Showing 81001 words to 84000 words out of 122360 words

Chapter 28 - A sanadin Son ki Hausa Novels Document complete by Aisha A Muhammad Sanaz.txt

sannan shima ya zauna yana zuba musu abinci, kasa barinshi tayi da ya zuba musu ta kar6i serving spoon tana zuba musu.


Abaki suka dunga bawa junan su har suka k'oshe sannan ta tattara kayan ta kai kitchen, ta dawo ta gyara dinning table d'in, zama suka yi a parlour suna kallo tare da ta6a 'yar soyayya.




Sai da Sabeer ya bawa Suhaima hutun kwanaki biyu sannan aka d'ora daga inda aka tsaya, soyayya, kulawa da duk wata kauna suke nuna wa junan su, cikin farinciki da kwanciyar hankali suke abin su, babu mai zuwa gidan sai Jiddah ce ke lek'o su, sai dai waya da take yi dasu Yaya Aliyu kullum Sabeer kuwa yana kok'arin zuwa gida gaida iyayen shi, amarcin su suke sha yanda suke so babu mai tak'ura musu ko house girl basu da ita Suhaima ta hana Jiddah ta kawo mata tace ba yanzu ba.




Akullum cikin nuna wa junan su so suke biyayya sosai da kyautatawa Suhaima ke yiwa Sabeer yayin da shima yana kok'arin wajen sanya ta farinciki koyaushe, idan ka shiga gidan su kuwa sai ya birge ka saboda tsananin yanda suke kula da junan su.




Motarta tuni Jiddah ta aiko mata da ita gashi Sabeer ma ya bata kyauta ta mota mai matuk'ar kyau da tsada da sabuwar tsadaddiyar phone, sosai Suhaima tayi mishi godiya ta nuna mishi dad'in da taji addu'a sosai yasha ta daga bakin ta, gashi yana koya mata driving duk weekend da yamma zasu fita yana koya mata, yanzu matsalar ta d'aya shine ta cigaba da karatu amman tun da tayi mishi maganar sau d'aya ya nuna ba yanzu ta hak'ura duk da tsananin son da take yiwa karatun ta cigaba da farantawa mijinta rai ta barwa Allah za6in alkhairi akan makaranta.






_*After 3 Month's*_




Zuwa wannan lokacin idan kaga Sabeer da Suhaima sai kayi mamaki sun k'ara wani kyau musamman Suhaima ta k'ara cika sosai tayi 'yar kiba kad'an, bata fita ko'ina sai zaman gida kullum sau d'aya ta sake jarraba zuwa gidan su Sabeer amman har ta karaci zaman ta babu wanda yace mata ci kanki har gwara lokacin da Daddy ya dawo ya zauna sun d'an ta6a hira dashi amman ko a fuska bata nunawa Sabeer jin haushin abin da suka yi mata, Sabeer a lokacin tuni ya fara aiki da company d'in shi da Daddy ya bashi kyauta.


Zaune suke a garden da wani yammaci lokacin damina ne garin yayi luf luf dashi sai iska mai dad'i da take kad'awa mai ratsa jiki da sanya mutum nishad'i.


Suhaima tana sanye da wani wandon jeans iyakar shi rabin cinyar ta blue sai half vest white, yayin da Sabeer kuma yake sanye cikin 3quater kawai suna zaune kan wani babban carpet ga kayan fruits da juice da ruwa a gefen su.


Sabeer ne yake danna laptop d'in shi da hannu d'aya, d'ayan hannun kuma yana rungume da Suhaima ta gefen shi, cikin shagwa6a ta bud'e baki tace
"Ni Allah ka bar aikin nan kazo ka goya ni idan ba haka ba zanyi maka kuka "


D'ago kanshi yayi ya kalle ta sai wani turo baki take murmishi yayi tare da jan hancin ta yace
"Oh Baby rigima naji zan goya ki amman kiyi min afuwa na k'arasa aikin nan please "
D'aga kanta tayi, da sauri ya rik'o d'ayan hannunta yace
"Amman ban da kuka please"
D'an murmishi tayi sannan tace
"Toh bazan yi ba "
"Yawwa 'yammata na "


Cikin 10 minute's ya k'arasa aikin tare da rufe laptop d'in ya kallo ta cikin murmishi sannan ya sunkuya yace
"Baby taho na gama "
Cikin sauri ta taso tare da d'anewa bayan shi, yatsina fuska yayi sannan yace
"Wash! Bayana Baby kin k'ara nauyi zaki karya min baya "


