Showing 45001 words to 48000 words out of 78322 words

Chapter 16 - MATAN Hafiz Book Complete Document .txt

Unknown   

27 Nov 2024

2513

ta hudu ba koda Allah zaisa yayi gamdakatar da mai dauke dukkan lalurorinsa ta basa farincikiba a rayuwar auransa kmr ynda yajima yana add'ua yana mafarkin samu? amman dai komi knn muje zuwa zamu gani yaya gidan Hafiz da matan Hafiz zai/su cigaba da kasancewa shin zai gyaru koko).


adda salma na fita ya juya karaf suka hada ido nan ya kamata tana satar kallonsa,saurin biye idanunta tayi, wata yar dariya yayi gamida furta ,yadai da satar kallo?''
yanzun dai ina sauraranki mi soja yai miki haka da zafi cikin rayuwarki gawani kuma sojan na son shigowa ya zauna a cikinta zama na dindindin"
kwata kwata bata fahimci ma'anar kalmnsa na qarshe gareta ba maimakon ta bashi amsa saiyaga tana goge qwalla ta tsurawa wani waje daban ido gamida furta
"har yau har gobe Idan na tuno abinda ya faru sai inji kmr lkcn ne abin yake faruwa tabas na qara tabbatarwa da mugu mugu be munafiki kuma bashida tsara a duka duka labarin nn dazan baka baifi shekara da faruwa ba lokacin ina ss2 kaf school dinmu banda qawar data wuce Rafi'a dan tun muna jss mike tare sit dinmu daya har kawo sanda muka ahiga aji 5, abbu da Ammi babu Wanda bai San rafia'a ba hatta adda salma ma, dan sautari nan mike zuwa muyi komi anan sai dare direban gidansu yazo yadauketa, har iyayen Rafi'a sun sha kawowa iyayena ziyara sosai zumunci ya qullu tsakaninsu, wataran muna zaune da Rafi'a byn mun fito break take cemun wani cousin dinta zata aura suraj soja ne har anmisu baiko jia itama batasan da mgnr ba sai yau dadynta ke fada mata,kuma bikin wata 2 aka sanyashi nan nake mata ftn Allah sa alheri har ina tsokanrta da cewa ni kadai zan ida school dina wata kam tanacan abinta, sai tai dariya tana cewa taji bakomi ai zata qarasa itama in akayi auran, baqaramin so Rafi'a na kula tanawa suraj ba wata sa'in har kuka nakan same ta tanayi Idan na tambayeta dalili sai tace mun takira suraj yaqi dagawa ko kuma yaci mata mutunci gamida fadin kada ta qara kiransa yana cikin aiki, nakan rarrasheta ahakn,dan akwai sanda tazo gidanmu tana kuka take gayamun suraj ne ta gansa da wata a hotel bacin a ranar sunyi waya dashi yace kwanansa uku baya gari anturasu operation.
take cemun koda ya ganta bai girgizaba saima borin kunya da ya hauyi wai mina zoyi otel a matsayina na matar dazai aura Shi bai son yawon banza auran ma zai iya fasawa Inda bashi ya ganni yace yanaso ba had'in iyaye ne temaka mata kawai zaiyi ya aureta dan yaga son da take masa yana niyyar zautar da ita, dudda a lokacin ta gaya masa saqo tazo amsan wa momynta wajen ma'aikacin wajen amman sai da ya qare mata cin mutunci tass snn yawuce shida budurwar tasa, daga nanne tayo nan gidan namu tana kuka,a lokacin nabata haquri na rarrasheta gamida bata shawarar data rage yawan nuna masa so haka inda amfani yake dason datake nuna masan yake wahalar da ita, to daga nan tadan samu sauqinsa kuma ana haka har biki yazo baifi saura sati ba wanda a ranar soraj ya tsara zaizo gidan su Rafi'a kan shirye shuryen bikin, ban mancewa ranar ranar wata talata CE tazo gidanmu muna fira da marece sai gashi ya kirata nan take cemasa tana gidanmu dudda sunana kawai yake yawanji a bakin Rafi'a baitaba ganina ba amman ni nasansa a photo dake wayan Rafi'a kala