Showing 54001 words to 57000 words out of 78322 words
kmr ya zuba ruwa qasa yasha yakeji, mus'ab ko sai tsokanarsa yake da cewa "angon bazata mai abin mamaki" saidai yai murmushi kawai.
mutane shima sunata masa fatan zaman lfy saida mutanen suka tattafi snn dadyn Hafiz da momynsa da da brothers haisam da nura suka ce zasu wuce a cewarsu bari suyi gaba sabida turo motocin daukar amarya gamida shirya abincin baqi, to momyn Hafiz ganin lokaci yaqure data isa gidan kawai saita sanarwa yaranta Aisha da mufeeda dasuje ayo odar abinci da lemuka kawai zaifi sauqi.
abbu ko yaja su hafiz gefe ya dubi mis'ab yace
"to mgnr kudin kayan dakin kasamu wani ya rakaka aje akai kudin inda daman anriga da anyi ciniki qwamma aje ayi jeren kamin 'yan daukan amarya su qaraso Mlm hafizu" girgiza kai Hafiz yai yace "ai abbu ba buqatar komi daga gareku domin dakin da za'akai basmah akwai komi a cikinsa Na dangane da abin buqata" girgiza kai abbu yai yace
"a'a Hafiz baza'ai haka ba kasan abin mgn baya wuya kabari a siyo inda anshirya hakan"
"Allah kuwa abbu babu damuwa nida momyna da yan uwana bamuda matsalar komi" yana gama dadar hkn yy saurin barin gun dan gudun kada abbun ma ya sake yo wata tirjiyar yana tsaka da farincikin sa,
abbu ya dubi mus'ab yace.
"dudda haka nan kudin aje a qaro kayan gara dasu mus'ab dukansu, snn kuma kayiwa mai furnitures din mgn yy haquri.
ahaka abbu yawuce wajen wasu baqinsa da suka zo daga gida Cameron, Hafiz kuwa yaja mus'ab zuwa wata qatuwar plaza,
nan ya siyowa amaryar tasa wata danqareriyar waya iPhone yar yayi had'e da sabon sim.
snn yacewa mus'ab yazabi tasa shima, da mus'ab ya fara musu saida yaga kmr ran Hafiz din zai baci sabida yace aiba roqonsa yaiba kuma an zama 1 snn fa mus'ab shima ya dauki tasa, haka suka gangara bangaren suturu less da atamfa da shadda materials inner wears inglish wears and sleeping dress, bags and shoes sarqoqi da 'yan hannu maya mayai kayan make up da turaruka saida Hafiz yayi wa kowane akwatinsa daban, wanda anan yabar wadinda za'a dinke dukknsu gamida cewa zuwa anjima zai kawo musu mergment din mai kayan, har mus'ab saida Hafiz yasaimasa shaddoji masu kyau da yadika, mus'ab yy gdy sosai kuma ya girgiza da ganin katafaren lefen da Hafiz din ya hada ynz lallaikam barikinka aljihunka inji masu iya mgn, gefe guda kuma yaga anqara hado wasu akwatunan manya guda 3 kowane da kit shaqe da kayan a cikinsu azhiri kuma Na fadar kishiya ne Hafiz yayo dan yasan saiya dade kunnuwansa yau kam ga matansa,
Motar kayance takai kayan basmah har gida Wanda tareda mus'ab suka tafi, shi kuma ya tsaya gamida bugawa lawai direbansa waya yace yazo ya dauki kaya a plaza s.s yakai gida yavarsu amotar saiyazo, hakan kuwa akayi lawai yazo ya dauki kaya yatafi shi kuma Hafiz yai musu transper din kudinsu snn ya wuce banki ya fiddo kudi ya dawo anguwar .
da suka hadu da abbu yai masa fadan kayan sunyi yawa Amman Hafiz saiya nuna yai haquri bakomi ay.
