Showing 132001 words to 135000 words out of 184891 words
Chapter 45 - DAURIN BOYE Complete Document by Safiya Abdullahi Huguma.txt
ya faru,suna cin albarkacin anni data roqeshi kada ya yarda ko sau daya ya biyesu ayi wani abu mara dadi,dalilin barin gidan ya fara samo asali ne daga sanda jama'ar gidan haj binta da ibrahim suka soma qorafin ana musu dauke dauke,kusan kullum Allah ne dakullum sai anyi cigiyar an nemi abu an rasa.
Rabon za'ayi ranar da khalipha ya shiga dakin dakin ibrahim yi masa shara,khalipha tun asali mutum me maison ado da qamshi,kwalliya na burgeshi qwarai,dalili daya sanya koya ya samu kudi bai rasa siyiwa hajar abun kwalliya na mata koda jambaki ne kuwa dan naira hamsin,koda shi bai saka ba ita ta saka,to ibrahim ba laifi akwai qwalisa da ado,duk sanda yayi kwalliya khalioha kan kalleshi,yana tuna sanda mahaifinsu keda rai,duk juma'ar duniya sababbin kaya suke sakawa,wani lokacima anko suke da babanshi,akwai wani turare da ibrahim din ke amfani dashi,kalipha na matuqar son qamshin turaren,ranar yaje yi masa shara saiya dauka ya fesa sau daya a jikinsa,yana shirin ajewa ibrahim ya shigo dakin,nan ya soma cuccusawa ma khalipha ashar yana fadin ashe shine barawon gidansu,ya gaya mishi don ubanshi mai ya dauka
"Babu abinda na dauka maka sai turare dana fesa,wanda shima nasan nayi kuskure kuma kayi haquri don Allah" khaliphan ya fada tunda yasan laifinsa ne,kafewa ibrahim yayi yace bai yarda ba sai khalipha ya tube ya dubashi
"Bazqiyiwu ba tunda na rantse maka ban dauka ba ban dauka ba,dana dauka din kai tsaye zan gaya maka na dauka,don nafi tsorin mahaliccina fiye dakai"
"Ni kake gayawa ba tsorona kake ba,kayimin sata ka dinga gayamin baka tsoro na?" Saifa ibrahim ya rufe khalipha da duka,a sannan ya girmeshi hakanan khaliphan ya rame ibrahim ya fushi gabaran jiki,hakan shi ya baiwa ubrahim damar yiwa khalipha duka bana wasa ba,ya gwara kanshi da bango sosai wanda yayi sanadiyyar sunewarshi,bai farfado ba sai a asibiti,tunda ya samu sauqi aka sallemshi ya koma gida,duk sanda ya tuno da abin yana qona mishi rai,sharrin sata abu ne ba qarami ba,amma anni tace ya barsu da Allah,ta kuma yi masa fadan fesa masa turaren da yayi,ta gaya masa shine silar komai,dabai fesa ba da duk hakan bata faru ba,wannan shine silar abinda ya gadarwa khalipha cuwon kai mai tsanani da yake shan wuya duk sanda ya tasarmasa har kwanan gobe.
sanda abun ya faru saura kwana biyu a biyashi albashinsa,kwana biyu na cika saiga kawu idris da albashin khaliphan,sunyi mamakin ganinshi don sunsan bata yadda za'ayi ya biyoshi da albashinsa,ilai kuwa bayan ya miqa albashin sai ya sassauta murya cikin murmushi,a lokacin khalipha na dakin annin yana kwance don bai gama murmurewa ba
"Wata magana nazo miki da ita mai muhimmanci aisha,wadda idan har kika amince da ita ni dake gaba daya kowa zai amfana"
"Inajinka,Allah yasa alkhairi" ta fada tana dubanshi a darare don ita har yanzu bata amince da zuwanshi ba
"Nace ba....me zai hana muyi aure ni dake,idan yaso saiki kwaso 'ya'yanki naci gaba da kuka dasu,'ya'yan sa'idu ai 'ya'yana ne" a zabure khalipha dake kwance ya miqe,cikin azama ya tashi tsaye ya fito falon
"Tashi ka fitar mana daga gida" kallonshi idris yayi
"Meyw haka khalipha?"
