Showing 27001 words to 30000 words out of 122360 words

Chapter 10 - A sanadin Son ki Hausa Novels Document complete by Aisha A Muhammad Sanaz.txt

idan da sabo ta saba da shariyar Sabeer wani lokacin musamman idan yana cikin damuwa bai fiye son magana ba.


Mumy tana fita ya zame ya kwanta kan sofa yayi matashin kai da hannayen shi, idanun shi lumshe su yana tunanin Suhaima sosai yake mamakin yanda yarinyar ta tsaya mishi cikin zuciyar shi, shi baisan so ba amman da alama ya fad'a son wannan yarinyar, dummm gaban shi ya fad'i da ya tuna yanda 'yan uwanshi da iyayen shi suka tsani talaka balle ita a k'auye ma take, yanzu shi ya zai yi zuwan shi wajen uku k'auyen ko mai kama da ita bai gani ba ya rasa yanda zai yi.


Son da yake mata bazai iya hak'ura da ita dole ne yasan yanda zai 6ullowa al'amarin, bayan bikin Jiddah dole ya koma k'auyen ya neme ta, zai nuna mata so sannan zai bawa iyayen ta kud'i sosai ya basu gida da mota da jari sosai yanda bazai samu matsala ba ta 6angaren iyayen shi idan suka ga iyayen ta masu kud'i ne, wani murmishi ya saki na kamar wanda ya samu nasara ma sai lokacin hankalin shi ya kwanta, kiran sallahr mangarib ne ya katse mishi tunani, toilet ya shiga yayi alwala ya fito kai tsaye masallaci ya wuce.




Babban hall ne wanda ya k'ayatu da decorations masu kyau da k'ayatuwa wajen ya tsaru yayi kyau sosai, ga haske tamkar ba dare ba sanyi Ac ta ko'ina ban da k'amshin tsadaddun turaren jikin manyan masu kud'in da suke zaune a wajen kamar anyi 6arin turare a wajen.


Manyan hamshak'an mutane ne masu kud'i sosai a wajen ansha kwalliya ta kece raini ga tsadaddun sutturu da aka sanya mutane suna zazzaune a wajen da aka tanadar musu, slow music ne ke tashi kawai a wajen duk mutane an hallara, family d'in Jiddah gasu nan ga friends na iyaye dana amarya sai na yayyanin amarya dana k'anen ta abin dai ya tsaru gwanin sha'awa kowanne da kalar ankwan su, haka 6angaren dangin ango gasu nan da nasu ankon daban suma sunyi kyau sosai.




Amarya da ango ake jiran shigowar su babu dad'e wa mc ya fara sanar wa shigowar ango da amarya kowa ya nutsu ya zubawa kofar shigowa kallo don ganin shigowar amarya da ango.


Cikin takun k'asaita da nutsuwa Jiddah da angon ta khaleel suka shigo hannun su sark'e da junan su, Jiddah tana sanye da wata farar gown har tana jan k'asa sai ash head da ta sanya yana da kwalliyar flowers silver ajiki pose da hill nata dukka ash ne masu kwalliyar silver ajiki tayi kyau sosai abin ta, haka angon ma Khaleel yasha shadda ash colour sun yi matukar kyau da dacewa da junan su, sai watsa musu wasu fararen furanni da red ake yi.


Bayan su kuma Suhaima ce tasha light pink na gown sai head nata pink mai d'an duhu tasha makeup tayi matukar kyau tamkar ba Suhaima ba, ba wanda zai ganta ya zaci daga k'auye ta fito tama fi 'yan birnin kyau a wajen don ba k'aramin haskawa tayi ba tamkar itace ma amaryar ba Jiddah, don kallo dawowa yayi kanta abin da yasa duk ta dibirbice ta rasa inda zata yi saboda idanun mutanen da suke kanta sai murmishin yak'e take.




Da haka ta samu waje ta zauna bayan ango da amarya sun wuce wajen zaman su, nan aka fara gabatar da dinner cikin nutsuwa da wayewa, gaba d'aya Suhaima a tak'ure take saboda bata saba zuwa irin wad'annan wuraren ba, har zuwa lokacin da amarya da ango suka fito domin taka rawa nan 'yan uwa da abokanan arzik'i suka fito domin yi musu lik'i.