yana baro gun abbu kuwa hafiz yayiwa Adda salma waya kan yanaso suyi mgn da basmah, dayake sit room din a cike yake da mutane sai tai dabarar futo da amaryar sanye da dogon hijab hadda niqab gudun surutun mutane,
har cikin motarsa tasata tana tsokanar Hafiz da ango kasha qamshi, dariya Hafiz yai yana cewa
"dudda ban kalli fuskan kyakkyawar amaryar tawa ba nasan adda ta gama hadamun ita kuma dole addanmu ta amshi tukwicinta ko, yana gama mgnr ya fiddo rafar dubu 200 ya miqa ma adda,
da adda taqi amsa amman saida taga ya langwabe ya marairaice uwa yaro snn ta amsa tana gdy, nan yake cewa ta ara masa basmah yakaita a aunata sbd dinkunan biki, nan adda take cewa yamata alkawarin zai medota cikin lkc kamin lkcn tafiyar ya ida, dan qarfe 5 akayi za'akai amaryar ynz kuma biyu da rabi daidai, yar dariya Hafiz yai yace ni adda dama an barni na wuce da abata gida"
hararar wasa adda tai masa nan yaja mortar yana dariya gamida cewa "afuwan adda tamu subutar baki nai zan cika miki alkawarinki kada kidamu ba jimawa zamuyi ba"
ahaka yaja motar sukabar layin, tafiya suke babu wnda yai mgn cikinsu kowa da abinda ke ransa na farinciki marar musultuwa ,
saida suka iso a harabar motor park din plaza din snn ya tsaida mortar gamida juyowa yana kasheta da murmushi,
saurin janye idanunta tai daga nasa ta sunkuyar dakai qasa tana sakin ata murmushin itama,
jitai ya d'age niqab din daga fuskarta yace
"My bride abin ko mgn?"
ya furta yana mai binta da wani sansanyen kallo wanda a hankali ta dago kanta suka kuma hada ido sai tayi saurin niyyar sake boye fuskarta aikam da sauri ya fizgota kan cinyarsa hannunsa daya riqeda habarta yace
"uhm baki ban amsana ba kike kokarin boyemun kuma kyakkyawar fuskar nan bacin data zama mallakina sai ynda nasoyi da abata".
ya qarashe mgnr yana mai kanne mata idonsa daya, lumshe idanunta tai cikin tsananin jin kunyarsa yayinda ta kuma budesu muryarta na sharking ta furta " inaa.w...u
wuni" jin sansanyar muryar tata yasashi lumshe idanu batareda ya shirya ba yasake matsoda ita cikin qirjinsa sosai zuciyoyinsu na bugawa a tare, a kunnenta ya rad'a mata "my baby yakikaji farinciki sanda labarin aurenmu ya isa kunnuwanki dan naso ace ina kusa inga ynda kyakkyawar fuskar nan zata qara kyau sanda farinciki ya cikata"
yana mgnr yana shafe bayanta zuwa wuyanta da illahiran tausasan tafukan hannuwansa, jiki a mace tace "yah Hafiz Alhamdulillah naji farinciki marar iyaka hakama adda salma"
dan marerecewa yai kmr wani baby gamida cewa
"to naji na bad'ini saura nuna farinciki na aikace wato Na zahiri amin sumba a baki danna qara tabbatarwa anji farincikin mallakan juna da mukai OK?"
dasauri ta boye fuskarta a qirjinsa tana lanlangwabewa uwa zatai kuka ta furta "ayyy... ayy... ni ban iya ba kuma"
d'age gira daya yai gamida furta "kai da gaske? to aini na qware abu mai sauqi bari ni na nuna miki yanda akeyi...."
