Showing 33001 words to 36000 words out of 78322 words
aikin mu, please wife ki daina fushin nan kinsan koda bana kusa dake kina cikin zuciyata a kowane bugun numfashi". nan yaita rarrashi gamida qara saqar mata zaqaqan kalamnsa ita kanta batasan sanda ta juyo ta na mai masa murmushin jin dadi ba, nan yake tambayr ta jikin take cewa da sauqi saidai rashin qarfin jiki da bataji kamr zata fadi inta tashi, yake sheda mata sunyi mgn da doctor yace tana buqatar jini sbd ta zubda jini sosai, sabida HK gobe za'a gwada nasa suga idan yayi sai a d'iba.
bud'a mata siyayan da yayo mata na kayan kwadai yai tahau ci dan wani sabon kwadai ta tashi dashi a tun farkowarta, anan heema ke sheda masa hjy ma tazo da 'yan gidansu dazun, fatema dake kwance tayi likimau uwa mai barcin gaske Wanda tun shigowarsa ta farka ta kasa kunne tana ta nad'ar firarsu sanka sanka, wani tsanar heema taji ta qara yi a zuciyarta, ta tsani ganin wata mace na ra6ar Hafiz a rayuwa ba ita ba, dan dai ba yanda zatayi ne, amman tasha alwashi a juri zuwa rafi dai saita zamo kwallin kwal mace 1 a zuciyar sa da gidan Hafiz wnn shine babbn burinta, ganin yanda Hafiz din ke sa mata nama a baki yasata miqewa tana Mirza idanu kamr mai magagin barci,
shi sai lokacin ma ya lura da ita ma, janye hannunsa yai bayan ida sawa heema naman cikin bakinta dayai ya furta "damn kina nan baki tafi gida ba?,
tun safe fa?
kinada hankali kuwa fateema ko ke ce kike iko da kanki ban sani ba?"
karyar da kai tayi gamida cewa "yi haquri yallabai naga babu kowa ne wajen heeman shiyasa...katseta yai a dan tsawace yace "sai kuma akace miki ba masu kulawa da patients a hospital din ko? look ni ba irin mazan nan bane masu sakin mata sakaka any how dan haka maza maza tashi na maidake gida"
yayi mgnr yana miqewa tsaye, heema bataso hkn ba taso yabar fateeman kodan tasamu abokin mgn amman babu ta cewa dan tasan Hafiz bai mgn ana maido masa, haka fateema ta miqe tana tuquburi snn tace ''to wazai kwana wajenta?" afusace yace " ban sani ba zaki wuce muje koko?" dasauri ko ta fita heema na mata saida safe ko amsawa bataiba dan gani take heema taji dadin wulaqanta ta dayai gabanta muna furci ne yahanata nunawa,dayake daman Hafiz sunyi mgn da yan gidansu heema kan qanwarta karimat zata zo ta kwana nan wajenta ko heman bata saniba sai ynz yake fada mata hkn bayn fitar fateman, dan suna fita ma babu jimawa sai ga karemat din ta iso danma matsalr abin hawa daya tsaidata da tuni ta iso tun sanda Hafiz din ya kirata a waya.
Hafiz ko suna isa gida fuuu fatima ta fice daga motar rai bace, shikam sam baima nuna yasan tana tuquburin nata ba Dn haka shima biyo bayanta yai bai samu kowa a falon ba, kai tsaye dakinsa ya wuce ya watsa ruwa ya fito ya canza kaya gamida fesa turarukan sa masu kamshin kwantar da hankali, dakin zee ya nufa dan yaga lafiyar ta yasameta tayi shame shame sai sharar barci takeyi, rage wutar dakin yai ya rufo mata kofar snn ya juya zuwa dakin fateema, dan a matuqar buqace yake jinsa, dan haka babu wani sanya ya haura gadon gamida maqalota a jikinsa yashiga kashe mata jiki da rikitaccen salonsa, itako sai nuna fushinta takeyi na disgin dayai mata, haka yaita kasheta da kalamn rarrashi abinka da mata da miji tuni ta mance komi suka fad'a tafkin qauna, saidai baisan miyasaba sanda yake sarrafa teema 'yar fulanin yarinyar nan dabai san sunan taba har ynz ta dinga masa gizo,
lumshe idanunsa yai gamida cigaba da murza Fatima iya karfinsa yana mata kallon yarinyar duk yabi ya rikice kota ina jinsa takeyi a jikinta itako fateema tun tanan daurewa tana rokonsa ya barta hakanan harta fara sakin kuka kashirban dan tasan muddin yafara mata wnn hanzarin sai inda mai yaqare, saida yaji ya gamsu iya gamsuwa snn ya rabu da ita,nan ya barta tana barcin gajiya yaje yayo wanka gamida dauro alwala ya tayar da sallan nafila dan lokacin kusan 3 na dare ne, saida yai asuba snn ya kwanta, lokaci daya kuma yarinyar ta qara fado masa arai , ya rasa isalin abin nan shikam, saima ya samu kansa da murmusawa dan tuno rigimarta ta dazun wai zata biyasa kudinsa? Zamu gani,to taya knn ma? a binda ya furta a ransa knn gamida sakin wani murmushi mai Sauti, sannu a hankali bacci yayo gaba dashi harda tsarabar mafarkin yarinyar tana qara jaddada masa biyansa dukiyarsa kota Yaya harda kukanta na shagwaba,
washe gari kuwa shi ya tilasta zee ta kan ta shirya masu heema abincika.
