Showing 165001 words to 168000 words out of 184891 words

Chapter 56 - DAURIN BOYE Complete Document by Safiya Abdullahi Huguma.txt

khalipha,wani abu kadan hamid yaji ya taba ranshi na kishi,sai kuma yake ganin tunda mijin 'yar uwarta ne me yiwuwa ya haqura din.




Aysha na shirin juyawa ta koma don bai bata damar gaida kowa ba cikinsu khaliphan ya damqe hannunta,cikin yaqe hamid yace
"Aysha ki...."
"Kar na sake jin sunan matata a bakinka,kasan ba kowane ke kishin matarshi ba amma ni nasan me nakeyi" ya gaya mishi magana a fakaice,cikin kwantar da kai yace
"Kayi haquri boss,ranki ya dade ki sanya mana baki mana don Allah boss yayi haquri ya daga mana qafa,kuskure ne munyi da yardar Allah ba zamu sake ba" duban khalipha tayi ranta duk a jagule,sai take jin babu dadi,daddy take tunawa,bai kamata ace diyarshi da mijinta na neman wani abu wajensu ba su gagara yi musu komai,idanu suka hada yana kurbar coffe dinshi,ya fuskanci tana son tankwa ne
"Kayi haquri don Allah ya khalipha ka daga musu qafa duk da bansan akan meye ba am......"
"Wuce ciki ina zuwa ya fada yana sakin hannunta,yanayin maganar tashi ya sanya ta juya zuwa ciki,amma duk bata ji dadi ba a ranta,sai dayaga bacewarta sannannya juya ya dubi alhj kutama
"Kar ka sake.gangancin zuwa min gida,saboda gida na iyalinane ba office bane,donsu kawai na gina,sannan nan da kwanaki uku idan baku dawomin da kudade na ba to ku saurari kiran hukuma" maganarshi ta qarshe duka ta kada hanjin hamid da alhj kutama,hukuma su da suke guje mata ta yaya zasu yarda ya jona su da ita?,haka suka miqe suka wuce gwiwa a sage,ran asma'u a dagule,bacin ran roqon da suka bata lokaci sunayi har a gaban aysha,ga rashin cikar buri,ga kuma burinta akan khalipha da bata ga wani sauyi ko ci gaba ba.




A falo ya sameta sanda ya shiga,ta daga kai tana amsa sallamarshi hadi da aje takardat hannunta,waje ya samu ya zauna kana ya kalleta sosai
"Humairaa"
"Na'am" ta amsa masa a sanyaye
"Banaso ki sake saka baki cikin lamarin da bakisan ya yake ba"
"In sha Allahu" ta fada kanta a qasa ba tare da musu ba
"Na dauki kudina na halak na basu saboda su juya su samu abinda zasu riqe kansu da iyalinsu,sai gashi daga baya suna siyo abinda zai cutatawa al'umma,ya ruguza rayuwa da future din al'ummarmu,kayan maye,kayan shaye shaye,dole na karbi kudina saboda shine kawai hanyar da zan karya su koda hukuma bata cafkesu ba,daga ranar basu da wata dama ta siye da siyarwar kayan mayen" ranta taji ya sosu,tabbas sun cancanci wannan hukuncin na khalipha
"Kayi haquri duka bansan wannan ba da bazan saka baki ba,lallai sun cancanci irin wannan hukuncin".




Cikin tashin hankali su hamid suka isa gida,inda suka zauna daga baya shida mahaifin nasa,sun tabbatar da cewa matuqar ya hadasu da hukuma babu abinda zai hana ba'a gane sune aka kama yaransu ba wajen safarar miyagun qwayoyi
"a shawarce mu siyar da gidajenmu da kadararmu matuqar muna son tsira da rayuwarmu bama son qareta a gidan kaso mu sallameshi,idan yaso sai mu sami inda zamuci bashi mu fidda yaranmu mu tsallakar da kayanmu,indai hakan ta kasance kasan zamu maida ninkin abinda muka rasa harma da riba akai"kai hamid yake gyadawa,tabbas wannan itace shawara,don su siyi kaya na maqudan kudade kuma kadan suka bayar a fita dasu,idan har suka samu saidasu to zasu iya ninka kudinsu na yanzu,don dama abinda ya sanyasu siyan kayan kenan kwadayin kudi da zasuyi.




