Showing 30001 words to 33000 words out of 122360 words
Chapter 11 - A sanadin Son ki Hausa Novels Document complete by Aisha A Muhammad Sanaz.txt
yana cilla key yana cafewa zuciyar shi yau cike take da farinciki da nishad'i ya ganta a inda bai ta6a zaton zai ganta ba kuma yana kyautata zaton dalilin Jiddah tazo tun da yasan itace mai shige shigen talakawa sosai a cikin families d'in su yayi mamakin yanda Jiddah har tasan k'auyen su Suhaima ta ganta suka fara k'awance. Da wannan tunanin ya k'arasa cikin part d'in su kai tsaye bedroom nashi ya wuce yayi wanka sannan ya sanya wasu fararen sleeping dress ya kwanta amman ya kasa bacci sai tunanin abin da ya faru tsakanin shi da Suhaima yake yana zuba murmishi shi kad'ai.
Da gudu Jiddah ta k'araso wajen Suhaima a lokacin da ta hango ta rungume ta tayi tana kuka tace
"Suhaima don Allah kiyi hak'uri wallahi na d'auka kin biyo wasu ne sai da na neme ki na rasa na d'auka kina gida sai da na dawo na neme ki na rasa, hankali na ya tashi sosai yanzu haka da kika ga na fito komawa zanyi na duba ki sai na hango ki... Waya kawo ki? Naga kamar motar Yah Sabeer kika fito ko shine ya dawo da ke? "
Duk wannan maganar da Jiddah take da tambaya babu saurarawa tana yi tana kallon Suhaima, abin ma sai ya bawa Suhaima dariya kafin ta bud'e baki tace
"Kaiii Jiddah irin wannan tambayar gashi na dawo sai hankali ya kwanta amman ni bansan sunan wanda ya taimaka min ba naga dai kuna yanayi dashi "
Ajiyar zuciya Jiddah ta sauke ta kwanciyar hankali kafin ta tace
"Mybe shine tun da naga motar shi ce amman naji dad'in abin da Yah Sabeer yayi dole nayi mishi godiya, gaskiya Suhaima kinci sa'a sosai don Yah Sabeer sai a slow wallahi"
"Koh? "
"Eh mana don baki san halin shi ba ne, gashi da miskilanci da shagwa6a don ko k'aramin yaro bazai nuna mishi shagwa6a ba "
"Hmmm ni bacci nake ji na gaji wallahi "
"Ai dole zo muje kiyi wanka ki kwanta "
Hannun ta Jiddah ta kama suka nufi side d'in shi shiru kake ji ko'ina kowa yayi bacci, don haka d'akin Jiddah suka nufa kai tsaye, bathroom Suhaima ta shiga wanka tayi tare da yin alwala ta fito wata catton sleeping dress dogowa Jiddah ta bata ta sanya da hula sannan ta sanya hijab sallahr isha'i tayi tare da yin shafa'i da wuturi tayi 'yan addu'o'in ta kafin ta tashi ta koma inda ta ajiye bag d'in da ta zo dashi.
D'auko wa tayi ta bud'e gift's d'in da Aunty Aliyah ta bata ta d'auko taso wa tayi ta zo inda Jiddah ta kwanta saman bed tace
"Jiddah ga gift's d'in da Aunty Aliyah ta bani na baki "
Cikin mamaki Jiddah ta tashi zaune tare da kar6ar sarkar tana dubawa, nan take ta fad'ad'a fara'ar ta sannan ta rungume Suhaima tana cewa
"Wayyo dad'i nagode sosai tana da kyau, me yasa baki fad'a min da wuri nayi mata godiya ba "
Suhaima fuskar ta d'auke da murmishi tace
"Itace ta hana na fad'a miki don babu waya tace sai mun tafi na baki "
"Naji dad'i sosai kiyi mata godiya Allah ya bata lafiya ya raba ta da abin da take d'auke dashi lafiya"
"Amin "
Cewar Suhaima kafin ta d'ora da cewa "sai wani godiya kike tamkar wadda aka bata wani babban abu "
D'an hararar ta Jiddah tayi tare da cewa "Hmm ke kika ga haka Suhaima amman tabbas wannan kyautat a wuri na babba ce "
'Yar dariya Suhaima kawai tayi ta kwanta ita ma bayan Jiddah tayi light off ne Suhaima tace
"Jiddah ina son gobe ki had'a ni da driver ya kaini wani mall zan yi siyayya "
"Me zaki siyo? "
"Ina ruwan ki idan na siyo kya gani "
"Alright Allah ya kaimu goben"
"Amin "
Da haka kowannen su yaja blanket ya lullu6a tare da addu'ar bacci babu dad'e wa bacci ya d'auke su mai nauyi da yake an gaji saboda hidima ta biki.