qarfe 10 na safe ya iza qeyarta zuwa hospital din itako sai faman baqin rai takeyi uwa wacce aka tura zuwa mahallaka,
koda suka isa dakin babu wata cikakkiyar gaisuwa tsakaninta da heema saima wani shasshan qamshi da zee keyi.
Hafiz ya Dan jima snn ya wuce office din doctor gameda dibar jinin ana gama abinda za'ayi ya fito ya shiga motarsa ya wuce office dinsa wanda dmn tuni ya umarci zee da ta zauna nan har sai ya dawo snn ya maidata gida, haka zee ta wuni wajen cikin baqin ciki da takaicin tsayar da ita da Hafiz yai Wanda da tuni ta cika bujenta da iska, babu wata mgnr arziqi daga bakin zee koda heema tayi niyyar janta da fira kuwa yanzun nn ta danqaro mata mai zafi, babu arziqi heema tayi shiru sukaci gaba da hira da kanwarta karimat sannu sannu, Wanda hakn ya hasala zee tamiqe a fusace tanata surfa ashar wai gulmarta sukeyi, kuma Allah ya isanta, cikin musifa ta figi jikkarta tace "qwamma na zauna a waje wlh Dana zauna da kidahumai jakkuna anan muna gwamutsa numfashi".
fuuuu tayi gaba,
suko da kallo suka bita gamida tunanin anya ko zee bata rasa iska kuwa.
ana haka sai wata likita tazo ta daura wa heema qarin jinin dayake tun jia da aka dibi nata shima Hafiz aka dibi nasa ynz anga yazo daya kuma.
zee ko waje ta samu a wani waje ta zauna bisa wata kujera dayake kujeru ne wajen reras na zaman 'yan awo side din, sai famn hura hanci takeyi tana karkada qafa, tarasa mike mata fadi masifar kishi kawai kecin ranta,
qawarta ramla ta fado mata arai kan mgnr malamin nan, dasauri ko ta zuge jikkarta ta fiddo wayarta tashiga neman layin ramlat din, taqi shiga wajen babu network sosai ahaka ta dinga matsawa tana hello hello ban jinki ramla...
kiceeeeeb!!
