinrinka na wulakantata. ya
dafa shi yace ka dan kula da shagon, bari na je
nemo gasasshiyar kaza. kasan dole anjima ta zo
鎷� ya xuba masa ido kawai, bai ce masa komai
ba. yayi dan saurayin murmushin. ya mike ya
fada motar sa yayi birnin gwarin tsinke. kai
tsaye mama dakinta ta shige. umma bata
gasganta idonta ba, irin yanayin da taga mama
saboda haka tatashi tabi bayanta. Kallo daya
tayi mata taji kanta ya ci gaba da sarawa, wani
kululu ya daure xuciyarta, idanuwanta suka tara
kwalla, saboda tsabar BAKIN CIKI. Ta jima kafin
tace, Mama kina da hankali da tunani kuwa? Ji
tayi an dafata ta biyu, muryar Yaya abdul rahma
ke fadin, baki da lfya Umma, karki daga
hankalinki, abba yace ki fito ki kyale ta. Ya
kamo ta suka fito, jiri na dibarta, shi ya sa tace
yawuce da ita dakinta. Abba ya taso ya biyo su,
yayin da take kwanciya a gado. Gefen gadon ya
xauna yace, bai kamata ki bar ciwon ki ya tashi
ba halima, kin ji dai abinda Dr. Ya fada, jininki
ne ke hawa saboda damuwar da kika sanya a
ranki. Ki hrk kawai. Tace, ba alamun yin nadama
a wajen Mama, ni kaina, nasan haka,amma
shawarar da mu ka yanke da 'yan uwanta shine
mu sanya mata ido tayi shirmen ta, sai ranar da
Al-ameen ya dawo xata gane mu ma ba muyi
nadama ba. Abdul yace saboda haka ki kwantar
da hankalinki, ISA sai dai mama ta mutu a dakin
Al-ameen, ba zamu ji kunya ba. Su Yaya babba
da Iyalnsu duk sunce gaishe ki, sai sun xo. Tace
ina amsawa, Allah ya taimake mu, suka amsa
ameen. Abba ya dube shi ya cigaba, kai ma ya
kamata ka hanxarta wucewa yamma tayi sosai.
Umma ta amshe, ba xai bari xuwa gobe ba?
Yace, akwai aiki Umma, yanxun nake so na
lallaba. Ta dan kada kai. Tace, to Allah ya Tsare
agaida min safiyya da kyau. Zata ji, ki daina
damuwa Umma, komai xai wuce da yardar Allah.
Ta amsa da kai, tana fadin shikenan abdul, Allah
yayi maka albarka. Yace amin. Ya wuce cikin
hanzari. A tsakar gida ya hadu da su Haj.Hajjo.
Ashe da gaske ne kun dawo? Yara ke fada mana
yanxun. Yace eh, nima xan wuce kd kenan. Gaba
daya suke to Allah ya tsare! Ya amsa yayi gaba
abinda, su kuwa ciki suka kutsa kai dakin
mama. Kwakwazon surutun su ya sa Abba ya ta
so fito. Sannuku da dawowa Yaya. Yace yauwa,
ga haliman can a dakin ta. Haj. Hajjo tace, muna
nan mun ganin ikon Allah. Mama ta dawo kashi
ba rai? Yace haka take so, ai ku daina bata
bakinku, kowa ya sa mata ido. Haj. Gaje tace,
lallai kam wannan al'amarin sai ido. Allah ya
kyauta. Ameen. Suka fice tare suka koma dakin
Umma, suka isheta da surutu. Duk iya kokarin
mama na son fita a wannan daren abin ya
faskara, domin dai Abba ya kasa ya tsare a falo
har goman dare ya garkame kofar ya shige
dakinsa barcinsa. Allah da ikon sa, abba bai
xare mukulin ba, domin bai taba tunanin Mama
xata iya aikata wani abu a wannan tym din ba
lallai abba bai san Mama ta wuce tunaninsa ba.