"Nace tashi ka fitar mana daga gida maciyin amana kawai,Allah ya tsare anni da aurenka har abada wallahi tafi qarfinka"
"Me kake haka khalipha?" Anni ta fada tana qoqarin tsawatar masa gajin yadda yataso haiqan kaman zai daki kawu idris,sam bai saurari zancan anni ba bai saurarawa kawu idris ba sai daya danganashi da gate din gidan sannan ya dawo,idanunshi kamar garwashin wuta haka suk a kada sukayi jajur,haka kawai ya kasa zaune ya kasa tsaye saboda bacin rai ya dinga kai kawo
"Anni,duk randa mutumin nan ya sake dawowa gidan nan saina nakasta shi" haka ya dinga fada saida annin ta tsawatar masa
"ka shiga hankalinka mana khalipha,ni din bansan me nake ba koko yaya?,idris ne fa na sanshi na kuma san halinshi da manufofinsa kaf tun kafin a haifeka" da qyar anni ta iya control dinsa,haka yake bai iya fushi ba,ya kuma qaro zafin zuciya sanadiyyar tsangwama da rashin kirki da azabar da suka dinga gwada masa da 'yan uwanshi.
Tun daga ranar bai sake waiwayarsu ba kamar sauran,su kadai suke rayuwarsu,su kadai suke fadi tashinsu,su kade suke cin wahalarsu,wataran subsamu wataran suyi kwana biyu uku basu samu ba.
Wata biyu da zuwan kawu idris da wannan maganar hajar ta soma wani irin ciwon ciki mai tsanani,idan ta fara wani lokaci har suma take,anyi gwaje gwaje ya tabbatar da appendixs ne kuma saidai ayi aiki,kasancewar babu babu kuma mai basu haka suka haqura suka zubawa sarautar Allah ido,haka hajar ta dinga fama,yau lafiya gobe babu,idan ciwon ya tasar mata kamar ba zata kai ba,ba wanda yasan halin da suke ciki ballantana ya nuna kulawarshi.
Idan ajali yayi kira ko babu ciwo aje,safiyar wata laraba ciwon ya tasarwa hajar sosai,a lokacin khalipha ya fita wajen nema musu abinda zasuci,don wayewar garin basu tashi da qwayar hatsi da zasu iya sanyawa a bakinsu ba,haidar ne ya dinga yawon nemanshi duk wajen da yasan za'a sameshi,da qyar ya samoshi wajen wani fili da ake kwashe bolar ciki za'a soma gini,khalipha na cikin masu kwashe sharar,a gigice ya tafi wajen ogan nasu ya masa bayanin halin da ake ciki,ya lissafa iya kai nawa khaliphan yayi aka biyashi,ya tausaya masa har qari yayi masa akai suka taho gida tare da haidar,kafin su qarasa tuni hajar ta galabaita ta fita hayyacinta,abun ya tsoratar da khalipha sosai don bata taba irin haka ba duk ciwon da take,nan suka kwasheta sai asibiti,a canma dan abunuwan da suka saya gwaje gwaje da sauransu duk sun cinye dan kudin daya riqo,duk da cewa asibitin gwamnati ne amma sunan a baki ne,kusan komai talaka shike ma kansa,duk abubuwan daya kamata gwamantin tayi ta saki.
Daga bisani likitan ya shaida musu cewa tilas a gaggauta yi mata aiki nan da awa ashirin da hudu,idan ba haka ba komai zai iya faruwa da ita.
Fadin irin tashin hankalin ma da suka shiga bata baki ne,hankalin khalipha ya kuma tashi sanda ya koma dakin ya iske hajar riqe da cikinta tana faman kuka annin na riqeta,idanunta kan khalipha,tsananin tashin hankali yasa ya kasa qarasowa,yana jin sautin kukanta a kunnensa ya fice daga asibitin,duk inda ya samu kawai jefa qafarsa yake,tunani yake ina zai samu kudin nan da awa goma sha?,abinda bai taba ba a ranar shi yayi wato roqo,saidai ba wani abun azo a samu ba ya samu har dare ya soma tsalawa,kawai sai ya siyi abinda su anni dasu haidar zasu iyaci ya koma asibitin,ai kuwa suna zaune waje daya yunwa ta addabi kowa,hajar kuwa barci ya kwasheta,haka ya bude musu suka rufu suka cinye tas,yacewa anni zai wuce gida gobe zai dawo da kudin da yardar Allah,dubanshi kawai take tana kallonshi,har yau khalipha da sauranshi game da halayyar mutanen duniya,wadanda basusan taimako ba,wadanda basu san kowa ba sai kansu,basu damu da damuwar kowa ba sai tasu,son kawunanmu yayi mana yawa,idan dai kai daya zaka rayu to ba matsalarka bace kowa ma ya mutu,idan dai kai daya zaka tsira ba matsalarka bace kowa ya cutu,har kullum kowa burinsa yaga komai nashi yana tafiya masa daidai ba ruwanka da halin da dan uwanka zai shiga sanadiyyar wani abu daka aikata masa,bata sace masa gwiwa ba,ta bishi da fatan alkhairi,ya fice zuciyarsa cike fal da tausayin mahaifiyarsa kamar yadda itama tata zuciyar cike da tausayinta da qannenshi,a qafa ya daba har gida ya shige ciki ya kwanta,saidai cikin wannan daren duk iya satar bacci bai samu nasarar daukeshi ba,duk juyin da zaiyi anni da hajar dasu haidar be cikin ranshi,cikin daren ya yankewa kanshi dole ya dangana da wajen kawun nan nashi,yana kyautata zaton a wannan karon zasu dubi halin da hajar din ke ciki su tausaya musu.
