Showing 36001 words to 39000 words out of 122360 words

Chapter 13 - A sanadin Son ki Hausa Novels Document complete by Aisha A Muhammad Sanaz.txt

nan, Sabeer kamar sabon kamu 😹 ya koma, ni Mumy da Alhj Ahmad sun fi ban dariya 😂 da suka sashi a gaba suna kuka, ina fatan zan ga Comment's, idan na samu Comment's da yawa zan k'ara muku 1 page anjima 😹






Aishat A Muh'd ✍
A SANADIN SON KI


Written by
Aishat A Muh'd


♻ EXCLUSIVE WRITER'S FORUM


Dedicated to my Sadeey saNaz






PAGE 44-45








Yana nan kwance kan bed idanun shi a lumshe hawaye ne har yanzu suke zuba gaba d'aya brain nashi ya d'auki zafi har ya kasa tunanin abin yi, banko k'ofar akayi da k'arfi aka shigo Hajjah Hauwaa ce ta shigo a matukar kid'ime bayan ta Alhj Ahmad, Mumy da Daddyn Sabeer ne suka k'arasa shigowa cikin bedroom d'in.


Cikin kuka Hajjah Hauwaa ta k'arasa inda Sabeer yake kwance idanu a lumshe suna zubar da hawaye, fyace hancin ta tayi da hankycif d'in hannun ta kafin ta zauna saman drower na gefen bed, hannun Sabeer ta kamo cikin tashin hankali tace
"Sabeer me yake damun ka?, wane ya 6ata maka rai?, ka sanar damu yanzu kaga irin mataki da zamu d'auka akan kowanne d'an mara mutunci ne, ka sanar da mu yanzu kaji d'an lele na ba wanda zai ta6a min kai ya kwana lafiya kowa ne maza ka sanar da ni...?"


Shiru Sabeer yayi mata tamkar baisan da mutum kusa dashi ba, "Bana son ka Sabeer bazan iya auren ka ba"
Maganar Suhaima ce take ta amsa kuwwa a kunnen shi tamkar yanzu take fad'i, hannu shi yasa ya damk'o zanin gadon da k'arfi tamkar irin mace mai nak'udar nan kafin ya furta
"Suhaima ki so ni bazan iya rayuwa bake ba please idan kika baki soni ba mutuwa zan yi "


Wayyo tashin hankali a wajen iyayen Sabeer da su Hajjah ba kad'an ba najin abin da Sabeer yake fad'a, hannu Hajjah Hauwaa ta d'ora saman kanta ga hawaye kace kace saman fuskar ta tana cewa


"Hussein kuyi wani abin kai na shiga uku Sabeer ya haukace ko wata aljannar ce ta shafe shi "


Abin da Hajjah ta fad'i ne yasa Sabeer bud'e jajayen idanun shi ya watsa mata wani kallo, ai tuni Hajjah tayi wani tsalle ta koma bayan Alhj Ahmad tana rawar jiki tare da zare idanu tana lek'en Sabeer ta d'auka fisgota zai yi ya shak'eta don da gani kasan baya cikin hayyacin shi.


Ganin haka ya sanya Daddy kallon iyayen shi da Mumy wadda take shar6ar kuka yace
"Abba ku d'an bani wuri zanyi magana dashi "
Jikin a sanyaye suka fita daga bedroom d'in kowanne na sak'e sak'e cikin zuciyar shi.


Bayan sun fita ne Daddy ya samu waje kusa da Sabeer ya zauna tare da janyo shi cikin jikin shi yana bubbuga bayan shi na rarrashi, sun d'an dad'e a haka kafin Daddy ya raba jikinshi dana Sabeer kallon shi yayi sannan ya janyo wata bottle d'in faro ya bud'e ya sanya wa Sabeer a bakin shi, ba musu Sabeer ya fara sha kafin ya d'auke bakin shi alamar ya isheshi ajiye bottle d'in yayi, ta6a jikin Sabeer yayi yaji har jikinshi ya d'auki d'umi alamar zazza6i yana son rufe shi.