Yana bada baya, taji motsin rufe kofarsa ta yi
wuf ta mike, takalmanta a hannu tare da
mayafinta. Tayo sanda ta fito jim, tsakar falon
bata ji mtsin kowa ba, sannan ta karasa kofar ta
bude ta cikin nutsuwa ta sulale ta fice. Can ma
kofar sassan hka ta bude ta, ta wuce zaurukan
gidan, ta zare sakatun ta bude ta fita ta maida
kofar ta sakaya. In bakayi bani wuri! Ta callah
da gudu bata ko jin rashin karfin jikinta, sai da
tayi rabin tafiya, sannan ta tsaya ta sa
takalmanta ta yafa gyalen tana ta xuba haki, ta
dau hanya babu jama'a sosai. Gata nan ga ta
nan har kofar shagon dan gogan. Ya tare da dije
a kofar shagon bisa banci, ta cukuikuye shi
kamar na goye fadi yake, wai dan Ubanki dole
ne? Kin fa matsa min da yawa, xan ci ubanki a
daren nan, in ga mai kwatar ki! Kawai ganin
mama yayi akan su. Ya banbare dije ya ture
gefe, bai bata lokacin ya daga kanta ya shige,
shagon yana jan tsaki. Mama ta daga itama ta
bishi. Dije kuwa mikewa tayi ta kakkabe jikinta
ta wuce tana kwafa. Ya hade rai a kujera, bai ko
kalle ta ba. Ta matsa gare shi murya sanyaye
tace, fushi kayi danliti? Ni ban yi fushi ba sai
kai? Ina can naki ci na ki sha saboda kai. Ashe
ka na nan ka tare da wata? Dubi yadda na rame
na sauya kamanni, saboda tunanin ka Danliti.
Bai kamata ka yi min haka ba. Ya dago
idanuwansa farare sol! Sunji kwalli ya dubeta, ko
mai nai miki ai kekika jawo, kinbi 'yan uwanki ki
manta da ni, ba dole in sami wata ba! Tun
yaushe kuka shigo garin nan? Nayi ta xuba ido,
amma ban ganki ba, me kike tunanin xan dauka?
Kafin tace wani abu ya fizgo hannunta xuwa
daki, yana kara fadin, idan karya nake yi, xo
muje ki gani! Ayuba dake kwance bisa katifa
yayi firgigi ya tashi yana kallon ikon Allah.
Ledar kaji ya janyo ya xaxxage su. Yace me kika
gani nan? Saboda ke na tafi har birnin gwari na
siyo miki gashin xamani kajin turawa. Dubi nan
juice ne kala-kala har sanyi su ya fita, baki xo
ba. Ba dole in yi fushi ba, in saurari mai so na!
Ta sauke numfashi, idanuwan ta taf! Da kwallah,
ba laifina bane Danliti, baka san irin bakar
wahalar da na sha ba, don kawai su dawo da ni.
Sau biyu ina kwanciya a ascibiti, dube ni da
kyau, kai kanka kasan ba haka nake ba. Amma
kayi hkr, tunda kana ganin kamar da gangan
nayi, ka hkr? Ya xura mata ido jim, sannan yayi
dan murmushi ya ware hannayensa yace, to
oyoyo! Ta sa hannaeyanta ta rufe fuska. Yace
kunya? Ashe baki so na, lallai na yarda ni kadai
nake haukan sonki. Yana rufe baki ta matso da
sauri ta rungunme shi. Ayuba, yayi gyaran
murya. Mama tayi wuf ta rabu da jikinsa. Ya
dubi Ayuba, yace malam ka fita ka bamu wuri!
