Showing 183001 words to 184891 words out of 184891 words

Chapter 62 - DAURIN BOYE Complete Document by Safiya Abdullahi Huguma.txt

A nutse cikin nishadi da qaunar iyalin nata ta shiga cikin gidan,ba kowa a falon sanda ta shiga katafaren falon da xai sadaka da sassa daban daban na gidan,dakunan matar gidan,dakunan yaran gidan,ban dakuna,kitchen da kuma sashen baqi mata,sai sashen mai gidan,tunda bata gansu ba tasan ba zasu wuce dakin yaran ba,murmushi ta saki ta zare mayafin rolling dake kanta ta nufi kitchen din gidan don duba masu aikin gidan wadanda dattijan mata be guda biyu rak suke mata aiki,sai guda daya da batakai shekarunsu ba,a yanzu haka tasan suna can don sunsan da dawowarsu.




A mutunce suka gaisa,kai baka ce 'yan aikinta bane,ta dudduba abinda sukeyi sannan ta gaya musu abinda zasu dafawa yara da abinda zasu hada mata wanda zata shigo da kanta ta yiwa khalipha girkinsa.




Daga nan dakin yaran ta nufa,dakin farha na bude saidai labulen a sake yake,budewa tayi ta tura ta shiga don ta dubata,qarar ruwa taji a toilet hakan ya sanya ta saki murmushi tasan wanka take kuma da alamun da qyar idan ba gidan annin zai kaisu ba,ficewa tayi daga dakin ta shiga nasu fu'ad,yana zaune saman gadansu dukka yaran daure da towel,da alama wanka yayi musu,don ga kayansu nan saman gadon yana feshesu da turare,saita samu gefan gado ta zauna kawai tana kallonsu,tamkar yaya da qannenshi,tamkar abokanshi haka wani lokaci yake mu'amala dasu,shi yasa zata iya cewa sunfi sonshi fiye da ita,kusan dukkan wata hidimarsu bai gajiya idan har yana qasar ko yana tare dasu shi yakeyi musu,hakan ya sanya yanzun ma tayi tagumi kawai tana kallonsu tana jin hirarsu da dararrakunsu,a haka ya kammala shiryasu tsaf dai dai sanda farha ta shigo,tayi kyau cikin shadda bubar har qasa yellow mai red din stone work,shigen kayan dake jikinsu jawad yellow and red
"Good qanwata(wani lokaci yakan kira farha da haka),kinfi kowa yin kyau" murmushi ta saki cikin jin dadi,yana son yarinyar sosai saboda kama da take dashi sosai ita da jawad,jawad din ne ya tabe fuska
"Abbi.....abbi" yana langabe kai,yasan me yake nufi saboda haka ya shafa kansa
"Bakaga yadda kayi kyau ba my twinny(shima hakan yake kiransa wani lokacin saboda kamarsa da shi)" sunan yana yiwa jawad dadi sosai,saboda haka ya saki murmushi shima yana sakewa farha gwalo a boye,duka takai masa ya boye bayan khalipha
"Abbi....gwalo yakemin"kamo hannun jawad yayi ya dawo dashi kusa da ita ya kama hancinsa ya dan riqe
"Bana son tsokana,bata haquri" baki a tabe ya bata haquri,shi kuma ya juya ya kallo farha
"Ke kuma big sis ce.....saikinyi haquri" kaman xatayi kuka tace
"Hademin kai suke fa shida fu'ad abbi....."
"Qyalesu qanwata.....ki cewa anna ta samo miki 'yar uwa kinga kema kin huta"juyawa tayi bangaren da aysha take tana kallonsu,hannayenta ta hade waje guda,alamun roqo,dan hararar farha tayi kadan saita juya kaman zatayi kuka ta kalli khalipha ta daga kafadunta dukka biyu tana tabe bakinta tana nuna mishi alamun ayshan taqi,shima narkewa yayi ya mata alama yayi mata na abun tausayi ya girgiza kai yana duban ayshan
"maman yara....pls a taimaka mana a sake bamu baby girl" dubanshi tayi ta masa signa da ido na yadda yaran sukayi shuru suna jiran amsar ayshan,ta rasa yadda yaran keda shegen son yara,hatta da fu'ad da bai wuce shekara bakwai ba idan yaga yaro ko yarinya,sai kawai ta miqe ta fice a dakin tana murmushi qasa qasa.




