Showing 72001 words to 75000 words out of 78322 words
'yar khairat a bayana harda jikarta Ina fatan ma ni ace na rigata mutuwa da ace tarigamu tafiya wlh har raina zan aminta da hkn inda ace za'abn za6i"
kallon banza zee ta wurga mata tace to ke kuma asuwa dazaki tsomomin baki a mgn ta? kokinji Na kama sunanki a cikin mgn ta?, dakike cewa kada baki ya kashe khairat to bata kiba wlh, ke din harkin isa kibawa khairat farincikin rayuwa ma aiba ga irinku ake samun wadann siffofin ba na kyautatawa matar data raina mgnr mijinta ta ina zata gyara rayuwarta bare ta wata"
Fatima ta hasalo zata maida martani knn hafiz ya daka musu tsawa yace
"it's enough waiku dan Allah mike damunku kullum abunku sai yayi sauqi saiya dawo to wlh Ku shiga hankalinku bansan raini kuma kunsani, to wai in baku girmama junanku ba ynz to sai yaushe zakusan ciwon kanku?, wani dogon tsoki yaja gamida barin wajen rai bace ya haye sama cikin takaicin halayen su.
zee girgiza kafa kawai takeyi alamun ko a jikinta kamin tabi heema da basmah da kallo tace
" to ku kuma muna fukai sai kallonmu kukeyi lfy?"
girgiza kai heema tayi tace "to ai kunyi abin kallon ne zee, dan Allah lokaci yayi da zaku aje wnn kishin naku muhade kanmu mu zauna lfy dutta kishi aita qare Inda an auro kowace kuma an sakata a dakinta to miyayi saura bacin mu had'e kanmu mu rungumi mijinmu?"
tsoki Fatima tayi tace
"dama kinyi shiru heema dan India wnn shedaniyar zee dince mai kwanyar kifi bazata taba fahintar kiba kullum zuciyarta cikin musifa take, ta yau daban ta gobe daban adaibi rayuwa a sannu dan inkace zaka dauki rayuwa da girma kamar bazaka mutu ba kinawa rayuwa dogon buri kina son ke saikin samu ynda kike so to wataran saidai kiji ki cikin qabarin ki kanki ya bugi tukunya qumm wlh, nikam rayuwar duniya bazata hanani jin dadi ba naci nama na na more dan rayuwar duniya bamai qarewa bace har sai ka mutu tukun".
ai wnn mgnr kmr ce wa zee tai bala'i assalamu alaikum saiga zee gabn Fatima ta cukwikwiyota fada suka shiga yi babu kama hannun yaro duk ynda su basmah suka so rabasu abin yaci tura basu ankaraba saijin kukan khairat sukayi a bayansu. dasauri suka saki junan su suka jiyo sunata haki, kowace na qoqarin saita kanta, khairat suka gani hawaye shabe shabe a fuskarta, da sauri zee da Fatima suka nufota itama tayi saurin ja da baya daga garesu ta makure a jikin bango tana tsaidasu da hannunta tana kuka take cewa "ni kada kujo wajena zan tafi ba jan qala dawowa galeku ba wajen hajiyan mu zan tafi"
kowace durqushewa tai daga nan Inda take cikin rawar jiki har suna hada baki wajen cewa " khairat mi..miya faru, laifin mi mukai miki haka da zafi?" miqewa tsaye tai daga nan Inda take tsaye ta kalli basmah da heema ta kuma kalli zee da Fatima cikin kuka tace
"kunga fa momys dudda ni qalaman yalinyace amman bantaba ganin su momy da big Momy na fad'a ba amman ku kusan kullum koda ban ganku ba to ina jiyowa kuna ta fada a tsakaninku ni kuma hkn nasani kuka sai nai ta kuka batareda kun sani ba, kuma dady na muku fada Ku daina amman sweet Momy da sugar momy kunki Ku Bali kamar kunayin gaba fa knn, kuma Mlm yace masu gaba da juna Allah na fushi dashu snn baa qala kalban aikincu na ibada harsai sun shilya snn amman Ku baku shilya ba ar yanju to nidai kunga Ina shonku dukanku a laina kuma malan dinmu yace in matan mutum taya shuka ad'e Kanshu sukai wa mijinsu biyayya Allah zai ta shesu gobe ranar ciyama a aljnar naba Firdaushi a tare duknsu kuma inashon ni na ganku a aljanna, amman ba jan iya ganin kunata fada kullum ba gasky inbaku Bali ba ni jan tafi ba jan shake dawowa ba galeku"
tana gama mgnr ta ruga dakin momynta basmah da gudu tana share kwalla,
nan fa jikin zee da Fatima yayi wani mugun sanyi aka rasa mai mgn mamakinsu shine ya akai yarinya qarama kamar khairat keda wnn tunanin mai kama da nasiha?, lallai baiwa ta Allah ce bawai a girma take ba, basu qara tsinkewa ba saida sukaga ta goyo yar jikkar ta ta makarnta ta sauqo qasa ta dubesu tace .
