Showing 102001 words to 105000 words out of 122360 words
Chapter 35 - A sanadin Son ki Hausa Novels Document complete by Aisha A Muhammad Sanaz.txt
mata kallon junan su kawai suka tsaya yi cikin wani irin shauk'i da tsananin kewar junan su............
Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻
*A̺͆ S̺͆A̺͆N̺͆A̺͆D̺͆I̺͆N̺͆ S̺͆O̺͆N̺͆ K̺͆I̺͆*
Wྂrྂiྂtྂtྂeྂnྂ bྂyྂ
Aྂıʂɧąɬ Aྂ Mྂųɧ'ɖ
ɖɛɖı¢ąɬɛɖ ɬơ ɱყ ʂąɖɛɛყ ʂąŋąʑ
♻ *єχ¢ℓυѕινє ωяιтєя'ѕ fσяυм*
*PAGE 106-107*
Kallon shi tayi da niyyar yi mishi tsiwa sai dai suna had'a ido duk wani abu ya kunce mata kallon junan su kawai suka tsaya yi cikin wani irin shauk'i da tsananin kewar junan su tare da wata irin zazzafar kauna, sun d'auki wajen 5 minute suna aikawa da junan su kallo yayin da Sabeer ya kasa jure kallon da suke aikawa junan su ya fara matsar da fuskar shi saitin fuskar ta da niyyar yayi kissing d'in cute pink lips nata wanda yayi tsananin missing d'in su a lot.
Jin saukar numfashin shi kusa da hancin ta sosai ya sanya Suhaima dawowa cikin hayyacin ta ta daddage ta fiske jikin ta daga jikinshi, sai dai yanda ta fisgi jikin nata ne ya sanya ta tafiya baya da d'an k'arfi kamar zata fad'i k'asa yayin da Sabeer wanda gaba d'aya kasala ta baibaye shi ya biyo ta shima.
Sauran kad'an Suhaima ta saki ihu na tsoro sai taji ta fad'a saman bed yayin da Sabeer ya biyo ta shima cikin jikinta, lokaci d'aya suka sauke wata ajiyar zuciya sai dai kowannen su da banbancin ajiyar zuciyar tasu Suhaima ita ta jin dad'in bata fad'i k'asa ba shi kuma Sabeer na jin shi rungume da Babyn shi a jikinshi wanda ya d'auke tsayin lokaci da su had'u kamar haka.
Kok'arin tashi take amman ya wani rik'e ta k'am kamar wanda za'a kwace mishi itaa haushi ne ya ishe Suhaima ta d'aure fuska cikin fusata tace
"Malam wai me kake nufi ne haka ni ka d'aga ni wallahi ko nayi maka ihu "
Murmishi Sabeer yayi kafin yace
"Haba Baby nah kinsan nayi missing d'in ki da yawa ki barni ko na samu kwanciyar hankali da nutsuwa cikin zuciya ta "
Haushi ne ya k'ule Suhaima don haka tace
"Kada ka mance da bakin ka kace min ka tsane ni me yasa zaka zo inda nake nima kasani na dad'e da tsanar ka tun lokacin da ka furta min haka "
Jikin Sabeer ne yayi wani irin sanyi wanda Suhaima har ta samu ta ture shi daga jikinta ta mik'e tare da d'aura d'an kwalin kanta ta wani kalle shi taja tsaki ta fice daga d'akin gaba d'aya.
Tana fitowa suka had'a ido da Aunty Aliyah da take zaune can gefen kitchen tana aiki, sake d'aure fuska Suhaima tayi don duk ita taja gashi ba don tayi kok'arin yakice shi ba da tuni ta bada kai bori ya hau, don haka ta samu waje ta zauna kawai ko kula Aliyah bata yi ba, sauran kad'an dariya ta kubce wa Aunty Aliyah amman ta danne ta kada ta janyo tayi mata kuka da rigima don kad'an daga aikin Suhaima don haka taja bakinta tayi tsit ta cigaba da aikinta.
Wani zafi da zugi ne yake ji cikin zuciyar shi kalaman Suhaima ne kawai suke fad'o mishi a rai da jan tsakin da tayi mishi don yaji ta ya dad'e kwance a haka yana tufka da warwara tare da yin d'unbin nadamar abin da yayi dakyar ya iya shiryawa cikin wani jeans blue da T-shirt fara mai k'aramin hannu ya d'an fesa perfumes kan ya zauna ya sha tea d'in da ya fara sanyi ma.