Dr Faridah ce ta fito filin wajen nan mutane suka bata hanya ta wuce zuwa inda su Jiddah suke tsaye ita da angonta suna taka rawa a nutse, bag d'in hannun ta ta bud'e ta fito da bandir d'in 1k ta fara watsa musu tamkar bata san zafin kud'i ba sai da ta gaji tukunna ta bar wajen.


D'ago kan Suhaima yayi dai dai da barin Dr Faridah wajen aikuwa suka had'a ido wani irin bugawa zuciyar Suhaima tayi da k'arfin gaske haka ma a 6angaren Dr Faridah d same abin da Suhaima taji haka taji itama, amman sai ta kawar da kanta daga barin kallon ta cikin zuciyar tana tunanin irin wannan kyan na yarinyar da bata ta6a ganin ta ba sai yau, gashi ta d'an birgeta kad'an da taga duk da kyan da take dashi but bata da rawar kai irin na 'yammatan da suka waye sosai kafin kuma watsar da tunanin ganin Suhaima ta cigaba da sha'anin gaban ta.


Har zuwa lokacin da aka buk'aci amarya da ango su yanka wedding cake nasu, nan 'yan uwan amarya da ango 'yan kad'an suka rakasu wurin cake d'in babu 6ata lokaci suka yanka Khaleel ya bawa Jiddah a baki itama ta yanko tare da d'an tsugunna wa kad'an ta bashi nan aka hau tafi.


Suhaima ba k'aramin birgeta suka yi ba sai sakin murmishi take ita kad'ai, zuwa yanzu ta d'an saki jikin ta da zaman wajen, amman sam duk da haka har yanzu bata ji sha'awar ta auri irin d'aya daga cikin wad'annan masu kud'in ba, tana kallon yanda su Zahra da sauran sisters d'in Jiddah suke wurgo mata harara tsanarta k'arara akan fuskar su, d'aga kafad'ar ta tayi alamar ko a jikin ta, tana fatan jibi iyanzu tana k'auyen su cikin gidan su, sai su harari wata ba ita ba.


Ana gaf da tashi a wurin Sabeer ya shigo cikin hall yana sanye cikin wata light blue sky na shadda tsadaddiya har da hula akanshi, d'inkin shi irin wanda matasan yanzu suke yin shi ba k'aramin kyau yayi ba, a daidai lokacin kuma Suhaima ta taso zata fita daga hall d'in don amsa kiran wayar da Yaya Aliyu yake yiwa Jiddah.




Karo suka yi da junan su inda Suhaima ta bige kanta da kafad'ar shi, dafe goshin tayi tare da yamutsa fuska tace
"Washh Allah na "


D'ago kan da zata yi ta bashi hak'uri suka had'a ido da junan su, kallon second 3 Suhaima tayi mishi ta gane ko wane tuni jikin ta ya fara rawa tsoro ya kamata kada ya d'auki fansar abin da tayi mishi a wajen da batasa kowa ba sai Jiddah, shima Sabeer kallon ta yake cikin mamakin me ya kawo ta nan kuma don ko acikin mafarki ya ganta sai ya gane ta wane ya kawo ta wajen bikin k'anwar shi? Ta dalilin wata zo nan? wad'annan tambayoyin ya yiwa kanshi a lokacin d'aya.


Ganin ya zuba ido yana kallon ta yasa ta saurin fita daga hall d'in, cikin zafin nama ya bita yana cewa
"Hey tsaya mana kece wan...."
Kafin ya k'arasa maganar tashi yaga wayam babu kowa a wajen, ta gudu kenan abin da zuciyar shi ta fad'a ba guduwa tayi ba 6oya tayi, ina ta 6uya kuma?.


Daga d'an nesa kad'an na hango Suhaima tana lek'en shi jikin ta na 6ari zuciyar ta na bugawa da k'arfi, ganin yana dube dube a wurin ya sake fad'ar mata da gaba, bata k'ara rud'ewa ba sai da taga ya nufo inda take.