Cikin nutsuwa Daddy ya kalle shi kafin yace "me yake damun ka Son ka fad'a min damuwar ka ko da abin da zan iya taimaka maka? "


Sai da Sabeer yayi shiru na tsayin lokaci kamar bazai yi magana ba kafin kuma ya bud'e baki yace
"Daddy ko na fad'a maka matsala ta babu abin da zaka iya akai saboda ba irin ra'ayin ku ba ne"
D'an shiru Daddy yayi cikin mamakin abin da Sabeer ya fad'a, kawar da mamakin yayi ta hanyar yin murmishi na kwantar da hankali kafin yace
"Ka sanar da ni Son idan abin da ka fad'a min abin da zai yiwu ne why not mu baka had'in kai "


Kai tsaye Sabeer yace "Daddy aure nake son yi kuma Suhaima nake so Daddy "
Abin ya bawa Daddy dariya sai kawai ya murmusa sannan yace
"Toh Sabeer ban da abin ka mene na damuwa kuma?, wace ce Suhaima?, me akai akayi ta fad'a min sunan Baban ta a fad'in Nigeria a gobe za'a d'aura aure "


Kallon Daddy kawai Sabeer yake cikin zuciyar shi yana cewa lallai Daddy bakasan wace Suhaima ba ita ba 'yar kowa bace amman ta fita daban da sauran mata sannan kud'in bazai iya siyan ra'ayin ta ba.......


Katse mishi tunani Daddy yayi ta hanyar rik'o hannun shi yace
"Son wace Suhaima tell me? "
Cikin muryar damuwa Sabeer yace "Daddy bata sona bazata iya aure na tace min"
"K'arya take yi Son dole ta soka kuma ta aure ka, fad'a min ita wace zata kalli idon d'ana tace batason shi, fad'a min wane Ubanta? "
Daddy ya k'arasa fad'in haka rai a 6ace.
"Daddy Suhaima ba kowa bace haka iyayenta bakowa bane infact ita a k'auye take renon k'auye ce"
"What! Son me kace, kasan abin da kake fad'a? "


Daddy ya fad'i hakan yana tashi tsaye, tashi Sabeer shima yayi tsaye babu alamar tsoro ko fargaba yace
"Yes! Daddy nasan abin da na fad'a kuma ina cikin hayyaci na "
"Bazai yiwu ba Son ka sake nemo wata amman sam wannan yarinyar bata dace da kai ba 'yar talaka ce kuma 'yar k'auye bata da ilimi ko kad'an bazan iya had'a zuri'a da ita, kai kad'ai Allah ya bani bazan iya zuba ido naga kayan takaicin nan ba don haka ka sake tunani! "


Cikin tsantsar 6acin rai da abin da Daddy ya fad'a yasa Sabeer naushin dressing mirror da k'afar shi da k'arfi wanda sai da tayi k'ara tsabar had'uwar kafar shi da katakon dressing mirror wata k'ara mai razanar wa Sabeer ya saki da sauri Daddy ya juyo a razane da sauri ya k'arasa wajen Sabeer zai rik'e shi
"Don't touch me! "
Ya fad'a cikin wata irin voice, hankalin Daddy ya tashi sosai cikin rarrashi yace
"Saboda na hanaka auren yarinyar nan zaka nakasta kanka Sabeer? "
Idanun shi na tsiyayar hawayen kallon shi yake cikin ido kafin yace
"Idan baku barni na aureta ba zan iya mutuwa ma Daddy!"
A matak'ar razane Daddy yake kallon d'an nashi cikin wani irin yanayi na tsantsar tashin hankali.


Sabeer bai k'ara kallon inda Daddy yake ba ya fara tafiya cikin d'ingisa d'ayan k'afar nashi wanda ya dakidaki dressing mirror da ita, yana runtse ido saboda azaba da haka ya shiga bathroom yana shiga ya kunna shower ya rasa yanda zaiyi sai kawai ya fashe da wani irin kuka yana bubbuga jikin bango da hannun shi ga ruwa yana zuba a kanshi da jikin shi.


Ya d'auki lokaci mai tsayi kafin ya fito k'afar shi ta isheshi da zugi da azaba ji yake tamkar ya cireta dakyar ya iya sanya kayan shi ya kwanta saman sofa fuskar nan tayi ja da ita saboda tsabar kuka, a haka wani wahalallen bacci yayi awon gaba dashi.




