Showing 156001 words to 159000 words out of 184891 words
Chapter 53 - DAURIN BOYE Complete Document by Safiya Abdullahi Huguma.txt
yayi hanzarin kashe wayar zuciyarsa na masa wasi wasin kiran asma'u,yanayin yadda take karya mishi murya dayi masa magana kadai ya isa ya karantar dashi akwai wata a qasa,yasan halin mata da yawa hakanan dai dai gwargwado ya karancesu,shikam saidai ya bawa wani labari,kiranta ne ya dinga shigowa babu adadi har sai daya gaji ya danna mata block,sai kuma ta koma sms wanda sukayita shigowa a jajjere,tsaki ya saki sannan ya kashe wayar gaba daya,bayan ya sake blocking yadda bata da damar sake tura masa wani saqo.
Kuka asma'un ta sako sanda ta fuskanci dukan abinda yay mata,saita zauna sosai saman gado tana sharban kukanta,tana jin cewa ba zata iya haqura ba dole tayi hanzarin fita daga gidan hamid,tana tsaka da haka ne hamid ya turo qofar dakin ya shigo,kallo daya yayi mata ya dauke kanshi bai tanka mata ba,sai daya gama sabgar gabanshi sannan ya dubeta da qyar
"Ke kuma waye ya mutu kika zauna kina yiwa mutane irin wannan kukan da daren nan?" Harara ta watsa masa,cikin izgili da rashin mutunci tace
"Ban sani ba,aikin banza aikin wofi,wallahi hamid ko kafi quda naci saika sakeni,don na gama zaman aure dakai"
"Ki iya bakinki tun bai jawo miki duka ba"
"Ai wallahi nabar zama ka taba lafiyata tunda bakai ka halicceni ba,banza wawa sakaran namiji dabai da aiki sai dukan matarsa" nan fa ya harzuqa,baiyi wata wata ba ya kasheta da mari sannan ya miqe yana huci
"Laifi nane dana sassauta miki kwana biyu kinga kina ci kina qoshi,to bari na sake jaddada miki tunda dama can ke jaka ce wadda ta fita makaranta da C.O,aure yanzu na fara,babu saki tsakaninmu har abada" ya juya yabar dakin,ashar takeson danna masa amma tana son lafiyarta,haka ta hadiye sai daya fice sannna ta dinga zage zagenta tare da cin alwashin gobe sai gida.
Zaune yake cikin office din nashi wanda yana sauka a qasar can ya soma zuwa,duk da yadda ya qagu matuqa yayi tozali da ita amma dole ya soma biyawa can,yantsunshi harde cikin juna,yayin daya dorasu saman table din gabanshi,ya kuma zubawa aljh kutama idanu yayin da alhj kutaman ya hada gumi sharkaf,ilahirin jikinsa rawa yake,tsananin tashin hankalin da yake ciki bazai misaltu ba
"Alhj kutama" khaliphan ya kira sunanshi kai tsaye abinda kusan bai taba yiba,kasancewar sunyi mu'amala da mahaifinshi kamar yaron mahaifinsa ne,amma hakan baisa ya daina bashi girma ba
"Alhj kutama" ya sake kiran sunan nashi
"Na'am yallabai,ranka ya dade Allah ya taimakeka...." Ya fada cikin dimuwa da rudu
"Duk abinda kake da kudina dana samu ta hanyar halas,nake baka saboda taimako darajar iyali da kake dashi kaje ka juya ta hanyar halas,duk sanda ka samu riba ta halas ka dawomin da kudina,nasan me kake dasu,haka mukayi dakai?"
"Wallahi yallabai akasi aka samu,ba halina bane"
"Alhj kutama"
"Na'am yallabai"
"Na bala nan da jibi ka tattara dukkan kudina dana ranta maka ka dawo min dasu,ban kuma yardaba ban lamunce ka kawomin wadanda ka samu ta qazantacciyar harqallarka ba" juya kai ya soma yi zai soma roqo da bashi haquri,cikin hanzari khaliphan ya dakatar dashi
"Banason naji komai daga bakinka,magana ce munyita dakai tsahon minti ashirin,duk cikin maganarka babu gaskiya a ciki,hakanan kuma ban sameka ba sai dana sanya aka yimin bincike a kanka,so ka riqe duk abinda kake da shirin fada kayi abinda nace maka" yasan halin yaron sarai,kaifi daya ne,ya riga daya karya duk wani abu da zai sanya ya tausaya masa ko ya janye hukuncinsa a kanshi,hakan ya sanya dole ya miqe yana jan qafa cikin tashin hankalin inda zai samo masa kudinsa ya fice,don dukka kudin ya tattara aka sayi cocain dasu da zummar idan suka wuce zasu samu riba mai yawa,sai gashi an kama yaran kuma suna shirin fadar sunanshi,tabbas daga shi har hamid suna cikin masifa,don har hamid din shima ya karbi bashin kudade masu yawa daga wajenshi,yace kuma dukansu su dawo masa da kudin,kuma baya jin a yanzu akwai kudin wajen hamid din shima,yace ya zuba kudin a wani kamfani da zasu dinga bashi ribar kudade mai yawa duk qarshen sati.
