Showing 75001 words to 78000 words out of 78322 words
shekin dawo"
"to khairat bari naje din"
saida ta sunkuyo ta sumbaci for head din khairat din gamida shafa gashin kanta da cikin tafin hannunta sunawa juna murmushi snn ta fita.
duka duka batafi minti 10 da futa ba tagama wanke lallen hannunta knn kmr ance ta d'aga kanta setin kofar dakinta,wani baqin hayaqi ta hango yana fitowa a cikin
sa.
wani azababben faduwa gabanta yai kamin kuma taji qarajin su zee,
aguje tabar wajen zuwa cikin gida, bakin kofa ta samesu suna ganinta suka rungumeta dan a tunanunsu ko tana cikin dakin wnn hayaqi ke tasowa to gata sunganta ga kuma mukarram nan Hannun heema inda sunsan khairat na islamiyya to koma miye zai zo da sauqi, gani sukai hayaqin ya qara ta'azzara kankacemi wuta ta kama cikin dakin basmah,
kuka basmah tasa gamida nufar kofar tana jijjigawa hucin wutar ya datse qofa ta kulle taqi motsi bare buduwa a gigice tadawo wajen su zee tana cewa
"k...khairat. khairat na ciki ynz ta dawo makaranta ku fiddomun khairat, duknsu arazane suka kalleta,dagudu zee da Fatima da heema suka hada qarfi suka dunga dukan kofan cikin qaraji, kuka suke suna kiran sunan khairat tazo ta bude musu kofa, hakan yajawo hankalin maikatan gidan mai gadi da direba suka iso wajen, ba qaramin tashin hankali suka rizqaba take suka kira yan fire service kana suka kira hafiz shima,
Zee da suketa dukn kofa har ynz kofa taqi motsi zubewa wajen sukayi suka rungume juna qara sakin wani irin gursasshen kuka mai kashe zuciya gamida qara ambaton khairat, da gudu Hafiz yazo wajen cikin tashin hankali dan kusan tare suka iso da motar ma'aikatan,
6alle qofan sukai suka dinga feso ruwa a dakin aqalla sun kwashe rabin awa snn wutar ta mace, kuma abin Allah dakin basmah kawai wutar taci,durqushewa Hafiz yai yana kokowa da nunfashinsa sanda yaga yan fire sun fito da gawar khairat a hannu ta sanqame mimmiqe, jikin ta yayi wani irin baqiqirin a kone hakama fuskarta takone wasu wuraren har sun fara taljewa haka aka aje khairat qasan falo,
aisu heema na ganin gawar khairat a haka gabansu cikin wnn dimautaccen yanayin tuni numfashinsu ya tsaya cak hadda basmahn, to fa daga nan basu qara sanin inda Kansu yake ba,
kuka Hafiz ya fashe dashi gamida tatta6a jikin khairat cikin futa hayyaci yk furta "mafarki nakeyi komi,
miya faru khairat dakin mamanki babu gas bare ashana miya kawo tashin wuta a cikin sa?!!!!
khairat kidawo dan Allah kada ki tafi ki barmu muna tsaka dajin dadinki a cikin rayuwarmu, surutai yadingayi kmr ya zauce, kankacemi tuni gidan yacika da mutane yayinda aka dauke su basmah zuwa asibiti dan dudda ruwan da aka dinga yayyafa musu babu wacce ta farka a cikin su, su hjyn mecca da hjyn hafiz da yn gidan gaba daya suma da suka zo hadda masu sumewa ana watsa musu ruwa suna qara komawa, tashin hankali matuqa ya wanzu a lokacin, mutane danqam qofar gida hadda yara abokon khairat yan islamiyyarsu kuka kawai suke suna fadin
"khairat ta mutu shiknn😭"
da qyar Hafiz yayi ta maza aka yiwa khairat wanka aka fiddota waje aka sallaci gawarta suka nufi kaita makwancinta na gsky,
Abin mamaji dakin basmah gadonta da suturunta basu kone ba ko kadan wuta bata ta6a suba, wutar dai daga Allah ce tazo ga wacce aka qadarto hakan kanta kuma Allahu ta'ala a'alamu,
Allah kadai yasan abunda ya faru sanda wuta ta fara ci a dakin har asu na cewa dama khairat ta hau gadon mamarta inda shi wutar bata ta6a sa ba wasu kuma na cewa ai komi zata hau inda kwana sun qare saita tafi, Hafiz kuwa jiyakeyi aransa to wai sanda wutar ta kama wanne hali khairat ta shiga ne? yasan zataita kiran sunayen su ne da sunan suzo su kawo mata dauki amman inaa Allah ya kawo iyakar knn,
shi qarin kukansa ma a ynz shine sanda ya farka basmah kece masa khairat Nata nacin zuwa wajensa yana barci bai tashi ba har ta tafi, shiknn ynz karshen ganawarsu knn da khairat a jiya?