Turo baki tayi cikin shagwa6a tace
"Ni.... Ni Allah ban wani k'ara nauyi ba kai ne ka dad'a zama babba "
"A'a Baby fad'i gaskiya "
"Toh bakai ne kake d'ura min abinci ba da yawa "


Dariya yayi yana cewa "a haba Baby fad'i gaskiya dai "
Hannun ta ta sanya tare da d'an mintsinin shi a damtsen hannun shi, wata 'yar k'ara ya saki
"Laaa Baby kika mintsine ne, aikuwa sai na rama "
Kafin ta ankara ya kwantar da ita akan carpet ya bi jikinta ya kwanta gaba d'aya sai ya saukar mata da nauyin shi , dakyar take jan numfashi tace
"Wayyo don Allah ka d'aga ni dear "
Yana dariya yace
"Nak'i wayon yarinya sai na rama ko kuma yau da dare na hanaki bacci kin yarda "
Da sauri ta d'aga kanta dariya ya sake yi sannan ya d'aga ta, hannun ta ta zube su kan carpet tana sauke numfashi, janyo ta yayi kan k'afafun shi tare da had'e bakin su waje d'aya wani salo na daban yake nuna mata itama babu 6ata lokaci take mayar mishi da martani.


Sunyi nisa cikin wannan yanayin ne yaji wayar shi na k'ara, ba don yaso ba ya d'auki wayar yana jan tsaki don an katse mishi jin dad'in shi.


"Hello Yaya na haihu "
"What! Da gaske kike? "
Cewar Sabeer yana tambayar Jiddah, cikin dariya tace
"Allah Yaya da gaske nake an samu Baby girl"
"Masha Allah na tayaki murna 'yar kanwata Allah ya raya "
"Yaya ka fad'awa Suhaima ita na fara kira wayan ba'a d'auka ba"
"Okay babu damuwa "
"Toh yaushe zaka kawo min Besty tun da kuka yi aure bata zo ba fah?"


"Jiddah surutu huh, yanzu kina buk'atar hutu ne kije ki huta zan kawo ta ne"
Cikin shagwa6a tace
"Yaya ka kawo min ita gobe don Allah idan zaka fita office "
"Okay naji "
Nan ya kashe wayar tashi, kallon Suhaima yayi wadda take kallon shi tun fara wayar shi ya ce
"Albishirin ki Baby "
Matsowa kusa dashi tayi sosai tace
"Goro fari k'al dear "
"Mene tukuici na idan na fad'a "
D'an dariya tayi kad'an sannan tace
"Ka fad'i duk abin da kake so zanyi maka "


"Jiddah ta haihu ansamu Baby girl "
Wani ihun murna ta saki tare da rungume shi tana dariyar farinciki kallonta yake duk tabi ta birkitashi ta kashe mishi jiki.


"Dear ka tashi mu tafi ganin Baby please "
"No Baby yanzu mangarib ta kusa ki bari sai gobe don gaskiya yanzu kin gama birkita ni tashi mu tafi ciki before mangarib tayi "




Sanin halin shi ya sanya ta biye mishi suka tafi, sai da suka sha soyayyar su tukunna sukayi wanka tare da yin alwala ya tafi masjid ita kuma ta shige bedroom nata don yin sallah, bayan ta idar da sallahr ne ta samu damar kiran Jiddah don yi mata barka kafin tazo sunsha hirarar su sosai kafin suyi sallama da juna.






_*Washe gari*_




Tun asuba da tayi sallah take faman gyaran aikin gidan bayan ta gama ta had'a breakfast sannan ta jera saman dining table, bedroom ta wuce ta cire kayanta ta d'aura towel ta shige bathroom don yin wanka, acan Sabeer ya same ta suka sha soyayya then sukayi wanka suka fito shirya junan su suka yi, yana sanye cikin wata blue na suits sai necktie black da black shoes yayi matuk'ar yin kyau.


Yayin da Suhaima kuma ta shirya cikin wani swiss lace brown da touch na red d'in flower's tayi kyau sosai, fita suka yi zuwa dinning table agurguje suka yi breakfast, sannan ta wuce d'aki ta d'auko mayafi babba red colour ta yafa sai flat shoes da handbag redred in colour perfumes masu sanyin k'amshi ta sanya sannan ta fito.


