Showing 144001 words to 147000 words out of 184891 words
Chapter 49 - DAURIN BOYE Complete Document by Safiya Abdullahi Huguma.txt
fita hanan tuni ta fice mmn hunaifa ce tayi saura tayi mata sallama ta fice,tana kan varender dinsu wadda zata kaita inda zata sauka daga saman ta ciro wayarta,saita samu kanta da rubuta masa saqon barka da safiya ta maida wayar tata jaka taci gaba da takawa,jefi jefi tana dan haduwa da wadanda ta sani tana tsayawa suna gaisawa,don zuwa yanzun itama ba laifi tana da mutane da abokan arizqi,da haka har ta qarasa theater din da zasuyi karatun ranar bata ji dawowar amsar saqon ba,basu bar aji ba sai uku na rana.
To hakama washegari kusan wuni sukayi,har a sannan tana zuba ido shuru ba amsa,sai ta soma tuhumar kanta kaman ta zaqe da yawa da saqon data tura mishi,a ranar ma sai wajen uku da rani ta koma daki,bandaki kawai ta wuce ta sake wanka saboda ranar da aka d'ana a ranar,doguwar rigar material mai hade da mayafinta ta zura,tana gyara kanta tana qorafi saboda yadda ya isheta da zafi,neman mai kitso kawai takeyi,'yar madaidaiciyar kwalliya tayi ta feshe jikinta sosai da turare,sosai material din yayi mata kyau saboda dacewa da yayi da kalar fatarta ya haskata qwarai,sallah la'asar ta tayar ganin lokaci ya cimmata,saboda tsabar gajiya ko yunwar ma tayi nata gu,gashi dama bata karya ba ta fita,hakanan ta dawo ta tadda dakin ba kowa da alama dukansu suma ba wadda ta dawo bare tasaka ran samun abinci,dole saita idar kafin tayi tunanin me zata dafa musu.
Hudu da rabi na yammacin motocinsa suka shigo cikin makarantar,kamar yadda suka saba duk inda motocin suka ratsa sai ido ya bisu hakance ta kasance ya riga daya saba da irin wannan har takai ma ga baikulawa zuwa yanzu,wani sakayau yake ji cikin zuciyarsa da wani nishadi kadan kadan yana ratsashi har suka samu gurin daya dace da tsaiwarsu duka suka faka,motar da yake ciki ce kadai ya bata umarnin ci gaba da tafiya har zuwa wajen da yake ganin zai iya tsaiwa,qasan wata bishiya data wadata da inuwa da iska mai sanyi.
Tana saman abun sallar bayan ta idar taji anyi knocking,izinin shigowa ta bada,daya daga cikin security nasu mata ne,suna mutunci da aysha hakanan tana ganin girman ayshan sosai wanda ita batasan dalili ba,bayan sun gaisa da ayshan take gaya mata tayi baqi,cikin mamaki take maimaita baqi kuma?,anya itace kodai hanan,murmushi tayi tace mata itace
"Gani nan" ta amsa tana miqewa gami da qissima su waye zasu zo nemanta?,mayafin doguwar rigar ta sake nadawa sosai a kanta,fuskarta da babu komai sai powder da man lebe ta fito tayi kyau,ta zira takalmi plate,zata dauki wayatta taga alewar da hanannta bata jiya da daddare saita dauketa ta jefa a bakinta waiko zata rage mata rashin dadin da bakinta ke mata saboda yunwa da takeji sannan ta fito,kafin ta sauka ta hadu da laila da zahra duka maqotansu ne suka gaisa sannan ta wuce.
Tun daga nesa rake duban motar cike fal da mamaki,tasan dai tabbas ire iren motocin khalipha kenan,saidai kuma me zaya dawo dashi bayan kwanaki biyu da dawo da ita da yayi,uwa uba ma tana zaton yau ko gobe shina zao wuce cyprus,a hankali yaci gaba da takawa tana duban motar,yayin da shi kuma dake zaune a cikin motar yake qare mata kallo ta cikin baqaqen gilasan da motar ke dashi ba tare data sani ba,tun daga sama har qasa yake kallonta yana jin wani yanayi yana ratsashi.
Qanqame hannunsa yayi waje guda,ya Allah,anya kuwa ba fara son yarinyar nan yayi ba,abinda yakeji a zuciyarsa game da ita bai taba jinsa akan wata diya mace ba,idan baso bane meye wannan?,tun shekaran jiya daya karanta saqonta da safe yaji ya kasa samun nutsuwa cikin zuciyarsa,kasa dauke idanunsa daga kanta yayi har ta qaraso dab da motar ta tsaya tana duban wani sashe daban,da alama neman baqin take.