Washe gari da safe wajen k'arfe 11 aka d'aura auren Jiddah da Khaleel wanda d'umbin mutane masu kud'i goggagun 'yan boko tare da 'yan siyasa manyan likitoci da 'yan kasuwa suka halatta bayan d'aurin aure ne suka wuce reception ta maza, cikin gida kuwa matane a ciki taf ana hidimomi irin na biki.
Jiddah ce gaban dressing mirror tana sanya sark'ar da Aunty Aliyah ta bata sai da ta gama sanyawa tsaf ta jiyo ta kalli Suhaima wanda taci gayun ta cikin wani lace ash mai touch d'in flowers pink tayi kyau tamkar itace amaryar sai kashe selfie take abin ta.
"Yah babe kin gani koh na had'u? "
Cewar Jiddah kenan tana kallon Suhaima, kallon ta Suhaima tayi a haka sark'ar tayi mata kyau amman bai kamata ta sanya ta yanzu a lokacin bikin ta don tayi arha da yawa tana kallo ta ajiye gold d'in ta a gefe ta d'auki wannan ta sanya. D'an murmishi Suhaima tayi tare da cewa
"Wow amarya a gidan Khaleel kinyi kyau sosai sai dai ki cire sark'ar nan please "
"Because of what? "
"Bata cancanta ki sanya ta ba yanzu "
Har Jiddah ta bud'e baki zata yi magana aka turo k'ofar bedroom d'in aka shigo, Umman Jiddah ce ta shigo tasha kwalliya cikin wata tsadaddiyar shadda an zuba gold's a jiki sai fitar da k'amshin turare take, da sauri Suhaima ta gaida ita ba yabo ba fallasa ta amsa tana nufar Jiddah wadda take tsaye, cikin mamaki tace
"Me zan gani Jiddah, mene haka a wuyan ki? "
"Uhm Umma sark'a ce tayi kyau? "
Wata harara Ummna ta zabga mata tare da cewa
"You're very stupid Jiddah na rasa mene akan ki wallahi ranar bikin ki zaki sanya wannan banzan sark'ar mai araha haka ko 'yan aikin gidan nan zasu sanya sark'ar da suka fi wannan tsada balle ki, wanne stupid ne ya baki ita?"
A hankali cikin sanyi jiki Suhaima ta tashi ta nufi bathroom ta shige idanun ta suna fitar da hawaye yau a gabanta ake kiran Aunty Aliyah stupid wadda ta d'auke ta tamkar mahaifiya a wajenta yau da ace wata ce ba Umman Jiddah ba da sai inda k'arfin ta ya k'are wallahi.
Gaba d'aya ran Jiddah ya 6aci sosai cikin jin haushin abin da Umman ta fad'a, Jiddah ta bud'e baki tace
"Haba Umma me yasa kike haka ne "
"Dalla can rufe min baki kafin ranki ya 6aci kiyi maza ki cire ta sannan ki fito parlour za'a d'auki pic's sauran ki taho mana da yarinyar nan "
Tana gama fad'in haka ta fice daga d'akin, wasu hawaye ne masu zafi suka zubo mata me yasa me yasa iyayen ta suke wannan halin na kyamar talaka me yasa suke abu tamkar basu da ilimi sun san Allah ne mai azurta bawan shi a lokacin da yaso, ba wayon su ko dabarar su ne yasa suke da kud'i ba a yanzu idan Allah yayi sai ya kwace kud'in.