Yace, ai ku ya kamata ku koma daga waje anan
nake so mu xauna, fita ka bamu wuri don Allah,
shago fah abude yake, ya yankura ya tashi yana
fadin, gaskiyya kuyi sauri ku gamacin kazaraku,
barci nakeji. Ba ruwanka wannan. Ya fice yana
waigen Danliti yana masa ishara da idanuwansa
dauke da gargadu, wanda shi kansa ya gane
nufinsa, shi yasa yake wani irin mur0ushin na
iya shege. Yana fita ya dubi Mama suka hada
ido dukkan su sukayi murmushi, sannan ya
kamo kafadunta yace, gashi dare yayi, amma
dole ki xauna ki cinye kajin nan, domin saboda
ke na siyo su. Ba tace komai bam ya xaunar da
ita gefen katifa, ya jawo kayan kwalama, ya baje
mata kajin, yana bata abaki, tun tana jin kunya
har ta saki jikinta, tana amssa sosai tana ci,
suka ci suka sha suna hirar bayan rabuwa. Bayan
sun kare. Danliti ya dubi agogonsa ya ce
shadaya da kwata yanxu, ya kamata kije gida
ko? Sai gobe, ina fatan xaki rika cin abinci don
ki gyagije kyanki ya dawo kamar da. Kinji ni?
Tace, naji kuma xan kiyaye, amma don Allah ka
daina bari 'yan mata na xuwa gunka, watarana
xamuyi dambe da su wlh, kaji na rantse. Ya
kyalkyale da dariya son ransa kafin yace, xaki
kuwa sha duka, don dai nasan sunfi karfinki.
Wannan jikin naki rugu-rugu babu kwari. Ya fadi
yana mammatsa hannayenta da kafafuwanta. Ta
yankura ta tashi tana cewa, haka kake gani, ka
maida abin wasa, zaka sha mamaki. Shima ya
mike ya kamo yatsunta, yace karki damu, ke
kadai nake so, ko da damben ya kama kuyi, xan
shigar miki balle ma banda lokacinsu. Ke me xai
dameki? Tayi murmushi, tace, to shikenan sai da
safe. Ya sumbaceta yace, muje na rakaki. Suka
fito yana rike da hannunta, tayi wa ayuba
sallama suka wuce. A kofar gida suka fuskanci
juna, tallafo kuncinta ya xura mata ido, yace
karfa ki damu da ganin Dije tare da ni, wlh ba
sonta nake ba, kawai ta matsa min ne dole muyi
soyayya, amma xan dauki mataki akanta, tinda
ta fara bata miki rai. Tayi murmushi, tace,
nayarda da kai, ina fatam Allah ya yarda mana,
ya bamu nasara abinda muka sa gaba. Da sauri
ya amsa amin sakeena. To sai da safe nagode,
wannan karon abin ya cigaba akan labbanta ya
sumbace ta. Ta juya da sauri, ta tura gida ta
shige ta maida sakatu. Danliti ya runtse ido ya
jinjina hannayensa, shege ni! Ya juya yana
takawa dda+dai kamar wani kasaitaccen
basarake. Mama kuwa sanda takeyi, kamar
barauniya ta turo kofar fa'aar dshigo ta mayar d
hankali ta kuleta, ta fada gado. Tana jan mayafi,
taji a; ttay bude kofa, tayi tsaye jim, sannan ya
mayar ya rufe. Muryar umma taji tana fadin,
menene alh.? Yace kamar motsin naji ana taba
mukulli.. Tace Innalillahi an shi ne? Yace amma
ban ga kowa ba. Ya dubi agogo, karfe sha biyu
saura kwata, dare ma bai yi ba sosai, to Allah
yai mana tsari da sharrin masu sharri. Yace
amin, je ki kwanta. Cikin fargaba suka bar falon.
Mama ta gyara kwanciya tana gyatsar naman
kaxa. Dan kanta tace kwanta naman kaza. Tayi
tunani Danliti har barci ya kwashe ta, shi take
marfi yana sa mata naman kaza abaki. Da safe
tayi wanka, duk 'yan ciwukan da suka rage ba su
warke ba, ta goga musu mai, ta shafa hoda ta
sa atamfah riga da xani, nan da nan ta dan yi
fasali, duk da cewa akwai rama sosai a jikinta.
Yau kam tayi dan kyan gani, ta fito falo wajen
Umma cikin kicin inda take aikace aikacenta,
tace sannu Umma ina kwna? Ta juyo da sauri ta
dubeta sama da kasa, tace kalau na kwana. Ta
kara matsowa tace, bari in gaida Abba, sai in xo
in tayaki aikin. Bata amsa ba ta fice, ta bita da
kallo sannan ta kada kai tace, Allah ya shirya.