A hankali ya sauke gilashin motar,qamshin turarensa da sanyin ac dake motar ya soma busowa zuwa waje,wanda hakam shi ya dauki hankalinta,qamshin turaren da take tunanin kamar ta sanshi,a hankali ta waiwayo zuwa sashen da take jin qamshin,idanunta suja sauka cikin nashi,faduwar gabar nan da'a koda yaushe takanji idan ta ganshi ita ta soma ziyartarta,sai kuma mamakin abinda ya kawoshi makarantar,duk ta watsar da wannan cikin sakanni ta sakar masa murmushi bisa shawarar zuciyarta,saita soma takowa a hankali zuwa bakin motar
"Sannu da zuwa" ta furta cikin nuna girmamawa,shima martanin murmushin ya maida mata yana mata nuni data zagayo cikin motar,ba musu ta zagaya daya bangaren ta shiga,saidai tabar murfin motar a bude,tuni drivern dama ya koma can wajen sa saura sukayi parking ya zauna a cikinsu.
Wani yanayi ne ya dinga ratsasu dukkansu tsahon mintuna ashirin kafin ya bude wani waje dage sit din gabanshi ya ciro laptop ya aje a tsakiyarsu
"Yau da daddare zamu tashi in sha Allah.....ga wannan kiyi amfani da ita a madadin waccar" sosai system din ta burgeta,da alama rahamalls sun iya kawo kaya masu kyau da inganci,don wannan tafi waccar tata kyau da tsada nesa ba kusa ba ko a ido ma
"Akwai abubuwa na akan waccan ina sonta na saba....."
"Shshshsh..." Ya fada yana dora yatsanshi kan lebanshi idonsa cikin nata
"Waccan haidar ne ya siya miki bana buqatar kuma ki amfani da ita,ni khalipha nine a haqqu da komai naki,so da wannan nakeso ki amfani,duk wani naki mai.muhimmanci na cire daga kai an dawo miki dashi nan,karma ki sake maganarta don already na riga na bayar da ita" hannu ta sanya ta dauka,bai cancanci musu ba sam sannan tace
"Na gode,Allah ya saka da alkhairi ya qara budi"
"Ameen" ya amsa yana lumshe idanunsa
"Ban amince kuma naga hoton kowa ba akai" saita daga kai tana dubanshi,sam ta mace hoton haidar ne akan screen din waccar,to me kenan?
"Uhmm,zan wuce me zan samu?" Ya fada idanunsa cikin nata,
"Ba komai" ta fada tana murmushi
"Shikenan" ya fada yana daga kafada duk da bai daina kallonta ba,saita motsa kadan ta fidda qafafunta waje sannan tace
"Allah ya tsare hanya ya bada sa'a" sam kasa amsa mata yayi ba,bayason ta wuce,bayason ta tafi,hannunta ya riqo cikin xafin nama da hanzari ganin da gaske ficewar zatayi,sannan ya miqa hannunshi ya rufe murfin motar,fuskarta ya sanya a cikin tafin hannunshi ya hada tsinin hancinsa da nata,cikin sakanni kadan ya kashe mata jiki gaba daya,a hankali cikin muryar dako cikin motar kake baka isa kaji me yake cewa ba yace da ita
"Ba haka nake buqata ba,sallama nakeso irinta masoya,so nake naji ya suke ji duk lokacin da rabuwa tazo....." Idanunta ta runtse gam,wani nauyi na sauka cikin zuciyarta da gangar jikinta ma gaba daya,gaba daya ya gama saukar mata da kasala,bugun qirjinta ya dadu wanda yasanya numfashinta shima sake gudu wajen fita,qamshin lemon dake fitowa daga bakinsa yana ratsa hancinta wanda ya gauraya da turarensa,tattausan lebanta dake gogar nashi ya sanyashi kama leban nata da haqoransa yadan ciza kadan ta yadd ba zata ji zafi ba.
