Showing 45001 words to 48000 words out of 110841 words

Chapter 16 - BAKIN CIKI BOOK COMPLETE BY ESHAT.txt

12 Sep 2025

63

kujera ta kama kai hannu
biyu ta matse kwallan ta tace wannan masifa
Allah ka yaye mana,muryar mai gidan taji yana
fadin kema zai zauna kina bata lokacinki yau mu
ma bazamu ci abinci ba ke nan Ta share fuska
ta dube shi yallabai ba ka ki kalaman dokta bane
su suka kara dafani wallahi ya ya zamuyi da
yarinyar nan ne yace oho!ni kizo ki ban abinci
ina jin yunwa ta mike ta nufi kicin shi kuma ya
wuce ebur yana kiran malami ya sauko da gudu
yana amsawa gani dadi kaima yau baza kaci
abinci. Bane yace ai na ci dadi to koma daki
kayi barci sai da safe,ya juya ya haye saman
yayin da anti amina ta fito da jerin kayan abinci
bisa tire ta jera bisa tebur sannan ta zuba masa
taja kujera ita ma ta zauna yana ci tana maida
masa kalaman al'ameen sai da ta kare ya kurbi
ruwa ya dube ta, Yace ni kinga duk wannan
shiriritar ina yi ne kawai saboda hajiyar sa ta
roki a rufe masa amma ni ban ga dalilin yawo da
hankali ba yanzu ina fa'idar yin shirun tunda
hankalin sa da ake so ya kwanta bai kwanta ba?
mama ko zata mutu shi zata aura to me ne ne
abin jin tsoron gaya masa matsalar da ake ciki
banda shiriritarku ta mata,ta ce ai ba haka bane
yallabai kaga kuma shi kansa marafa ya goyi
bayan hakan"shi ke nan sai ki yi ta rarrashinta
kafin gobe idan ta amince yin maga da shi shi ke
nan idan kuma taki kya nemi wata karyar ki
shirya masa kinga sharo karya ya same mu ke
nan sai abinda Allah yayi ina amfanin sa Ta
numfasa tace al'amarin hakuri zamuyi tayi
rokona gare ka don Allah ka daina dukanta
wallahi taurin kai zai kara mata ido waje yake
magana muddin tayi min rashin kunya zan
tabbatar da na hukunta ta yadda ya kamata don
ni ba sa'an ta bane,you know that so ba zan
dauki iskanci ba kina iya hawa sama idan kin
kare maganar,tace ran maza ya huce yallabai ba
ina nufin wani abu bane yaci gaba da cin
abincinsa bai tanka ba ta zura masa ido tana
dan murmushi ta san halin yan kayan ta idan
kayi magana kaji yayi shiru to kaima ka tsuke
dan bakin ka ka kama kanka shi zai fi zama
alkairi. Garin Allah ya waye,baya ga sallah babu
abinda Mama ta aikata,ta yada kai bisa kafet
tayi lamo kamar sumammiya.Gaba daya ta
rame,fuskar ta ta tsuke duk ta bushe idanuwanta
sun kode sun firfito waje, sbd tsabar
kuka.Malami ya fito wanka ya tsugunna gabanta
yace "鐭沶a kwana Anti?Tayi banza dashi,ya zura
mata ido,Baki da lafiya ne Anti? Tunda ku ka zo
da Daddy baki min mgna ba. Ta ballo masa
harara,sai na tsinka mka mari ka sake min
magana! Ta ja tsaki,ta juya kan ta wani
gefen.Haushi ya kama shi,ya tashi ya ci gaba da
shirin sa. Wannan karon kam bai gane kan gadon
Antinsa ba. Me ke faruwane? Karfe bakwai daidai
Anti Amina ta shigo,tana shigowa Mama ta
rintse ido. Anti Amina ta dauko bisa kanta,ta
dan dafa ta na san ba barci kike yi ba,ki tashi
don girman Allah ga Dokta can ya kira. Kamar
yadda na gaya miki jiya so yake yaji muryar
ki,hankalinsa ya kwanta ko da gaisuwar sa ki
amsa,zai ji dadi Mama.