"Wow! Baby na kinyi kyau sosai "
Cewar Sabeer yana rungume ta ajikin shi.
"Nagode Dear kai ma kayi min kyau "
Kissing ya bata goshi sannan ya rik'o hannun ta suka fito zuwa compound.




Suna zaune bayan mota driver nayin tuk'i suka fita daga gidan hanyar gidan Jiddah suka nufa.


"Baby nima yaushe zaki haifa mana Baby? "
Ya fad'a yana shafa flat tummy d'in ta, kunya ce ta kama Suhaima dakyar ta iyacewa
"Duk lokacin da Allah ya bani sai na haifa mana "
"Haba Baby ina kula fah dake tun daga kika zo gidan nan baki yi period ba yau 3 Month's har da 'yan kwanaki da auren mu, ai nasan da ajiyata anan shiru kawai nayi miki "


D'an tunani ta fad'a yi tabbas rabon ta da yin period tun lokacin sauran 2 week's bikin su amman koda tana gida sai tayi 2 months bata ga period yazo mata shiyasa idan ta tashi yi take fama da menstruation pain mai tsananin zafi.


"Kinyi shiru Baby ko ba haka bane? "
Tana shirin yin magana suka shiga gidan Jiddah don haka sai ta mayar da bakin ta tayi shiru.


Tare suka fito daga motar hannun su sark'e cikin na junan su, suna kok'arin shiga parlour ne aka bud'e kofa tare da fitowa, sai da gaban Suhaima yayi mugun fad'uwa ganin Mumyn Sabeer ce wadda ta jima da zuwa duba Jiddah da Babyn ta, idanun ta akan hannayen Sabeer da Suhaima fuskar ta sam babu alamar fara'a.


Jikin Suhaima na rawa take kok'arin kwace hannun ta amman Sabeer ya rik'e k'am yak'i ya cikata don haka kawai ta tsugunna tana gaida Mumy, bata amsa ba sai kau da kai da tayi.


Sakin hannun Suhaima yayi bugging d'in Mumy tare da bata peck a cheek nata, cikin sanyin jiki Suhaima ta mik'e daga tsugunnan da tayi.


Kallon ta Mumy take yi sosai wanda ya sanya Suhaima k'ara rikicewa gabanta banda fad'uwa babu abin da yake, wani irin fad'uwa gaban Mumy yayi masifar yi a lokaci d'aya da ta hango wasu canji atattare da Suhaima wanda tasan tabbas sai mace mai ciki ne take canjawa irin haka abin ka da likita, wani mugun gumi taji ya karyo mata tun daga saman gashin kanta zuwa fuskarta da jikinta.


Zame hannun ta tayi daga na Sabeer ta fara tafiya zuwa wajen motar ta hankalin ta a masifar tashe duk yanda zata yi sai tayi don ganin ba'a haifi wannan cikin ba, don bazata ta6a had'a zuri'a da 'yar kauye ba abin da bazai ta6a yiwuwa ba dole tasan yanda zatayi cikin ya fita idan yaso duk lokacin da ta samu ciki sai tana zubar dashi.


Tasan halin Sabeer yanda yake masifar son yara dole ya rabu da ita daga lokacin da ya gane ita take zubar mishi da ciki duk da son da yake mata kuwa a wannan lokacin ne zata aura mishi yarinyar da take son ya aura wannan dabarar ta shine kawai zai kawo k'arshen zaman Sabeer da Suhaima, wani shegen murmishi Dr Faridah ta saki tare da shiga mota tabar gidan zuciyar ta fes take jin ta gani take kamar ma Sabeer ya rabu da matsiyaciyar yarinyar nan..........






_To fah reader's kunji tunanin Dr Faridah ko zata yi nasara akan Suhaima ta rabata da Sabeer, ina jiran comments naku yanzu labari zai fara, ƙų ¢ıɠąცą ɖą ცıŋą ɖơŋ ʝıŋ ყąŋɖą ʑąɬą ƙąʂąŋ¢ɛ_.






Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻
*A̺͆ S̺͆A̺͆N̺͆A̺͆D̺͆I̺͆N̺͆ S̺͆O̺͆N̺͆ K̺͆I̺͆*








Wྂrྂiྂtྂtྂeྂnྂ bྂyྂ
Aྂıʂɧąɬ Aྂ Mྂųɧ'ɖ




ɖɛɖı¢ąɬɛɖ ɬơ ɱყ ʂąɖɛɛყ ʂąŋąʑ











*PAGE 85-86*










Da kallon mamaki Sabeer da Suhaima suka bita dashi kawai kafin kuma Sabeer ya rik'o hannunta yace
"Sorry Baby nah akan abin da Mumy take miki bana jin dad'in haka ko kad'an "
Cikin rarrashi ya k'arasa maganar gashi fuskar shi d'auke da damuwa, d'an murmishin yak'e Suhaima ta saki sannan tace
"Kada ka damu don Allah komai mai wuce wa ne, mu tafi ka ga Baby kada ka makara a office ".
"Thank U Baby nah da yanda kike da fahimta i luv U "
Suhaima na shirin bashi amsa kenan Jiddah ta lek'o da kanta tana cewa
"Don Allah Yah Sabeer mene haka tun d'azu kuna tsaye anan ka hanata shigowa "


Hannun shi ya sanya tare da janyo kunnen ta d'aya yace
"Jiddah kin raina ni da yawa zan miki duka na tsayar da ita d'in mata ta ce ai "
D'an ihu ta saki na jin zafi kafin ta marairaice fuska tace
"Sorry Yah Sabeer na tuba na daina "
Yanda tayi d'in dole yasan ya shi murmishi ya cika mata kunnen, kamo hannun Suhaima tayi suka wuce cikin gidan.


Masha Allah abin da Sabeer ya fad'a lokacin da ya kar6i Babyn fara ce tas har wani ja ja take yi kyakkyawa da ita ta d'ebo kamannin D'an fillo family, wani son yarinyar ne ya shiga zuciyar Sabeer har yana imagine gashi Suhaima ta haifa mishi Baby yana d'auke da shi.


Kallon Suhaima yayi wadda take zaune kusa dashi tana lek'en Babyn don itama kanta tayi mata kyau ba kad'an ba.


"Baby kema kina so koh, ki haifa mana mu ma please "
D'an murmishi tayi kafin tace
"Toh my dear kayi addu'a Allah ya bamu masu albarka "
"Amin Baby "
Jiddah ya mik'awa Babyn don ya makara ma sosai, tashi Suhaima tayi ta rakashi har bakin mota suka yi sallama ta dawo cikin gidan, bayan ta gama ganin Babyn ne sai ta gyarawa Jiddah bedroom nata sannan ta wuce kitchen don shirya abincin rana.


Tana tsaka da girkin 'yan uwan Jiddah suka fara zuwa gidan kasa fita tayi su gaisa tayi don gabanta sai fad'uwa yake, dakyar ta k'arasa girkin ta zuba a foodflaks sai kawai taja kujera a kitchen ta zauna tare da had'a kai da gwiwa tana tunani.


Awannan yanayin Jiddah tazo ta same ta tausayin Suhaima ne ya kamata, dafa kafad'ar ta tayi a tsorace Suhaima ta d'ago kanta ganin Jiddah ce ya sanyata sakin ajiyar zuciya.


"Suhaima ki rage tsoron su fah wallahi, taya zaki zauna a kitchen bazaki fito ba saboda su? "
"Uhmmm Jiddah wallahi bana son kallon wulak'anci da k'ask'ancin da suke min, ina jin tsoron fita mu gaisa dasu kada su gwasale ni kamar yanda suke yi min "


"Kada ki damu Suhaima komai zai wuce amman baza ki tak'ura kanki ba saboda su don haka ki fito daga kitchen "


Babu yanda zatayi haka ta fito hannunta rik'e dana Jiddah, wani kallo na wulak'anci suka bita dashi kamar yanda Suhaima ta tsani ayi mata, babu wanda ya amsa gaisuwar ta sai ta6e baki da suke Jiddah ma sai da ta samu alakoran harara a wajen su.


Bedroom d'in ta Jiddah ta kaita ta zauna amman duk da haka a tak'ure take har so take lokacin tashin Sabeer daga office yayi yazo su wuce gida, duk da ya kirawo ta awaya amman ba'a kwanciyar hankali ta amsa ba mishi ba, har tunanin ranar suna take batasan irin wulak'ancin da zasu yi mata cikin mutane ba.