Wasu zafafan kwallan sa suka dinga d'iga a bisa kabarin khairat daga idanunsa,
ya jima yana mata add'ua haka ma mutane snn suka baro wajen yana waiwayen qabarin juya nason kada shi saida yaya nura ya riqesa snn,
ahaka ma jama'a wasu na fitowa a makabartar wasu na shiga dandai suga kabarin khairat suyi mata addua kuma,
yarinyar tayi mutane na ban mamaki har turereniya akeyi a tsakani.
Allahu Akbar, rai baqin duniya, kullinafseen za'iqatil mauti kowane mai rai mamaci ne,
Allah baya barin wani dan wani yaji dadi,
a wann gabar nake sanar daku reader's cewa tabbas labarin khairat gaskiya ne ya faru da gaske true life story ne agaremu ya faru,
muna barar addu'anku gareta Allah yaimata Rahma ita da sauran musulmai gaba daya😭👏🏼
Yah haisam ko fada ya dingayi wa Hafiz akn wnn ai gangancin matansa ne, danmi zasubar yarinya qarama ita kadai bawani tareda ita ynz hk sun hada kayan wuta ne sun barsa a kunne har ya jawo hakan,
wnn ai ba rayuwa bace sun canci hukunci kwarai.
cikin jan ido Hafiz ya d'ago ya dubesa gamida cewa...
.
[8/4, 10:38 AM] Xainab Documen: *♨️♨️MATAN HAFIZ♨️♨️*!!!
*FASAHA ONLINE WRITERS*
F.o.w.
Written by.
*FOUR GORGEOUS WRITERS*
-Raheenat mahmud.
-Mmn Abduljalal.
-Xayyneb💤💤 (xexen Fasaha).
-Matan Borno.
*♨️Impacting valuable knowledge and entertainment is our concern.♨️*
Bismillahirrahmanirraheem.
*Gargad'i*
Bamu yarda a juya mana littafi ko ta wacce siga ba tare da izini ba.
48.
Cikin jan ido Hafiz ya d'ago ya dubesa gamida cewa
"dan Allah yayah haisam kama daina wnn zancen, wnn fa mgnr taka kmr kana yin jayayya da hukuncin Allah ne, wnn lamari a yanda yazo kowa yasan hakan rubutacce ne daga Allah domin babu wani Abu mai kama da wuta dake cikin dakin d wnn nufi ne na Allah haka kuma qaddarar khairat tazo mata fatanmu agareta ubangiji Allah yasa hakan shine alheri a gareta damu baki daya" sosai Yaya haisam jikinsa yayi sanyi musamman daya lura da ynda Hafiz ke mgn yana share qwalla a idanunsa cikin dabara, dafa kafadar Hafiz yai yace "d'an uwa na fahinta amnan ka gafarceni kan mgn ta danai Allah yajikn khairat yasa mai ceton iyace ce"
ya fada a fili, take yan zaman makokin dake gefensa suka amsa da fadin
"Aminnnnnn ya Rabbi".