Yana gama sha ya mik'e ya d'auki kayan shi ya rik'e mai dattin a d'ayan hannun ya fito waje kallon Suhaima ya d'an yi kan ya kalli Aunty Aliyah yace
"Auntyn mu nagode bari na d'an fita waje ko zanga Ashiru don bamu had'u ba tun da nazo "
"Toh Sabeer sai ka dawo, amman ina zaka tafi da kayan nan masu datti haka a hannu? "
D'an murmishi yayi yana cewa
"Anjima zan wanke su ne zan ajiye su a inda nake kwana "
Tausayin Sabeer ne ya kama Aunty Aliyah tasan bai ta6a tsammanin zai yi irin wannan kwatankwacin rayuwa ko zuwan da yayi na farko baya yin wanki Yah Aliyu ne yake had'a wa ya wanke musu da nashi.
Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻*A̺͆ S̺͆A̺͆N̺͆A̺͆D̺͆I̺͆N̺͆ S̺͆O̺͆N̺͆ K̺͆I̺͆*
Wྂrྂiྂtྂtྂeྂnྂ bྂyྂ
Aྂıʂɧąɬ Aྂ Mྂųɧ'ɖ
ɖɛɖı¢ąɬɛɖ ɬơ ɱყ ʂąɖɛɛყ ʂąŋąʑ
♻ *єχ¢ℓυѕινє ωяιтєя'ѕ fσяυм*
*PAGE 106-107*
Kallon shi tayi da niyyar yi mishi tsiwa sai dai suna had'a ido duk wani abu ya kunce mata kallon junan su kawai suka tsaya yi cikin wani irin shauk'i da tsananin kewar junan su tare da wata irin zazzafar kauna, sun d'auki wajen 5 minute suna aikawa da junan su kallo yayin da Sabeer ya kasa jure kallon da suke aikawa junan su ya fara matsar da fuskar shi saitin fuskar ta da niyyar yayi kissing d'in cute pink lips nata wanda yayi tsananin missing d'in su a lot.
Jin saukar numfashin shi kusa da hancin ta sosai ya sanya Suhaima dawowa cikin hayyacin ta ta daddage ta fiske jikin ta daga jikinshi, sai dai yanda ta fisgi jikin nata ne ya sanya ta tafiya baya da d'an k'arfi kamar zata fad'i k'asa yayin da Sabeer wanda gaba d'aya kasala ta baibaye shi ya biyo ta shima.
Sauran kad'an Suhaima ta saki ihu na tsoro sai taji ta fad'a saman bed yayin da Sabeer ya biyo ta shima cikin jikinta, lokaci d'aya suka sauke wata ajiyar zuciya sai dai kowannen su da banbancin ajiyar zuciyar tasu Suhaima ita ta jin dad'in bata fad'i k'asa ba shi kuma Sabeer na jin shi rungume da Babyn shi a jikinshi wanda ya d'auke tsayin lokaci da su had'u kamar haka.
Kok'arin tashi take amman ya wani rik'e ta k'am kamar wanda za'a kwace mishi itaa haushi ne ya ishe Suhaima ta d'aure fuska cikin fusata tace
"Malam wai me kake nufi ne haka ni ka d'aga ni wallahi ko nayi maka ihu "
Murmishi Sabeer yayi kafin yace
"Haba Baby nah kinsan nayi missing d'in ki da yawa ki barni ko na samu kwanciyar hankali da nutsuwa cikin zuciya ta "
Haushi ne ya k'ule Suhaima don haka tace
"Kada ka mance da bakin ka kace min ka tsane ni me yasa zaka zo inda nake nima kasani na dad'e da tsanar ka tun lokacin da ka furta min haka "
Jikin Sabeer ne yayi wani irin sanyi wanda Suhaima har ta samu ta ture shi daga jikinta ta mik'e tare da d'aura d'an kwalin kanta ta wani kalle shi taja tsaki ta fice daga d'akin gaba d'aya.
Tana fitowa suka had'a ido da Aunty Aliyah da take zaune can gefen kitchen tana aiki, sake d'aure fuska Suhaima tayi don duk ita taja gashi ba don tayi kok'arin yakice shi ba da tuni ta bada kai bori ya hau, don haka ta samu waje ta zauna kawai ko kula Aliyah bata yi ba, sauran kad'an dariya ta kubce wa Aunty Aliyah amman ta danne ta kada ta janyo tayi mata kuka da rigima don kad'an daga aikin Suhaima don haka taja bakinta tayi tsit ta cigaba da aikinta.