kala pics dinsa wasu da kaki wasu babu, wasuma wajen aikinsu ne yayisu yake turo mata, saiji nai tana masa kwatancen gidanmu babu jimawa ko saiga shi yakirata da ya iso, lokacin abbu yana kasuwa Ammi kuma bata nan mafarin knn nakawo shimfida zaure nayi musu, ya shigo ya zauna nikuma naje dauko ruwa tunda ya ganni naga ko'ina nayi sai yana faman bina da kallo ga idanunsa jajjaye gwanin tsoro haka na kasa sukuni babu shiri nabar gun, azuciyar suraj ko a lkcn jiyai ya girgiza da ganin yarinyar tunda yake yawon neman matansa bai taba cin karo da wacce ta tafi da tunaninsa ba sai basmah, gashi ga alama yarinyar lafiyayya ce zatai mai, tun daga nan bacin yatafi ranar da qyar ya runtsa banda tsananin sha'awar basmah baya komi gawani bala'itacciyar soyyr ta na ruruwa masa, jiyake dama da ita ya fara had'uwa da yayi aure tuni amman ynz kam Rafi'a ta kwafsa masa wata zuciyar tace masa to ka kyankyasa yarinyar kaji ko itama "yar hannu ce ,
dan haka cikin dabara ya amshi number wayarta (wayar ammi knn)
wajen Rafi'a da mgnr cewar zaya tambayeta abinda su qawayen amarya zasu buqata ga biki, Rafi'a bata kawo komi a ranta ba aranar kuma ya kirani lfy lau muka gaisa saidaga baya naji wasu baqin maganganu marar tsari da dadin sauraro daga garesa,wai muddin na amince masa muna tarayya komi na rayuwa zai daukemn hatta su Ammi saiya kaisu qasa mai tsarki yasake mana gida kuma zai dauki nauyin karatuna muddin zan dinga binsa ko Ina zaije, ma'ana ya maisheni matarsa, wa'iyazubillahee haka suraj yaita mun wnn maganganun a lkcn, dudda na girgiza dajin hkn ammn ban nuna ba nan hau nuna masa ya tubarwa Allah yabar wnn shedancin amman yaqiyi daga qarshema kaca kaca nai masa koya kirani bana dagawa, daya matsa mun da text marassa màana sainai block dinsa hakn baimai ba saiya dinga zaryar zuwa gidanmu yana aikowa inzo abbu kuma yakan bada amsar kowaye yayi haquri an fidda mata miji, dayaga hakan yayi masa wuyan koda ganina ma katsam saiga Rafi'a wanshekare tazo gidanmu taroqi Ammi akan zan rakata kasuwa siyayan kuloli, to koda muka fita sai naga ba kasuwar muka nufa ba mun dauki wata hnya, nan take cemun dan Allah na rakata gidan suraj bashida lfy waya yayi mata, niko nashiga tunanin tomi yasame shi mutumin dayazo jia yana nacin neman nazo, ko kusa banji tausan shi ba a raina saima tsanarsa data qaru, dandai babu yacce za'ayi naiwa Rafi'a musu gudun kada takawo wani Abu a ranta, haka muka isa gidan, suraj dake tsaye ta taga yana hango shigowar mortar Rafi'a yayi wani uban tsalle gamida naushin iska ya furta "yes, qwallona zai shiga kyakkyawar raga yau knn"
da sauri yakoma kan kujera ya kwanta tareda jan bargo ya rufe rabin jikinsa ya langwabe uwa mai ciwon gaske,
ahaka suka iso suka same shi, Rafi'a dud ta rude sai sannu takemasa basmah ko tankawa bataiba Rafi'a batama lura da hknba saifmn tmbaya ya sha magani take, anan ya sake langwabe kai yace yasha ynz abu daya yakeso, dasauri tace minenne, yace kamin ta shigo Layin daga titi akwai wasu masu saida danwake toshi yake so yaci ynx sai yasha magani, da sauri Rafi'a ta miqe tace tobari naje nasiyo ma, basmah ma ta miqe daniyyar bin baynta aisai ya qara lanqwashewa yace dear kisa qawarki ta dafamun ruwan zafi nasamu nayi wnka kamin kidawo, hakanko akayi Rafi'a taroqi basmah data daga masa hakan ita kuma ta shige motarta da sauri tabar gidan,