ko kamin ta yunqura ta matsa saga garesa sai jitai bakinsa kan nata ya damko lips dinta da suka sha janbaki da balm lips mai kamshin strawberry ya hau tsotsewa cikin kwarancewa, basmah ko sai mutsu mutsu take takasa mayin koda kwakkwaran numfashi domin tunda ammi ta kawota duniya bata taba jin haka ba jitakeyi kamar wasu taurari da tsuntsaye na mata kuka aka, bata qara tsinkewa ba saida taji harshensa na yawo zuwa wuyanta da bayan kunnuwan ta aikm saida numfashinta ya dauke na wucin gadi ana haka kuma katsam taji sauqar fuskarsa a kimtsattsun manyan nashanunta yana gogga fuskarsa a kai dudda cikin riga suke kuwa amman hakan bai hana Hafiz sunsuno tsabar yawansu da taushinsu ba, jiyai ta fashe masa da wani razanannen kuka na tsoro,
babu arziqi yabar abinda yake ya rungumeta jikinsa yana dan bubbuga bayanta alamun rarrashi, saida ta nutsu snn ya dagota suka hade ido tayi saurin yin qasa da nata idon shiko murmushi
ya saki gamida furta
"matsoraciya''
dan turo baki tai aiko yai shirin kuma damqosa da nasa nan tayi saurin kaucewa tana mai sakin kukan shagwaba wanda ba hawaye a cikinsa sai sangarta,
wanda hkn kuma ba qaramin ruda oga Hafiz yaiba, babu yanda ya iya dole ya haqura harta iso hannunsa wnn tsoron nata duk saiya kauda mata shi, shi dai fatansa Allah sa kada nan gaba tazamo kalar matansa yana fatan zuwanta gidan yakawo gyara a ciki, dan bai tunanin basmah zata canza kyawawan d'abiunta a ynda ya santa dudda dai d'an Adam ajizi ne, gefe guda ga faman kira adda salma take danna masa dud bayan minti dole tasashi fitowa a motar ya riqo hannunta suka qarasa shiga plazan, mutane sai kallonsu suke dan ba qaramin burgesu sukai ba, basmah ko dud kunya ta isheta sai kokarin cire hannunta a nasa take ya hana, qarshe ma sai jitai ya ida rungumota baren jikinsa babu yanda ta iya haka ta sadda kanta gefe mutane ko wasu da suka kasa daurewa har saida suka furta cewa
"yayi kyau yallabai Allah sa alheri"
shiko sai amshewa yake da amin cikin farinciki.
ahaka suka isa wajen dinkin, dayake telolin hadda mata a wajen shiyasa Hafiz ya yarda aka aune masa ita dud Inda ya kamata snn suka dauko hanyar gida bacin matsa mata dayai suka je restaurant din cikin plaza din taci dambun nama da ferfesun kaza gamida mutunenta ice cream dan a cewarsa yasan hakanan take wnn hidimar babu komi cikinta azahiri kuwa hakane dan rabonta da wadataccen abinci tun jia da abbu yakawo mata mgnr aurenta da hamiz.
bats wayar yai taita murna tana gdy.
sai yaji wani iri dan bai saba yiwa matansa abuba yaji suna gdy saidai su amshe kawai heema mace maiyi wani lokacin.
suna isa ko a kofar gida suka samu adda tana jiran isowarsu dan anbugo mata waya ance motocin daukar amarya suna hanya.
dan haka shiga tai da basmah gida ta hau qara gyarata da salon kwalliyarta.
ana haka har motocin daukar amarya suka qaraso, nanfa mutanen Unguwa yan ganin qwaf da wanda ba yan gwanin qwam ba sukai ta shiga motoci yayinda aka fito da basmah daga gidansu lullube da mayafi sai kuka take dan abbu da Ammi baqaramin kuka nasiharsu gareta ta sanyata ba ga kewar rabuwa da juna dan daqyar Adda salma ta banbarota a jikin ammin suka fito waje suka shiga mota aka dau hanya zuwa gidan Hafiz.
matan Hafiz kuwa kamar daga sama suka dinga ganin shigowar dimbin baqin mutane a gidan, dan daman sunyi mamakin ganin su Anty Aisha da mufeeda harma da fadeela ga abokansu su kusan 7 sai faman zirga zirgan shige da fice suke a dayan dakin sama spare din nan dudda dmn akwai kaya a cikinsa badai su cika shigar sa ba ne,
heema kam har wajensu taje suka gaisa cikin fara'ar ta har take tambayar ko wani taro zasuyi a gidan halan,