"Na tafi dileba yakaini gidan ajiya shiknn na barku ba zan qala dawowa ba harsai kun shirya in kuna son na dawo nan gida"
riqeta sukayi data fara alamun tafiya suna kuka suna cewa "khairat wlh mun shirya min daina bazamu iya jure rashin kiba a cikin mu ke din kyautace daga Allah mai girma a garemu tabbas Allah ya kawoki cikin mu ne dominn ki gyara rayuwarmu khairat kedin alheri ce khairat kizauna damu bazamu kara fada da junanmu ba"!
cikin murna kuwa khairat ta durqusa gabansu tace
"dan Allah sweet Momy da sugar momy ar cikin lanku kun yalda bazaku qala fada ba , wlh banson naji ana fada jinakeyi kmr zan fad'i numfashina ya tafi"
share mata hawaye sukai da hannuwan su sukace
"har cikin ranmu khairat daga yau zamu ajiye wnn aqidar kishin zamu hada kanmu kmr ynda kike so bazaki kuma samun wani abinqi daga garemu ba"
tace "to inkun yarda kuma kunyi alqawari koda bayan raina bazaku qara fada ba zaku zauna lfy a tsakaninku da kowa to ku aja annunku bisa kaina shine jai bani yaldal cewa kun min alqawali"
kallonta sukeyi suna dariyar wayon ta suna ganin yar qwalln murnarta mai hade da kuka,share mata hawaye sukai gamida sumbatar fuskarta,zee ce tafara aza hannunta kan khairat tana murmushi snn Fatima ta aza itama cikin fara'a da qwalla,
kuma hkn har cikin ransu ya hwato su heema khairat tai alamun suma suzo su dora, hakan kuwa akayi suka hade hannuwansu kantta sai ita kuma khairat din daga qarshe ta aza dayan hannuta kan nasu ,wato ta rufesu,
ga mamakin su addu'an hada kan iyali ta dingayi karantowa alokacin daga qarshe kuma ta rufe musu da salatin fiyayyen halitta annabi Muhammad saw kmr ynda ake koyar dasu a islamiyya. babu wacce bata zubda qwalla ba cikinsu dan gaba daya zuciyarsu ta gama yin sanyi, zee rungume juna sukai da Fatima suna kuka gamida neman yafiyar junnasu dasu heema khairat na gefe tana kallon su fuskarta cikin fara'a ta rungume hannuwanta a qirji, tanaji suka yafewa juna snn ta qarasa ta kamo hannuwan basmah da heema takawosu wajensu zee nan sukai kamayya suka rumgume juna gamida saka khairat tsakiya suna hawayen farinciki,
ji sukayi sautin tafi na fitowa daga bayansu RAF RAF RAF, Hafiz ne dan tun farkon fara mgnr su yasauqo daukar wayarsa daya bari a falon yaji abinda ke faruwa, suna ganinsa ya ware hannuwansa alamun su taho garesa shima, nan take suka iso garesa dukansu ya rungumesu cikin tsananin farinciki, sai daga bisani suka zauna ya jawo khairat jikinsa ya zaunar da ita gamida furta "gud girl, tabbas kin amsa sunanki ummul khairi kedin lallai umman alheri ce,
kuma na yarda cewar daukar Shawara bawai sai babba zai baka Shawara ka dauka ba,
a'a ana samun yaro da halin manya misali ga khairat, dan kuma mu manyan da muka jima muna nuna muku rashin alfanun kalar zamn da kukeyi baku daukaba sai ynz da qaramar yarinya tashigo rayuwarku kuka tashi da soyaayyar ta to kunga knn Allah yariga ya qadarto shiriyanku nadaga gareta kunsan komi Nada sila da kuma iyakarsa a rayuwa, to gashi tsawon shekaru nawa kukai a wnn aqida wnda hatta iyayenmu sunsan da hkn anyi anyi a gyara kuka ki gyarawan to kunga knn silar shiryuwar taku ba a garemu bane sai da aka kawo mamar yarinya har akasamu yarinar snn iyakar komi tazo daga gareta,tabbas alqawarin Allah bai tashi komi ya hukunto zai faru saiya faru to Allah tabbar da hkn kuma yahade mana kawunanku" duknsu suka amsa da amin zuciyarsu fes Allah mai ynda yaso Allah mai gyara zuqatan bayinsa mai shiryar da Wanda yaso a sanda yaso kuma, gashi ta faru ga iyalan Hafiz.