BAKIN CIKI 2***6(TRUE LIFE STORY) Ku da baku
wurin in kun amsa.To Mama ta amsa. Haushi
kamar ya kashe anti Amina.ta mike tsaye tace,
kar ki tashi Mamaa,idan kin sake jin nayi mik閾�
mgn akan Al-Ameen,duk abinda kika so kiyi
min! Mts....... Ta ja tsaki ta wuce. Mama ta
rakata da nata dogon tsakin anti amina ta waigo
rike da kugu ta zubo mata ido,lallai mama,ni
kike yiwa tsaki? Yayi miki kyau! Taja kofa ta
fice.kan wayar ta duka rai bace. Tace, hello!
Yace hello anti,ta tashi? Bata tashi ba dokta.
(nace"dokto ka fiya nace dolene?) "ba matsala,ai
barcin ma yana da amfani a gareta.zan sake
kira,ngd ant閾�. Cike da tausayinsa ta amsa,kar ka
damu sai anjima. To suka aje waya. Ta haye
sama shake da haushi,amma bata nuna wa
yallabai ba,don ta san ita zai tsatstsage danya.
Iyaka tace da shi bata tashi barci ba Wasa wasa
mama fa har ta sake kai bayan la'asar batasa
kwayar abinci a bakinta ba hankalin anti amina
ya tashi kwarai da gaske mama kam bata cikin
hayyacinta gaba daya ta galabaita yunwa na
neman tayi mata illa koma in ce tayi
matan,shiyasa tana jin waya na ta bugawa taki
dagawa don tasab mai kiran kuma bata da
abinda zata gaya masa a hakikanin gaskiya ma
hankalinta yafi rinjaye akan mama dake ta zama
da yunwa tun safiyar jiya Tayi fada tayi rarrashi
duk a banza misalin karfe biyar ta hada tea ta
shigo da shi dakin wai ko Allah ya bata sa'a ta
dan kurba me zata gani mama ke ta madedewa
tsakar daki wata irin farar kuffa na hauhawa bisa
bakin ta,tasaki kofin tea ta tarairayo ta tana
sallalami kinga irinta ko mama nayi nayi dake
kice abinci kin ki kina so ki kashe kanki a banza
a rude ta sake bazamowa falo ta dauki waya ta
kira wayar ofishin yaya abdul kadeea ta shaida
masa halin da mama ta shiga Amma yanzu za a
fara wucewa da ita asibiti nan take ya bata izini
yace zai same ta asibitin babu baa lokaci soja
daya ya sakata mota anti amina na tare da ita a
gidan baya tana shafa mata ruwa a fuska sojan
na jan motar an bata gado ga ledar ruwa na aiki
a jikinta, wucewa minti talatin yayan ya iso ya
same su jugum jugum,suna kallon ta rai bace ya
watsa hannaye aljihu yace dama haka take so ba
kuma shi zai taimaketa ba muddin tana motsin
rai al'ameen ne mijinta so idan ta farfado ki fara
gaya mata kafin na dawo zan koma ofis muna da
mitin,tace to adawo lafiya ya wuce cikin
kuzarinsa kuratan sa na biye da shi har bakin
mota suka koma sannan guda ya bude masa ya
shiga direban yaja suka wuce,anti amina ta ci
gaba da zama dauke da tagumi zuciyar ta na
mata saka iri iri haka wayar al'ameen ke ci gaba
da bugawa cikin gidan ba a dauka ba malami ya
shigo gidan dawo war sa ke nan daga maka
ranta,kicin ya wuce kai tsaye saboda yunwa ce
ta koro shi ya debo abinci ya zauna ya fara ci
waya ta sake daukar ruri ya mike da filet din a
hannunsa yana kara lomar shinkafa da salad ya
dauki waya baki cike da abinci ya ce hello hello
malami al'ameen ne ba kowa ne a gidan yace eh
nima yanzu na dawo school mai gadi ya gaya
min sun tafi kai anti mama asibiti wai ta suma.