Waya ya dauka ya kira hamid din,yace kome yake yabarshi ya sameshi a gida,sannan ya wuce gidan shima afujajan cikin motocin da yake yawo dasu kamar wani gwamna,yaga alama talauci ne yakeson yayi masa saukar gaggawa alhalin bai shirya taryarshi ba daga nan har randa zai bar duniya,haka motocin suka dinga tafiya da sauri sauri,wannan burgar tashi da nunawa duniya shi lallai wani ne yasa sunanshi yayi suna yayi tambari,bayan kuma baikai inda yakeson ace yakai din ba,hakanan a wajenshi dukka yaranshi suka gado qarya da fafa.
Numfashi khalipha ya sauke yana sakin ajiyar zuciya gami da lumshe idanunshi,ya kara bayanshi da kujerar da hake kai yana istigfari,sosai ranshi ya baci matuqa,ya jima yana baiwa mutumin rance ga zatonshi yana amsa ne donya tallafi kanshi,duk da ya dade yana mamakin salon rayuwarshi,ya daukaki komai nashi bayan kusan qashin bayan arziqin nasa bashi ne,saidai ganin komai na tafiya dai dai tsakaninsu ya sanya ya kauda kai daga gareshi,daga bayane yadda kudim suke saurin dawo masa gami da gwaggwabar ribar da yake gaya masa yana samu a lokaci kadan kan kasuwancin da yakeyi ne yasa masa ayar tambaya,don duk abinda khaliphan zaiyi yakanyi takatsantsan da kaucewa haramun,saboda annabi S A W yana cewa haram a bayyane take hakama halal,saidai tsakaninsu akwai al'amura masu rikitarwa da shubha,wanda ya kiyaye wannan shubhar haqiqa ya kubutar da addininsa da mutuncinsa.
Bazai lamunci ko ya yarda ya ciyar da duk wanda ya danganceshi da haramun ba,walau kana aiki qarqashinsa ne ko kuma kankat mai gaba daya mahaifiyarsa da 'yan uwansa,saboda annabi S A W yayi bayani cewa,duk jikin daya ginu da haram,to wuta ita tafi cancanta da ita(wato wuta ita tafi cancanta ta cinye wannan tsokar,jan hankali a nan a garemu mata shine,muyi qoqari mu dinga tunasar da mazanmu koda yaushe su nemo halal su kawo mana halal,musamman yanzu da babu tayi yawa,albarka ta ragu cikin dukiyoyi da kayayyakinmu,don billhil azim maganar ma'aiki ba zata tashi a banza ba,duk wanda bai kiyaye haramun ba,ya yadda ake ci dashi a tufatar dashi asha dashi da haramun,to babu shakka ranar qiyama ya lissafa kansa cikin wanda wuta zata ci,saboda haka mu yiwa kanmu 'ya'yanmu da mazajenmu gata mu dorasu kan neman halali domin samun dace da tsira ranar da wata rai ba zata tsinanawa wata rai komai ba,matan sahabbai sun kasance kullum ta Allah idan mazanau zasu fita nema,sukan tsaidasu auce,yakai wane kaji tsoron Allah,ka nemo mana halak,don zamu iya haquri da yunwa amma ba zamu iya haquri da azabar Allah ba,Allah yasa mu dace)mutane da yawa sun shaida sirrin yauqaqar arziqinsa da albarkarsa shine kiyaye haqqin Allah da yakeyi a ciki,sannan kuma biyayya ga mahaifa.
Saida ya shiga toilet ya daura alwala sannan yaji zuciyarshi na sanyaya(ki riqe wannan 'yar uwa,a duk sanda kike jin bacin rai,ko wani abu ya bata miki rai,walau tsakaninki da mijinki ko wani daban,kije ki dauro alwala sannan kiyita karanta a'uzubillahi minash shaidanir rajim,da yardar Allah zakiji zuciyarki tana, sanyi)shauqin isa zuwa gida ya dawo mishi fil,sai ya zauna kan kujerar sofa din dake office din ya tura gajeran saqo,cikin 'yan mintina mutum biyu suka shigo,daya ya soma rufe mishi jakarshi,yayin da dayan ke tsaye saman kanshi,duqawa yayi.ya maida safarshi sannan ya saka takalminshi ya miqe yayi gaba suka rufa mishi baya suka fice da kamfanin gaba daya.