aranar tsabar farincikin har saida Hafiz yaiwa hajiyansa waya yayi mata bayanin komi, sosai tayi murna dan har gidan tazo taqara hadasu tamu su nasiha mai shiga jiki gamida addua snn ta tafi, hakama ya dauko su ya kaisu ga mahaifin basmah shima nn yaqara musu nasiha mai ratsa gabobi ta rayuwar aure wacce har kuka saida su zee sukai suna tunanin ashe dai rayuwa sukai tayi cikin bata sai ynz Allah ya kebo su daga son zuciyar da suka azawa zuqatansu, haka suka dawo gida bayin yinin da suka sha agidansu basmah a ranar.
daga lokacin kuwa komi tare sukeyi Kansu a hade had baka iya banbance ranar girkin wnn ko wnn domin komi tare suke yinsa sun qara zama cikakkun manyan mata Hutu da kwanciyar hankali sun gama ratsa su, heema tayi jiki sosai kowa yagani saiyayi mamaki domin kwanciyr hankali ya mamaye su, ana haka azumi yazo aka shiga ibada alokacin,
kullum sai sunyi abincika lokacin shan ruwa hafiz yakai masallaci mutane su ci su sha sunyi wa iyali guzuri sunawa hafiz addua da matansa,
ana haka bar qarashen satin da ramadan zai fita suka daga zuwa qasa mai tsarki don aikin umara harda khairat dasu sultan da sultana, sai wanshekaren salla snn suka dawo,
nan fa gida ya kacame da yanuwa da abokan arziqi ana musu barka da dawowa,
sun karrama baqinsu sosai suma da abincin salla kowa yazo sai yaci yayi ginigis snn zasu barshi in zai tafi su hada sa da tsarabarsa, basu samu nutsuwa ba sai bayan salla da kwana 5 snn su kuma suka shiga tsantsarawa oga Hafiz kwalliyan sallansu,
kamar yau knn ta kama juma'a bayan an sauqo masallaci telansu ya kawo musu dunkunan su wani tsadadden less din gaske da Hafiz ya musu ankonsa daga cikin dinkunan da aka kawo shi suka zaba suka sa, masha Allah zo kuga ynda ya haskasu yai musu kyau matuqa,
khairat sai santin iyayensu takeyi hakama Hafiz yana faman bibiyan su a gidan duk inada suka saka qafarsu saiya maida tasa, farincikin maqil a ransa jiyake ynz fa wadannan fa duk nasa ne shikam godiya ga Allah ba adadi, khairat ce ta rugo da gudu garesa shikam ya cafeta suna dariya, akunne tabrada masa cewa
"dady hjyn mecca tayo waya a falon qasa na tauka,
gasu sultana nan zasuzo zomuje mu tarosu harabar gida hadda au hjyn ka da Anty Aisha muyiwa su Momy surprise dasu kawai ko?"
tafawa sukai da shi yace "yeah ,
hakane my daughter maza muje, saia ya matsa garesu ya saki murmushi gamida rungume kowacensu yayi kissing nata a baki gamida furta
" hmnn,
inye kaga matan Hafiz fa kalar camera ne, to kujiramu zamu dawo ynz nida daughter, dariya sukai kawai shi kuma suka fice daga wajen.
nan ya barsu zee nata aikin daukan pics din kwalliyan sallarsu da basu samu sunyi ba sai ynz,hadda video sukayi suna rawa a cikin nishadi basu da damuwar komi a ransu sai ta son junansu ziryan.
da suka gama kowace kokarin abata video din tagani sukeyi qarshe dai heema ta shammacesu ta qwace tayi falo da Sauri suma suka biyota suna dariya....
turus suka tsaya ganin yanda....