Jikin al ameen Ya kara mutuwa ya ce gaskiya
Uncle duk ta rame kamar ba ita ba bata magana
sai kuka Tunda suka dawo da dadi ba ta ci
komai ba ko ni bata. Yi min magana ba sai yau
ta ce za ta mare ni idan na sake gaishe ta wane
irin ciwo take yi uncle hawaye suka tsunke wa Al
Ameen. Bai san lokacin da ya kife kan wayar ba
malami yabi ta hannunsa da kallo. Bai gane
komai ba dan haka shima ya aje ya dauki
abincinsa ya cigaba da ci yayi sallar magariba
dadinsa ya shigo yayi masa sannu da zuwa ya
amsa ya haye sama ya cire kaki yasa kana nan
kaya jaket da wando ya sauko ya shiga kicin ya
hada kayan abinci cikin dan matsakaicin kwando
ya kira malami yace kai mota ya jirashi can su
tafi asibitin,yace dadi yauwa uncle al'ameen ya
kira waya dazun me kagaya masa na gaya masa
anti ta sume kunje kai ta asibit to ke ka kirani a
mota ya dauki kwando yayi waje jim kadan
dadinsa ya fito suka tafi har zuwa lokacin mama
bata gane kowa yayan ta ya zauna nan zuwa
goman dare sannan suka koma gida da malami
Anti amina ta kwana tare da ita kiran asubahin
farko ta dawo hayyacinta ido ta zurawa anti
amina kafin ta fasa kuka anti amina ta matsa
gare ta ta dafa ta saman goshinta tace me yasa
kike wahalar da kanki bayan ki na sane da cewa
aure tsakaninki da al'ameen babu fashi,ta goge
hawaye wallahi wallahi anti bazan. Taba cin
abinci ba har sai yaya ya maida ni inda ya
dauko ni kinji kuma na rantse bazan kaffara
ba,baki sake take kallonta tama rasa ta cewa
mama ke ci gaba da fadin na gwammace na
mutu da a raba ni da dan liti sabo da haka mu
zuba nida yaya idan jan idonsa zai sa in daina
son dan'liti anti amina tace gadkiya ne kuma
yanzu kika tabbatar min kinyi nisa ka kya jin
kira To abinda zan gaya miki shine ki guji bacin
ran iyaye rayuwa ki ba zatayi kyau ba muddin
kika bar mahaifanki da BAKIN CIKI sannan dole
ki fuskanci kalubale tunda kika ci amanar dokta
bazan rufe miki ba mama koda nan gaba in ta
Allah ta kasance zaki tuna dani kice na gaya
miki a asibitin nan wallahi yadda kika sanya
al'ameen kuka da radadin zuciya kema sai dan
liti ya dandana miki fiye da hakan Da namiji ne
fa ki bari ya gama shanye romon da yake hange
a jikin ki kisha mamaki daidaiku ke da rikon
amana su ajiye ki ke kadai suna girmamaki a
matsayin matar sunna mai tsananin kamanta
gaskiya shi ne zai ce kik zai kara aur amma
sauran shagalinsu suke sha a waje su barki hoto
a gida balle wannan Dan'liti daya sami shaidar
banza don haka kibi a hankali mama so ba
hauka bane tace na ji kin fada amman yarda ba
dole bane ko ashe kin gane domin ni duk abinda
mutun zai fadi akan Dan'liti ina daukar sa a
matsayin hassada ina abin hassadar ga Dan'liti
koda ban san shiba labarinsa ya gamsar dani
kuma na tsane shi idan kin tsane shi ki daina
maganar sa don zai sanima in tsane ki Ta ware
ido sosai tana kallon ta ban yi mamakin jin
kalamanki ba tunda kika iya shafawa idanuwanki
toka ba kya ganin mahaifanki ki balle ki saurari
nasihohinsu gareki kin ban kunya mama ban
taba zaton wata rana mai kamar wannan zata
zoba in sha Allahu zan rarrashin dadin malami
ya kyale ki duniya ta koya miki hankali,ido cikin
ido ta bata amsa zaifi kyau idan kika yimin
wannan kokarin haushi yasa anti amina ta mikie
