Showing 51001 words to 54000 words out of 78322 words
snn ya dauko wata dakakkiyar gizna dinsa darkblue yasa, aikin gaban babbar rigar anyisa da golden and White color sai mai takeyi hularsa ya daura akai yayi masifaffen kyau marar masaltuwa dudda ba cikin walwala yk ba ammn hkn nai tauye kyaunsa ba, sosai zee ta rud'e da ganin kyakkyawan jinin balaraben mijin nata kamar ta lashesa, saitaji kishin su heema ya kuma kameta zagi ta dinga dura musu a ranta gamida cewa yan banten uwa ynz dani kadaice dashi dasai nafi samun kulawa nayita tsula tsiyata a gidannan gamida ninka yiwa qawyena fankama ammn babu komi lkc na zuwa da mafarkina zai zama gsky duk saina koraku a gidannan, yayinda a fili ta dinga santin shigar tana daukarsa PIC da wayarta dudda bawai shirin tsayuwan PIC din yaiba amman yayi masifar kyau, kamin tace "wai sojana na tambayeka wnn shirin na miye kamar wani sabon ango?"
tayi mgnr tana turbine fuska, hannun links din rigar sa da ya fara datsewa shi ta amsa ta qarasa daddatse masa kwantaccen gashin dake Kn farar fatatsa ya fito sosai ta qasan hannun rigar links din hannun yai gwanin kyau Masha Allah, babbar rigarsa dabai warware ba tana linkenta lub ya sagala ta a hannunsa hakan ba qaramin sake ruda zee yaiba tana shirin mgn knn saiga teema ta sigo,
turus ta tsaya ganin wankan da Hafiz ya zuba a jikinsa, gabanta ya buga
damm!!
data tuno mgnr Neman auransa wata zuciyar tace to ko yau ne daurin auren bamuda labari?,
dasauri wata zuciyar tazo ta Kore wnn tana cewa tub da mugun bakinki tayama zaiyi aure bai sheda ma iyayensa da muba, kuma bacin mufeeda tace ta bincika babu mgnr wani aure da yake nema shaci fadi ne kawai na mutane, sai lkcn ta saki ajiyar zuciya ammn taji fa kishin ganin zee kusa dashi uwa ta shaqeta takeji, da gangan ta ingije je ta isa jikinsa aiko a kufule zee tace
"ke dilla malama ke makauniya ce kike ingijeni haka ko yane?"!
cikin barikanci teema tace "oh sorry Bn luraba bane hankalina ya dauko ga handsome din mijina,kinsan in Ina taredashi komi tarkace yake komamin inks daukesa,
ta dawo da kallonta garesa yayinda zee ta dinga binta da harara tanaji uwa ta fara da kwakule mata maqoshi kota samu sauqin zuciyarta,har ita zata gayawa ba dad'i?.
shafa kwantaccen sajensa teema ta hauyi tace
"my handsome wnn shirin fa ya tsoratani ai wnn sai kasa na 6arke da gudawa nayi zaton ko kishiya ta iso kaina" murmushin gefen baki yayi gamida shirin sa rufaffun shoes dinsa da sauri teema ta matso masa dasu a gbnsa yasa snn ya dubi zee ya dubi fateema gamida cewa
"daurin auren wani abokinmu zani naga duk kunbi kun tashi hankali, kusan atare zee da fateema suka sauqe ajiyar rai, cikin fari da ido zee tace "oh har naji sanyi wlh dudda dai koda hakan yakance na tunaninmu akan zuwan kishiyar toni miye na damuwata inda ga tawa a gabana anyi an wuce wajen sai dai wasu su tallafi qaddarar daukar ta danni najima da amsar qaramar tsakuwar qasqantattar tawa" sarai fateema tasan da ita zee take gaya wnn mgnr wato idan kishiyan ma zai yi ba itace za'ai waba kuma itace qasqantacciya?!
qutawa tai gamida cewa
"a qasqance na samu babbar qasqantacciyar data nuna ta gaza saida aka kawo karamar qasqantacciyar mai nasara take bata kashi,
shin tayaya babbar qasqantacciyar ynz take kokarin shiga taitayinta bacin ta baro bid'a baya tun farko data gane cewa bakin rijiya ba wajen was an makaho bane".
duk wnn habaicin dasuke sarai Hafiz na jinsu ammn bai nuna alamun hakanba saida ya gama saka watch din hanunsa snn yace
"heema fa?"