Dakin Abban tayi sallama, ya amsa ya bita da
kallo, ta karaso gunsa ta tsugunna, ina kwana
Abba? Yace Kalau, ta dan dube shi, amma bata
kara komai ba, ta mike tayi waje ta koma kicin:
Umma me xan tayaki? Tace ban so, koma
dakinki kawai. Saboda me Umma? Ai ban isa na
fadi ko saboda mene ba, tunda kin xama
shafaffiya da mai. Je ki kawai ki sha xamanki.
Kai tsaye kuwa ta wuce daki abinta. Tana fadi
cikin ranta, kya gama girkawa, mu zo mu jajja
(hmmm mama tayi nisa walle). Kan Umma ya
sara ganin yadda mama ta wuce ko ajikinta,
bata damu ba. Mamaki bai gama kashe Umma
ba sai da ta hange ta kicin din tana diban abinda
take son ci. Tana kallo ta koma dakinta ta cinye,
ta maida kayan kitchen ta fito. Haushi ya kume
Umma bata san tym din da tace, Uban wa kika
ajewa kayan ya wanke miki? Tabbatacciya! Ta
dan bata rai ta juya ta kwaso kayna ta wanke.
Karfe 9 abba ya fita harkokinsa. 9:30 mama figi
gyale tayi waje, Umma nace na wanka. Ta sha
hirarta wajen Danliti har 12pm sannan ta
tsallaka ta gangara wajen Baraka. Sosai taga
sauyin fuska wajen Inna saude. Sam abin be
dame ta ba. Suna kebewa da Baraka tace.
Kawata ban gane ba, sai da nayi miki kallon
kurulla. Yanxun saboda Allah dawowa kikayi?
Tace ga ni kuma kina ganina. Matsala tace,
babu ruwan kowa. Mutane masharanta ne kawai,
saboda Allah yayi wa Danliti kyau da farin jini,
ga shi ya Rufa masa asiri, shi ya sa ake masa
hassada.... Ta katse ta, idan hassada ce, ai
kuwa kem kinyi masa da. Menen baki fada ba
akansa? Tace, Rashin sani ne, duk surutan da
akeyi wai dan Iska ne dan guguwa. Dan wata
tsiyace, ni har yanxun Danliti bai taba furta min
maganar banxa ba balle ya nemi aikata wani
shashanci. Rashin fahimta ne kawai yasa ake
masa zargi, kisan mutum mai farin jinin
'yammata (Kuji fa wai bai taba mata komai ba?)
baki ganin ko mace ce ta fiye samari sai arinka
mata wani irin kallo? Baraka ta sauke fuska,
tayi guntun tsaki, baki jin kira Mama. Allah ya
shirye ki. Ameen, ni bari in koma gida, dama
lekowa nayi mu gaisa kisan na dawo. Tabita da
kallo, ki na san kin dawo wajenki xano? Menene
anfani kawancen mu? Bayan ko na gaya miki
gaskiyya bakyaji. Allah ko? To Allah ya bamu
alkhairi ki gaida mohd dinki, in yazo. Yaushe
xasu kawo gaisuwane? Ko bai shirya aure bane?
Wlh ban masa zargin komai ba, amma sonsa bai
rufe min ido ba, ina bukatar in gama sanin ko
shi waye tunda ba gari daya muke ba. Ta tabe
baki, Baraka ke nan, Miss kakale! Ba kakale
bane, gaskiyya ce kawai, daga kinta sai bata.
Shi ya sa nake nuna mikita, don banson ki bata.