Yana isa gida ya shaidawa asma'u ta hada iya kayan sawarta kawai zasu sauya gida ne basai ta dauki komai ba,baiyi gigin gaya mata gaskiya ba saboda tabbas yasan idan ya gaya mata inda zasu koma to ta gama zama dashi,shi kuma har yanzu yana son abarsa bai kuma shirya rabuwa da itaba ko kadan,musamman idan ya tuna abinda ya kashe kafin ya samu nasarar aurenta,duk da tana shirin rabuwa da shine amma hakan yayi mata dadi,ko banza darajarta zata qaru tadan wani lokaci,kuma khalipha koda zai aureta yasan cewa ba daga qaramin gida ta fito ba,bataso ma ya gane wahala tasha hannun hamid,tafison su tafi akan cewa kawai sonshi take yanzu shi yasa taqi hamid.




Haka kuwa ya shirya iya kayan sawarta kawai sai dan abinda ba'a rasa ba suka bar gidan,don hatta da motarta a gidan ta barta,bata tashi gane cewa ajine zai fado qasa warwas ba sai da taga gidan daya sauke ta,plate house safecontain,wanda a haka ma zasu zauna ne da uwar mijinta da qannen hamid hudu,babban falo mai dauke da dakunan bacci masu toilet,sai kitchen a falon da wani spare ban daki,toh nata dakin akwai falo kafin bedroom din,wani kallo ta watsawa hamid
"Waime kake nufi banfa fahimceka ba,ina ne nan?"
"Nan shine sabon gidanmu,nayi gwanjon wancan gidan da duka kayan cikinsa zanyi biyan bashi dasu" tuni fuskarta ta sauya saiya juya da jakarta zata fice,tareta yayi cikin hargagi
"Ina kuma zaki?"
"Gidan ubana mana,don bamuyi haka dakai ba ai,idan ka gama uzurinka ka biyoni da takardar sakina,don wallahi bazan zauna dakai ba na gama zama dakai"
"Amma dai ke ba'yar halak bace ba macen zama bace,muci dadi tare kice ba zamuci wuya tare ba,ni zaki yiwa butulci?,kudin da zan biya kusan kece silar cinyewarsu"
"Kai ka sani kuma kai ka jiyo" ta fada tana rabeshi kamar zata bankeshi ta fice,dariya ya saki bayan ta fita
"Idan kinsan wata bakisan wata ba,bari na gama cinikin gidan" kusan duk wata kadara tasu saida suka saida,yayin da suka cika mutane da cewa ai zasu bar nigeria ne shi yasa.




Sanda asma'u ta isa gida qarya da gaskiya ta zauna ta shiryawa daddy,bata damu da rashin cikakkiyar lafiya dabai da ita ba ta zauna ta tsara masa maganganu na qarya,tun baya mutum ne shi mai dattako da sanin ya kamata,saboda haka yace ta koma gidanta zuwa gobe zaizo ya samesu ita da hamid din yaji ta bakin kowa,saidai tana shiga ciki ta sanar da mommy gaskiya,ta kuwa dire tace ba inda diyarta zata koma,dakinta nada tasa aka bude aka share mata ta shige ciki,farinciki.kamar ta taka rawa,tana ganin nesa gab take da zuwa kusa,hankalinta kwance taci abinda ranta yakeso tayi kwanciyarta,sai a sannan take ganin me ya kaitama auren nan don Allaj,ashe rayuwar gidansu tafi dadi.