Allah sarki basmah batasan wnn dud shirine suraj yayi akanta ba, dan a zahiri qarya ya shirgawa Rafi'a safiyar yau kan bai lafia kuma yana mararin son ganinta dan Allah tazo da qawarta basham Dan inya gnsu tare da juna suna burgesa hakan kuma zai qara masa kuzari, da yake son da take masa yafi wnda yake mata yawa shiyasa batai tunanin mgnrsaba sonsa ya rufe mata idanu ruf bataji bata gani,ahaka ta amsa masa da to gasunan zuwa, kuma ynz ma plan ne ya hadawa Rafi'a din dan ta tafi koya samu dmr karkarewa tsakaninsa da masoyiyar rayuwar tasa data addawabawa zuciyarsa tahanata saqat a ynz, basmah na shiga kichin taga babu ashana fuska babu wasa ta fito tace" ina ashana?, Sam baiyi wani reaction knta ba da hannu ya nuna bedroom dinsa yace
" kije tana kan side mirror leta ce zaki ganta, nufar dakin nai a lkcn hakanan naji gabana na faduwa add'ua na shiga yi har na shige dakin,ganin na shige dakin da sauri suraj yature bargon jikinsa ya yasar da kayan jikinsa trouser kawai yabari yabi bayana yashigo dakin tare da sawa kofar key....
shiru basmah tai sabida kukan dayaci qarfinta jitakeyi kmr ynx abin yafaru kuka take hadda shessheqa yayinda idanun Hafiz sun kada sunyi jajir jijiyoyin hannunsa sun fito burdun burdun jikinsa har rawa yakeyi, wani silver cup dake hannunsa ya matsesa gam sai da ya lomaqe kuwa uwa takarda,
Cikin wata mahaukaciyar murya taji ya furta......"what!?"
still kasa mgn tai sabida miyau daya sartesta cikin kukan tahau tari babu kakakutawa,jiki na rawa ya zuba ruwa a dayan cup din ya miqa mata ta amsa ta fara sha yayinda gaba daya Hafiz yaji kmr rayuwar na jujjuya masa yna,
fatan sa Allah sa abinda yake tunanin bai kasantuba inko ya kasnace yai rantsuwa dud Inda suraj yake sai ya lalubo sa a duniyar nan ya amshi hukuncinsa ga hannu ko awane Barack yk kuwa, tabbas tunkn labaarin ma ya qarashe ynz kma ya tabbatar ko iya HK aka tsaya dole basmah takasa mance soja a rayuwarta komima zata furta a Kansa daidai ne dan zanba cikin aminci babu abinda yakaishi ciwo a rayuwar dan Adam ta duniya......




*By 4 writer's fasaha*👩‍👩‍👧‍👧😍


*fasaha tamu ce*😎
[7/12, 8:34 AM] Xainab Documen: *♨️♨️MATAN HAFIZ♨️♨️*!!!




*FASAHA ONLINE WRITERS*
F.o.w.


Written by.


*FOUR GORGEOUS WRITERS*


-Raheenat mahmud.


-Mmn Abduljalal.


-Xayyneb💤💤 (xexen Fasaha).


-Matan Borno.




*♨️Impacting valuable knowledge and entertainment is our concern.♨️*


Bismillahirrahmanirraheem.




*Gargad'i*


Bamu yarda a juya mana littafi ko ta wacce siga ba tare da izini ba.