tabe baki sukai kamin teema ta kauda zancen da cewa "breakfast is ready habiby" agogon hannunsa ya kalla yaga 12 da kusan minti 40 sai ynz za'ace zaka samu arziqin karya kumallo a gidankan, murmushin takaici yai gamida nufar falo suka biyo bayansa Suna masu ingizar kafadun juna dudda teema tafi zee auki nesa ba kusa ba ammn HK zee take shigemata masifan kishin nacinta.
zee yasa ta kirawo heema haka ta tafi tana guni,
ta dawo tasheda masa gatanan, ba jimawa heema ta sauqo daga benen d'akinta ga alama ko wanka bataiba ko ace shi takeshirin yi dan daurin qirje ne a jikinta kanta sanye da hula mai raga tana tafe tana danne2 wayar tata ta qa'ida kuma,
binta yai da kallo ya girgiza kai gamida basmala yafara cin abinci, ajiye wayar heema tai tana kalkonsa dan sai lkcn ta kura da shirinsa, cikin fara'a tace
"Ah abbun sultan wnn shirinfa sai ina?"
tayi mgnr tana Sosa qeyarta, hade rai Hafiz yai yace
" kinzo kin samemu a wuri babu sallama bare gaisuwa saima tambaya da kika fara kuma?
Why heema yaushe zaki gyara ne dan Allah, jibi ynda kika zo a gabn minjinku aqalla ko rigar wanka kya sanyo kinsan na tsani ganin mace da zane daurin qirji gwara acemun na ganki towel kinn sane kema kinsani kuma"
maimakon ranta ya baci da abinda ya fada ta zuciya kota Gyara saitai dariya tace "yi haquri dadyn sultan banson bata mk lkc ne shiyasa nafito hkn ammn bari naje nasanyo rigar inyaso wankan ko zuwa da marece ko dare sai nayi Dan daman bawata daud'a nayi ba inda shekaranjia nai wanka, da sonai ma nabari sai gobe nai wankan sai kuma na canza Shawara sabida inason naje gamida gajiyanka kwana 2 bamu hadu ba" baiwar Allah tadage tana fiddo gskiyan abinda ke ranta aiko zee da teema suka kwashe mata da dariya hadda kyakkyatawa itako tabisu da kallo fuska hade batareda tace komi ba, dafe kai Hafiz yai gamida ajiye spoon din hannunsa ya miqe tareda kallonta yace
"shawarata gareki kibar irin wadan nan maganganun agaban abokan zamanki zaifi kyau kimin ita dagani saike dudda nasan gskiyan ki kika fada baki qarya ammn ki gyara harshenki bakina sakina sa kina maganganu ba kinga ynz kinyi mgn sunyi dariya ranki kuma ya baci to laifin wa?, snn Ku kuma banson wata na mgn cikinku kuna dariya domin dariya tana daya daga cikin alamun raini, shiru heema tai jitai yace
"daurin aure zanje natafi saina dawo"
teema cikin iyayi tace
"adawo lfy my handsome" yayinda heema tace "
to abbun sultan Allah tsare yasadaka da alheran cikin wnn rana"
yaji dadin kalamansu yaji inama su tabbata a hkn , zee kuwa tace muje na rakaka angon gobe...harara teema ta watsa mata aranta tace
tuf bakinki bazai taba kama niba kishiya babu ita gareni agidan nan dagani kam an rufe kofa,
Saida ya shiga mota ya fita snn ze ta dawo tasamu heema tana kalaci ta kuwa kwashe da dariya tace
"yo Allah na tuba astagfirillah wadannan mazan na yanzu kana tsabtar kana komi ya aka qare dasu bare ba ko daya ahadun, Ina amfanin mace ba kimtsi ba gyara, tirr qazantar duniya ta tattara ta qare a kanki heema wlh kinyi asara...tsagal teema ta fada cikin caftar da cewa
''yo akwai wata asararriya Bacin ke zee da har kike bibiyan mijin da ba hannunki yake ba, koyau kwananki ne dahar zanje na sameki tareda dashi wlh kinamun mugun halin nan sai munyi bura uba dake a gidan nan banza kawai karya"
zee tace
" ki shekara kina kirana da karya Indai kan Hafiz ne bazan damu ba banza agola kawai kokin dauka cewa bamusan uwaki agolanci tazo dake ba a gidan miji"
shewa teema tai tace
"ahayye nanaye kidai gyara kalamanki wato an riga an saba da bin maza shine ake lafewa da Indai kan wane ne, mtsww aikin banza 6arauniya kawai mai had'a sata"
ran zee ya baci a mgnr teema aiko nan suka fara dambe yayinda heema ta cika cikinta ta barsu nan kowace ta jigata sai damn hami take.