Knocking din qofar da akayi shi ya sanyashi sakin fuskar tata da yayiwa ruqon tsauri,kowannensu ya janye a hankali,ta bangaren aysha ake knocing din saboda haka ta juya ta dannan madannin sauke glass,gilasan suka sauka qasa,hanan ce a tsaye rungume da litattafanta
"Ina can ina bulayin nemanki,keys din daki zaki bani ban fita da nawa ba mmn hunaifa na bari a dakin"
"Ohkey" ta fada cikin sanyi tana yunqurin lalubo maqullin da tuni ya subuce qasan kujerun motar,dagowa tayi ta miqa mata idanun hanan din na kanta,kana kallon fuskarta kasan dariya take hadiyewa,kallon na kamaki ba yadda zakuyi takewa ayshan itama ta fuskanci me take nufi,saboda haka saita waiwaya sashen da khalipha ke zaune cikin sanyi tace
"Meet hanan,my roommate" cikin fara'a hanan din ta gaida khaliphan,shima a sake ya amsa mata yana tambayarta karatu tace komai lafiya
"Ranka ya dade aikinka na kyau fa,saidai a dan sassauta mata karta gagara hada masters din tata" da sauri ayshan ta kalli hanan dake dariya,maganar tata saita baiwa khalipha dariya,can cikin ranshi kuma yana mamaki kan lafazin hanan din,idanu ya kafe aysha dashi
"Wai haka humairaaah?"kunya ta mata dabaibayi sosai,tana kada kai kamar zatayi kuka tace
"Tsokana ce kawai takeyi,batasan waye kai a wajena bane" dariya sukayi hanan din da khalipha,sannan tayi sallama dasu ta wuce
"Waye ni a wajenki?" Ya jefo mata tambayar data rasa amsar daya dace ta bashi
"Matsayin daka dade da baiwa kanka"
"A yanzun idan na sauya matsayin zuwa mataki na gaba yayi dai dai?" Shuru tayi tana nazarin maganarsa,kalma ce mai harshen damo dake da buqatar nazari,hannunta taji ya kama ya sumbata na tsahon sakan goma sannan ya sake mata hannu
"Zan wuce,ki kula da kanki" sai a sannan itama taji wani iri babu dadi,addu'a tayi masa sosai sannan ta zira qafarta ta fito daga motar,harta rufe idanunsu nakan nakan na juna duk da kunyar abinda ya mata dazu dake addabarta
"Baki bani komai ba da zan dinga tunawa dashi" sadda kanta tayi tana murmushi qasan ranta,tome yakeso ta bashi?" Bata gama wannan tunanin ba ta jiyo muryarshi mai taushi
"Allah ya bamu alkhairi,saina dawo"
"Ameen" ta furta,saita kasa tafiya taci gaba da tsaiwa a wajen har ya ryfe gilasan motar ta daga tabar wajen,shi dinma ta cikin mirrow yaci gaba da kallonta har suka bacewa ganin juna.
*_Mutane masu son zuciya ma sunada rana a gareka, koba komai zasu tara maka ladansu ka karɓa a ranar da kowa ke fafutukar neman ƙari a littafin ayyukansa. Dan haka karkai baƙin ciki da zaluncin azzalumi, koda ɓatanci yay maka bisa son zuciya ribace a gareka, shi ko bai gane faɗuwace a garesa sai randa babu wata ƙofa ko damar da zai roƙi gafarar ka._*
49
Tana tsaye tamkar jiran shigowar ayshan take,koda yake hakanne ma,dafeta tayi tana dan ihu,wanda hakan ya sanya zubewarsu saman gadon maman hunaifa,qoqarin qwace kanta aysha take
"Hanan....hanan what r u doing ne?,pls" sai data gama ihunta sannan ta saki qaramar dariya
"Wallahi banga laifinki ba,wannan halitta haka aysha dole ki susuce ki sauya lokaci daya,wallahi kunyi masiiiiifar dacewa,hadin ya hadu wallahi" dubanta aysha take tana hadiye dariyarta,yayin da a zahiri tadan hade gira
"Wai....akanme kike magana ne?dawa muka dace?"