Asubar fari bayan ya idar da sallah daga masallaci ya zarce gidan kawu hamza,duk da halin da suke ciki bai taba yarda sallah asuba ta kubce masa cikin jam'i ba,sanda ya ganshi fada ya soma balbaleshi da shi kafin ya saurara yaji abinda ke tafe dashi,sai daya gama tsaf sannan yace dashi
"To nidai yanzu bani da abinda zan baku ko qwandala kuwa,saboda nima kudin makarantar yara da zan biya nake nema,tunda yanzu babu maiyi mana dole na tashi ka nema da kaina" hakanan ya fito jiki ba qwari ya tunkari gidan kawu munzali,kawu habibu,kawu saminu
"Tabdi,amma bansan baka da hankali ba yaro sai yau,yanzu wake neman kudi wajen jama'a kowa tashi ta isheshi?"
"Ni ta kayqn sallar yara na nake,dama mahaifinka kedan tabukawa yanzu ko babu shi kaga dole mu tsaya mu share musu hawaye a madadinsa"
"Motar maryam ta lalace wata takeso na sauya mata,saidai ka jira nan da qarshen wani watan ina bin wani maqofcina akasuwa bashi ya yimin alqawarin zai bani,sai kazo ko rabi ne na bayar"
"Tashi ka bani waje,kun gama diga mana rashin mutunci wato sai yanxu kuka san damu" wannan shine ire iren kalaman daya gamu dasu a dukka gidajen,gida na qarshe daya je shine gidan kawu idris,bai taba tunanin zuwan ba amma zuciyarshi ta bashi qwarin gwiwar zuwan.
A falon gidan ya taddashi zaune shida ibrahim suna lissafin kudi,yana ganinsa ya miqe tsaye cikin hayagaga da hargowa
"Ubanka kazo yimin cikin gida?"kai ya girgixa masa
"ohhhh,uwar kace kenan ta sake turoka kazo ka qarashe cin mutuncin da baka gama yimin ba kenan ko?"
"Ba haka bane kawu kayi haquri,hajar ce a asibiti bata da lafiya sosai za'a yi mata aiki,to kudin aikin da suka fada din bamu dasu....."
"Shine kazo gamai indararo mai aikin banza ko,Allah yana bani ina watsarwa" ya fada yana ware hannayensa kamar mai shirin yin daquwa
"A'ah kawu,ka taimaka wallahi tana matuqar buqatar taimako tana jin jiki sosai kawu,ko bashi ne ka bani nizan biyaka daga biya in sha Allahu"
"Kaga kudaden nan?" Ya fada yana nuna daurin kudin dake gabanshi,har zuciyar khalipha ta soma sanyi ya gyada kai,sai ta jefeshi da mummunan furucin da har yau idan ya tuna sai yaji tsanarsa
"To ko ubanka dake kabari ne zai fito bai isa in bashi kudin nan ba,koshi yayi kadan ballantana kai,hajar kuwa tama mutu mana asara ta ce?,kai gwara ta mutu ma mun rage iri mun huta aurarwa" daga jajayen idanun sa khalipha yayi ya zubawa kawu su,wanda shi kansa sai daya tsorata da sauyawar da yayi lokaci daya,ji yayi idan ya qara minti daya a gidan zai iya mutuwa,ji yayi kamar kawun ya yuwa hajar baki mutuwar zatayi,tamkar iskar guguwa ya miqe ya fice wanda badan ibrahim yayi saurin matsawa ba tafiyar yaaji zaiyi dashi.