sai kuma suka koma aitaba juna teema ke cewa zee dawani qaton goshinta uwa jirgi ya doso tasha🤣, yayin da zee kecewa teema shirgegiyar banza da wofi ahaka zata qare tana mulla qiba uwa wata saniya😂.
haka sukai tayi har suka gaji kowace ta koma dakinta tana haki.
*
hjy Aisha sai da ta ga lokacin da akasa na daurin auren baifi minti 50 ba snn ta ja nusaiba sukai wa gidan abbu tsinke, suna isa nan cikin zauren gidan sukaci karo da hamiz da mus'ab da Hafiz... Kowanensa cikin shirinsa lokaci kawai ake jira Inda ga masallacin kofar gidan nan cike dam da mutane da abokan ango dana musab da sauran mutanen arziqa.
fuska hade hjy Aisha ta dubi musab tace "kai ina mahaifink... Kamin ta ida mgn saiga abbu ya shigo zauren yana gyara Babbar rigarsa, ganin hjy Aisha yasa abbu fadada fara'arsa yace "sannu dai hjy ya kowa da...dakatar dashi tai tace "dakata Mlm ba abinda yakawo niba knn, kyautar da kabamu ce nazo na maido maka abarka,
kai wato a mtsayinka na malami saikai amfani da siddabarunku na malamai ka sammace mun d'ana tareda liqawa 'yarka shi dan azo aci arziqi ko? to ai an rarrabo da kyau tun wajen haihuwa wlh dan da kananda rabon arziqi da tuni kayisa inda ko har ka kako a ynz a haka ay babu batun arziqi a rayuwarka bare wani naka ya yishi Inda abbun gadon gado ne, dan haka kasani cewa babu aure tsakanin d'ana da 'yarka bamu so akai kasuwa bamu buqata, wnn ai cin fuska ne aka mana"
sosai ran Hafiz ya baci da ganin rashin mutuncin matar haka ma mus'ab abin na kad'i aiba hauka bane yayasu sunyi Abu da sigar had'a zumunci nahar abada snn azo ana tozartasu gamida aibatasu?.
lkc daya Hafiz da mus'ab sukai kokarin yin mgn abbu ya dakayar dasu da hannu hamiz yace "haba Momy yaz...kamin ya qarashe mgnr ta zuba masa mari tace
" nace bakai babu auran ahalin gidan nan in kuma ka nace kace kaji ka gani wlh nonona da kasha ban yafe ba kuma saina tsine maka albarka zabi nagareka"
tana gama fadar haka tana kokarin barin wajen knn abbu yace
" hjy Aisha inason yin mgn dake, a wulaqance ta juyo tana kallonsa cikin rashin kunya nusaiba tace "mgnr mi zakayi kuma dattijo shugaban kwadayayyun malamn duniya baki.......
kamin ta qarasa mgnr a zuciye Hafiz ya bayyana gabanta uwa walqiya gamida dauketa da wani mugun mari aiko ta dafe kumatu tana kallonsa a razane,
gabnta ya buga da qarfi dan ita sai ynz ma ta lura da wnn kyakkyawar halittar a gun,
kasa dauke idanunta tai a kansa domin jitai a wnn lokacin a kuma dudduniya babu wani mahaluki da kyansa ya taba gigitata farad daya bayaga hadadden gayen nan, wnn wacce qaddara ce ta fado mata haka kokaci daya, taga ynda yake mata wani kallo na tsabar tsana ga alma bazai taba qaunatarta ba a rayuwa tunanin hakan yasata fashewa da kuka yayinda kowa na wajen yayi tsammanin marin ne ya shigeta, a fili yace "ki iya bakinki kisan da wakike mgn kona karkaryaki wajen nan marar tarbiyyar kawai"
cikin masifa hjy Aisha ta dubi Hafiz tace "kai waye dahar zaka iya samun qwarin gwiwar tabamun jikin yarinya??.."