Qarfe takwas na daren ranar a cikin gidansu asma'u ta yiwa hamid gaban daddy,idanunshi cike fal da qwalla yake cewa daddy
"Jarrabawa ce ta fado mana,munci bashin banki mun siyi kaya suka nutse a ruwa,jirgin wancan satin da aka fada a labarai kusan rabi duka kayanmu ne,banki suka tasomu a gaba mu biya bashin da muka ci,daddy kasan sarai halinsu ba mutunci ko daga qafa,hakan ya sanya muka saida duk abinda muka mallaka nida daddy donmu rufawa kanm asiri muka biya,yau muka koma gidan da muka siya daddy bansan asma'u da gaske take ba zata zauna dani ba wai na zama talaka sai dana dawo na tadda bata gidan,ko hajiya bata yiwa sallama ba tayi ficewarta" ran daddy yayi matuqar baci,wato saboda raini daya ce ta koma gidan ma bata koma ba,waya ya dauka ya kira mummy yace ta turota,tana jin hakan tasan da walakin,saboda haka suka shirya dukkan abinda zata fada sannan ta iso falon
"Daddy....wallahi macuci ne,tun kafin sannan ya dauki dukkan kadarata ya saida min,yanzu haka bani da komai"
"Mijin naki kike kallan tsabar qwayar idanuna kike cewa macuci asma'u?" Daddy ya fada cikin bacin rai,saitayi laqwas data tuna barnar data tafka
"Ashe ke baki cikin matan dake rufawa mazajensu asiri idan babu ta samesu?,koma.meye ya saida nakin ina cewa shi ya malllaka miki shi ko?,idan kuma akwai wansa na mallaka miki shi bani na siya ba?,to na bar mishi har zuwa sanda Allah zai hore mishi ya musanya miki da wani,maza tun muna mu biyu ki tashi kibi mijinki,kiyi haquri sa samunshi da babu,wannan shine cikar mace ta gari" kuka take wiwi kamar ance ga ranar mutuwarta,hamid ya zame mata qarfen qafa kenan,bayan fitarta daddy ya dubeshi shima,yana sane da yadda yakema asma'un qanqamo saboda haka cikin hikima yamasa dan jan hankali
"Duk mutumin dake yalwatawa iyalinshi ba shakka zaka sameshi ko yaushe cikin budi shima da samu,Allah baya taba hanashi,saboda ma'aiki ya bamu labari cewa,ako da yaushe kullum ta Allah wasu mala'ikun Allah biyu na sauka,dayan yana cewa,ya Allah wanda yake ciyarwa ka ninka dukiyarshi,yayin da dayan yake cewa,ya Allah wanda yake riqe dukiyarshi baya ciyarwa ka hadashi da asara,zai iya yiwuwa sanadin quntatawa.iyali da qin yalwata musu Allah ya saukar maka da asara cikin dukiya,ya hana arziqinka ci gaba" sai yaji jikinsa yayi dam sanyi,don na wanda ke masa magana ta wannan sigar,sosai ya yiwa daddyn godiya,qimarshi ta dadu a idanunshi,wanda sanadiyyar haka yayi damarar gyarawa ko yaya ne,sa zasu tafin ya sallami asma'un da wasu kudin haka shima hamid,duk daba'a gaban asma'un ya bashi ba amma sai daya ji girman kan karba,sai kace wanda talauci ya kama?,yake gayawa.kansa,ni kuwa nace uhmm me kake ci na baka na zuba?,tukunna dai,haka ya dauketa tana bala'i da zumbure zumbure suka wuce.
*_wanan littafin na kudi ne,idan kika gani don girman Allah karki tura,ga mai buqatar siya ya tuntubi wannan number_*
56


Cikin satin kafin tafiyarsu umara wani irin sabo da shaquwa mai qarfi ya shiga tsakaninsu,qaunar khalipha babu inda bata jinta cikin jiki da jininta,bata taba sanin tayi nisa a qaunarshi ba sai yanzu,haka ta nashi fannin ya gama sallamawa gaba daya,hakanan ya gama tafiya,dukkan wasu hakaye na aysha wadanda baisan dasu ba a yanzu ya karancesu,komai nata yayi masa,komai nata yadda yakeso ne,irin matar da yake mafarki da fata gami da burin aure a yanzu ya samu,wani lokaci yakanji kanshi kamar bashi ba,ayshan ta sauya dukkan wanin tunani nasa,burinta ya zama nashi nashi ya zama nata,qiris yake jira su zama abu guda,sai yanzu yake jinsa cikin wata sabuwar duniya,jinsa yake kamar an sauyashi,kamar ba shine khalipha ba na ainihi,ta wanke masa duk wani burbushin bacin rai da yayi saura a rayuwarshi,shi yasa yake da fata da kuma burin ya zama silar wankewar duk wata damuwa tata da tayi saura a zuciyarta.




Ana ya gobe zasu tafi da daddare ya sanyata ta shirya don ya kaita suyi sallama da daddy,tsaf ta shirya tayi adonta kamar yadda ta saba ya kuma zame mata jiki dai dai misali mai sanyi ba hayaniya,shi kansa khaliphan yayi kyau cikin shaddar daya buga,ya kawo hularshi gaban goshi shigar cikakken bakano abun sai wanda ya gani 🤪.




Tare suka jero shida ita,duk wanda ya gansu a lokacin saiya juya ya sake dubansu,cikakkun masoyan da sukayi nutso duniyar soyayya suka dandana zaqinta,masoyan da tun a siffa da kama suka dace da juna zuwa ga halaye,bude mishi motar akayi saiya matsa mata ita ta shiga,shi kuma ya bude da kanshi sannan suka rufe suka tada motocin suka fice.