Azabar da k'afar shi ya dame shi da ita ne yasa shi farka wa daga baccin da ba wani jin dad'in shi yake ba, kallon k'afar yayi yaga ta kumbura sosai tamkar ba k'afar shi ba, tsura mata ido kawai yayi yana kallo, yana jin an bud'e k'ofar d'akin an shigo.


"Subhnallah Son haka k'afar ka ta koma? "
Bai kalle shi ba balle yasa ran zai amsa mishi, ganin haka yasa Daddy d'auko wayar shi ya kirawo mai gyaran k'afa tare da kiran family doctor d'in su Kafin ya ajiye wayar ya zubawa Sabeer ido yana kallon shi, ya hana kowa shigowa inda yake amman dukkanin su suna parlour a zaune Mummy da Hajjah sun sha kuka sun more yak'i sanar musu da ainahin abin da Sabeer ya fad'a mishi saboda yasan ba k'aramin ruguntsumi za'a sha ba.


Suna zaune har mai gyaran k'afa yazo bayan ya shigo d'akin sun gaisa da Daddy zai ta6a k'afar Sabeer ya janye ta da sauri tare da cewa
"Bana buk'ata a duba min"
"Haba Son taya ga ciwo a jikin ka kak'i yarda a duba maka, kayi hak'uri a duba maka please "


Duk wani rarrashi da lalla6a Daddy yayi wa Sabeer amman yak'i yarda har Doctor d'in da Daddy ya kirawo yazo amman duk Sabeer yak'i yarda gashi k'afar dad'a kumbura take, Daddy kasa jure ganin tilon d'an shi a haka yayi don haka ya bud'e baki yace......






Mu had'u next page fan's, naga Comment's naku na jiya sosai naji dad'i Allah ya bar k'auna.




Aishat A Muh'd ✍🏻


A SANADIN SON KI


Written by
Aishat A Muh'd


♻ EXCLUSIVE WRITER'S FORUM


Dedicated to my Sadeey saNaz






PAGE 46-47







Daddy kasa jure ganin tilon d'an nashi a haka yayi don sam bazai iya ganin Sabeer cikin mawuyacin hali ba don haka ya bud'e baki yace
"Ammm ku d'an bamu wuri zamu yi magana da Sabeer please idan muka gama zan kirawo ku"


Tashi suka yi suka fita kafin Daddy ya matso kusa da Sabeer ya dafa kafad'ar shi da hannun shi d'aya, zame hannun Daddy yayi tare da juyawa ya kalli wani 6ari daban, d'an murmishin yak'e Daddy yayi wai yau Sabeer d'in shi akan soyayya yake juya mishi baya wannan wanne irin so yake mata, bar tunanin yayi ta hanyar cewa
"Son look at me please"
Fuska a had'e Sabeer ya jiyo yana kallon Daddy sai wani had'e rai yake. Girgiza kai kawai Daddy yayi kafin yace
"Son bazan iya jurar ganin ka cikin wannan yanayin ba, na amince ka auri wannan yarinyar sai dai kuma wani hanzari ba gudu ba tace maka bata son ka ya za'a yi? "


Tuni fuskar Sabeer ta fad'ad'a da wani irin fara'a na tsantsar farinciki saboda jin abin da Daddyn shi yace, rungume shi yayi cikin dariya mai hawaye yace
"Thank U Daddyna nasan kai mai k'aunar farinciki na ne duk abin da nake so kana kok'arin yi min, sannan zan tafi inda Suhaima take nayi rayuwa irin tasu don na sami soyayyar ta A SANADIN SON Suhaima zan iya jure duk wata wahala Daddy indai zan same ta "


Kallon shi Daddy yake kawai cikin d'umbin mamakin abin da Sabeer ya fad'a ajiyar numfashi yayi kafin yace "Son kana nufin k'auyen zaka koma da rayuwa, kaci irin abincin su, ruwan su ka kwana irin d'akin su?"