rufe mata baki nusaiba tai tana cewa "barshi kawai Momy yace mun komi yaso ma,banso ya kuma yin fushi ni ba marin bane yasani kuka Momy kice ya aureni wlh soyayyarsa ta shigeni ynzun nan bazan iya rayuwaba saidashi na yarda zan zauna dashi koda ace yafi kowa talauci a duniyar nan kuwa" taqarashe mgnr cikin ihun kuka.
sakin baki hjy Aisha tai yana kallon 'yar tata yau itace ke kuka kan namijin farad 1 bacin ita ke wulaqanta mazan ma?
anya kuwa wnn saurayin ba aljani bane Kodai gamo yar tata tai, tambayar da takewa knta batareda tai la'akari da cewa shi in akace arziqi bawai na kudi kawai ake nufi ba, wani Allah arziqin ilimi yai masa wani kuma na lafia wani na basira da fasaha wani na farinjini wani na saurin janye hankalin mutum kai gasu nan da yawa komi na zuwan maka maka daga littafin arziqinka da ubangiji Allah ya qadarto maka wani ma baida arziqin komi a cikin littafinsa haka kuma Allah ya so garesa,duk wanda ka wulaqan ta kan abinda baida iko dashi a rayuwa saiya baka mamaki wataran Indai da rai da rayuwa kuwa domin Allah da Kansa ya furta ya karrama d'an Adam to danmi kai dan yayi maka arziqi zaka dauka kafi kowa arayuwa arziqin da inyaso zai amshesa batareda sanin kaba Inda ba shawara yai dakai dazai baka ba bare har ka samu damn wulaqanta bayinsa akansa...
a kufule hjy Aisha ta fizgi hannun nusaiba tana kokarin barin wajen taji muryar abbu na cewa...
"banda burin kwadayin abbun kowa a rayuwata kamar yanda kike tunani hjy Aisha,kuma in nayi burin wannan hadinn auren ne sabida zumunci daya taba kulluwa tsakanina da marigayi Alhj muttaqa Allah jiknsa yai masa rahma yakai haske qabarinsa,
naso zumuncin nan yaci gaba da gudana har asami zuria a tsakani dan haka kibar batun tsinewa d'a, d'a dai naki ne kuma aljannarsa na tafin qafarki macece aljannarta ke tafin qafar mijinta dan haka kamar ynda kika nuna baki buqatar wnn auren to an soke shi insha Allah, nazata hakan danai zai Samar da farinciki banyi tunanin bacin rai zai kawo ba, babu komi Allah yaiwa kowa zabin alheri a tsakanin su,
hamiz kabi mahaifiyarka Allah shi maka albarka kada ka taba bijerewa umarnin ta kuma a rayuwa inba saidai abin daya sabawa Allah shine zaka janye."
Wann kuma ruwanka kaita shafa, dakake cewa Allah yai masa rahma in katashi ni ka roqar mun azaba ince shiknn ba"
cewar hhy Aisha tana mai figar hannun nusaiba datake kokari isaga Hafiz
" wuce kai kuma muje dan ba nan zan barka ba alallaba bayan idanuna adaura maka qayar Allahn can Inda babu zuciya"
Haka hamiz yabi mahaifiyarsa yana sharban qwalla suka shiga motarta sukabar anguwar dayake ita taja motar saida ta tayar musu da qura a waje.
mus'ab yace "abbu Ashe matar nan rashin mutuncinta har yakai hk? abbun dubi ynda aka tara mutane ynz mi zamuje muce musu dan Allah?"
kasa mgn abbu yai dan shima taron mutanen yafi komi daga masa hankali a ynzun, daqyar abbu yace "babu komi mus'ab zanje na shaida musu an janye mgnr da'ace abarsu suyita zamn jiran lkc"
dasauri Hafiz yafurta cewa
"abbu indai ka amince dani kuma zaka bani auren basmah toni a shirye nake da amsar wnn tsarkakaken ahalin naka abbu"
ya qarashe mgnr yana mai kai gwiwowinsa qasa gaban abbu, gaba daya daga abbu har mus'ab da kallo suka bisa, girgiza kai abbu yai gamida d'agosa tsaye yace
"Inaaaa a'a Hafiz bazai yuwu ba..wnn kmr takurawane a gareka ngd da kulawanka gareni"
nan abbu yanufi cikin gida yabar Hafiz sandare yayinda mus'ab ke gefensa.. had'e kai da bango Hafiz yai yana sakin wani numfashi mai wahala,
wayarsa yayi daurin fiddowa a aljihu gamida saurin fita waje...