Yana fita yaci karo da motar kawun sanuwa wadda cikin gadonsu da suka wawashe suka kasafta ya siya,idamunshi suka sauka kan wani qaton dutse dake girke a gefe,baiyi wata wata ba ya cirashi yabi dukka gilasan motar ya fashesu tas ya kuma lallotseta ya qara gaba.
Asibitin kawai ya nufa don yaga halin da suke ciki,tun daga harabar asibitin yaji haka kawai gabanshi ya yanke ya fadi,qafafunsa sunyi sanyi,haka ya dinga takawa har dakin da aka kwantar da hajar.
Anni na tsugune gaban wani abu dake shimfide a gabansu,gefa haidar da mus'ab kowanne cikinsu kuka yake banda anni data zubawa abin ido,take qwaqwalwarsa ta gaya masa hajar ce ta tafi,haka ya dinga takowa kamar gunki yayi tsaye a kansu anni,sai a sannan ta lura da zuwanshi
"Yauwa khalipha,kamata mu tafi,hajar ta tafi ta huta,kaga hadonma har an dora wani a kai" anni ta fada tana miqewa tsaye,kallo daya yayi mata ya fuskanci ba cikin hayyacinta itama take ba,duk da bala'in da yayi masa yawa haka ya dinga kiran sunan Allah ya sami nutsuwar daya juya ya samo abun hawa suka sanya gawar hajar badon yana da kudin da zai biya mai taxin ba,cikinsu ba wanda yake cewa da danuwansa wani abu sai haidar da mus'ab dake faman kuka,annin ce ke yawan ce musu
"Ku daina kuka,hajar hutawa tayi", bayan mai motar ya saukesu ya buqaci kudinsa,sai a sannan ya tuna baida ko sisi
"kayi haquri bamu da abun biyanka,kayi haquri nayi kuskure daban gaya maka ba tun wuri"
"Babu komai....Allah ya jiqan rai yasa ya huta"daga kai khalipha yayi ya dubeshi,don baizaci jin haka daga bakinsa ba,ya shirya yaji jafa'i da alkaba'i daga bakinsa kaman yadda sauran mutane suke,cikin mamaki ya amsa ya dinga jera masa godiya,dama har yanzu akwai sauran mutane masu imani a duniya?,akwai mutane masu tausayi?
('Yan uwa ku duba halin da khalipha suke ciki,wallahi azim acikin al'ummarmu akwai mutane kwatankwacinsu sunfi dubu,wallahi wallahi muji tsoron Allah,mu tallafi marayu,muji tsoron haduwarmu da ubangiji,muji tsoro randa zamu tashi Allah ya tambayemu ya kayi da haqqin wane maqocinka ko makusancinka mu rasa amsar da zamu bawa ubangijinmu).
*DAURIN BOYE*
45
Haka khalipha yaje masallacin unguwar ya fada,aka hadu aka yiwa hajar sallah aka kaita gidanta na gaskiya,sai a sannan anni tayi kuka,irin kukan da tunda suka shiga wannan halin bata taba yarda tayi gaban yaranta ba saboda karta karya musu gwiwa,daya daga cikin aninda ya hadarwa khalipha kenan ciwon kanshi ya tashi,yayi jinya sosai,Allah ya taqaita musu wahala ya warke ba tare da an dauki dogon lokaci ba.
A wannan karon anni bata yarda ta sake zama haka ba,domin tana tsoron faruwar abinda ya faru a baya,sana'a ta kama wanda duka dai bai wuce wankau ba,abinka da bata saba duk,sanda tayin sai hannunta sun kumbura suyita ciwo,amma gobe haka zata sake yin wani,tun suna kumbura har suka daina,daga bisani ta samu aikatau na shara da wanke wanke a wani gida dake bayansu,aikine mai shegen yawa,duk randa taje ta dawo zaiyi wuya bata kwana sa zazzabi ba sabida yawan aikin da take tilliqa,gashi dama tunda hajar ta rasu bata qara lafiya ba,khalipha shi ya hanata zuwa saboda yanayin lafiyarta,haka ta haqura taci gaba da wankau da sauran sana'o'in hannu.
To tunda hajar ta mutu anni batayi cikakkiyar lafiya ba,sannu sannu sai ciwo itama ya kwantar da ita,hankalin khalipha yayi mugun tashi tamkar zai zauce,yana ganin kamar zasu rasa annin ne kamar yadda suka rasa hajar dinsu,suka shiga sintirin asibiti duk da basu dako sisi,hawan jini ne yayi mata mummunan kamu ya haifar mata da matsalar qoda,wanda tana buqatar ayi mata aiki,wanda indai akayi mata akan lokaci shikenan zata warke sumul kamar bata taba yiba,amma matuqar aka jinkirta tofa la shakka ciwon zai girmama ne ya zame mata wani abu na daban.