Itace a gaba kai tsaye zuwa sashen daddyn,saboda tun a harabar gidan mai gadin ya shaida mata mummyn na can sashen,dawowa tayi ta shaidawa khalipha saiya gyada kai
"Ki fara shiga ki sanar mishi shigowata ko?,kaman hakan yafi tsari"
"To" ta amsa mishi tana juyawa saiya bita da kallo
"Uwaishahh..." Ya kirata,ta waiwayo tana murmushi can qasan ranta,don idan da sabo ta saba,don khalipha saiya kirata sau nawa kafin taje waje musamman idan tayi kwalliya,kawai sai yace tafiyarta yakeson kalla,ko kuma kai kawonta yakeson gani,hakan kawai ya isheshi abun farinciki,saitinshi ta ranqwafo,saiya miqa hannunashi saitin bakinta
"Ciromin sweet dita,yanzu yaci ace kinsha rabi aiko?" Murmushi ta saki,cikin motarshi ta dauka,suna nan sunfi talatin,amma kawai bazai sha ba sai wadda tasha ta rage
"Kayi haquri ka barmin wannan ka dauki wata mana ya khalipha"ta fada tana langabe kai
"aifa bazaiyiwu ba,amma.idan kina so zan.barmikin,saidai da sharadi" sai yayi qasa da muryarshi yadda ita dashi ne kawai zasuji abinda yace mata,kunya ta tilastata rufe fuskarta da hannayenta tana son tashi a wajen amma ya danne mayafinta
"If kin yarda nima nafison hakan,saboda wannan bakin yafi sweet din dadi nesa ba kusa ba" da sauri ta ciro alewar daga bakinta tana miqa mishi,saiya turbune fuska kadan yana kallonta bayan ya narke kamar qaramin yaro
"Rowa ko?,tona fasa shan sweet dinma"
"Am sorry ba haka bane,yi haquri ka amsa kasha" hannu ya sanya ya karba alewar ya saka a bakinsa,sai ya lumshe ido yana cewa
"Nifa ban taba sanin haka alewar nan keda dadi ba saida kema kika soma sha,duk sanda ta taba miyan bakinki kamar yana qara mata dadi ne" dariya ta saki sosai tana ficewa a wajen,indai khalipha ne yanzu zai shagaltar da ita,tana murmushi gami da miqa godiyarta ga sarki Allah daya mata baiwa da miji irin khalipha har ta isa sashen daddy.




Asma'u dake tsaye can gefen wasu shukoki tana ganin abinda ke faruwa ta saki ajiyar zuciya,wani sashe na zuciyarta na bata qwarin gwiwar tunkarar khaliphan,komai nashi yayi mata,dukkan wani abu da take bida ta ganshi tattare da shi,matuqar zai amince mata kashe aurenta ba wani abu bane mai wahala a wajenta,bare a yanzu da take jin auren tamkar ana dorata saman qaya ne,ko qawaye yanzu ta yanke alaqa da kowa,don kada ma wani ya rabeta ya fahimci halin da take ciki,kayan da daddy ya mata order tuni sun taru sunci uwar kayan da kudin ita da qawaye tun suna wancan gidan nasu,bata iya adani ba,bata iya tattali ba,batasan ta juya biyar ta koma goma ba,ta riga ta saba tun agida saidai ta bid'a a bata,takowa ta dinga yi har zuwa inda khalipha ke zaune cikin motar tayi knocking,ya tsammaci aysha ce saiya sauke gilashin yana murmushi,idanu biyu sukayi da asma'u,take yayi gaggawar gimtse fuskarshi yana dubanta
"Ranka ya dade yau kaine a gidan namu da kanka?"
"Eh...yaron oga ne da 'yar aikin gidan sukazo gaida mai gidan" saita danyi dum saboda tasan magana dai yake gaya mata,cikin barikanci tace
"Banda dai tuna baya,abinda ya wuce ya riga daya wuce,na baka haquri amma na fuskanci har yau baka haqura ba" tsaki yaja yana shirin daga gilasanshi saboda sauraton tama sam baida amfani saita dafe cikin karyewar zuciya
"Don Allah khalipha kayi haquri,ka taimaka ka karbeni kamar yadda ka amshi aysha,ba sonta kake ba tun asali nice wadda kakeso,qaddara ita takawo faruwar komai,kai kadai kai zaka cikamin burina"
"Burinki na kudi ko?,baki da matsala waisaita kudi ne?,a duniya babu wani abu mai daraja bayan kudi?,inasom in miki gargadi na qarshe kar bakinki ya sake kuskuren cewa bana son aysha na aureta,har abada aysha itace zabina,tun kafin nasanta nake qaunarta,tin kafin nasan zatazo cikin qaddarata nakesonta,kin fahimta?"
"Kamar yaya?" Ta yiwa kanta tambayar,saidai bai tsaya bata amsa ba yadaga gilasanshi yana jan tsaki ranshi yana baci,wato a rayuwa ma ka aikatawa mutum ba dai dai ba kazo daga bisani kana jin kunyarshi ka rahama ne?,wannan kenan na nuna zuciyarka akwai ragowar danshi,idanunka basu qarasa qeqashewa ba.