34.
da qyar ya rarrashi zuciyarsa ta d'an nutsu gamida dawowa gabanta ya zauna ya na kallonta baidai ce komi ba,ammn har lokacin idanunsa jajir suke, tsagaita kukan tai tahau sakin ajiyar rai daqyar ta cigaba da cewa "sanda naga suraj ya biyoni cikin dakin na razana matuqa nayi qoqarin barin dakin ya yazare key din ya saka a aljihu, da qarfi ya riqoni jikinsa yana wata shedaniyar dariya yake cewa "haba yarinya inda nabi miki ta hanyar arziqi kinqi yadda kin nuna ke matsiyaciya ce buqatarki ki mutu cikin talauci toni wnn bai dameni ba tunda har kika yarda kika fada tarkona yau sai nayi abinda naga dama dake kamin in ankara suraj yafara kokarin ciremun hijab cikin qarfi, kokowa muka hau yi jinai ya dare hijab dina tundaga sama har kaqa ya wurgar dashi yayinda ya turani kan gadonsa kuka nake ina kiran sunan Rafi'a amman babu mai jina wanda ahaka har yai nasarar cire doguwar rigar jikina bra da pant gamida inner siket yamun saura ajiki, suraj ba qaramin rudewa yaiba dayaga surar ta nan yafara kokarin rungumoni na tashi a guje na nufi kofa ina gunjin kuka gamida dukan kofan uwa zan ballata sai kiran sunayen Allah nake Kan samun dauki ya miqe knn zai cafkoni yaji dirar mota,
ga alama Rafi'a ce ta dawo, dafe kansa yai gamida furta "oh my god mtsww wnn banzar ta batamun budget"! kamin ya ankara yajiyo muryarta a falo tana kiran sunansa dana basmah tana furta ina suka shige ta duba kitchen bataga kowaba, ganin dayai yana shirin bata 10 daya bata gyaru ba ya sashi canja salon wasan ta hnyar maido laifin kaina nan naga ya ruqoni gamida dafe bakina da hannunsa tayanda bazan iya mgn ba cikin daga murya yanda Rafi'a zata jiyo yake cewa "basmah nace miki ni bazan iyacin amanar qawarki ba na kwanta dake kmr ynda kike nacin hkn tunda kika ganni, haba ku miyasa mata bakuda amana ynzun kirasa wacce zaki ciwa amana sai qawarki data yarda dake tabaki amanarta da yardarki to gsky kin kaini kwano wlh saina fadamata kina bibiyan mijinta...yana mgnr yayi saurin jawoni jikinsa yadinga goga jikinsa ga bakina da fuskarsa ta ynda shatin janvakina zai fito a jikinsa cikin dabara yabude dakin yayinda ya yi saurin zuqunnawa kasa yana kakkare fuskarsa da tafukansa yana sake cewa
"futarmun daga daki banson ganinki a haka kuma ina mai tabbatar miki da cewar baxaki taba samun abinda kikeso ba daga gareni" basmah mamaki ya kasheta a wajen gaba daya jinta da ganinta ya dauke na wucin gadi, bata ankara ba taga Rafi'a kanta tana mata wani hargitsattsen kallo mai dauke da tsana, kamin ta yunqura saiji tai Rafi'a ta shaqota tana kuka tana kaimata duka tana "maciya amana wlh basmah banyi tunanin haka daga gareki ba kinban mamamki kowani yazomun da wnn batun bazan taba yadda ba amman babu komi kije kanki kika cuta, kullum kina yawo da hijab Ashe karuwar gida ce nake tare da ita ban sani ba, kije Ddn kanki mijina yafi qarfin iskancin ki basmah kuma Allah ya isa abotarmu datai girma takawo ya yanzun"
tana kuka tana cewa "wlh Rafi'a bani na cucekiba shine ya nemine naqi yarda ki aminta dani....
marina Rafi'a ta kumayi har saida jini ya fitomun ahanci takama cewa basmah babu sauran yadda atsakaninmu natsaneki bansan qara ganinki arayuwata dud sanda kika kara kokarin shigowa rayuwata wlh saina kasheki har lahira, haka na kwanta qasa naita kuka ina bata haquri gamida nuna mata bani bace amman inaaa idanunta sun rufe haka ta jawoni waje ta watsar gamida watsomin kaya a jikina, da sauri nazura doguwar rigata namaida abayar gyale nafita gidan ina kuka dan a sanda take jawoni waje suraj har gwalo naga yanamin, haka na iso gidan adda salma a lkcn ina kukan fitar rai dan banyi gigin tunkarar gidanmu ba a ynda nk hargitse, adda salma ta shiga tashin hankali dataji miya faru, ta rungumeni tana rarrashina tana cewa na kwatar da hankalina nafita rayuwar Rafi'a inda halinsa ne neman mata dakanta zata ganewa kanta wataran, haka na haqura na fidda Rafi'a a cikin rayuwata ko haduwa mukai wani waje tadinga aibatani knn tana yadamun zance, haka naji labarin anyi auransu da suraj sun koma Lagos da zama.