"Ban sani ba 'yar gaba da rainin hankali,kinsan Allah gulmarku kawai ke tashi a varender dana hau,ina can nemanki wajajen department dinku ina zuwa nan nace ke nake nema aka nunan inda kike,kaiiii aysha ashe ba banza ba kike figawa maza dawa ashe ke kin gama gwangwajewa abinki,kai ma sha Allah wallahi d'an d'ashi,dole mmn hunaifa tasha wannan labarin" ta lura idan bada gaske tayi ba hanan zata mata kwaroroto,kusan halinsu daya da aliya,banbancin dan kadan ne
"Wai da kiketa wannan surutun ce miki nayi saurayina ne?,toki rage zumudi wanda dai kika gani yaya na ne,kuma ga abinda yazo kawomin nan" ta fada tana nuna laptop din data aje kan dan teburin da take dora littafanta tayi karatu,dariya sosai hanan ta saki bayan fa kalli system din harda tafa hannu sannan ta samu gefan ayshan ta zauna,hannunta ta dora kan kafadarta
"A qalla na doshi shekara takwas ko bakwai ina soyayya,kin manta wace ce hanan?,to bari kiji wannan tatsuniyar taki bata samu wajen shiga ba,ko wanda ya fara soyayya yau kallo daya zai muku yasan cewa ba qaramin narkewa kukayi cikin son junanku ba,idan ma ba saurayinki bane bari na gaya miki ku binciki kanku,don ba shakka dukkaninku kuna yiwa junanku soyayya mai zafi,idanunku kawai sun isa su gayawa koma waye haka,saidai wataqila kun afka son junanku ba tare dakun sani ba,ko kuna daga cikin masu qaryata cewa sun fara son waninsu" idanu aysha kawai tasa tana kallon hanan gami da yunqurin faffasa maganar cikin kwanyarta,wanne ne a ciki?,wanne ne ba wanne ba?.
"Wa akewa irin wannan sharhin haka?" Mmn hunaifa dake shigowa ta fada bayan ta zauna saman gadon aysha
"Kinzo a dai dai,wallahi yarinyar nan ba banza ba taqi ayi mata maganar kowa,mmn hunaifa kinga guy dinta kuwa?,hasbunallahu wa ni'imal wakil,wannan shi ake kira da komai yaji,kinga wata iriyar soyayya da ake bugawa mai sanyi" ai aysha batasan ta durmawa hanan dundu ba tana fadin
"Zubaida....mmn hunaifa karki yarda da sharrinta
" a'ah nima fa dana shigo daga waje na danji ana qushin qushin,ko maganar ce?"
"Itace daiiii mamn hunaifa,hostel din nan duka ya dauka" ganin yadda hanan ke faman zubawa mmn hunaifa lbr kawai saita barta ta miqe ta cire rolling din kanta ta daurashi a matsayin dan kwali ta hau dora musu girki,don shaf ta mance ma tana jin yunwa sai yanzu,tana aikin amma tunanin maganganun hanan ke mata yawo a ka,da gaske idanunsu na bayyana soyayya kamar yadda hanan din tace?,to wai shin yama soyayyar take bare har ta ganeta,kalma daya da bata santa ba a rayuwarta wato soyayya.
A bun mamaki a daren saita kasa barci,tayita juyi tana tuna zuwan khalipha a yammacin dazu,duk wani motsai daya faru tsakaninsu sai data tunashi kar a kanta,miqewa tayi daga kwancen ta janyo syatem din daya kawo mata ta kunnata.
Hotonta ne ya mamaye screen din,wanda batasan inda ya samu hoton ba,hakanan ba zata iya tuna sanda aka dauki hoton ba,a nutse ta dinga shiga ma'ajiyar adana hotuna,hotunanshi zallah a ciki wadanda yayi masifar kyau kamar a kirashi ya amsa,ya rabata da duk wani hoto na haidar sai nashi zalla me kenan?,
"Kishi" zuciyarta ta bata amsa,kanta ta kada tana qaryata hasashen zuciyar taya,kishi ana yinsa ne ga abinda akeso ai,yaushe khalipha yace yana sonta ma da har zata zaci ganin kishi a qwayar idanunsa?,amma sone kawai yake haufar da kishi aiko?,zuciyarta ta jeho mata tambayar,saita ture gaba daya tunanin gefe guda.
Wajen videos ta shiga,films ne na soyayya sunfi talatin,kuma duka na jaruman nan da ranar ya tayata kallon fim din ta gudu ta barshi,murmushi ta saki ita daya tana rufe fuskarta kamar yana ganinta,wato yana sane kenan,shi da yace aure takeso?,yace kuma me take gani haka,wani murmushin ya sake subuce mata ba tare data shirya ba,tuna maganarshi ta dazun tayi,hakan ya sanyata zama dirshan ta jawo wayarta,a qalla ta kusa kashe minti talatin tana rubuta saqon tana gogewa,inda daga bisani tayi bismillah kawai ta tura,saikuma tayi tsam tana tuna abinda ta tura din,kamar ta wuce makadi da rawa,tunda ya riga daya shiga haka ta haqura ta koma ta kwanta tana kunna daya daga cikin fina finan ta soma kalla.