"Yes Daddy zan iya indai zan samu Suhaima "
6ata fuska Daddy yayi tare da cewa "ina Son bazai yiwu ba, kaje dai ka taho dasu ita da Family d'in ta zan basu gida da kud'i sosai sannan na bawa mahaifin ta aiki amman kaje k'auye kana matsayin jikan mafi soyuwa acikin family d'in d'an fillo kaje ka zauna a k'auye haba Son "


D'an yatsina fuska yayi tamkar zai fashe da kuka yace "ni dai zan iya Daddy idan naje zanyi musu maganar dawowa nan da abin da zaka yi musu nasan zasu biyo ni "


Girgiza kai Daddy ya fara alamar bai yarda ba, aikuwa Sabeer ya ta6e fuska irin ta shagwa6a66un yaran nan zai fashe da kuka da sauri Daddy ya rungume shi yana bubbuga bayan shi yace
"Nooo Son don't cry please na amince Allah ya baka nasarar sace zuciyar ka kamar yanda ta sace maka zuciya lover boy"


Wani sanyin dad'i ne ya kwaranya cikin zuciyar Sabeer, kafin ya saki wani murmishi cikin zuciyar shi yana cewa ganin tafe zuwa gare ki Suhaima, rungume Daddy yayi cikin farinciki yace
"Thank U so much Daddy i am proud of U"
Bubbuga bayan shi Daddy yayi kafin yace
"Don't worry Son farinciki ka shine nawa all the best"


"K'arya kake Sabeer daman akan 'yar talaka 'yar k'auye kake wannan haukan duk ka d'aga mana hankali, danasan saboda haka kayi wannan abin da wallahi bazan zo wajen ka balle har na zubar maka da hawayen tausayi "


Gaba d'aya suka jiyo a matukar razani daga Daddyn har Sabeer d'in had'a ido suka yi da Mummy tana tsaye sai faman sauke numfashi take fuskar nan ko kad'an babu fara'a.


"Nima ina goyan bayan ta bazan ta6a zuba ido ya auro mana 'yar matsiyata ba daman akan haka kake wannan haukar to ko zaka mutu baza mu ta6a yarda ba, amman Sabeer ka bani kunya da mamaki, kai ma Hussein ka ban kunya da ka amince da buk'atar shi " cewar Hajjoh cikin tsananin 6acin rai.


Alhj Ahmad d'an fillo kuwa ya kasa magana ma saboda tsantsar 6acin rai har wani rawa fuskar shi take lol, saboda 6acin rai magana ma ya kasa yi. Had'e fuska Sabeer yayi alamar ba wasa ya mik'e tsaye yana d'ingishi ya k'arasa wajen Hajjah yace
"Hajjah kada ki k'ara kiran Suhaima da 'yar matsiyata ni Suhaima nake so ba ruwana da kud'in su don haka sai na aure ta babu wanda ya isa ya hanani! "


Tasss Sabeer yaji saukar zazzafan mari a saman kuncin shi wanda tunda Mumy ta haifo shi ba'a ta6a marin shi ba, marin ba k'aramin shigar shi yayi ba don sai da gefen bakin shi ya fashe kad'an jini ya fito, dafe kumatun shi yayi cikin mamaki ya d'ago kanshi ya kalli wanda ya mare shi ba kowa bane sai Alhj Ahmad d'an fillo sai huci yake zuba kamar wanda ya had'iyi kunama har da had'a gumi tamkar babu ac da fanka a bedroom d'in yayin da Daddy, Mummy da Hajjah suka kusan suman tsaye tsabar kid'ima da abin da akayi wa Sabeer.


Yana dafe da kumatun shi yana kallon Alhj Ahmad kafin kuma ya lumshe idon shi sai gani suka yi yayi baya luuu zai fad'i k'asa cikin zafin nama Alhj Ahmad da Daddy suka taro shi ya fad'o jikin su. Daddy jiki na rawa ya d'auko wayar shi ya kirawo Doctor, Hajjah da Mumy kuma kuka suka sanya tare da zube wa kusa da inda Sabeer yake suna cewa
"Sabeer ka tashi please "


Daddy ne ya d'auke shi ya d'ora kan bed da taimakon Doctor ya shigo don Alhj Ahmad zube wa yayi a k'asa yayi zaman 'yan bori hannun shi yake bi da kallo wanda ya mari Sabeer dashi tamkar wani soko haka yake kallon hannun, wai shi yau ya mari Sabeer mafi soyuwa cikin zuciyar a gaba d'aya cikin jikokin shi, anya shine kuwa da hankalin shi ya aikata wannan abin ko dai mafarki yake yi ba gaske ba ne kamar wani mutum mutumi haka ya koma ya rasa me zaiyi ma.