haka zaman makokin ya kasance har tsawon kwana daya da wuni daya, alokacin kuma zee da heema da Fatima suka farko suma dan ita basmah tun a daran ranar ta farko sune dai sai da suka yi kwana da wuni snn suka farko,
aikam nan suka rungume juna dukansu suka kuka Hafiz yayi iya yinsa suyi shiru basmah da heema ne suka fara dangana dankuwa zee da Fatima har suka koma gida kuka sukeyi kowa yazo yi musu gaisuwa sai hawaye, ahaka har akayi sadaqar 3, abbun basmah ma yazo musu k'arin gaisuwa shims nan ya jima yana lallasansu gamida wa'azantarwa danuna musu cewa gaba daya duniyar ba matabbabata bace Inda ma'aiki shugabanmu fiyayyen halitta Annabi Muhammad saw yabar ta babu wani dazai zo ya zauna a cikinta shiyasa kai mutum karage dogon buri a cikin rayuwarka domin rayuwarka Na hannun ubanigiji duk sanda ya buqaceka dole zaka amsa kira sa,
to khairat itama kunga knn lokacinta ne yayi na tafiya kuma su da suka tafi ba suyi sauri ba mu da muka tsaya ba jinkiri mukai ba fatanmu dai Allah yabamu ikon cikawa da kyau da imani kuma ahalin ynz a ikirarin nuna soyayyar da kukewa khairat zaku iya juya sa da yawan addua gareta domin ita tafi buqata a gareku ynx fiye da son da kuke mata ba koke-koke ba,
ta tafi ba dawowa zatai ba ammn kudaina mata kuka haka nan addu'ankun nan dai ne zai risketa yasata farinciki a makwancinta,,, abbu ya jima yana musu nasiha gamida jawo musu hadisai na mahaqurta a rayuwa saida jikinsu yayi snyi matuqa dan ko tun daga ranar suka rage yawan kuka sosai,
addu'ansu kuma ta qara yawa gareta,
mutuwar khairat taqara bawasu zee tsoro domin sunqara tabatarwa da rayuwar dan Adam ba komi bace a wajen Allah ynz mutum ynz ba mutum ba, gashi khairat ta zama tarihi a cikin rayuwar su ta tafi ta barsu cikin tsananin hadin kai ga junansu gamida qaunar junansu fisabililla da kuma temakon juna duk ata sanadiyyarta to sukam miyafi su sakawa khairat dashi inba add'ua ba ammn tabbas har abada tarihin khairat bai taba gogewa a rayuwarsu har sai sun kwanta dama suma snn, shima haka ata bangaren Hafiz sautari yakan zauna tunanin halayen khairat dan sauda dama sanda tana a raye yakan rasa shin minene khairat tafiso dazai siyomata najin dadin rayuwa danya burgeta? to ko ya sawo din bata irin juna murnarta nan naturally kmr na yara komi ita tasamu lfy lau yk mata batada zabin komi a rayuwar ta komin qarantar abu gareta bata damuwa akabata zata amsa,
sam bata dauki son jin dadin ryuwa ba tasa a ranta ba to sai gashi Allah ya sama bamai yawancin rai bace, sosai yakan jima a cikin sujudarsa ta salla yana wa
khairat addua izuwa babban makwancinta, hakama ta bangaren basmah takan share hawaye duk idan ta tuno khairat zuciyarta na gaya mata ashe rayuwr ta da 'yarta bamai daurewa bace? saida suka fara sakin jiki da juna tana burin bawa 'yarta cikakkiyar kulawarta saidai mutuwa mai raba tsakani Allah ya kawo qarshen zaman ashe,takan lumshe idanunta taqara sakin wani sanyayyen 6oyayyenb
kuka a daki ita 1,
yayinda koda yaushe bakinta bai taba mancewa da aikawa da khairat dinta addu'a zuwa k'abarinta tareda sauran musulmn Allah baki daya ba, kwanci tashi har akayi sadaqar 40 anyi taro sosai gamida addu'oe, aka rarraba abinci da abinsha yayinda kowane kullin abinci da kudi a jiki dubu 5 ga dukkan wnda Allah yabawa ikon zuwa gaisuwan, dan Hafiz ji yakeyi da zai qarar da dukiyarsa gaba 1 a medo musu khairat da ya fimasa sauqi domin zama da yarinya kmr khairat ga ilimi da hangen nesa tausayi ahaka tuntanama qaramarta inaga ace ta girma tabbas hkn ba qaramin alheri bane a rayuwar su da ta al'umma amman yasan inaaaa bamai yuyuwa bace Allah ya fisu sonta shiya basu kuma shiya karbi abinsa kuma mudin ma duk mallakinsa ne duk sanda ya kirayi waninmu dole ya amsa kiranai sarki rabba.
haka rayuwar gidan Hafiz tamiqa har yau gashi kusan shekara 1 knn da rasuwar khairat, a cikin watan qarshen shekarar ne kuma Allah ya azurta duk matan Hafiz da samun cikunna murna kamar suyi me kowace na kokarin ganin ta temakawa yar uwarta a sanda laulayi ya taso mata, Hafiz ma yayi farinciki ba kadan bs Allah knn mai kyauta asanada ya karbe khairat sukai haquri kuma gashi ya kuma azurtasa dasamun wasu yayan,
waton sultan da sultana zasuyi yan uwa suma, dan har gobe ba subar maganr khairat ba yaran,
ahaka ahaka har watan haihuwar su ya kama cikin ikon Allah heema ta fara haihuwar y'aya maza 2 adaren ranar kuma Fatima ta haiho namiji yayinda zee kuma ta haihi namijin itama basmah kuma ta haihu macen, yaran masha Allah Hafiz harda kukan murna yai yana rungumesu gamida sa musu albarka, Allah ya tsara masa rayuwa komi nazo masa daki daki kwarai yake jin dadin kyautar Allah garesa ahakan dan jiyakeyi ma duk duniya babu wanda yakaisa farinciki.