Shawara ta qarshe da khalipha ya yankewa kanshi shine su saida gidan da suke ciki abiya maqudan kudaden aikin,tunda yana da yaqinin idan ba hakan sukayi ba saidai annin ta mutu ta barsu kamar yadda hajar tayi.
Akan hanyarsa ta zuwa neman dillalan da zasu sayi gidansu ne ya tsinci jakar kudin daddy har ya zama sila na biyan kudin aikin anni,zuwan ibrahim kuwa da 'yan sanda kawu idris yaji labarin saida gidan ne,so yayi ya qullawa khalipha sharrin da za'a kaishi birsin,shi kuma ya samu damar saida gidan ya kora anni daga ciki.
Bayan samun lafiyar anni khalipha bai fasa saida gidan ba bisa shawarar anni,saboda babban abinda hankalinta ya karkatu akai shine ya samu ya koma karatu,saboda shine gatan duk wani dan adam,Allah ya taimakeshi sukayi masa tayi mai kyau suka karbi kudin,qaramin gida suka sami wanda daki daya ne ciki da falo da bandaki,sai dan mitsitsin tsakar gida suka siya,sai wani dakin a soro,sauran kudin kuwa suka cire wanda zasu fara sana'a dashi sannan ya musu duk wani kai kawon makaranta a ciki,gaba dayansu makarantun gwamnati suka koma,cikin qanqanin lokaci al'amuran suka soma dan daidaita,tunda a qalla suna da abincin da zasuci susha,sun dan sauya suturu ga makaranta sun koma islamiyya da boko,sannan anni na sana'o'inta sosao wanda Allah ya dubi maraicinsu ya soma sawa abun albarka.
Zuwan khalipha makarantar cikin qanqanin lokaci yayi suna yayi fice,sakamakon tarin baiwa da basirar da Allah ya bashi,bugu da qari kuma ya samu background mai kyau don makarantar da yayi a baya duka ba qananun makarantu bane,qoqarinsa har ya wuce tunani,sai aka kaishi ss3 kawai,don sunce da akwai ajin gaba dahaka ma can zasu kaishi.
Bayan ya kammala secondry dinsa yana zaune gida suna qulla yadda zaici gaba da karatunsa katsam saiga kira daga makarantar daya gama,khaliphan yazo ya samu schoolarship,abinda bai taba zata ba ko tsammani koda cikin mafarkinsa,cikin makarantun gwamnati tasa aka bata dalibai bibbiyu masu hazaqa,ba bata lokaci akayi dukkan abinda ya dace khaliphan ya daga yabar qasar.
Koda yaje din sai ya zama dalibi na daban,karatu babu kama hannun yaro,bai zauna acan ba saboda neman kudi daya shiga jikinsa,ya dinga karbar duk aikin daya shigo hannunsa matuqat bai kauce hanya ba yanayi yana turowa annin da kudin,duk da cewa basu da wata matsala a yanzu ta rashin ci sha ko sutura,har wanke wanke khalipha da dafa coffe yayi a gidajen abinci nacan.
Cikin haka wani mai kudi ya saka gasar zane a can qasar,zai gina companynsa yana buqatar a zana masa yadda zai kasance,khalipha nada tarin baiwa ta wannan fannin,kamar wasa ya dawo daga aikin da yake a wani restaurant yaga takardar tallar,bai taba zaton zaici ba ganin yawan mutanen da suka shiga gasar,sai gashi yazo na daya,ya rabauta kuwa da tarin kudade masu dimbin yawa da bai taba mafarkin samunsu ba.
Yana can anni ta hadashi da ruqayya a wayar daya siyawa annin ya aiko mata da ita wadda sai a lokacin Allah yayi dawowarta gida ita da mai gidan nata da yaranta data haifa guda biyu,tayi kuka tayi kuka,tayi baqinciki tayi takaici,tayi Allah wadarao da 'yan uwanta,tayi kewar sa'id da alhinin mutuwarshi kamar ta hadiyi zuciya itama
"Allah sarki yayana makwafin mahaifina,ina can ina jin dadin rayuwa ashe kai ka jima kwance cikin qasa,ubangiji ya gafarta