Yana daf da k'arasa wa inda take ne yaji an rik'o hannun shi da sauri ya juya ga ashe Mumy ce da tarin kannen shi, wayyo Allah ya furta cikin zuciyar shi don yasan yanzu yaran nan zasu sa mishi ciwon kai da hayaniyar su
"Yah Sabeer kazo mu d'auki pic's please "
Cewar wata sistern shi zai yi magana kenan Mumy tayi musu magana da ido, dariya suka yi don su fahimci me take nufi, aikuwa hannun shi suka kama zuwa cikin hall d'in bashi da yanda zaiyi ya bisu yana tafiya yana dube dube har sai da suka wuce ciki sam ranshi babu dad'i ba haka yaso ba yaso ta tsaya su yi magana ta fahimta amman dole ya binciko wanda yayi inviting d'in ta zuwa wajen nan.


Fitowa Suhaima tayi daga inda ta 6uya tana sauke ajiyar zuciya har da gumi ta had'a duk tayi wani iri kallo d'aya mutum zai mata yasan a firgice take, zama tayi a gefen wasu flower's tana sauke numfashi....










Aishat A Muh'd πŸ€ΈπŸ»β€β™€


A SANADIN SON KI


Written by
Aishat A Muh'd


β™» EXCLUSIVE WRITER'S FORUM


Dedicated to my Sadeey saNaz






PAGE 36-37









Suhaima ta d'auki wajen 5 minutes kafin ta d'an nutsu ajiyar zuciya ta sake saukewa a karo na ba adadi tace
"Alhmdllh Allah nagode ma da wannan mutumin bai kamani ba da yau nasan zai ya rama abin da nayi mishi"
Suhaima ta furta hakan a sarari, wayar hannun ta ne ya cigaba da ringing dole ta dai daita nutsuwar ta tayi picking ganin sunan Yaya Aliyu ne akai.


Bayan sun gaisa ta tambaye shi jikin Aunty Aliyah daga nan shima ya tambaye ta yanayin zaman nata don tun da ya tafi hankalin shi yak'i kwanciya sam ga jikin Aliyah sai a hankali, boye mishi gaskiya Suhaima tayi tace tana nan lafiya yanzu ma suna wajen party dinner d'in Jiddah, daga k'arshe yayi mata nasiha sosai tukunna suka yi sallama ta ajiye phone d'in saman k'afarta tare da rafka tagumi tana tunanin yanda za'a yi ta koma cikin hall d'in bayan taga Sabeer ya shiga ciki, nan take zuciyarta ta bata shawarar zaman ta anan waje har a tashi nan take ta aminta da shawarar zuciyar ta sake gyara zama tayi tana jiyo sautin kid'an da yake tashi a wajen partyn.




Sai wurin 11 na dare aka tashi lokacin Suhaima har ta fara gajiya da zaman jiran Jiddah ta fara gyangyad'i a wurin, sam Suhaima batasan har an tashi ba gyangyad'in ta kawai take sabida ta gaji gashi bata saba kaiwa wannan lokacin ba batayi bacci ba gashi ba'a saitin k'ofar shiga hall d'in take ba balle a taji fitowar mutane.




Sai da aka watse a wurin bai fi mutane d'ai d'aiku ba Suhaima ta farka daga gyangyad'in da take tamkar wadda aka tasa haka ta bud'e ido firgigit, ganin yanda duhu yayi sosai yasa Suhaima rarumo wayar Jiddah dake saman k'afarta ta duba time, wani zabura tayi ta mik'e tsaye cikin tashin hankali ganin har k'arfe 11:30 tayi na dare, ai d'ora hannun ta tayi dukka biyun a saman kanta tace
"Wayyo Allahna na shiga uku ni Suhaima yau nice a waje har k'arfe goma sha d'aya da rabi innalillahi "


Lokaci d'aya hawaye suka fara zubo mata ga wani mugun tsoro da sanyi da take ji, tafiya ta fara yi ta nufi k'ofar hall d'in taga duk yawan mutanen nan wayam sai wasu d'ai d'aiku wanda batasan fuskar su ba, tuni Suhaima ta samu waje d'aya ta raku6e ta fara rasgar kuka kamar wadda akai mata dukan tsiya.