53
Tunda gari ya waye ranar bata shiga sashen anni ba,tana sashensu bayan ta gama duka gyare gyaren da zatayi ta sake kwanciya,ta ware fanka da acn dake falon duka saboda zafin da ake zubawa,wanda alamun zuwan damina duka sun gama bayyana,donko a jiya hadari sosai garin ya hada har aka tsammaci samun ruwan sama,saidai ruwan bai samu ba sai yayyafi da akayi wanda shi ya sake tada zafi a garin duka yau,da kuma wani sabon hadarin dake hadowa kadan kadan yana curewa waje daya gami da bada kala mai duhu,hakan ya sanya rana ta kasa samun dama fidda haskenta,qarfe hudu saura ta tashi daga bacci,ta daura alwala ta bada faralin sallah sannan ta shiga bandaki ta saki ruwa mai sanyi ba tare data sirka ba tayi wanka,hakan ya haifarwa da zuciyarta wani irin nishadi,zuciyar da gangar jikin dukka sukayi fes dasu,iskar dake busowa cikin windows din dakin tayi mata dari,sai taji tana bata wani sanyi na musamman dake ratsawa har cikin qwaqwalwa da zuciyarta.
Tana shafawa qafafunta mai murmushi ya subuce a fuskarta sabida tuna hirarsu da khalipha ta jiya,sassanyar muryarshi,yanayin maganarshi dake fita a nutse da sauransu,saita kada kai kawai tana dariya,itama sai taga wautarta,ba lallai yana nufin abinda ya fada din ba,don yanayin maganar bai nuna cikin zafi ko fushi yayita ba,bayan ta kammala ta shafa powder da man lebe kadan don kada ya dameta,jikinta ta feshe da turare sannan ta ciro kayanta da tuni dama sun rine da qamshin turaren wuta na kaya,doguwar rigar material ce cotton mai taushi yadda bazai dameta ba,saidai hannun rigar iya dantsenta ya tsaya,sai kuma mayafinshi wanda tayi rolling daya sauka mata har gwiwar hannu ya rufe hannun nata kenan bayan ta matse kanta da ribbom wanda yasha relaxer jiya,fuskarta ta kalla a mudubi,kayan sun mata kyau sosai,bata taba sanyasu ba saiyau,bata zaci ka zasuyi mata kyau haka ba,plat din takalmi ta sanya wanda ya dace da kayan sannan ta zira carbinta a yatsanta ta fito daga sashen.
Maryam ce kawai zaune a falon,saboda haka sallama tayi mata don fita haqqin addini,ganin ta amsa mata saita wuce kitchen ba tare data ce mata komai ba,don ta lura tunda annin ta tafi kowa kanshi rawa yake,dama ita maryam ba magana take mata ba,hakan ya sanya itama ta yi mata aji irin wanda ya dace da ita ta sanyata.
Bara'atu ke kiciniyar aiki ita kadsi,duk kitchen din a lalace yake kaman wanda akayi dafe dafe na mutum talatin
"Sannu da fitowar uwar masu gida" murmushi ta saki saita tuna da baba atika,tayi kewarsu sosai ita da anni
"Yauwa bara'atu sannu da aiki,ya haka gaba daya kitchen din ya kacame?" Ajiyar numfashi tayi sannan tace
"Ai kinsan aikin su waye,wallahi bansan me yasa suke abu ba bayan sunsan bai kamata ba sarai" sai aysha taji ranta ya baci,karo na farko tun sanda suka soma iskance iskancensu na kowacce ta dafa abinda ranta yayi mata,koda anyi girkin gida in general,koda su haidar dake yaran gidan duk abinda bara'atun ta dafa ci suke,bare ita da abinci bai dameta ba
"Kiyi haquri,komai mai wucewa ne,da zarar anni ta dawo naga wanda zaici gaba da yin hakan" aysha ta fada tana tausar zuciyarta,don bata son tayi musu magana sam,hannu ta sanya tana taya bara'atun gyaran kitchen din,sai da taga komai ya hau saiti sannan ta bar mata sauran,ta samu waje ta zauna suna jira jifa jifa,bayan ta zuba dan abincin da zata ci cikin plate.