Atak'ure take har zuwa bayan mangarib sannan Sabeer yazo suka tafi gida, kallo d'aya yayi mata ya fuskanci tana cikin damuwa girgiza kanshi yayi yana yana sauke numfashi dole ya takawa 'yan uwan shi birki akan abin da suke yiwa Babyn shi bazai jure ba ko kad'an ganin ta cikin damuwa.


Duk damuwar da take tattare da ita sai da Sabeer ya cire mata ita ya mayar da gurbin farinciki a wannan daren sosai Suhaima ta k'ara jin wani son mijinta cikin zuciyar ta yanda yake faranta mata rai itama tana addu'ar Allah ya sanya ta haihu don cika mishi burin shi.




Ranar suna tun safe Sabeer ya kaita don yak'i barin ta ta kwana ko komawa bata sake yi ba sabida yana gudun kada a sake 6ata mata rai duk da kuwa nacin da tayi mishi, sosai Sabeer da Suhaima suka kashe kud'i wajen had'a wa Babyn kaya da kuma ita kanta Jiddah don duk abin da suka yi mata baza su biyata abin da tayi musu ba ita kadai ce mai kaunar ganin su tare sai Daddy adukkan familyn Sabeer.


Sosai Jiddah taji dad'i abubuwan da suka kai mata tayi musu godiya tare da addu'ar Allah ya basu suma yaran masu albarka, Sabeer yaji dad'in addu'ar da tayi musu sosai duk cikin 'yan uwanshi yafison Jiddah fiye da kowa don itace mai kaunar abin da yake so.


Baby taci sunan Babar Khaleel wato Khadijah suna ce mata Islam, ansha suna sosai don har walima da yamma sai da aka shirya an kashe kud'i sosai, amman duk wannan abun Suhaima bata shigaba tana zaune waje d'aya kanta ma yake masifar ciwo sosai, gashi tasha kukan habaici da wulak'ancin da su kayi mata.


Sai bayan mangarib 'yan uwa suka fara tafiya, zaune Suhaima take kan abin sallah idar da sallahr ishsha da tayi kenan tana addu'a cikin zuciyar ta tana mai tunanin inda Sabeer ya tsaya baizo sun tafi ba don kanta sosa yake ciwo kamar ya cire ga idanun ta da suka kumbura saboda kuka, ta kirawo phones nashi basa shiga dukka, gashi hadari ya had'u sosai sai walk'iya ake.


"Munafuka har yanzu zaman me kike da baki tafi ba, mun gaji da ganin fah ya kamata kisan nayi "
Cewar Aunty Fadilah 'yar autar su Daddy kenan tana wani hararar Suhaima, sunkuyar da kanta Suhaima kawai tayi idanun ta suna zubar da hawaye.


"Wallahi na tsani yarinyar nan kyau kamar aljanna duk tabi ta asirce mana Sabeer sai yanda tayi dashi daman 'yan kauyen nan da shegen yin asiri"


Dariya aka kwashe da ita irin mai k'ulawar nan suna cewa
"Sai Auntyn mu fad'a mata dai munsan asiri tayi ta mallake mana d'an uwa don Yah Sabeer bazai ta6a son wannan talakar ba yana cikin hayyacin shi"
Cewar Zahra kenan, bak'inciki da takaici ya ishe Jiddah cikin d'aga murya tace
"Ke Zahra wallahi ki kiyayi kanki Allah zan fad'awa Yah Sabeer yaci uban ki matar shi kike fad'awa haka "
Make mata bakinta Aunty Fadilah tayi tana cewa
"Ta fad'a d'in ya kashe ta idan ya isa "
Kuka Jiddah ta sanya saboda make mata bakin da tayi don da ba k'aramin zafi taji ba, yayi da Zahra take danna mata harara.


"Ni na rasa abin da zamu yiwa wannan mayyar yarinyar ta rabu da Sabeer ba irin wulak'anci da bamu yi mata ba amman ta lik'e mishi "
Dariya aka sake kwashewa da ita, sannan Khairat tace
"Ina fah zata rabu dashi Aunty taga kyakkyawan saurayi sabon jini ga kud'i da ilimi inace ko aji ma ta ta6a shiga wannan shegiyar Jiddah ce ta wayar da ita "


Wani irin kuka mai tattare da bak'inciki Suhaima ta saki saboda ta kasa rik'e kukan nata,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login