to dayake Anty aysha da sauran qannen nata suna danyi da heema akan sauran sabida tana musu kirki ga sakin fuska ako yaushe suka hadu, tsagal kuwa saiga zee da fateema sun iso wajen suna masu son jin amsar mi zasu bawa heema, aiko budar bajin Anty Aisha sai cewa tai "heema mai gidanku ne aka daurawa aure yau yanzun ma gyaran da kukaga munayi Na tarvar amaryar ne kinga amaryar ma harta iso,tana radar haka ko fadeela tayi shashin amarya tabarsu nan,
dudda heema bata cika saka damuwar komina ranta ba sai da taji ba dadi dan a qalla Hafiz ya fada musu zaiyi aure amman yana sane haka yayi musu shiru alhalin suna tare dashi dazun nn kuma hadda cewa daurin auren abokinsu zaije ashe su yamaida garmahwawa, amman a fili sai tai murmushi gamida furta "ayya Allah sanya alheri ya bamu zaman lfy a tsakani"
suka masa da amin, zee kuwa sai faman tabe baki takeyi gamida riqe ha6a a fili tace "oh ni zee namiji bashida tabbas kowa yace zai dauki namiji uba zai mutu maraya dan yau na sake tabbatar da Karin mgnr nan da akecewa namiji qanin ajali wato tadai tabbata namiji qudan zuma ne ga zaqi ga harbi ,
to in bancin wulaqanci kishiyar ma a gagara fada muna cewa za'a qaro mumu saidai mu ganta uwa daga sama kenan anmaishemu hotihon gantalallun mata" cikin masifa mufeeda tace ''ke qaramar marar kunya ki iya bakinki wlh kinsan ni na sanki batun yauba idan kikace zaki qara nuna mun wnn banzancin naki wlh zaki sha mamaki snn kuma da kike fadar an maidaku hotihon gantalallun mata tominene din basu ba?, danmu agaremu dangin miji duk macen dabata kyautatawa mijinta wato d'anuwan mu to wlh hotihoce a garemu fiyema da haka ma"
zee bata sake cewa komiba Na yan second sai wani dogon tsoki dataja snn tace ''yo dmn dangin miji ko asararru mi suka aje banda munafinci da zaman jiran ace kayi su samu na magantawa da kayin da baka yiba ma sai ance to gara kayin sai afada da hujja, ahaka zaku qare a gantale inba'a canza hali ba" mufeeda ta zuciya ta yunqro zata cafki zee Anty Aisha tayi saurin riqeta tace "haba dan Allah ya kuna abu kamar wasu qananun yara, kun sani fa cewa da baqi a gidan nan fa ko so kuke kujawo mana abin fadi mufeeda?''
qutawa mufeeda tai snn tace "shiknn Anty Aisha amman koba ynx ba saina koyawa wnn mai bakin uwar hankali wlh marar da'a"
tsoki zee ta kuma yi gamida furta "nice ke ay"
kuma kishiya ai bata dameni ba gadai wacce zata magantu nan takasa mgn tazama sanda a wurin"
tayi mgnr tana kallon fateema datale jingine a bango wacce ta sume tuni basu ankara ba tun farkon fara rigimar mgnr kan qarin auren haifiz,
ta6ata zee tai aiko sai taga ta sulale wajen bata motsi, ankara da hkn da sukai ne nan da nan anty Aisha cikin sauri ta figi robar ruwan faro daga hannun mufeeda ta qarasa ga fateema ta tuttule mata ita a jiki saiga fateema ta saki dogon ajiyan zuciya tahau bin su da kallo tana fatan ace wnn mummunan mafarkin nata yazo qarshe,
jitai zee ta bushe mata da dariya gamida fadar "au da waike suma kikayi knn kan batun? tab to wlh da sauranki Indai namiji ne batakaran ki suma ba Ia Kansa Ina mai tabbatar miki in baki juri haqurin kauda ido ga lamurran da suka so ba a lokacin to wlh sai dai kiji ki wataran a cikin kabarinki ana tanbayar ki man rabbuki yake Fatima😂.."
da dai fateema taga abin da gaske ne ai batasan sanda ta hantsala ta miqeba gamida sakin wata razananniyar qara tanufi Kansu anty Aisha haiqan dawata qaramar wuqan da zee tagama amfani dashi wajen yanka lemu data wawuro kan table...
*By 4 writer's fasaha👩👩👧👧😍*
*Fasahar mu tamu ce😎*
[7/12, 8:34 AM] Xainab Documen: *♨️♨️MATAN HAFIZ♨️♨️*!!!
*FASAHA ONLINE WRITERS*
F.o.w.
Written by.
*FOUR GORGEOUS WRITERS*
-Raheenat mahmud.
-Mmn Abduljalal.
-Xayyneb💤💤 (xexen Fasaha).
-Matan Borno.
*♨️Impacting valuable knowledge and entertainment is our concern.♨️*
Bismillahirrahmanirraheem.
*Gargad'i*
Bamu yarda a juya mana littafi ko ta wacce siga ba tare da izini ba.