Kadan kadan take tsakurar abincin suna hirarsu,bata wani ci da yawa ba zeenart ta shigo kitchen,tana ganin ayshan ta hade girar sama data qasa,tana yiwa ayshan kallon wata babbar naqasu a garesu,wadda ta kawo cikas da kuma hana ci gaban gudanuwar dukkan al'amuransu
"Bara'atu,maza maza dafamin couse jallop,ki saka nama da yawa a ciki yunwa nakeji" a ladabce bara'atun tace da ita
"Gafa abincin da kika asaka a aka dafa dazun baki cinye ba,sannan maryam da anty rahama dukansu an dafa musu abinci gasunan duk ba wanda ya cinye,ki duba ko wani abun a ciki zaiyi miki" ta fada tana buda mata fulasan dake shaqe da abinci
"Dalla malama ban tambayeki wannan ba,couse couse nake sha'awa shi nace ko dafamin"
"Ba za'a sake dafa komai ba a gidan nan sai Allah ya kaimu gobe" aysha ta fada hankali kwance kuma kari na farko tunda suka fara rashin mutunce mutuncensu,,saidai can qasan ranta a hasale take,ta karanci takunsu gaba dayansu babu abinda ke damunsu face tsantsar mugunta da almubazzaranci,saidai muguntar da qetar ma tafi yawa,waiwayawa zeenart tayi tana dubanta
"Au,harda su kaza a cin danqo?,ke kuma waya saka da ke?to bari na gaya miki tun ba'ayi nisa ba baki isa ba"cokalin hannunta ta aje sannan ta amsata
" na isa?,ban isa ba duka wannan bata taso ba ba'akai ga can ba,magana daya ce babu abinda za'a sake dafawa a gidan nan saidai idan har mun iya cinye duk abincin dake gidan nan muna da buqatar qari to wannan fa,barema nasan wannan abincin saidai a fitarwa da mabuqata a waje"
"Ke aisha!'muryar rahama dake takowa cikin kitchen din ta katsewa zeenart niyyar bata amsa da takeyi,hannunta harde a qirji fuskarta a dinke tsaf ta qaraso gaban ayshan,hannu kawai ta miqa mata sannan tace
"Bani muqullin dakin anni"sosai ta dubi rahaman cikin ido sannan tace
"Bamuyi wannan da anni ba"
"Ki bani malama ko,abina zan dauko a ciki"
"Idan kina da buqatarsa saidai ki jirayi dawowarta,saboda amana ce a gareni bazan iya wofantar da ita ba,ni dinma ban sake taka dakin ba tun randa na rufeshi"ta bata amsa tana janyo faranti ta rufe abincin dake gefanta,tsaiwa rahaman ta gyara tana dubanta cikin bacin rai
" ke ki saurara fa,naga alamun kina wuce gona da iri,saboda kinga an zuba miko ido kina yadda kikaga dama,toba tsoronki kowa keji ba"
"Duk saboda taga anni ta daure mata gindi ai take komai,ta fifitata a kanmu" zeenart dake cike ta fada
"Koma meya karki manta auroki akayi,a yau idan aka sakeki.magana ta qare,hakanan ana iya sauya mata amma dan uwa komai lalacewarshi lalala lalala"
"Don Allah anty rahama duka mai ya kawo wannan maganganun marasa dadi haka?" Bara'atu ta fada cikin tsoro da nuna rashin jin dadi,da hannu aysha ta dakatar da ita,murmushi ta saki tana dan kada qafarta kadan kadan sannan ta dubesu daya bayan daya
"Shi dan uwa suna ya tara ai,baku da labari?,da wani dan uwan gwara bare sau dubu?" Dukkansu sai kowacce tasha jinin jikinta,ba zasu so ace tasan komai game dasu ba,ganin karta ramfo wani abu ya sanya rahama sake yunqurowa cikin kurari tace
"Malama ki bani maqullin dakin uwarki anni tunda indai bana uwarrr........"