Kuka sosai take har da majina ta rasa mafita don duk a rud'e take ta kasa dai daita nutsuwar ta balle ta sami mafita gashi phone d'in Jiddah a hannun ta wa zata kirawo acikin familyn ta mutanen da basu yi maraba da zuwan ta cikin su ba matsayin bak'unta na kwanaki biyu, balle ta samu damar kiran wani daga ciki ya taimaka mata, gashi idan ma ta kirawo Yaya Aliyu d'aga musu hankali kafin ma yazo ma koma mai ne ya cinye ta kuma bata yi wa Jiddah adalci ba idan ta fad'a mishi yanzu ya zata yi wayyo Allah na, sake rushe wa da kuka Suhaima tayi sosai tana nan a raku6e taji an dafa mata kafad'a tare da cewa
"Hey what are you doing here? "
Wata irin firgita Suhaima tayi tare da jiyowa a tsorace had'a ido tayi da wannan guy d'in na d'azu yana tsaye daf da ita ya hard'e hannun shi a kirji, wani k'ugi cikin ta yayi wanda tana tunanin ma Sabeer yaji k'arar da cikin nata yayi matse k'afafun ta ta fara yi saboda daf take da sakin fitsari a tsaye jikin ta kuwa sai rawa yake wanda ya sanya wayar Jiddah ta fad'i a k'asa da bag d'in ta.


Kallon ta Sabeer yake up and down yana sakin wani murmishi wani sanyin dad'i ne yake ratsa cikin zuciyar shi da gangar jikin shi, sauran kad'an dariya ta kubce mishi ganin yanda take matse k'afa tamkar wanda yake jin fitsari ya matse shi irin sosai d'in nan har k'arar da jikin ta yayi sai da yaji sautin.


Ganin murmishin da yake ba k'aramin sake rud'ar da Suhaima yayi ba aikuwa fakar idon shi tayi ta tattara gown d'in ta da hannun ta kafin Sabeer ya ankara yaga Suhaima ta zura da gudu tayi hanyar fita daga gate, ba shiri shima ya d'auki phone d'in da bag nata da suka fad'i ya bita da gudu shima.


Suhaima da ta bud'e kofar gate d'in zata fita da sauri ta dawo baya jin wani irin sanyi da ya busa ta gashi wajen duhu babu wadaccen haske sosai a wurin nan ta tsaya waje d'aya tana rawar jiki, da haka Sabeer ya cimmata tana tsaye sai ruwan hawaye da yake tsere saman kyakkyawar face d'in ta, ganin Sabeer a kusa da ita da sauri Suhaima ta bud'e baki tace
"Don girman Allah kayi hak'uri da abin da nayi maka tsautsayi ni bazan sake ba har abada kayi hak'uri kada kayi min komai bansan kowa anan ba "


Sosai ta bashi tausayi ganin irin rud'ewar da tayi cikin sanyin murya yace
"Hey calm down babe babu abin da zan miki just I'll help you"
Kamo hannun ta yayi ganin har yanzu bata daina rawar jiki ba kuma a rud'e take, jan hannun ta yake har cikin mota ya zaunar da ita tukunna ya zagayo seat d'in driver ya zauna kallon ta ya tsayayi na tsayin wasu minutes, kallon yake cikin wani irin yanayi ita kuwa kanta a sunkuye batasan abin da yake ba tsoro ne fal a tattare da ita addu'a take cikin zuciyar ta Allah yasa kada ya cutar da ni, kafin yayi wa motar key suka bar wajen sun d'an yi nisa suna tafiya tukunna ya jiyo ya kalle ta still har yanzu kanta a sunkuye.


D'an girgiza kai yayi tare da sakin dan murmishi yace
"Ina zamu je, i mean ina ne gidan da zan kai ki? "


D'an satar kallon shi tayi ta fad'a duniyar tunani ita da take bak'uwa a garin yau ne zuwan ta na farko ina zata gane gidan, don haka sai tayi shiru kawai.