.
[8/4, 10:37 AM] Xainab Documen: *♨️♨️MATAN HAFIZ♨️♨️*!!!
*FASAHA ONLINE WRITERS*
F.o.w.
Written by.
*FOUR GORGEOUS WRITERS*
-Raheenat mahmud.
-Mmn Abduljalal.
-Xayyneb💤💤 (xexen Fasaha).
-Matan Borno.
*♨️Impacting valuable knowledge and entertainment is our concern.♨️*
Bismillahirrahmanirraheem.
*Gargad'i*
Bamu yarda a juya mana littafi ko ta wacce siga ba tare da izini ba.
47.
Turus suka tsaya ganin yanda hafiz yayo gaba baqin nasu na biyo su a baya, dukkan su sunyi mamakin ganinsu kuwa,
hjyr mecca taji matan jikan nata sun burgeta dayake wnn shine karonta na farko data ta6a zuwa gidan,
su ko sun rasa ina suka aje ina suka saka da baqin nasu kankace mi sun cike musu tebur da kayan ci da sha, snn suka zauna suka sake gaishesu cikin nutsuwa, murmushi hjyn hafiz tai ta fara gabatar da matan Hafiz ga hajiyan tata da cewa "hjy wnn itace uwrgidan sa raheema saita 2 gata itace zainab saita uku gata Fatima saita hudun itace basmah" hjyn mecca ko sai fara'a takeyi tace "gasu kam fa tubarakalla masha Allah, Allah shi qare hade mana kanku ya qaro zuri'a managar ciya a tsakani, cikin kunya suka amsa da amin,
dasuka tashi tafiya ko har bakin mota suka rakasu nan hjyn mecca ke musu wasa da cewa "Ai da khairat zan tafi mecca danna ga alamun bakuson nisa da ita"
zee sukai dariya hjyn hafiz ta dafe baki tace "a rufa mana asiri hjy wnn shine daukan dala ba ganmo inko kikace zaki tafi da khairat mecca ai insha miki Allahu gasu can suma sun koma can da zama wadannan hanta da jinin da kike gani ai basa rabuwa"
dariya akayi gun hadda Hafiz kamin daga bisani suyi bankwana suka tafi, har hjyn mecca na cewa zata dawo su qara gaisawa jibi inda gata zata tafi gida sukai mata ftn Allah medota lfy.
su kuma suka dawo cikin gida, waje daya suka zauna dukansu suna cin kayan maqulashe khairat na tsakan kanin zee da Fatima kamin daga bisani suka fiddo vidion suna kallo suna dariya, Hafiz ko murmushi kawai yakeyi yana mai yabawa shima.
wanshekare kuwa gidan yai saura daga basmah sai khairat, dan heema da zee da Fatima sunje gaisuwa cikin unguwar ta Alhj mu'aruf dattijon mutunin kirki wnda ya rasu yana cikin salla ba ciwon kai bare na qafa.
anji rasuwan bawan Allahn nan kuwa ba kadan ba.
to shi a tsarin Hafiz bai yarda akwashe afita gida gaba daya ba sai dai in wnn ta dawo wnn ta tafi inbashi zai kai suba duka gidan,
to mafarin knn basmah ta zauna babu jimawa da fitar tasu ne khairat ta dawo daga makarantar islamiyya ta safe dayake yau ta kama asabar,
tana cire kayan jikinta jikin basmah tazo ta shige gamida furta momy"momy ina su momys ban gansu ba adda mukarram shima"
dan rungumeta a jikin ta basmah tayi sannan tace "sunje gaisuwa nan cikin anguwa da kuma mukarram suka tafi"
shiru khairat tai kmr mai tunanin wani abu sai can tace "momy wanene ya lashu?"
"Alhj muaruf ne wnn farin dattijon mai farin gemu dake bawa yara sadaqa kokin san shi?"
basmah ta bata wnn amsar gamida tsayar da ita tana mai cigaba da cewa
"khairat bari na kwance miki kan nan naki dan adda salma tace gobe akaiki ta miki kitso irin na yan garinsu"
murmushi tai tace
"to momy"
tana cikin mata tsifar ne taji tace "momy wnn mutumin yanada kilki ko?"