ta fito babban falon asibitin tayi zaune har aka
kira asalatu tayi alwala tayi sallah ta je ro
addu'o'I tare da rokon Allah ya sanya wa
al'ameen dangana idan har ya rasa mama Cikin
shigar kakinsa tsaf ya shigo asibitin tare da
malami shi ma sanye da kayan makaranta
kuratan sojoji biyu na take masa baya dauke da
kwandon kayan karin kumallon safe a babban
falo ya same ta zaune bisa dardumar
sallah,malami ya fara isa gun ta ya gaisheta ta
amsa sojojin dake biye suka kwashi gaishuwa
yayin da ta miki ta tarbi yallabai amma fuskarta
babu walwala sannu da zuwa tace dashi ya amsa
yauwa ya dai jikin na ta, tana ciki shiga ka
ganta ai ta farfado tun asuba,ko?suka jera zuwa
dakin tana gaishe shi jin muryarsa yasa mama ta
runtse ido ya tsaya kanta yace ki daina matsr
ido nasan kina ji na ina fatan amina ta gaya
miki sako na saboda haka ina son ki gane
wannan sakarcin bazai firgitani ba abinda na
sani kawai al'ameen ya dawo a daura maku aure
middin kina numfashi sauran shawara ta rage
gare ki, Anti amina dake ta kallon ledar ruwa
tasa hannu ta dago igiyar tabbas abinda take
zato shine din. Ruwan ba a jikin mama yake ba
cirewa kikayi mama, ta juya kan yallabai tayi
masa kuri ka gani ko ta cire ruwan yaya ya kawo
iya wuya kamar ya nannausheta yake. Ji cikin
fushi ya juya ya fita anti amina tace da kanki ki
ka kama drip din ki ka tuge,sau dubu aka samin
sau dubu zan cire me ruwanku dani tunda baku
kauna ta tana rufe baki yayan na shigowa da
wasu nosis biyu amma abin karin haushin mama
taki yarda su mai da mata ledar ruwan nan basu
san lokacin da yayanta ya cire hannu ya tsinka
mata mari ba,sai da bakinta ya tsatso jini
saboda haushi da takaici kafin ayi haka ya bar
dakin anti amina ta biyo bayan sa ta bar nosis
na rarrashin mama yana shiga mota ita ma ta
fada ciki tace kayi wa girman Allah yallabai
karkayi fushi ka tsaya ka saurareni kar ki min
magana akan wannan wawayar yarinya," I have
finish with her, dama munyi waya da abdul-
kareem sun ce za su zo harda abdul-rahman so
suna zuwa zasu wuce da ita daga can su bata
kudin mota ta wuce fandogari zan iya kashe
yarinyar nan idan ina ganinta, tace wallahi ni ma
shawarar dana ke son in ba ka ke nan idan kaji
maganganun da mama ke fadi zaka tabbatar da
tayi nisa bata jin kira sai addu'a kawai zamu
zauna ne tana bamu wahala koda yaushe mu ma
asibiti a aikin banza?ba zai yuwu ba a irin take
taken ta tana gab da fara sufa mana zagi ku
kyale ta da dan-litin shi ne zai koya mata
hankali,yace ai an gama dokta zuwa kice ya
sallame ku kawai zan sake kiran abdul- kareem
din in ce su dame mi gida ta numfasa don murna
kafin tace,"!58,naji dadi yallabai Allah shi
taimake ka ita kuma ya shiryar da ita amin ga
break fast can kije kici ki kyale ta bari mu kai
malami school gada can zan shiga ofis to a
dawo lafiya amin,ta fito sannan sojojin suka
taso daga. Inda suke tsaye tare da malami suna
jiran su babu bata lokaci suka bar harabar
asibitin anti amina ta koma ciki tace wa nosis su
kyale ta su tafi abinsu guda tace oga zaiyi fada
madam idan ya shigo. ni nace ku tafi kawai abin
ku ba mu muka kawota ba,kuma mu zamu biya
bill ku wuce kwai ba wani abu"nosis suka wuce
da mamaki anti amina ta hada abin kari ta hau
ci bata sake komawa ta kan mama ba har likita