ranar suna kuwa sa 5 ya yanka da raguna yaran heema sunci sunan iyayen basmah kmr ynda heema ta buqata asa musu yayinda dan Fatima yaci sunan babn zee itama haka ta alqawarta hakama zee tasawa yaronta sunan baban Fatima,
sosai hadin kan matan nasa ke burgesa komi nasu cikin nuna tsantsan soyayyan junansu a ynz maras algus ke gudana a tsakaninsu,
yayin basmah ta basu zabin sunan jaririyarta, aiko babu bata lkc sukace amaida mata khairat dan dmn Masha Allah jinjirar khairat CE sak, shiyasa sukai ta murna suna cewa khairat ta tafi khairat ta dawo, mai karatu duk ynda zamu fada muku hadin kan matan Hafiz a ynz abun yawuce tunaninku su kansu idan suka zauna hiran rayuwarsu ta baya sukan dinga yiwa Kansu dariya da takaici na fahintar lallaikm da sunyi abu ammn gashi ynz yazamo tarihi,
a wnn lokacin kuma ne Allah ya hada hjy Aisha mamar hamiz da 'yan danfara suka yimata gaba da dukiya hat abin yakusan zamr mata kmr zauci saida addu'oi da roqon Allah aka samu ta dawo hayyacinta, ynz kam komi na arziqinta ya tafi sai abinda Hamiz ya kawo suke amfani dashi, hjy Aisha tayi nadamar kuskuranta nakin talakawa a rayuwa har saida tasamu su abbu ta nemi gafararsu kan tozarcin ta garesu data hana auren hamiz da yarsu ranar daurin aure, suka yafe mata suma snn fa ta fara son kulla sabon zumunci a tsakaninsu a cewarta tanson dorawa daga Inda mijinta Alhj muttaqa ya mutu akai, hamiz ma ya auri auri sister dinsa har sun haihu amman har gobe yana jimamin rasa basmah dayai a matsayin mata, nusaiba ma ta haqura tai aure ta auri yaya mus'ab yyn basmah suna zamnsu abinsu cikin soyayya, dan shims lokacin yy mus'ab kasuwancinsa nata bunqasa.
Hafiz har makka ya kai surukan sa wato iyayen matansa ammi da abbu gami gyara musu gidajensu sukam sai faman sa masa albarka sukeyi.
Lokacin Hafiz yakai matsayin Major general Na army' dinsu ga kasuwanci yanayi arziqin sa kota Ina qara habaka yake ga temakon mabuqata da yakeyi koda yaushe masha Allah hatta da sansanin 'yan gudun hijira sunsan da zaman temakon major general Hafiz Ahmed gare su.
*
yau takasance laraba yau kuma Hafiz yabar dakin heema sunjima rungune da juna sai shagwaba takeyi masa gamida rirriqesa tana matsarsa kamar ko yaushe in suna tare salo salon heema garesa na mstuqar narkar da zuciyarsa taqara tsumewa a sonta , mannota cikin qirjinsa yai gamida bada full kisses masu saka nutsuwa kamin yaji tai carab da lips dinsa nan suka hau bawa juna wuta saida suka kwantarwa da juna kwadayi snn yanufi dakin zee dan yimata saida safe dayake darene wuzin 10 ma,
saida ta tsaresa yasha fresh milk acewarta ta gyara masu shi shima tana mgnr gamida karkashe masa ido gamida narke masa a qirji tana dan shafa qirjin nasa, kunsan zee din taku da jan hankali baisan sanda ya biye mata ba suka zube kan gado suna mitsir tsikan juna saida suka lugwigwice juna snn suka rabu da tana sa6e da babynta dasuke kira da haidar ta rakosa bakin kofa gamida d'aga masa hannu alamun bye bye saida ya sumbacesu snn ya wuce itakuma ta koma ciki,
haka koda yaje bangaren Fatima yimata goodnight saida yasamar mata relief snn kuma yajima ana wasa da babynsu da suke kirada dady snn dazai tafo hadda masa kashedin kada ya zautar da qanwarsu yau (basmah take nufi) dan a cewarta taga alamun kmr ya sha zaqami ne yau, tana mgnr cikin tsokana shiko da yar dariyarsa ta muskilancin sa yajawota gamida cewa
"OK bari nafara rage zaqamin akanki sai in tabbataz da nasha ko ban sha ba... Ay kamin ya ida mgnr har ta juya bedroom dinta da gudu ta riqo dady a jikinta tana dariya gamida cewa
"sry yallabai goodnight Sweet sleep"
haka yanufi dakin basmah cikin jin dad'i,
wani sanyin dadi daya shaqa saida ya lumshe idanunsa komi nata mai kamshi kamar sauran,
saida ya sumbaci little khairat dake barci cikin dan baby bed dinta da yake mukaram yaje Hutu gidan hjyn Hafiz shima wajen su sultana,.