Wani zafi da zugi ne yake ji cikin zuciyar shi kalaman Suhaima ne kawai suke fad'o mishi a rai da jan tsakin da tayi mishi don yaji ta ya dad'e kwance a haka yana tufka da warwara tare da yin d'unbin nadamar abin da yayi dakyar ya iya shiryawa cikin wani jeans blue da T-shirt fara mai k'aramin hannu ya d'an fesa perfumes kan ya zauna ya sha tea d'in da ya fara sanyi ma.
Yana gama sha ya mik'e ya d'auki kayan shi ya rik'e mai dattin a d'ayan hannun ya fito waje kallon Suhaima ya d'an yi kan ya kalli Aunty Aliyah yace
"Auntyn mu nagode bari na d'an fita waje ko zanga Ashiru don bamu had'u ba tun da nazo "
"Toh Sabeer sai ka dawo, amman ina zaka tafi da kayan nan masu datti haka a hannu? "
D'an murmishi yayi yana cewa
"Anjima zan wanke su ne zan ajiye su a inda nake kwana "
Tausayin Sabeer ne ya kama Aunty Aliyah tasan bai ta6a tsammanin zai yi irin wannan kwatankwacin rayuwa ko zuwan da yayi na farko baya yin wanki Yah Aliyu ne yake had'a wa ya wanke musu da nashi.
"Sabeer kabar shi Suhaima zata wanke maka "
"A'a Auntyn mu kada na wahalar da Mata ta "
Ya k'arasa maganar fuskar shi d'auke da murmishi wanda ya k'ara mishi kyau.
'Yar dariya Aunty Aliyah tayi kan tace
"Mata manya ni ai ban ta6a ganin matar da take gudun mijinta ba akan wani abu da ya faru bisa kuskure "
"Kaiii Auntyn mu kada mu yi haka da ke waya gaya miki tana gudun mijinta? "
Ya fad'i yana satar kallon Suhaima wanda ta cika tayi fam,
"Ai abin a fili yake K'anina "
Daga jin dai yanda Aunty Aliyah ke maganar kasan ta tsokana ce, sai akayi sa'a Suhaima bata tanka musu ba, ajiye kayan Sabeer yayi kusa da k'afar Suhaima kan yayi wa Aunty Aliyah sallama ya fita daga gidan.
"Allah Aunty ki daina yi min haka taya ina zaman hutawa na ki had'a ni da wanki don Allah "Cewar Suhaima cikin turo baki.
"Haba K'anwata bansan ki da fushi mai yawa ba ki d'auka ki wanke mishi na tabbatar Allah zai rubuta miki lada tunda da auren shi akan ki "
Cewar Aunty Aliyah cikin rarrashin Suhaima.
"Aunty kawai naga alama yanzu kin fi son shi da ni "
"Tabd'i kinsan dai Suhaima son da nake miki na daban shak'uwar mu da ke ma ba d'aya ce da ta Sabeer ba dukkanin ku matsayin k'annena ba don na girmi Sabeer ba, ina son ku had'a kanku da Sabeer ne da zarar Aliyu yaga haka duk fushin da yake dashi zai daina, Allah ya gani ina sonki da Sabeer wallahi gashi yana ban tausayi jiya da dare ji ruwa da aka tafka amman kusan akanshi ya k'are ga sanyin waje da duhu dalilin da ya tashi da mura kenan don tun da na tashi da asuba nake jin tarin shi da atishawa yana yi kuma duk wannan abun yana yi ne saboda A DALILIN SONKI Suhaima ya kamata kiyi tunani sosai kisan Sabeer masoyin ki ne na gaskiya "
Tana gama fad'in haka ta tashi ta wuce don cigaba da aikin ta yayin da tabar Suhaima cikin wani irin yanayi wanda lokaci d'aya ta fara jin haushin Sabeer yana raguwa cikin zuciyar ta.