taji an kifo mata abu a jikinta babu shiri ta kai dubanta ga jikinta , kwakkwo ne ya 6ata mata illahirin gaban mayafin jikinta gashi da zafinsa kuwa, aikuwa a fusace takai dubnta ga Wanda yai mata wnn danyan aikin, basmah ko dud a rude sai famn bata haquri takeyi yayinda tasan da cewa laifintane ta tafo a hanya tana tunanin abinda ta kwana dashi a ranta, na mgnr da sukai da sojan nan jia datace zata biyasa kudad'ensa basu son kyautatawarsa, tunani take Inda zata samo wadannan makudan kudade, mafarin knn data siyo kokon tafo tana tunani abin har ma batsan ta fadowa wnn hajiyar ba, saida Zee ta kuma kallon jikinta kamar ta yi kuka takeji tsabar wani Sabon takaicin da wnn qajagar yarinyar ta sake daura mata, itadai bata shigo asibitin nan da sa'a ba,
to itakam ba kanwar lasa bace kowaye yai mata kuskure a duniya saita nuna masa batasan uzuri ba dan haka babu zato basmah taji sauqar mari tauuuu tauuu a kumatunta har saida ta hantsila tai tagataga uwa zata fadi snn ta tsaya kan qafafunta safe da kumatunta,
dan har saida kingin kokon dake hannunta cikin jug ya zube qasa,
zee tacigaba da masifa tana furta "haka kawai matsiyatan mutane talauci ya addabi rayuwarku ko mima kun manta burinku kushafi masu kudi don Ku goga musu kashin tsiya, dan daga ganinki gidan matsiyata kika fito dubi shigar tufar jikinki dawani qaton hijabi can naki dubi cimar da kika taho dashi kika batamun jiki mtswww ga alama irin kune kuke zuwa kuna fad'awa gab@n mota dan ta bankeku kusamu nacin abinci koda kuwa zaku rasa rayuwarku bazaku damu ba inda iyaye na nan zasu karba suci,dalla malama zaki wuce mun a hanya koko saina ballaki?!
har lokacin basmah dafe da kumatunta take tana kallon zee tana hawaye, ita bawai marin ne yasata kuka ba aibata mata iyaye da takeyi ne alhalin bata santa ba basu santaba, Sam basmah bamaison hayaniya bace koda yaushe, dan haka bata sake furta komi ba kawai sai ta duqa ta dauki jug din tabar gun tana share qwalla,
zee tabita da tsoki tana juyowa taga doctor blessing tanufota cikin fara'a, haka taja zee din zuwa office din ta dan taga jikinta ya baci kota gyara,basmah ko daqyar ta sawa kanta natsuwa ta isa jikin famfo ta wanke sauran kokon da qasa ta manne a jikin cup din duknsa snn ta sake siyo musu wani kokon ta kaimasu ammi sai lkacin sukai kalaci Dn qarfe 11 da wani Abu sa'in, ahaka doctor Husain ya shigo yasake duba jikin abbu yaga dasauqi komi lfy babu bata lkc kam ya rubuta musu sallama,gamida sake basu shawarwari ynda zasu cigaba da kula da shan magungunan abbu harsu qare.
Doctor Husain Nada kirki sosai babban mutum ne sosai ya iya tarairayar patients dinsa, sosai yk tsokanar basmah da sarkin kuka kan abbun ta,
itako saidai ta sinne kai kana 'yar dariya.
sosai su ammi sukaji dadin hkn nan sukahau shirya yan kayansu kuwa, saidai babu ledan dazasu saka kayan Dan haka ammi tasa basmah ta samo musu ledan babba anan bakin asibitin, ahaka basmah ta siyo ledan kamin ta iso dakin nasu suka hadu da doctor kusada office dinta hannunta daukeda gyale ga alama ajiqe yake, ta dai bazasa a wani qarfe dake gefen office din nata.
nan Dr blessing take tambyrta da "ina zakije beauty?" nan basmah ke sheda mata Dr Husain ya sallamesu ay, Dr blessing tai musu murna har take tambayar ta number wayarta tana cewa zata kawo musu ziyara wataran dan tana sonta sosai, nan basmah ta shiga karantowa Dr blessing din number ammi dudda wayar batta hannunta tana wajen gyara dan tunda ta fadi a ruwa ana ya gobe zasuzo asibitin, basmahn tabawa wani mai Gyara nan anguwarsu tanada tabbacin yama gyarta Dn idris nada cika alkawali, yayinda zee ke tsaye daga bakin office din doctor blessing din tana kallo yarinyar, tabe baki tai tana hararota dan gsky kam hakan takejin tsanar yarinyar can a ranta hakanan batareda tasan daliliba dudda yau ta taba ganinta kuwa, tasan komi haduwar jini ne ammn nata baizo daidai da nata ba,, itafa dud wacce taga tacika kyau da yawa tsanarta takeyi sabida tana ganin irin sune suke qwace musu mazaje idan har Allah yasa sukai gamdakatar dasu bare ita wnn din datake ganin kmr kyaunta yasha ma bambam da sauran matan duniya datake gani, kynta yafita dabn, nata mai sanyi ne, wato sanyin kyau ne da ita,, tsoki taja dan taqagara ma taga yarinyar tabar gun, Dan HK ta shiga kwalawa doctor blessing kira....
ba shiri Dr blessing ta sallami basmah snn ta qaraso wajen zee din taja hannunta suka koma office din uwa nata tana wata tafiyar taqama.
basmah ko suna gama parking kayansu ta tsaido musu napep sukasa kayan suma suka shiga ammi da abbu sunsata tsakiya sukabar asibitin.