Ganin haka yasa Sabeer yace
"Ina jiran ki fah kinsan dare yayi fah idan baki da wajen zuwa kuma sai mu wuce guest house d'ina mu d'an huta zuwa gobe "


Wani zaro ido Suhaima tayi tamkar idanun ta zasu firfirto wani tsoro da nadamar shiga motar shi ya dirar mata lokaci d'aya ashe d'an iska ma ta shiga motar shi yau na shiga tara ba uku ba, dariya sauran kad'an ta kubce wa Sabeer ganin yanda Suhaima ta koma.


"Don Allah kasan gidan su amaryar Jiddah? "
Suhaima ta fad'a cikin rawar murya, da mamaki ya kalle ta kafin yace
"Oh nan zaki je kenan? "
Da sauri Suhaima ta d'aga kanta alamar eh, mamaki ne sosai ya kama shi ta yanda akayi Suhaima tazo gidan tun da yasan halin 'yan gidan su da basa huld'a da talaka sai mai kud'i d'an uwan su.




Kuyi hak'uri da wannan fan's mu had'u a next page muji ya zata kasance.
Ga Sabeer da Suhaima sun had'u shin komai zai faru kuma?...




Aishat A Muh'd ✍🏻
A SANADIN SON KI


Written by
Aishat A Muh'd


β™» EXCLUSIVE WRITER'S FORUM


Dedicated to my Sadeey saNaz






PAGE 38-39








Babu wanda ya sake magana a cikin su kowannen su da tunanin da yake cikin zuciyar shi, amman Suhaima har yanzu hankalin tashe yake ganin har yanzu basu zo gidan ba ta sadaukar sace ta ma yayi tuni wasu sababbin waye sun cigaba da zuba saman fuskar ta, d'an kallon ta Sabeer yayi kad'an yana girgiza kai cike da mamakin ta ko wahalar kuka bata yi. Da haka suka k'arasa gidan Suhaima tana ganin an shiga cikin gidan ta tabbatar shine sai da ta saki ajiyar zuciya na kwanciyar hankali kafin ta sanya hannun ta saman face nata da niyyar goge hawaye sai taga an mik'a mata tissue kar6a tayi ta goge tukunna ta fara kok'arin bud'e kofar motar, kamar ance ta jiyo ta kalli side d'in su Jiddah aikuwa ta hango Jiddah tana tafiya cikin sauri tana goge fuska, da sauri Suhaima ta k'arasa fita kamar abin arzik'i ta rufe kofar motar sai ta zuro kanta ta jikin window da yake ya sauke glass d'in.


Sabeer har zai yi wuce zuwa parking lot sai yaga ta zuro kanta sai ya tsaya ya d'auka godiya zata yi mishi sai hasashen shi yasha banban da na Suhaima don cikin tsiwa ta fara cewa
"Uhm Malam ka d'auka godiya zan maka da ka zuba ido kana kallona har da bud'e kunnuwa don jin abin da zance, to ban gode ba kuma hak'urin da na baka d'azu in mistake ne, me yasa ma ka tausaya min ka d'auko ni da ka barni acan ma da nafi jin dad'i... "


Da sauri Suhaima ta fitar da kanta tare da zurawa da gudu zuwa inda ta hango Jiddah a tsaye sai safa da marwa take, sakamakon wata cafka da Sabeer ya kawo mata ganin ta gudu ne yasa shi dunk'ule hannun shi ya naushi d'aya hannun kafin ya jingina kanshi jikin kujera yace
"Hmmm lallai babe d'in nan da na kama ki yau a hannuna da sai gane kuren ki sai tsiwa da shegen tsoro fal ciki"


Shi mamakin ta ma yake tun da suka taho take kuka jiki yana rawar tsoro, amman wai har ta samu bakin tsiwa da taga ya kawo ta inda take buk'ata, kwafa yayi tare da k'arasa wa parking lot yayi parking tukunna ya nufi part d'in su

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login