*By 4 writer's fasaha*👩👩👧👧😍
*Fasahar mu tamu CE😎*
[7/12, 8:34 AM] Xainab Documen: *♨️♨️MATAN HAFIZ♨️♨️*!!!
*FASAHA ONLINE WRITERS*
F.o.w.
Written by.
*FOUR GORGEOUS WRITERS*
-Raheenat mahmud.
-Mmn Abduljalal.
-Xayyneb💤💤 (xexen Fasaha).
-Matan Borno.
*♨️Impacting valuable knowledge and entertainment is our concern.♨️*
Bismillahirrahmanirraheem.
*Gargad'i*
Bamu yarda a juya mana littafi ko ta wacce siga ba tare da izini ba.
36.
Momynsa ya kira ya sheda mata halin da ake ciki kan ya samu dama kuma tana shirin subuce masa lokaci daya, Momy ta basa tabbacin gasunan zuwa itada dadynsa inda daman suna tare a lokacin,
tace ya kwantar da hankalin sa, haka ya kashe wayar yayi ta zurubtu yana duban hanyarsu cikin tsananin qagara.
yayinda abbu ke can cikin daki yana shedawa Ammi yanda akayi, ammi ta juya ta kalli taron 'yan biki dake cike da tsakar gida anata hidimar abinci har an fara fidddawa waje, tagumi tai tarasa yacce zatayi,dan komi jitai ya tsaya mata cak, ana haka akace ana mgn da abbu waje, cikin sanyin jiki abbu ya fita, Alhj Ahmed ne dadyn Hafiz nan suka gaisa momyn ta wuto ciki itada fadeela, Alhj Ahmed ya sanarwa abbu shine mahaifin hafiz snn kuma yazo nemawa dansa auren yarsa a yau, farinciki ya lullube abbu dan baiyi zaton Hafiz da gaske yakeba daya furta zai auri basmah, dayake mgnr manya ce kuma abbu yanajin kirkin Alhj Ahmed a gari mutane nata yabonsa dan kowa nasa ne baruwansa da mai kudi ko talaka to taya jinin wnn babban mutumin mai karamci za'a ki basa 'ya, nan abbu ya ce ya basa daman auren yar tasa amman xaije yayiwa mahaifiyrta bayani itama, haka abbu yaje yaiwa ammi bayani ammi taji farinciki sosai dan koba komi Hafiz ya fiddasu jin kunyar mutane yau, tasan yan unguwar nan da ace an fasa daurin auren nan sunji to sai sun musu dariya,amman dayake Allah karimun raheemun ne gashi lokaci daya ya canza wa yar tasu wani wnda suke fatan kuma yazame mata alheri ga rayuwarta gaba daya,
sosai ammi ta karrama su Momy da abincika suma sun yaba da karamcin gidan su amaryar tasu kuwa da har ynz basu taba ganin taba, fadeela kam ta damu ammi Ina amaryar Momy tace ''kekam kinfiya azarbabi fadeela ai saikin gaji da ganin tama"
ammi kuwa dariya tai gamida sawa aka raka fadeela gidan adda salma dayake basmah din na can, adda na shiryata da kwalliya, koda basmah ta ga fadeela saida gabanta ya yanke ya fadi domin taga kamannin hafiz dinta sak a tattare da ita, dudda HK saida adda ta mata mgn cikin sigar qwarewa anan sukejin cikakken bayani daga bakin fadeela sunzo daurin auren tane da yayansu.
basmah tai kasaqe takasa mgn a ranta tana cewa Hafiz kuma? Bata qara tsinkewa ba saida mus'ab ya kira ta a waya yana sheda mata yanda akayi, basma tsabar farinciki kamar ta zuba ruwa qasa tasha , dayake fadeela tana waje wajen sauran yan matan anguwa da adda salma ta aikawa walima sunata aikin had'a take away Na baqi.
da gudu ko basmah ta rungume adda salma tana kukan farinciki tanan cewa "adda shiknn ya hafiz zai zama Nawa adda,
nan tafadawa adda komi, suka rungume juna suna murna,
hakan ko akayi ana gama sallar azhur aka daura auren Hafiz da basma akan sadaqi dubu 50.
mutane sai mamakin wnn juyin da akayi na ango suke, nan abbu yaita gaisawa da mutane anata masa Allah sa alheri.
ango Hafiz kuwa baki yaqi rufuwa