*
sai ana sallar isha'e Hafiz ya iso asibitin, fitowa daga motarsa yai agajiye, burinsa ya gabatar da salla kawai a lokacin, alwala yayi salla a masallacin asibitin, yana gamawa ko nan ya fito direct dakinsu ammi zuciyarsa ta raya masa ya shiga ya dubosu, dan suna cikin ransa family din har lokacin, saidai yana isa yaga wayam babu kowa a dakin, sosai mamaki ya kamasa da sauri ko ya rufo dakin yajuya knn yaji mgnr doctor Husain a baynsa, yajuyo ya dubesa gani yai ya fito daga wani room hannunsa riqeda files, kokarin seta kansa Hafiz yai byn sun gaisa yake cewa ay yazo ne duba mutumin da akaiwa aiki nan dakin,
Dr Husain ke sheda masa ay an basu sallama sun tafi tun dazun, baisan sanda ya dafe Kansa ba gamida furta what?! ganin yanda Dr Husain ke kallonsa da mamaki ya sashi furta
"Ok bkm naso muyi bankwana ne dasu shiyasa, dan mutanen nada kirki sosai"
mgnr da yaji knn tana fitowa daga bakinsa, cikin sakin rai Dr Husain yace ahi
" eh gsky kam, sunada kirki ai yaji sauqi Alhmdlla jikin wa warware dan tun safe ma suka wuce, Nima wasu Patients na duba ynz"
nan sukai sallama Dr Husain ya wuce, wanda yallabai Hafiz kuwa waje ya samu gun ya tsugunna samn kafafunsa baynsa jingine bayansa da bango da yai, tafukansa yasa cikin fuskarsa yana tunanin shikenan yanzun bazai qara sakata aidanunsa ba knn? Abu kamr film sanda ta shigo rayuwarsa farat 1 snn zai nemeta ya rasa ta kyauta wa rayuwarsa knn?? why? Whyy?! tambayar da ya hau yiwa Kansa knn cikin tsananin kasala na mutuwar jiki...✍🏻
*By 4 writer's fasaha👩👩👧👧😍*
[7/12, 8:34 AM] Xainab Documen: *♨️♨️MATAN HAFIZ♨️♨️*!!!
*FASAHA ONLINE WRITERS*
F.o.w.
Written by.
*FOUR GORGEOUS WRITERS*
-Raheenat mahmud.
-Mmn Abduljalal.
-Xayyneb💤💤 (xexen Fasaha).
-Matan Borno.
*♨️Impacting valuable knowledge and entertainment is our concern.♨️*
Bismillahirrahmanirraheem.
*Gargad'i*
Bamu yarda a juya mana littafi ko ta wacce siga ba tare da izini ba.
26.
Da qyar basmah ta samu hawayen suka koma ammi ta furta "basmah ki zubawa hamiz abinci yaci"
dasauri hamiz din yace
" a'a ammi Alhamdulillah" ammi tace dawowarka knn fa kace daga katsina kaga kuwa kana buqatar sawa cikinka wani abu, abbu ma yasa baki dan haka hamiz ya amince zaici abincin, sosai kuwa yaji dadin girkin yasan daman basmah indai ta bangaren girki ne kam Alhmdlla, dan haka duka ya cinye abincin ko cokali bai bari ba, saida ammi tace ko 'a qaro masa snn ma ya ankara da yaiwa plate din empty kaff, snn fa kunya ta kamasa ya shafa sumar kansa yace " a'a ammi, miqewa tsaye yai yace "akwai abinda doctor yace yana buqata ne ammi ayi?" shiru ammi da basmah suka danyi dan gaskiya kam su keda buqata ammn sunajin nauyin furta hakn, shirun da yaga ammi tayi ne yasashi fahimtar da wani abun, yasan kuma halin su ammi da kawaici dudda yayi yayi su dunga daukarsa kamr dansu mus'ab komi suke buqata su dinga masa mgn ammn sun kasa har ynz, qarsawa yai ya amshi takardar hannun basma ya duba snn ya riqeta ga hannunsa yace "ammi zamu d'an fita da basmah ynz zamu dawo"
ahaka suka fita ammi tahau zuba wa abbu abinci, yaci abincin kam ba laifi wnda yarage baifi cokali 5 ba sauran ammi ta ci.