Cikin sanyin jiki ta tashi ta fara wanke mishi kayan fes ta wanke su ta shanya saman igiya sannan tayi alwala ta tafi d'aki don yin sallah, bayan ta idar ne tana nan kwance saman abin sallahr Aunty Aliyah ta shigo cikin shirin tafiya suna tace
"Suhaima ni zan tafi idan Yayan ki da Sabeer sun dawo ga abinci nan a foodflaks ki zuba musu "
"Kaiii Aunty yanzu ki fasa tafiya dani? "
"Kiyi hak'uri Suhaima bazai yiwu mu tafi tare ba saboda baki tambayi mijin ki ba amman zan dawo da wuri kafin mangarib insha Allah "
"Toh Aunty adawo lafiya "
"Yawwa K'anwata haka nake son ji kin fad'a "
Tashi tayi suka fito har k'ofar zaure ta rakata ta tafi sannan ta rufe gidan ta wuce ta zuwa d'akin ta, kwanciya tayi kawai maganganun Aunty Aliyah ne suke dawo mata, da taga tunanin ba mai k'arewa bane ya sanya ta tashi taje ta had'a wuta a dutsen guga ta zauna ta gogewa Sabeer kayan shi tsaf ta d'auke su taje ta ajiye mishi saman jakar shi.
Tana zama kenan taji ana buga k'ofar gidan tashi tayi taje tana tambayar wane sai taji muryar Yayanta Aliyu bud'e k'ofar tayi tana murmishi tace
"Yayah sannu da dawowa? "
Shima fuskar shi d'auke da murmishin yace
"Yawwa Suhaima ya zaman gida ke kadai don nasan Aliyah ta tafi gidan suna koh? "
"Eh Yaya ta tafi sai ni kadai duk tsoro ya kama ni "
"Ai dama ke matsoraciya"
Cewar Yah Aliyu yana dariya cikin shagwa6a tace
"Kaiii Yayah aikuwa ni jaruma ce "
Hannun ta ya kamo suka k'arasa cikin gidan yana biye mata, bayan yayi wanka ta zuba mishi abinci yana ci suna hira yana bata labari akan harkar karatun shi tana yi mishi addu'ar Allah ya taimaka, yana tsaka da cin abincin Sabeer ya shigo gidan bakin shi d'auke da sallama.
Sanin muhimmancin sallamar ne ya sanya Yah Aliyu amsa mishi ko k'arasa shiga tsakar gidan bai yi ba ya juya zuwa cikin zaure ya shimfid'a tabarma ya zauna akai kawai, wani tausayin shine ya kama Suhaima wanda ya sanya ta binshi da kallon tausayi, ashe duk wannan kallon da take binshi dashi Yah Aliyu yana kallonta shima girgiza kanshi yayi kawa ya cigaba da cin abincin shi.
"Ki zuba mishi abinci ki kai mishi "
Ya furta hakan kamar bashi yayi maganar ba, aikuwa tsam ta mik'e da sauri taje kitchen ta zuba mishi tare da d'iban ruwa ta kai mishi, duk abin da take Yah Aliyu yana kallon ta yana kula da yanayin ta, bayan ta dawo daga kaiwa Sabeer abinci ta wuce d'akin ta kawai.
Ahaka har aka kwashi tsayin sati biyu Sabeer na kwana a zaure har zuwa yanzu babu wata kyakkyawar fahimta tsakanin shi da Aliyu, ga wani irin tari da zazza6i mai zafin gaske da yake yi da cikin dare baya iyayin wani cikakken bacci duk yabi ya rame sosai yayi bak'i ga rashin aski duk gashi ya cika mishi fuska ko abincin kirki baya iya ci, gashi kirjin shi yayi mishi wani irin nauyi gashi tsakiyar damina akai ana samun ruwa akai akai sosai.
Suhaima tana tausayin Sabeer ganin yanda ya koma har kuka take a 6uye, Aunty Aliyah tayi tayi dashi Ashiru ya rakashi chemist yak'i zuwa yayin da Yah Aliyu yake ce mishi ya tafi gidan su bazai iya zaman nan ba tunda shi ba d'an wahala bane kawai ya sakar mishi k'anwar shi, Sabeer idan yaji haka sai kawai yayi murmishi kawai shi ciwon da yake damunshi da k'in kulashi da Suhaima take yafi komai d'aga mishi hankali.