37.
da sauri heema ta riqeta tana fadin "haba kekuwa Fatima cikin hankalinki kike kuwa?" zee tace
" 'aa daina fadar hankali nan heema domin tabbas babu shi yayi qaura, dangin miji da kike gani ba qaramin masheranta bane yanzun nan sa sa a daureki har igiya tai rara to na haninssheki bari ko Na sanki, saita canza salon mgnr ganin wani kallo da Anty Aisha ke mata da cewa
" ynz ke sabida tabewar basira yayar mijin naki zaki kashe harda yan uwansa? (zee irin mutanen nan ne masu fuska 2 wato zulwajahaini in taso zata rikide nan take ta koma uwa ta Allah dansan samun gindin zama, inkun lura ynx ai tagama fad'a dasu mufeeda ammn ynx ganin fateema ta yunquro sai take son qara rura wutar abin gamida son tsame kanta a ciki)
cigaba tai da cewa
"tab lallai abin naki azimun ne toni miya hana in tada tangarayen bala'oina sanda aka yomin ke a matsayin kishiya em?"
cikin masifa fateema race
'' ke qaramar jahila munafuka badake nake ba, ta juya gasu Anty Aisha tace tun sanda aka fara mgnr Hafiz zai aureni Na lura baku farinciki mahaifiyarku ce kawai keson lamarin to wlh nidin naci dubu sai ceto dud wacce tacemun kulle zan cemata cas wnn ai tsabar kiyayya CE dududu yaushe akayi auren namu dahar za'a turasa ya qaroman wata to wlh anshiga haqqina Allah ya isa na kuma"
cikin tafasar rai mufeeda tace "yoke Fatima har kinada bakin mgn ba rufa miki asiri mukai ba har yaya ya auroki Inda angama karatun ansamu aiki babu mashinshine to wlh bari kiji muddin kikai tarangazar da kikabar gidan nan yanda kikeda nauyin jinin nan kilan saidai ki auri masinjan ofis dinku ama kinyi sa'a knn"
zee kuwa ta amshe da fadar "haka yake Anty mufeeda gaya mata dai, nima dai Ina neman afuwanki da sa6anin da muka samu yanzun tuntuben harshe ne da sherrin shedan,koda yake kuma inada matsalar iska ba kowa yasanfa hakan ba wani lokacin nakanyi Abu ba cikin hankali naba in raina ya baci sai daga baya"
ta yanko wnn qaryar nan take Rana qunshe dariya.
Heema tace "anty Aisha ayi haquri dai kuje kuci gaba da hidimanku kunga da baqi a gidan bai dace muna wnn maganganun ba kmr yanda kika ce, snn fa muma zamu shigo ayi damu ynx, haka Anty Aisha da mufeeda suka wuce bangaren amarya akabar fateema nata bubutai.
hakan kuwa akayi zee anje anciyo wanka akafito anata taku d'aid'ai aka shige cikin dangin miji itama heema tayo wankanta Masha Allah tayi kyau har saida zee ta yadda mata mgn da cewa " oh su agwawar ruwa yau an fito tsab Allah sa ad'aure, dudda ta fahimci mgnr zee inda ta dosa Amman sai bata nuna ba aranta kuma tasha alwashin indai kan tsabtar jikinta ne yanzun zata gyara babu macen dazata mata gori ko dariya kan hakan, sosai zee tai mamakin ganin kyawun amaryar tasu saidai ga alama girman jikine daka kalli fuskarta zaka gane yarinya ce domin duk sun girmeta, murmushi zee tai aranta tace "wnn aiba abar kishi bace dazarar ka zare mata ido ka kwatsa mata tsawa zatai maka komi kasata, ahaka sukaita hidimarsu yankawo amarya ko sai santin gidan akeyi da dukiyar dake cikinsa da aka narka kota Ina, yan gulma da tsegumi qagare suke sukoma su bazarwa da wanda baisamu zuwa ba labari a anguwa.
fateema ko tana can ta kulle kanta a daki taqi fitowa,
sai bayan isha'e snn gidan yai tsit, su Anty Aisha basu tafiba saida suka sa aka gyara gidan duka ya dawo normal yanata kyallinsa ga turaren wuta da akasa komi ya koma mahallinsa uwa ba'ayi taro ba cikin sa snn suka tafi zee hadda musu rakiya ganin heema ta rakasu itama har suka shiga motarsu suka wuce.
suna dawowa kowace ta shige dakinta ta kulle.
basmah ko tana qudundune kan gadonta har dare ya tsala bataji motsin kowa ba, haka ta miqe tanata sakin ajiyar zuciyar kukan data sha, warware lafayar jikinta tai tabar kayan jikinta, tai tsaye tana qarewa dakin kallo, komi ya zauna a muhallinsa gwanin burgewa,