Gurine da sau tari yakan je ya zauna kawai idan zaiyi karatu ko zai duba wasu mihimman abubuwa da suka shafi kamfaninsu wanda ya zama dole ya duba din,a yau dai babu ko daya daga ciki,yana zaune ne kawai yana shan ni'imar da Allah ya yiwa wajen,bai jima da gama waya da anni ba a nan ya jiyo kamar hayaniya,ta gaya mishi su amal ne ke rigima da zeenart,dama dazun nan ta gama yi musu shari'a,sosai ranshi ya baci ya dinga fada yana fadin basu isa su hanawa uwarshi zama lafiya ba,don haka kowacce ta kama gabanta,dama shi sun isheshi baisan ubanme suke zaune gidan sukeyi ba,annin ce ta dakatar dashi,tace suma duk abinda zayayi zai zama ne saboda Allah ya fifitasu a kansu,bayan basu suka tsamo kansu daga halin da suke ciki ba ganin dama ce ta ubangiji da baiwarsa,hakan ya haqura,amma yayi waya da haidar ya gaya mishi lallai kome ake ciki zaman kowa ya saitu a gidan,amma karya bari anni ta sani saboda zata hana ruwa gudu ne,ya sani haidar din kome zaiyi tamkar yana nan ne,da wannan tunanin da baci da ranshi yayi yaji shigowar saqon,da fari banza yayi dashi sai wani bari na zuciyarshi ya dinga azalzalarsa da ya duba din,fuska a tamke ta soma danna wayar sai gashi ya buge da sakin sassanyar murmushi,gyara zamanshi yayi sosai ya soma maida mata reply.
Tsaida kallon tayi da taji shigowar saqo cikin mamakin ganin number khalipha ce,tana duba saqon tana murmushi,wani abu ya dinga tsumata,saita biye mishi ta sake maida masa amsa,wasa wasa sai da suka dauki mintuna goma suna musayar saqonni,wanda sai daga baya aysha ta dinga duba saqonnin tana zaro ido,ya akayi ta rubuta wannan kalaman?,sai taji kamar yana gabanta saboda kunyar data kamata.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Suna kan hanyar dawowa daga daga aji ita da hanan da suka kammala daukan karatu kisan lokaci daya wayarta ta dauki kida,tana dubawa taga mero ce,cikin zumudi ta daga wayar ta kara a kunneta,gaisawa sukayi daga bisani take shaida mata ta haihu jibi suna,cikin bata rai aysha tace
"Yanzu qawa ki haihu kamarni sai yau kwana biyar nake ji?,ai shikenan babu komai na gode
"Don Allah indo kiyi haquri,wallahi wayarce ta samu matsala saida habu ya sauyamin wata yanzu yanzu aka kawota kena fara kira wallahi" sai a sannan aysha ta saki ranta,hira suka dan taba daga bisani tayi mata alqawarin halartar sunan.
Sai data zo kwanciya ta tura masa masa saqo kamar yadda ta saba koda yaushe ya kuma zame mata jiki,ta gaya mishi zuwa takai din,tana kwance idanunta a lumshe tana tsammanin jin reply kamar yadda ta saba sai taji shuru,duka sai taji yau babu dadi wani banbarakwai,tun tana sauraro har bacci ya dauketa.
Qarfe uku na yammacin washegari suna tsaka da kammala shirinsu na tafiya takai,hanan ita zata mata rakiya wannan karon,ana ya gobe suna ta shirya zasu daman ta dawo ranar sunan saboda washegari tara na safe zasuyi presentation,saidai gaba daya hankalinta kacokam yana kan wayarta,tun jiya data tura mishi saqo har yau bata ji daga gareshi ba,sai taji gaba daya bata dokin tafiyar.
Tana riqe da powder tana shafawa wayar tata ta dauki ruri,da sauri ta aje powder din ta rarumi wayar tana duba mai kiran,khalipha ne kamar yadda tasa capital K a sunanshi,cikin hanzari ta daga ta kara a kunnenta tana aje boyayyar ajiyar zuciya,saidai tuni ya jita,sallama yayi mata sai a sannan ta tuna cewa batayi masa sallama ba,a kunyace ta