Kamar yau tun kafin mangarib ake ruwa har zuwa bayan sallahr ishsha bai tsayaba sai dai idan lokacin sallah yayi ya d'an tsaya, Sabeer yana tukunkune a zaure yana rawar sanyi sosai ga tari da yake faman yi idanun shi sunyi ja sun k'ara fitowa sosai saboda tarin da yake yi zuwa can kuwa numfashin shi ya fara d'auke wa kafin daga bisani ya tuntsire a k'asa yana jan numfashi dakyar.
Suhaima kuwa tana zaune a d'aki sai faman kukan zuci take tasan Sabeer yana can yana fama da dukan ruwan wani tausayin shine yake ratsa mata zuciya tana fitar da hawaye.
Yah Aliyu kuwa da Aunty Aliyah sai fad'a suke tana fad'a mishi idan Sabeer ya mutu mai zai cewa iyayen shi wannan horan haka ya isa duk yaro yabi ya rame yayi bak'i ga rashin lafiyar da yake fama da ita nasan zuwa yanzu yayi horan da bazai sake maimaita abin da yayi ba.
"Aliyah ana dole ne nace ya rabu da ita kuma bani na ce yazo ba fah ya zauna ra'ayin shine to ni mene ruwana "
"Haba Yah Aliyu nasan ka da tausayi zuciyar ka mai kyau ce kayi hak'uri ka yafe mishi, baka ganin yanda Suhaima ma ta shiga damuwa kada ka shiga hakk'in su fah da yawa tana son mijinta shima yana son matar shi don me yasa baza ka hakura ka bashi matar shi ba kuma na tabbatar kana son Sabeer ya kasance da Suhaima har k'arshe rayuwar ta, bakasan abin da Allah ya 6oye ba kawai ni a shawara ta ka bashi matar shi don Allah Yah Aliyu "
Cewar Aunty Aliyah tana kama hannun shi fuskar ta tab da hawaye, shiru Yah Aliyu yayi yau Aliyah ta tunasar dashi abubuwa da dama, take yaji zuciyar shi tayi sanyi ya kalli Aliyah yace
"Naji na amince zan bashi matar shi "
Wani dad'i ne ya ratsa zuciyar Aunty Aliyah tayi murmishi tana cewa
"Ko kaifa Yah Aliyu naji dad'i sosai don Allah yanzu ka taso muje ka ce ya koma d'akin Suhaima "
Hannun shi yasa ya ja hancin Aliyah yana cewa
"Toh Mata tagari angama taso mu tafi "
Ya mik'e tsaye yana murmishi tare da kamo hannun Aliyah suka fito zuwa zaure, sai dai suna shiga zauren hankalin su yayi masifar tashi ganin yanda Sabeer yake jan numfashi dakyar yana rik'e da kirjin shi ga kuma tarin da yake.
Da sauri suka k'arasa inda yake Yah Aliyu ya tashe shi zaune tare da rik'e shi yace
"Sabeer me yake damun ka? "
Kallon Yah Aliyu yayi kafin yayi luuu da eyes nashi kamar wanda yasha kwaya bashi da k'arfin bud'e baki yayi magana ma, ganin haka ya sanya Yah Aliyu d'ago shi yana rik'e dashi suka k'arasa d'akin Suhaima.
Da sauri Aunty Aliyah take buga k'ofar d'akin Suhaima tana kiran sunan ta, a firgice Suhaima ta duro daga saman gado tare da bud'e k'ofar nata.
Kafin tayi magana Yah Aliyu ya shiga da Sabeer cikin d'akin tare da zaunar dashi ya juyo ya kalli Suhaima wadda sai rarraba ido take hanaklin ta atashe yace
"Kiyi maza ki cire mishi kayan jikin shi ki canja mishi bari naje na samo mishi magani, Aliyah kije ki dafa mishi tea da kayan k'amshi ki dafa da lemon tsami a ciki "
Yana gama fad'in haka ya wuce ya tafi da sauri yayi da Aunty Aliyah ma ta wuce zuwa kitchen da sauri duk da kuwa ana yin yayyafi, Suhaima kasa motsi tayi saboda ganin Yah Aliyu da kanshi ya kawo Sabeer har da cewa na cire mishi kayan jikin shi, ganin halin da Sabeer yake ciki ne ya sanya ta kok'arin cire mishi kayan shi dakyar ta iya cire mishi saboda gaba d'aya babu k'arfi ajikin shi balle ya mik'e tsaye, bayan ta gama cire mishi ta duba kayan nashi ta ciro dogon wandon jeans ta sanya mishi sai dai babu wata