a mota kuwa anan hamiz kejin mus'ab baya gari yaje Cameron daga bakin basmah, bai tambayeta dai miya kaisa ba dan yasan komi nason sirri a rayuwa.
saidai yaci gaba da janta da fira tana basa amsa jifa jifa, bayan sun je ya siyo magungunan dukansu kai tsaye ya canza hanya, wani babban Oasis's taga yayi parking yace ta jira yana zuwa, ahaka ta sauke glass din motar ta lumshe idanunta tana shaqar iskan yanayin damina mai dadi kamar ance ta bude idanunta nan taga wnn sojan ya fito daga cikin oasis din hannunsa riqe da leda ga alama waya yake amsawa ahaka yaqaraso ya shiga motarsa yabar gun.
bin sawun motar tai da kallo ta sauqe wani numfashi taso ace face to face suka hadu, sosai take son yin magana dashi.
haka ta hango fitowar hamiz shima hannunsa riqeda manyan ledoji 2 yashigo motar yana furta "sannu qanwarmu nabarki zaman jira ko?" Murmushi ta yi tace
"hmn a'a naga dai duhu yafara sosai kadda su ammi suji shiru"
" hakane ynz zan maidaki ai qanwrmu mai tsoron dare" yayi mgnr cikin son tsokanarta, murmushi takumayi mai sauti batace dai komi ba dai, sun shigo asibitin ta fito daga motar shi kuma bai fito ba, da ido tai masa alaman yadai ya tsaya? murmushi ya saki gamida fitowa ya miqo mata ledojin yace ki kaiwa su ammi ni zan tafi, gobe zan kawo su Momy suga abbu da jiki, kamar bata amsa ba dan taga dawainiyar da yawa, maida hannuwanta tai duka baya ta 6oye irin na yara dai, daqyar ta furta ''kayan nan sunyi yawa fa yaya hamiz" gintse fuska yai gamida galla mata harara yace "kena kyautarwa koko iyayena?" Sunkuyar dakai tayi tace "afuwan yaya hamiz, mun gode Allah saka"
bayan ya amshi kayan.
sakin fuska yai yace "yawwa kokefa dear qanwas sai goben ko?"
ta gyada kai har zai wuce yadawo yace "mine qanwata zata fadamun dazai Sani farinciki tsawon daren nan ayau sakamakon mun kwana 2 bamu tare umh?"
Yayi mgnr a marairaice, ita saima ya bata dariya kuma Sam bata kawo komi a ranta ba dan haka kai tsaye tace "Allah tsaremun kai yayana kuma kayi bacci lfy tsawon daren nan mai albarka" saida ya lumshe idanunsa snn ya bude yace ''godiya nake qanwarmu ki kula mun da kanki"ahaka yashiga motar kamr karya tafi yakeji baiqi sun dawwama ahaka ba shikam.
Murmushi tai tabi motar da kallo ta juya tanufi bangarensu knn shi kuma Hafiz ya fito daga office din doctor Husain anan suka had'e kici6is kan hanya, sosai yayi mamakin daga Ina yarinyar take ynz, d'an birki yaja yasata gaba yana kallo kmr ynda itama tayi, kamr an mintsilesa yayi saurin duba watch din hannunsa yaga 11:43 pm, jiyai ransa ya baci batareda yasan dalili ba, sai kuma ya dauke kansa da sauri daga gareta ya juya yana shirin barin gun, da sauri yaji saukar sautin sansanyar muryarta ta furta
"Yall6ai dan dakata mana"
cak ya tsaya na tareda ya juyo ba, gabansa ta zo ta tsaya cikin nutsuwa ta furta"Kaine ka biyawa abbu kudin aikinsa ko?"
cikin mamaki ya dubeta kamar bazaiyi mgn ba sai kuma ya furzar da iskar bakinsa daya qunsa snn yace "for what reason?"
"I don't know"
ta baahi amsa itama, cije lips dinsa yai kamin ya sake furta "bani bane!"
" Kaine !"
ta bashi amsa da qarfi,
zuba mata idanuwansa yai yace "ina