Kallo daya tayi masa tasan yauma baida lpy,hankalinta ya tashi sosai,tunda yayi wancan rashin lafiyar kullum saita kirashi amma ko sau daya bai taba nuna mata yana kwance ba,amma saboda qarfin hali irin na daddy nuna mata yake ba komai,ta sanar mishi tarr da khalipha suke,yace
"maza shigo dashi mana indo,yaron kirki dan albarka".




Tana juyawa daga wajen motar sukaci karo da aysha,kallon data jefa mata shi ya sanya jikin ayshan ya bata akwai wata a qasa,me take jikin motar khalipha?,tasan halin asma'u sarai shekarun da suka diba gida daya ba wasa bane,saita gifta ayshan ba tare data ce mata komai ba,itama ganin haka yasa ta kama kanta tunda tasan ba wani abu data yi mata.




Tare suka jero har cikin parlour din,a sannan mummy na zaune tana hada magunganan daddy daya gama sha,idanunta kan khalipha sanda yake gaisheta,banbanci muraran ta ganshi,qyashi ya cika ranta,saita kasa zama tabar musu falon ta koma sashenta,wanda hakan ya basu damar hira sosai duka su ukun harda khalipha,irin hirar da zata ce ma bata tabayinta da daddy ba,har tayi mamakin dadewarsu sanda suka tashi zasu tafi suna mishi sallama kan gobe zasu wuce umara,dai dai sanda asma'u ta shigo falon,sai ta samu waje ta zauna tana jinsu,cikin farinciki daddy yayiwa ayshan murna,saboda yasa yunqurin kaita sai mummy ta sako wasu qorafe qorafe da zai sanya a dage zuwan da ita koda daddyn bai shiryawa hakan ba
"Uhmmm,ba sabanba,su umara manya,kai bawa da baka taba zuwa ba daka shiga uku" asma'u ta fada qasa qasa yadda ayshan zata jiyota,murmushi tayi sannan itama ta mayar matan ta yadda zata jita da kyau
"Mun godewa Allah da bai banbanta saudiyyan masu kudi da talakawa ba,duka dai gurin daya ne inda kaje nima can zani,Allah ya kirani babu damar dakatarwa" saita miqe ta isa gaban daddy tana masa sallama bayan fitar khalipha wanda yadan basu waje ne suyi sallama
"Allah ya qara maka lafiya daddy,bansan wanne irin abu zan saka maka dashi ba a rayuwarta,don Allah daddy ka tambayi koda abu daya ne a wajena wanda kake buqata daga gareni" murmushi ya saki
"Aysha indo har kullum kedin ta dabance,haka Allah yake tsarinsa cikin halittunsa saiya fifita wani kan wani,dukkan abinda nayi miki nayi miki ne Saboda Allah,na miki saboda a lokacin kina cancanci kuma kina da buqatar ayi mikin,abu guda daya da zan nema a gareki shine,ko bayan raina karki manta dani kici gaba da yimin addu'a"zuciyarta ce taji ta karye da kalamanshi,wani rauni ya kamata,take hawaye ya balle mata,asma'u dake zaune gefe ta tabe baki
"Kalen dangin masifa,kamar ta fimu sonshi,sai kace ita ya haifa bamu ba" ta fada a zuciyarta
"Indai xan manta dakai daddy to lallai zan manta da kaina,baka cikin jerin mutanen da zan iya mancewa dasu har numfashina yabar gangar jikina,ubangiji yayi maka jagora a dukka lamuranka duniya da lahira"
"Amin ya Allah ayshatu,idan na taba yi miki wani abu naba daidai ba tsahon zamanki a gidan nan ina neman afuwarki" kuka ta saki sosai harda sheshsheqa
"Daddy niya cancanci na nema afuwarka da zanyi tafiya,ba zaka taba laifi ba awajena daddy koda naman jikina kake yanka kullum"
"Daina kuka ayshatu,ubangiji yayi miki albarka duniya da lahira,idan kinje kimin dawafi na musamman kiyimin addu'a sosai"
"Zan maka addu'a daddy in sha Allahu fiye da yadda zan yiwa kaina"da haka sukayi sallama,haka kawai taji zuciyarta ta karye qwarai,hakanan taji kamar karta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login