Kayan jikinta ta fidda ta soma daura towel,tana tsaka da daurawar taji ya rungumota ta baya,amsar daura towel din yayi tana rungume a jikinsa yana daura mata kanshi saman kafadarta yake cewa
"Kinqi kawo mana agaji nida yarana ko?" Murmushi ta fitar kawai bata ce komai ba,yana gama daura mata ya birkitota gaba daya suna fuskantar juna,yana shaqar qamshin turaren jikinta,idanunshi cikin nata yana mata wani kallo mai tafiyar da xuciya
"Da gaske muke annah....muna son yara ba zaki agazo mana ba" hannunta ta dunqule ta dora a qirjinta tana murmushi
"Allah ya kawo abbi" dan jim yayi sannan yace
"Ameen....muje in wanke matata" cak ya dagata yana takawa a hankali tana dariya tace
"Abbi baka gajiya?,ka wanke yara ka wanke mamansu?" Murmushi ya saki
"Dama ce....ai ina da cikakken time ne,idan kuma ban muku hidima ba wa zan yiwa?" Shuru tayi tana gyada kai cike da jin dadi da hamadala ga Allah.




Sai daya sakata cikin bathtube ya juya ya fice yana cewa
"Ina zuwa" minti daya sai gashi ya dawo,tare sukayi wankansu sannan suka fito,tsaf suka shirya,shi ya bata wasu kaya wanda kalarsu daya da nashi da kuma na yaran,shadda ce irinta farha,tana ta tambayarsa me ake ina zasu baice mata komai ba yace su zuba ido zata gani.




Cikin sabuwar motarshi fara qal suka shiga suka bar gidan,ita dai tanata zuba ido,basu sauka ko ina ba sai gidan anni,sam bata gane meke faruwa ba sai da suka shiga cikin gidan,tafkeken falon annin cike yake da decoration da kayan ciye ciye da qyale qyale,matar mus'ab,basma qanwarta kuma matar haidar da yaransu gaba daya a falon,suna shiga dukka qwayayen dake falon masu dauke da kaloli suka kama,wasu rubutu suka bayyana,ta daga kai tana karantawa,sai a sannan ta gane me yake nufi,murnar cikar aurensu shekara goma sha hudu cif cif dayi ya hada musu.




Sun jima a gidan annin ana sada zumunta gami da ciye ciye da shaye shaye,dukkan familyn kana ganinsu kasan cewa cikin farinciki da walwala suke,basu tashi barin gidan ba sai bayan sallar magariba,tun kafin a soma maganar tafiyar dama su jawad suka soma nacin a barsu gidan annin,dama ya shirya hakan saboda haka yace su zauna din,har sun miqe suna mata sallama ta dakatar da khalipha
"Auren amal ya taso fa,inatason gaya maka ita da zeenatu za'a hada" dan sosa kunnenshi yayi kadan sannan yace
"Yanzu ya za'ayi anni?"
"Dukkan abinda ya dace yanda ka yiwa maryam"
"To shikenan ba damuwa.....za'ayi duk abinda ya dace in sha Allahu"
"To Allah ya taimaka ya yiwa dukiya da rayuwa albarka"
"Amin ya Allah anni,amin" da haka suka juya zasu wuce,babban yaron haidar affan dake zaune waje daya yana cin abinci khalipha ya kalla
"Affan ya jikin dai?"
"Da sauqi abbi"
"Ma sha Allah Allah ya qara lpy"
"Amin" ya amsa mishi
"Anty na asha amarci lafiya" fatima matar mus'ab ta fada qasa qasa tana dariya,hararta aysha tayi,sosai jininsu ya hadi da fatiman,tana girmamata kamar yadda basma take girmamata,hakanan itama ta dauketa a qanwa kamar yadda ta dauki basma
"Wane amarci shekaru sha hudu ba wasa ba,ko kin manta daku muka gama murna yanzu"
"Kullum jin kanku da daukar kanku kuke kamar sabbin ma'aurata,abun naku da ban birgewa yake daban sha'awa,kullum hirarku muke da abban ummu salma,wai ba za'a bamu sirrin ba muma mu hau network?" Dariya sosai ta baiwa aysha,tasha jin wadan nan maganganun daga bakin mutane da yawa,kada ma hanan taji labari,har wani lokaci ta rasa amsar basu,itadai tasan qaunarsu daga Allah ce,jigon tafiyarsu shine haquri da juriya,uwa uba kawaici da yiwa juna uzuri,soyayya ta domin Allah bata gushewa haka bata qarewa,indai dukkanku zaku yarda kuna bautar Allah ne sannan kowannenku yayi qoqarin sauke haqqin Allah na dan uwanshi daya da Allah ya dora mishi cikin girmamawa da kyautatawa,wannan sune kalaman data gayawa fatima wadandan ta jima tana yi musu dalla dalla,haqiqa sun qunshi abubuwa masu muhimmanci da dama wanda sai sun samu zama da ayshan sosai zata nemi sani da cikakken qarin bayani akai.