Ta mike hannu daya kame da kugu, tace,
nagode, ni nayi gida, kar Umma ta neme ni. Tasa
kai tafice. Baraka ta biyota, ta sallami Inna ta
rako ta iya zaure ta juya. Ta shige gida, tabar
mama dauke da mamaki. Tai kwafa tace, kiyi da
gwana yarinya. Ta kama hanya ta koma wajen
Danliti, wasa-wasa sai da ta bata mini talatin
anan, sannan ta karasa gida. Umma na zaune
tskar falo ta sha tagumi, ta gaji Mama ta shigo
babu ko tsoro ko fargaba tace, sannu da gida
Umma. Inna saude na gaisheki. Ta zura mata ido
ba tare da cire tagumin ba, jima kafin tace, da
izinin wa ki ka bar gidan nan Mama? Ta
mimmike kafa sosai akujera. Tace ai kinshifa
wanka ne Umma shi yasa banyi miki magana ba.
Umma ta numfasa, tayi hucin BAKIN CIKi tace,
lallai kin isa mama, duk son danliti ne yasa kika
zama maras kunya? To kibi a hankali, duniya
zata koya miki hankali, muddin kika dauke ta
kika goya. Ta figi gyalenta, ta mike cikin sauri
tana fadin, Uhm.....! Ta wuce ta fada dakinta,
tayi kwanciyarta. Umma ta kada kai, kwallah
suka xubo mata, ta share tace, Allah kana kallo,
munyi iya yinmu, amma shiriya na wajenka, kayi
mana gaji Ya Allah. Nan Umma taci gaba da
zama tana shan BAKIN CIKI tare da takaici mai
tarin yawa har aka kira azhar, ta tashi tayi
sallah. Abba ya dawo ta labarta masa, hannaye
biyi ya kama kai, takaici kamar ya kashe shi,
bai niyyara kara yiwa Mama wata magana ba
akan Danliti, amma dole tasa ya kira tazo
dakinsa ta xauna. Yayi mata kaca-kaca, sannan
ya sa mata dokar fita ko'ina, duk da yasan ba
dole bane tabi umarninsa. Tabbas hakan ne,
yadda Mama ta fito dakin bakin nan nata ya kai
wani gari wai shi ZUNTU. Shi kasna ya san
rashin kunyta Mama ta kai wani mataki na
kololuwa kwatance, ta xauna bakin gadon ta
tana fadin a fili, wannan shine bature ke kira
Impossible! Tunda kuka hana shi xuwa guna,
dole inje gunsa mu ga juna. Ta saki wani
lafiyayyen tsaki, ta yada kai bisa filo.........
Maganar mama dutse. 7days kenan babu abinda
ta fasa, muna iya cewa al'amarin kara haukata
yayi. Domin a halin yanxun Mama bata shayi,
agaban Umma zata dauki mayafinta, ta fice.
Umma na kira, tana fadin tana xuwa yanxu xata
dawo. Sau uku Umma na xuwa da kanta kofar
shagon Danlinti, tana taso keyarta. Jama'a na
kallon su, gwanin ban kunya. Sai da Abba ya
hanata xuwa. Yace tasa mata ido, tunda ta zama
gagararriya. Wannan abin kunya ya zama abin
yayatawa awajen su hajjo, duk inda suka xauna
xancan kenan. Babu abinda bai dawowa kunnen
Umma ba, sai dai tayi kuka ta share hawayenta
ta barwa Allah komai. Mama fa ta gagari kowa,
suna ji suna gani mummunan labari na ta
yaduwa har gidan Gwaggo Hausi. Daga can
labarin ya mika gidan Marafa. Nana take mami
ta tsani auran mama da Al-ameen. Shi kuwa
Marafa nuna mata yake su daina kama jita-jita.
Aure dai nufi ne na Allah, idan sakeena matar
Al- ameen ce, bbu makawa xai aureta, idan kuwa
ba matar sa bace si barwa Allah yayi masa zabin
alkhairi. Duk da haka al'amarin yana jefa Mamai
cikin tunani ba kadan ba, kuma da Al-ameen zai
ji shawarar ta, da ta umarace shi daya hakura da
sakeena, tunda shasahnci tasa gaba. Sallar
la'asar ta kammala, amma bata bar sallayar ba,
saboda gabatar da lazimi takeyi. Wata tasi tayi
fakin kofar gidan, direban ya fito ya bude but,
yana fido jakar kaya. Yana rufe but din,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login