ahaka oga Hafiz ya lallabo gamida haurowa gadon ya shige jikinta gamida rungumota qam, tana jinsa tai lamo tana sauqe numfashi kadan2, saida taji yafara shinshinata ne gamida yaye yar sleeging dress dinta ya jefar yafara murzata fa snn ta sauqe dogon ajiyan zuciya gamida qara narkewa a jikinsa,
a shwagwa6e tace
"please yah Hafiz barci fa....
"shihhh ya furta mata yana mai bin cikakkun qirjinta da kallo kmr bata taba shayarwa ba, murmushi yai gamida sakin ajiyar zuciya batai aune ba sai jitai ya cika hannuwan sa da dukiyar fulaninta ya fara wasa dasu yana rad'a mata a kunne cewa
" babyn Hafiz kominki yana qara bunqasa gaki gard'inki ma kullum qaruwa yakeyi fadamun miye Sirrin uhm ko saina siyi mgnr snn?,
murmushin qasan lips yai yana mai bin fyskarta da kallo,simple makeup dinta ya matuqar burgesa, riqo fyskarta yai yace
"nabiya kudin wnn kwalliyan zaqin zuciyata"
turo baki tai shikam hakan ya bashi dry yace
"oh sorry nafa mnta ashe fa babyn tawa hjy CE komi soja yai mata saita biyasa bata buqatar tallafinsa gareta sbd ta tsanesa a ratuwarta,
yayi mgnr gamida kanne mata ido, yace koba hakan bane babyn Hafiz?"
kukan shagwaba tasaki sabida tasan tsokanarta yakeyi gamida tuno mata sanda ya biyawa abbu kudin aikinda akai masa hospital din dadynsa, wanda shi kansa abbu sai daga baya yasan Hafiz ne yabiya daga bakin basmah, kamota yai yana dariya.
itako cewa takeyi
"Allah ko yah Hafiz kadaina zanyima kuka,
ai ni ynz bnda gwani kmr soja,
soja na shine jigon rayuwata dajin dadinta gaba daya"
had'e fuskarsu yai waje daya hana jifanta da wani sihirtaccen kallo yace
"are you sure Baby na?"
dage masa gira 1 tai, lumshe idanu yai ya kwantar da ita jikinsa yana yana shafa bynta yace, my pleasure, amman fa ina binki bashi na tambayeki miye sirrin kinki ban amsa?" yayi mgnr yana sakar mata isakan bakinsa mai dumi a kan kunnuwanta.
cikin jin kunya tai saurin boye fuskarta a kirjinsa tana jan gashin kirjinsa cikin wani salo ta furta
"jeka tambayi adda salma wann...."
murmushi ya kufcemasa gamida cewa
"Ok kamin na tambayi adda salmar bari nafara tanbayanki ke"
kamin kacemi tuni yafara playing Bob's dinta a bakinsa gamida rude mata jiki da salonsa mai gigitata gamida fiddata daga hayyacinta, dayake itama ta horu da horonsa babu bata lokaci ta dinga tayasa aiki ba qaqqautawa,
jiyarda junansu dadin sukeyi kota ina ranar saida basmah ta raina kanta dan saida Hafiz ya nuna mata soyayyar dahar abada bazata taba manceshi ba snn fa ta samu ya qyaleta,
daga qarshe suka shiga wanka dan ko awajen wankan wata soyayyar ce suka dinga kwasa har kukan dadi saida sukaiwa junansu snn suka fito rungume da juna, sukasa baby khairat tsakiyan su ahaka sukai barci cikin farinciki da nishad'in rayuwa.
kwanci tashi basmah ta daura daga karatunta data tsaya Na secondary cikin ikon Allah ana kwana