"Rahama!!" Dakakkiyar muryarshi mai cike da mazantaka ta karade ilahirin kitchen din gami da bada sautin amsa kuwwa,ba rahama ba hatta bara'atu da zeenart hantar cikinsu sai data kada,da hanzari dukkansu suka waiwaya bakin qofa,yana takowa ne cike da nutsuwa saidai kana duban fuskarshi zaka san cewa ran 'yan maza ya baci,tun kafin ya iso zeenart ta samu wajen jingina,yayin da rahama ta gyara tsaiwarta kamar mai shirin tarbar isowarshi saidai sam jikinta ne ke rawa takeson bawa kanta qwarin gwiwa,sai daya iso tsakiyarsu ya dubesu tsaf,sannan cikin wani irin sauti yace
"Matata?,kukewa haka a cikin gidanta?" Ya jefesu da tambayar yana binsu da kallo,zeenart kam babu bakin magana,sai rahama ce don kada ta bada kanta da shekarunta tayi qarfin halin cewa
"Haba khalipha?,kai bakagani ba kuma bakasan duk abinda take mana ba tunda anni ta tafi don kawai ta......"
"Will you shutup kosai nayi qasa qasa dake a nan" zaro ido tayi cikin mamaki,kalmar da bai taba gaya mata ita ba koda wasa,ko vanza yana dan bata girmanta ta wani bangaren saboda shekarunsu da suka kusa zuwa daya,waiwayawa yayi ya yiwa zeenart wani kallo wanda ya sanya take gumi ya rufeta
"Har da ke ko?....stupid,idiot....banda darajar anni da kuke ci ke kin isa kiga matata ma nare ki samu damar yin sa'insa da ita?banda kima da isar da anni ke dashi kin isa cin abincin gida na?,banda anni abincin gidana ko wanda na zubar ne bazan lamunci kuci ba" sai ya waiwaya wajen rahama
"Baki da damar da zaki nuna cewa anni wata ce a wajenki ko ke wata ce a wajenta,sanda muke wahala daga wannan mataki zuwa wancan na rayuwa kuna ina?,sanda muke tsakanin mutuwa da rayuwa kun taba tunawa damu?,kun taba kwana da tunanin ya rayuwar ayshatu zata kasance bayan kun sallamata a dangi?,to na meye a yanzu da muka samu nutsuwar zuciya da gangar jiki duka zaku kutso cikin rayuwarmu ku hanamu sukuni?,mu ba wawaye bane hakanan kyautatawa ba rashin sanin ciwo da darajar kai bane,saka sharri da alkhairi bai nufin ka manta komai daya faru,saka sharri da alkhairi bai nufin kai shashasha ne koka sarayar da dukka haqqi da mutuncinka" waiwayawa yayi ya dubi zeenart cikin kakkausar murya
"Kije ki kiramin dukkan yarinyar da tayi saura cikin gidan nan na baku minti biyu kacal" da hanzarinta ta fice,ba jimawa sai gasu sun dawo gaba daya,yatsunshi ya hada ya murza suka bata sauti sannan cikin kaushi yace
"Na baku nan da awa guda kowacce qarfe shida tayi mata cikin gidan mahaifanta,karku yadda na fito sallar magariba na samu daya daga cikinku...ko wacece kuwa...kome nisan da take dashi" ya qarashe maganar idanunshi yana kan rahama,tasan da ita yake ita da take nijer,wani abu mai tauri ta hadiye idanunta sun sauya launi saboda bacin rai,bai kuma bi ta kansu ba ya damqi hannun aysha da duka take jin babu dadi cikin ranta,tamkar ita ta zama sila kenan ta faruwar komai,batasan ya anni zata dauki hukuncin ba,kada hakan ya zama Silar tabarbarewar kyakkyawar alaqar dake tsakaninsu,haka suka ratsasu suka fice tana biye da shi.
A hankali ya tura qofar sashen nasu ya sanya kai tana biye dashi,sanyi da qamshin dake falon ya cika hancinsa ya haifar masa da wata nutsuwa ta musamman,suna isa falon ya aje jakar hannunshi ba tare daya saketa ba,idanunta ta daga ta dubi qwayar idanunshi,ta sauya kala hakanan kana dubansu kasan an tono wani abu dake zuciyarshi,sai ta zame hannyenta cikin sauri ya rungumoshi ta baya,kusan a tare suka sauke ajiyar zuciya shi da ita,bacin ran daya tabashi sai taji duka babu dadi,bai kamata daga dawowarsa yaci karo da wata matsala ba,ya kamata zuwa yanzu ya samu hutu da kulawa da kuma dukkan wani kwanciyar hankali daya kamata,bata taba ganin bacin rai a fuskarshi kamar haka ba,bata taba ganin fadanshi kamar yau ba,da alama wannan gyambon dake zuciyarshi ne aka taba,sai taji zuciyarta ta karye,hawaye suka biyo kuncinta,wanda sukayi nasarar taba jikinsa,idanunshi na lumshe ya sanya hannunshi ya dawo da ita gabanshi,ya bude hannayensa ya sakata cikin faffadan