ni kuma haka nacigaba da rayuwata cikin tsanar kowane soja dan muddin zanga mutim da kakin soja zanji abin ya dawo mun sabo dan soja yamun sherrin dahar na mutu bazan mance dashiba, ana haka har nashiga ajin qarshe na secondary ban mantawa wataran ina dawowa daya makaranta adda salma ta aiko kirana uniform kawai na canja natafi ,ina zuwa wacce nasamu gidan adda salma ba qaramin mamaki naiba,Rafi'a ce nagani tayi baqi ta rame ga tsohon cikin a jikinta, tana ganina tataso da gudu ta rungumeni tana kuka take cewa na yafe Mata suraj ya cuceta shida bakinsa yake fada mata shine ya qullamun Sherri a ranar da ta samesa da karuwarsa kan gadonsu ma sunna data dawo daga anguwa, take cewa a halin da ake ciki ma ynzu yasaketa yabar garin dan Allah in yafe mata, ganin ynda tadawo abin tausayi yasa naji zuciyata ta kare nan muka rungume juna muna kuka, ahaka na yafewa Rafi'a taita gdy dazamu rabu tana sake sakin Sabon kuka gamida tsinewa suraj, kamar kada tatafi haka taji saidai babu ynda zatayi haka tatafi tabar basmah Wanda kunyar abinda tai mata kan namiji yaketa dawainiya da ita har ynz dudda ta yafe mata kuwa amman jitakeyi dud ta tsani kanta, tunda Rafi'a tatafi ban sake jin labarinta ba sai daga baya nikeji daga bakin adda salma ashe ita da iyayenta sun koma jos sun bar garin kano, kuma harta auri wani babban mutum, sai daga baya kuma bansan ina tasamu number Ammi ba take kirana mike gaisawa, ashe tasamu number ne daga wajen Yaya mus'ab da suka hade dashi jos dayaje wani d'aurin auren abokinsa to angon ashe kuma qanin mijinta ne, haka take sheda mun,harma take cewa ai suraj yadawo yana nan gida ba lfy ciwon HIV AIDS yayi masa mummunan kamu komi sai anmasa kashi da fitsari nan, kwana kadan da muka sakeyin waya take shedamun ai suraj ma ya rasu, nai masa fatan samun rahmar Allah, har nan take roqona dana yafe masa koya samu sauqi a kabarinsa ata fannun haqqina daya dauka dan Allah Bayya yace laifin tsakanin bawa da bawa har sai inshi bawan be yafe ba, haka na haqura nayafe masa domin nasan muma muna laifi Allah na yafe mana kuma Allah bason masu yafiya sai dai dud a haka da zarar naga wani soja sai suraj ya fadomun Rafi'a kuma har ynz muna gaisawa ta waya duk bayan lokaci, to wnn shine labarin da kake son ji dangane da had'ina da soja, kaima kuma ina roqonka dan Allah kayi haquri kabar rayuwata haka nan kona samun nabar tuna baya" sauqe ajiyar rai Hafiz yai gamida zama kan kujera ya rufe idanunsa yana qara godewa Allah da suraj bai haiqe mata ba daya cucesa shi ma.
bude idanunsa yai yana kallon yanda take goge qwalla,
tasowa yai ya tsugunna a gabnta yace "wnn sojan dake durqushe a gabanki basmah ba kalar sojan da kika Sani bane, wnn mai qaunarki ne tsakani da Allah tunda ya fara arba dake, burinsa kizamo uwar ya'yansa ta har abada shin basmah zakimin wnn almafarmar na kasance miji a gareki?"
yayi mgnr murysa na rawa gaba daya yakoma kalar tausayi, kallonsa takeyi takasa mgn bata ankara ba taga ya kanne mata ido daya gamida cewa "please my pleasure say something"
kasa tai da idanunta murya na rawa tace " abbu...pleas kada kicemun HK wlh zuciyata bugawa zatayi,zanbarki kiyi tunanin akai kuma snn insha Allah zan share mini hawaye, soja zai saki farinciki a rayuwar ki fiyeda ynda kk tunani nai miki alkawarin zan goge damuwar da suraj ya darsa miki a zuciya ki yarda dani basmah bazan cucekiba Nima inada qanwa inada yara bazanso hkn daga garesu ba, kiyi tunani kmr ynda nace, nabarki lfy sai munyi waya" haka yafice daga gidan yabarta cikin tunanin, Adda salma take bawa labarin yacce sukai anan adda ke cewa to tayi tunanin dan gsky tana ganin dacewar su, HK basmah ta kwanta a daran ranar cikin tunani, qarshe dai ta tashi ta dauro alwala ta shiga salla tana neman zabin Allah.


*
tun daga ranar ko kullum sai Hafiz yabugo mata wata tun tana qin dauka har ta fara dauka suyi fira sosai, da yake yanada da saurin shiga rai basmah bata ankara ba tajita lumtsum cikin soyayyar matashin balaraben soja, zata iya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login