"wa knn?" inji basmah ita,
kuma tace
"wannan wanda kikace ya lashu aina shansa nima d'in, dan kullum ina ganinsha a masallaci in jani ishlamiyyan mu yana bawa yala shadaqan alewa nima yana banu inna gansha kuma"
gyada kai basmah tai gamida cewa
"eh shi ne fa khairat, yana da kirki matuqa ay shiyasa akeso mutum ya zauna da kowa lfy cikin rayuwarsa domin yasamu shedar kirki ko bayan ransa,
lumshe idanu khairat tai tace "momy mlmin islamiyanmu ma yace mala'iku na zuwa wajen gaisuwa dan suji mi ake fada gameda mamacin na dab'iunsa da yana raye dudda sun sani amman yace shedar mutane tana anfani ga mutum koda bayan ransa, nima inna rasu momy Allah sa nasamu irin wnn shedan" zuba mata idanu basmah tai ta rasa miyasa muddin zaka zauna da khairat saita maka irin maganganun nan masu kashe jiki, ammn ynz tariga ta tabbatar lallai hkn a jinin khairat yake, dan haka murmushi tai tace
"amin khairat kowa nason haka ay"
to Momy kinga in kuka rigani mutuwa zan dawwama ina miku adduan samun rahma shin kema idan na rigaki zaki mun ko?"
'yar dariya basmah tayi tace "sosaima addu'an ay takobin mumine ce"
tsallen murna tai ta juyo ta rungume uwar gamida kissing dinta a kumatu tana cewa "yeeh gsky naji dadi yau momy na ta zauna muna yin fira da ita, Allah sa kullum ma haka amin"
cikin qaunar 'yar tata itama ta rungumeta tace
"khairat ina sonki har cikin raina kunya da fulako ne dai ke tauyeni agaban mutane har nake gaza baki kulawa sosai amman kimin addu'an ko zan rage khairat"
'yar dariya tai tace to Momy, zanyi amman minene kunyan fulako ke nufi?"
medota gabanta tai tana cigaba da mata tsifan tace "bari zan fada miki wani lokacin ynz muyi muyi mu gama miki tsifan kan sai nai miki wanka ki salla kici sbinci kamin lokacin islamiyya yayi, hakan ko akayi koda lokacin islamiyya yai ta shirya ta gamida bata jikkar litattafanta har zata tafi sai ta dawo tace "momy har ynz dady bai tashi daga barci ba?"
basmah tace
"yagajine khairat shiyasa yk bacci mai tsawo HK yk inya kwanta, amman jeki gani ynz maybe koya tashi"
tace "to momy bari naje nai masa bye bye"
koda ta shiga Hafiz kwance yk still yana barci fitowa tayi tace "momy barci yakeyi har yanju"
"to khairat kije sai kin dawo Allah ya kiyaye"
"aminn momy"
haka ta tafi islamiyya itada direbansu dake rakata har mkrnta snn ya juyo.
a islamiyya ta kwantar da kanta a jikin ta sbd jitakeyi kmr bata lfy ma,hatta Mlman sun lura da kmr bata lfy SBD in lafiyan khairat lau to bata yin shiru komi akayi wnda bata gane ba sai tai kokarin tambaya har ta fahimci abin snn.
Suna dawowa mkrnta wajen 5 lokacin har Hafiz ya fita, dakin momynta ta wuce da sallamarta, nanta samu basmah na saka lalle a yatsunta, tana shirin zagayawa famfon baya ta wanke dan lallen nada ja sosai, kwanciya taga khairat din tayi a doguwar kujera ta mimmiqe,
tace "harkin dawo khairat" juyowa tayi ta kalleta tace
"eh momy"
basmah tace "kinga su sugar momys dinki sun dawo ay ko?"
lafewa ta qarayi ita kanta ta rasa mike mata dadi a jikin ta ko mgn ma batason yi da qyar tace "to momy bari na huta sai naje, nagaji shiyasa nk jin kamar jikins na ciwo" miqewa basmah tai ta shafa wuyanta da bayan hannunta sanyi qalau taji babu zazzabi kuma,
cewa tayi "gajiyan dai ce khairat sabida banji masassara ba a jikinki bari naje na wanke lallen na dawo nai miki robbing din jikinki ko zakizo muje tare?"
girgiza kai tayi tace
"a'a momi jeki nidai ina nan