ya shigo misalin takwas da rabi na safiya anti
amina ta maida masa bayanini yallabai likita
yace a'a baza ayi haka ba nan ya ja kujera yayi
ta rarrashin mama,tayi shiru kamar da gaske
sauraronsa takeyi da kansa ya nemo jijiya ya
maida mata ruwan amman me yana gamawa bai
ko bar dakin ba ta sa hannu ta zare ta aje masa
robobin sa haushi ya shake likita ya jima yana
kallon ta sannan ya dauki (file)din ta yayi
rubutu,ya dubi anti amina yace kuna iya tafiya
gida madam da alama ba zamu shirya da
sakeena ba tace ai dama na gaya maka kayi
hakuri dokta kan ta tayi mawa tace ba wani abu
shawa ta kawai ia ce ku kyale ta ta auri wanda
ta zaba may be rabon wahala ke kiranta,tace
sosai kuwa dokta mun gode ji suka yi mama taja
wani shegen tsaki duk suka bita da kallo likita
yace I'am sorry for yau,a tunaninki kinyi abu Mai
kyau ke-nan? NO,ba hk rayuwa take ba. Ya
kamata ki rinka kulaw. Ya sa kai ya fice.Nosis
din sa suka take masa baya,kowanne su babu
wanda bai shak鐭� taikacin Mama ba. Tana hada
kaya direba na shigowa, yaya ya turo shi,idan
anyi sallamar ya kaisu gida. Shi ke nan kaya sun
tsunke karkashin kaba. Ya kwashe kaya,ta dubi
Mama tace, ki na iya tasowa muje gida,idan kin
so.Ta yunkura ta tashi,Anti Amina bata
saurareta ba ta wuce abin ta. Da kyar ta sauko
daga gadon,wani mugun jiri yayi tafiyar ruwa da
ita,ta koma dabas! Ta zauna.(maganin mara jin
magana,yarinyar nan tana ban haush鐭�! Mts!) Tafi
minti uku dafe da kai,sannan ta sake mikewa ta
daddafa bango ta fito tana layi. Kowa kallon ta
yakeyi,musamman Noisis din da komai ya faru a
gaban su,ai nan take aka shiga maida labari. A
mota ta same su. Anti Amina na gidan baya,duk
ta kulle sakatun kofofin biyu,saboda haka dole
Mama ta bude murfin gaba ta zauna tare da
direba. Ko a cikin gidan ma,babu mai kula
wani,hasalima Anti Amina kwanciyar ta tayi
tasha barci,bayan ta yi wanka ta sauya kaya.Ita
kuwa Mama taci gaba da sanya tsananin kunci
cikin ranta,ji take kamar ana hura wa zuciya ta
wuta.Tsananin son ganin Dan-Lati da kewarsa
suka hana ta sukuni. A yadda jiri ke dibar ta,sau
uku tana fitowa waje ta tsaya wai ko zata ga
lakwa-lakwa ta sulale ta gudu.Amma ina,ko
fuska babu a wajen kuratan nan,balle ta sami
hanyar fita.Don haka ta kifa ciki tsakar falo,tayi
ta sharara kuka har azahar,bata san lokacin da
barcin wuya ya sace ta ba. Anti Amina ta sauko
tayi girki ta gama bata farka ba.Dawowar
Malami ya kwarara sallama',shi ya tashe ta,tayi
doguwar mika tare da hamma mai kunshi da
yunwa da wahalar duniya. Ta tashi zaune taja
jikin ta,ta zauna ta jingina da kujera,wucewar
'yan mintoci.sannan idanuwan ta suka kwalli
agogo.karfe daya hard a rabi. Da kyar ta yunkura
ta tashi ta haye sama a wahale,tana shiga dakin
ta zube a kasa,sbd babu karfi a jikinta.Malami
da ke cire kayan makaranta,ya zubo mata
ido.yana so ya gaisheta yana jin tsoran mari. Ya
sauya kaya,ya fice daga dakin,wajen Momin sa
ya shiga idanuwan sa cike da damuwa. Ya zauna
kusa da ita,tana kallon yadda ran sa ke bace,don
hk ta rungumo kafadun sa tace, "Yaya dai,yunwa
akeji? Ya kada kai yace, Momi Anti fa zaa
mutu,ku maida ta asibiti.Allah bata warke ba. Ta
zura masa ido,tace,Ba laifin mu bane Malami,a
gaban ka ai kana kallo taki yarda asa mata Drip.