Ita ta soma gama shirin kwanciyarta tsaf ta haye gadon tana jiranshi,duk wani shiri ta gamashi don ta gama karantar mijinta,cikin satin da suke shirin tahowa nijeria yanata zirga zirga bai samu zama ba,tana kallonshi ya gama komai ya isketa,yana murmushi sanyata cikin jikinsa sosai yana shaqar daddadan qamshinta mai shiga rai da tsayawa a zuciya
"Uwaishahh......meye labari,naga bakinki akwai magana da alama" qanqameshi itama tayi sosai,ta zagaya hannunta a bayanshi tana murmushi
"Ina godewa Allah da baiwar da yayimin da kuma ni'imar nagartaccen miji wanda babu tamkarsa kamar kai,kaine baiwa ta farko kuma ni'ima ta farko cikin rayuwata,ina roqa maka alkhairin Allah rahamar Allah da kuma jin qan ubangiji a gareka nan duniya da gobe qiyama......my life...ina maka albishir ina dauke da juna biyu" idanu ya zaro cikin xumudi yake duban idanunta
"Are you seriouse uwaisha?" Kai ta kada
"Da gaske nake maka my babu irin wannan zolayar a tsakaninmu,bazan taba ja maka rai ba kan abinda nasan kana so"
"Allah na gode maka da dukkanin baiwa da ni'imar daka yiwa rayuwata,Allah na gode maka daka bani matar aljanna tun a duniyata,uwaishaaa,duk abinda zan gaya miki a kanki ina kin tamkar na rage darajar so da qimarki da nake gani a rayuwata"
"Ni ya cancani nayi wannan godoyar wa uba giji,farincikin daka baiwa rayuwata baya misaltuwa,ka zama silar warwarewa dukkan wani DAURIN BOYE da ya yiwa, rayuwata dabaibayi,ina sonka abbi,ina sonka sosai abban farha jawad da fu'ad"
"Da unborn ba....." Dariya ta saki tana sake shigewa jikinsa
"Zumudi dai your royal highness"
"Kinga lafina?,yara nakeson dozen biyu.....bari ma kiga ni na sake bada himma ko zasu zama biyu idan kin tashi haihuwa" dariya sosai ya bata,a ranta take cewa ko ina ake haka?,cikin aminci salama da kuma sallamawa suka shiga wata duniya mai cike da nutsuwa da aminci wa juna.




*Alhamdulillahil lazi bini'imatihi tatimmus salihat*🙏🏽




_muna miqa dumbin godiyarmu ga dubun nan masoyanmu da suka kasance damu,suka bamu goyon baya,suka kasance cikin group na zafafa biyar,haqiqa soyayya ba qarya bace,Allah ya qara zumunci ya sadamu da dukkan alkhairinsa,rabbi ya yafemana dukkan kurakurenmi cikin rubutunmu,ya hadamu a ladan amin summa amin_




*subhanakallahumma wabi hamdika,ashahadu an la'ilaha illa anta,astagfiruka wa'a tubu ilaika*🤲🏽🤲🏽


*mrs muhammad ce*👑
*mrs muhammad ce*👑
*mrs muhammad ce*👑
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*




*DAURIN BOYE*
_HUGUMA_


*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_


*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_


*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_


*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_


*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
08030811300


*ko kuma*
07067124863
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*




*DAURIN BOYE*
_HUGUMA_


*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_


*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_


*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_


*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_


*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
08030811300


*ko kuma*
07067124863
*mrs muhammad ce*👑
4
_HAFSAT RANO_


*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_


*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
08030811300


*ko kuma*
07067124863_HUGUMA_


*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_


*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_


*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_


*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_


*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
08030811300


*ko kuma*
07067124863




*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*




*DAURIN BOYE*
_HUGUMA_


*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_


*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_


*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_


*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_


*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
08030811300


*ko kuma*
07067124863


*mrs muhammad ce*👑
*mrs muhammad ce*👑


*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_


*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_


*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_


*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_


*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_


*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
08030811300


*KO KUMA*
07067124863


*DAURIN BOYE*
_HUGUMA_


*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_


*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_


*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_


*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_


*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
08030811300


*ko kuma*
07067124863
_Ya Allah ka rabamu da sharrin mutum da aljan_🙏🏽i




*mrs muhammad ce*👑


_Ya Allah,ka rabamu da sharrin mutum da aljan_🙏🏽🙏🏽


*mrs muhammad ce*👑


_Ya Allah ka rabamu da sharrin mutum da aljan_🙏🏽
********************** ⬇ **************************
********** Ai Hausa Novels ****************
*************************⬆ **********************


DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.


Visit > https://www.aihausanovels.com.ng


Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post.

Email > aihausabooks@gmail.com


******* FOLLOW US ******


Facebook: Ai Hausa Novels


Twitter: Ai Hausa Novels


Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels


WhatsApp Number: 08138873799




Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.


********************** ⬇ **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** ⬆ **************************

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login