Da sauri ta sanya hannu ta goge hawayen fuskar ta tare da jiyowa jin an dafa kafad'ar ta, Suhaima ta gani tana murmishi itama murmishin yak'e tayi kafin tace
"I'm so sorry Suhaima akan abin da Umma tayi miki"
"Haba Jiddah ni fah babu abin da akayi min "
Ta k'arasa fad'i tana cire sark'ar jikin Jiddah bayan ta gama cirewa ne ta d'auko mata wanda su zata sanya ta d'auko wannan ta sanya.
"Wow kin had'u tawan ni yanzu ki had'a ni da driver na tafi "
"Okay dear "
D'auko phones nata tayi ta kirawo driver magana tayi na tsayin 2 minute's sannan ta mik'a wa Suhaima wayar tace
"Yana waje yana jiran ki driven "
"Okay thank U "
Daga haka ta d'auki bag nata suka fito tare ta kofar baya Jiddah ta nuna wa Suhaima ta fita don batason wani ya sake 6atawa Suhaima rai, bayan Suhaima ta fita driven shi ya hango ta yayi mata magana aikuwa nan ta shiga mota yaja suka bar gidan.
Tun da Suhaima ta fito daga part d'in su Jiddah tazo ta wuce ta shiga mota yana kallon ta, wani mirmishin mugunta ya saki duk gajiyar da yayi dakyar yake d'aga k'afa gudowar shi daga wajen reception ko gamawa ba'a yi ba ya taho don duk ya gaji da hayaniya ganin Suhaima ne yasa duk yaji gajiyar ta wartsake cikin sauri ya shiga mota ya bisu a baya...
Aishat A Muh'd ✍🏻
A SANADIN SON KI
Written by
Aishat A Muh'd
♻ EXCLUSIVE WRITER'S FORUM
Dedicated to my Sadeey saNaz
PAGE 40-41
Tafiya suke Suhaima sai wara ido tana kalle kalle sosai taji garin na Kano ya birgeta daman Yaya Aliyu yana bata labarin yanda yanayin garin yake kodayaushe cikin sha'awar zuwa take sai gashi a dalilin Jiddah tazo ta, karatun Qur'an ne yake tashi a motar k'ira'ar Shureim cikin suratul Ma'idah sosai karatun yake ratsa cikin zuciyar Suhaima har wani lumshe ido take tana bin karatun a hankali cikin k'asa k'asa da muryar ta.
Agaban wani k'ayataccen mall driver yayi parking tare da cewa "mun iso ranki ya dad'e"
D'an murmishi Suhaima tayi tare da cewa
"Okay bari na shiga na fito "
"A fito lafiya "
Bud'e k'ofar motar tayi ta fito cikin takun nutsuwa take tafiyar duk da kuwa yanda gaban ta yake fad'uwa don bata ta6a zuwa irin wannan wajen ba, kawai d'auriya tayi kada ta ba da kanta amman zuciyar ta fal tsoro kamar ace kyat ta zura da gudu, har ta k'arasa wajen k'ofar shiga ta shiga ciki.
A hankali Sabeer yayi parking kusa da motar da ta kawo Suhaima, fitowa Sabeer yayi sannan ya k'arasa wajen motar tun kafin ya k'araso drive ya ganshi don haka da sauri ya fito daga motar yana cewa
"Yalla6ai barka da rana"
Sabeer bai tsaya bawa driven amsa ba yace
"Salisu me kake anan? "
"Yalla6ai na kawo k'awar Jiddah nan zata yi shopping "
"Okay zaka iya tafiya gida "
D'an shiru Salisu yayi kafin yace "Yalla6ai Jiddah tace na jirata ta gama na mayar da ita gida don bak'uwace anan "
D'an shan mur Sabeer yayi kafin yace "Oh baza kayi abin da na saka ba? "
Cikin d'an tsoro da biyayya Salisu yace
"Ayi min afuwa Yalla6ai yanzu zan tafi "
Yana gama fad'in haka ya shiga mota yaja ya bar wajen zuciyar shi cike da d'an tsoro yanzu idan ya koma gida me zai cewa Jiddah idan ta tambaye shi ina k'awar ta, gashi bazai iya musu da Sabeer ba don kada ya rasa aikin shi don dashi ya dogara.