To ya take so muyi?" Yace, kawai ku kira mata
abba yayi mata fada. Wlh bana son Ant閾� ta mutu.
Ina son ta Mom鐭�,me yasa take ta wannan ciwon
ne? Ta kara rungume shi tace, kowa ma nason
Antin ka Malami,kuma babu mai son mutuwar
ta,Matsalar taki cin abinci ne,shi yasa ka ganta
haka. To sbd me? Tace kaga ka yi shiru da bakin
ka,kai yaro ne ba ruwanka da maganar
manya.kai da鐭� idan ka yi sallah ka roki Allah ya
bata lafiya. Yace, To Momi,tace. Maza kicin ka
zuba abincin ka.'ya fice tana kallon sa. Zuwa
karfe biyar Mama ta sake fadawa cikin
mummunan hali,bata gane kowa. Anti Amina ta
rasa inda zata sa ranta,domin ta rasa yadda
zata yi da Mama don ta ceto ran ta. Ta sauko
falo da nufin kiran wayar ofishin yallabai.
Shigowar mota harabar gidan,shi ya dauki
hnklnta ta zage labulan taga ta daga.Motar
Abdulkareem ke fakin a harabar aje motoci,ta
dawo da sauri ta nufi kofa cike da farin ciki da
baya misaltuwa. Ta bude kofar tayi waje,farin
cikin ta ya karu,ganin har da Abba acikin su.
Sannun ku da zuwa! Ta isa wajen tana fadi. Duk
suka amsa,sannan suka rankayo cikin gida.
Malami ya rugo ya rungume Abba. Bayan gaishe
gaishe suka tambayi Mama. Tace,tana daki babu
kyan gani,nama fito ne,in kira dadin Malami ko
za mu sake komawa asibitin ne,sai gaku. Wlhy
Abba taki cin komai tunda suka zo garin. Ban jin
tasa ruwa a bakinta,wannan masifa dame tayi
kama? Duk suka yi shiru sbd takaici,babu wanda
ya tanka har Anti Amina ta mike ta kawo musu
abincin da ababen sha. Ruwa kawai suka sha
Abba. Ya-ce, muje mu ganta. Duk suka rankaya
saman. Yanayin da suka riski Mama,ba karamin
daga hankulan su yayi ba. Abba ya zura mata
ido,idan da zai hadu da ita a hanya,ba zai shaida
ta ba,sbd sauya kamannin da tayi,sbd tsananin
son cikawa al-ameen alkawari ko alama bai bar鐭�
tausayinta ya rinjaye shi ba. Don hk ya dubi
sauran yace,wannan ba shi zaisa mutuncin mu
ya zube a idon duniya ba.sbd hk zamu koma da
ita asibiti,ta farfado.sannan mu wuce da ita
fandogari. Farin ciki na Mama ta mutu a dakin
nauran al-ameen wanan shne kwanciyar hnkli na.
Ku dauko ta mu tafi.
gaskiya ne abba shi kuwa yaya abdul-rahman
abin ne ya zame masa banbarakwai don bai taba
zaton labarin da yakeji abin ya kai haka ba duk
da yana jin zafin abinda mama

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login