Dakyar Daddy ya lalla6a su Mumy da Hajjah suka fita don a bawa Doctor damar duba Sabeer haka Daddy yazo ya janye Alhj Ahmad dakyar suka fita tare da jan k'ofar bedroom d'in.


Likita yana cikin duba Sabeer yaga ya bud'e idon shi tare da tashi ya zauna cike da mamaki Doctor yake kallon shi, kamo hannun likitan Sabeer yayi sannan yace
"Doctor ina son abin da zan fad'a maka yanzu ka sanar da iyaye na bana son a samu matsala fah"
Gid'a kai likita yayi kafin yace "Okay baza'a samu matsala ba insha Allah "
A hankali Sabeer ya matso kusa da likitan kafin ya fara yi mishi magana cikin k'asa k'asan murya, bayan ya gama yi mishi maganar ne ya koma ya kwanta tare da rufe idon shi.


Suna zaune jugum jugum a parlour kowannen su ya rafka tagumi suna tunani ba mai yin magana a tsakanin su, k'arar bud'e door suka ji da sauri suka mik'e tsaye tare da nufar Doctor da sauri kowanne na jefo mishi tambayar jikin Sabeer.


D'an share zufa likitan yayi yayi shiru baiyi magana ba, cakumar wuyan shi Alhj Ahmad yayi tare da cewa
"Kai wanne irin wawa ne muna maka magana ya jikin Sabeer zaka zuba mana ido kana kallon mu kamar ka samu tv"


Ba k'aramin shak'a likita yasha ba dakyar Daddy ya cire hannun Alhj Ahmad daga wuyan shi, kafin yace
"Abba mu bi a hankali please "


Zama suka yi sannan likita ya shafa wuyan shi tare da jujjuya shi yace
"A binciken da nayi damuwa ce tayi wa Sabeer yawa sosai wanda a yanzu yana d'auke da hawan jini, idan kuka cigaba da matsanta mishi da 6acin rai ko ku k'i mishi abin da yake so idan ranshi ya 6aci zuciyar shi zata iya bugawa na lokaci d'aya don haka ku kiyaye "


"K'arya kake zuciyar Sabeer bazata ta6a bugawa ba "
Cewar Alhj Ahmad cikin tsawa gaba d'aya hankalin shi a tashe yake, "a cigaba da kwantar mishi da hankali a bashi abin da yake so, zanje na kawo maganin da zai sha yanzu "


Babu wanda ya kula shi haka ya zame ya tafi sannan suka shiga cikin d'akin inda Sabeer yake kwance, nan Alhj Ahmad ya zauna kusa dashi tare da rik'o hannun Sabeer yana mai nadamar abin da yayi mishi, a lokacin Daddy ya kirawo mai gyaran k'afa ya fara gyarawa Sabeer kafar shi kuka sosai Sabeer yasha shi a lokacin haka Hajjah da Mummy tare da Alhj Ahmad sun zubar mishi da hawayen tausayi Daddy ne kawai yayi dauriya ta rik'e Sabeer har aka gama gyara mishi kafin daga k'arshe wani wahalallen bacci ya sake d'aukan shi sai sauke ajiyar zuciya yake.......






Aishat A Muh'd ✍🏻
*A SANADIN SON KI*




Written by
Aishat A Muh'd




Dedicated to my Sadeey SaNaz






Dis page is dedicated to my Biebie dee ina tayaki murnar k'arin shekara Allah ya k'aro shekaru masu albarka Allah ya baki miji nagari wanda zai kular mana dake muzo musha biki 💃🏻😍😅.






_fan's kuyi hak'uri akan rashin yi muku typing kwana 2 akwai uzirin da ya dakatar da ni

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login