Salisu driver na tafiya Sabeer ya saki wani murmishi dani kaina bansan ma'anar shi ba kafin ya shiga cikin mall d'in cikin takun shi na k'asaita, zuciyar shi cike da tunanin yanda yarinyar da ko sunan ta baisani ba zai tunkare ta da magana mafi daraja a wajen shi wanda babu 'ya macen da ta6a furtawa.
Bayan Suhaima ta gama duk siyayyan gift's d'in da zata bawa Jiddah ne ta nufi wajen biyan kud'i, ga mamakin ta akace an biya mata cikin mamaki take kallon matar da ta fad'a mata da gani yare ce don hausan ta baya fitowa sosai.
"Wane ya biya min anya nice?"
Suhaima ta tambayi matar, d'an murmishi tayi tare da cewa
"Yes kene aka biyawa ba ke da mijin ka bane? "
Ad'an tsorace Suhaima tace
" A'a ba mijina ba ne ko zanyi iya sanin wanda ya biya min?" Da mamakin abin da Suhaima ta fad'i tace mata "Yawwa ga Yalla6an can wanda ya biya miki "
Matar ta nuna wajen da d'an yatsanta, bin d'an yatsan matar Suhaima tayi kallo zuwa inda take nuna mata wani irin buguwa zuciyar Suhaima tayi sakamakon had'a ido da Sabeer da tayi yana wani kasheta da murmishi zaune yake kan kujera yana kallon ta suna had'a ido ya d'aga mata gira tare da yi mata wink, wayyo Allah nah yanzu wannan mutumin duk inda nayi sai ya biyo ni yanzu ya zanyi na guje mishi?, fad'in haka cikin zuciyar ta.
A sace ta k'ara kallon matar inda Sabeer yake sai taga ya tashi tsaye yana gyara rigar dake jikin shi, da sauri ta fara tafiya zuwa hanyar da zai kaita ta fita sauri kawai take tana fatan ta ganta a cikin mota ta shiga ciki ta zauna sun bar wajen.
Tana fitowa ta k'arasa inda suka yi parking amman wayam bata ga motar ba nan ta sake dudduba wa ko ba wurin ba ne taga dai still anan suka yi parking, toh ina motar da driven? Zuciyar Suhaima ta ambata.
"Ni nace ya tafi "
Fad'in Sabeer kenan wanda ke tsaye a bayan ta tamkar yasan abin da zuciyar ta take sak'amata, bata kula shi ba ta fara tafiya a wajen don bata da abin cewa tun da driven su ne d'auko shi suka yi yana musu aiki su biyashi dole yaji maganar shi tun da ita ba komai bace.
Ganin tana tafiya yasa Sabeer bin bayan ta yasha gabanta yana cewa
"Hey beauty kizo nayi dropping naki zuwa gida "
Ja Suhaima tayi ta tsaya tare da d'an kallon shi gaban ta na fad'uwa ta daure tace
"Bana so zan kai kaina inda nake buk'ata "
Tana gama fad'i haka ta kauce tare da zagaye shi zata wuce da sauri ya rik'o hannun ta, tsayawa Suhaima tayi tare da jiyowa ta kalli tsintsiyar hannun ta inda ya rik'e mata wani bak'inciki ne ya kamata ganin namijin da ba mijin ta ba muharraminta ba ya rik'e mata hannu a cikin bayyanar jama'a, ko jiya ma da ya rik'e mata hannu ba cikin nutsuwar ta take ba.
Wasu hawaye ne suka hau zubo mata a idanun ta kallon shi tayi tare da cewa
"Ka cika ni "
Muryar ta can k'asan mak'oshi ta furta hakan, ganin babu wasa a fuskar ta ya sanya shi cikata tana ganin haka yasa Suhaima juyawa zata cigaba da tafiya, cikin wata irin murya Sabeer yace
"Banason ki k'ara tafiya ba tare da na fad'a miki wani abu ba ina son kizo ki shiga mota akwai maganar da zan fad'a miki please "
D'an jim Suhaima tayi daman ko da zai barta ta tafi batasan inda zata nufa ba gashi ta bar wayar Jiddah a cikin mota.
"Na rok'e ki please "
Sabeer ya furta hakan yana kallon ta, juyawa tayi ta fara tafiya kawai shima bin ta yake a baya har suka k'arasa inda yayi parking motar shi ya bud'e mata seat na gaba ta shiga ta zauna sannan ya rufe ya koma ya shiga mazaunin driver ya zauna yana nai mamakin kanshi yau wai shine yake bud'e wa wata mace k'ofar mota ta zauna lallai so ya canja shi daga d'abi'un halayyar shi na da zuwa wasu daban.
"Suna na Sabeer Hussein d'an fillo, ke mene sunan ki? "
Shiru Suhaima tayi bata yi mishi magana ba shima bai k'ara cewa komai sai da suka yi nisa da tafiya ta bud'e baki tamkar batason magana tace
"Suhaima "
A hankali ta furta hakan bata d'auka yaji ba sai da taji yace
"Nice name "
Jingina kanta tayi jikin kujerar da take zaune ta lumshe idanun ta, dan kallon ta Sabeer yayi ganin ta rufe idon ta ne yasa shi jan wani birki, a rikice Suhaima ta bud'e idon ta har ta buge kanta ta kalli gaban su ta d'auka wani abin ya faru sai taga ya cigaba da tuk'in shi ko kallo inda take bai yi ba, hararar shi tayi ta gefen ido tare da murgud'a bakin ta kad'an kafin ta koma ta sake lumshe idon ta.
Dariya ce taso kubce mishi amman ya danne cikin zuciyar shi yana cewa wanna yarinyar akwai tsiwa huh, gaban wani gida yayi parking mai kyau da gani gidan kasan sabo ne tun daga wajen kasan an kashe kud'i sosai idan ka kalla.
Jin an tsaya da motar yasa Suhaima bud'e idon ta ganin ba irin yanayin unguwar gidan su Jiddah ba ne yasa jiyowa ta kalle shi na alamr tambaya nan ina ne. Bai ce mata komai ba ya fito daga cikin motar ya bud'e mata ita ma sai tak'i fitowa tace
"Nan ba gidan su Jiddah ba ne don Allah ni ka kai ni gidan su... "
"Zan mayar da ke gida Suhaima but ina son ki bani wasu minute's akwai maganar da zamu yi "
D'an kallon shi tayi sai taga babu wasa saman fuskar shi duk da a tsorace take dashi haka ta fito daga motar ya rufe sannan suka nufi cikin gidan duk takun d'aya da Suhaima zata yi gaban ta fad'uwa yake.
Tura k'ofar gate d'in yayi ya shiga tana biye dashi, gate man na ganin shi ya zube yana gaida su Sabeer ne ya iya amsawa dakyar Suhaima kuwa bakin ta ne yayi mata nauyi ta kasa bud'e shi, gidan babba ne ya had'u sosai cikin parlourn gidan suka shiga.
Zama yayi akan kujera ya d'ago kanshi yana kallon Suhaima wadda take tsaye k'ik'am tamkar wata soja yace
"Suhaima ki zauna ina son ki ban hankalin shi da nutsuwar ki "
Ba tare da ta kalle shi ba ta zauna don ta k'osa ta ganta a kusa da Jiddah. Shiru suka yi tamkar babu mutane a cikin parlourn har sai da Suhaima ta k'osa da shirun nashi tace
"Kai nake jira fah "
Tashi tsaye yayi ya dawo gaban ta ya zauna akan carpet d'in dake shimfid'e a k'asa, tsugunna wa yayi tamkar mai neman afuwa yace
"Suhaima kin tuna ranar da muka fara had'u wa da ke tun daga lokacin na kasa manta ki zuciya kullum cikin tunanin ki take haka idanuna kullum cikin son sake ganin ki suke, na je wajen sau uku k'auyen ku neman ki but ko mai kama da ke ban sake gani ba sai ajiya Allah ya nufa zan sake ganin ki "
Dan shiru yayi yana kallon Suhaima wadda take kallon shi take kuma sauraren abin da yake cewa cikin mamakin shi, ajiyar numfashi yayi kafin ya cigaba da cewa
"Naji dad'i Sosai a lokacin da na ganki a takaice Suhaima zan sanar miki zuciya ta ta kamu da son ki! I luv U Suhaima i really luv U, ban ta6a son wata mace a duniyar nan