Showing 150001 words to 153000 words out of 184891 words
Chapter 51 - DAURIN BOYE Complete Document by Safiya Abdullahi Huguma.txt
ayshan ta girgiza tana duban hanan fuskarta qunshe da murmushi
"Ban yarda da wannan sharhin naki ba malamar love" saita maida kanta ta kwantar
"Ki gama qi fadinki tsaf da kauce kaucenki,baki da wata makawa kan zancena,zaki ce kuma na gaya miki nan da wani qanqanin lokaci" itama hanan din ta fada tana gyara rufarta tare da gyara kwanciyarta,shuru aysha tayi tana sauraronta tana fidda boyayyen murmushi,
saidai can qasan ranta tana taraddadin rashin jin khalipha da bata yi ba har a sannan.
Washegari suna idar da sallar asuba ta zari slippers dinta tayi gidan suna koda akwai wani aikin da zasuyi a lokacin tabar hanan tana bacci,tasan yanayin yadda mutan qauye kesa asubanci,haka kuwa tayita cin karo da mata jefi jefi,tana tsayawa suna gaisawa,wanda hakan yana musu dadi sosai.
Sanda ta isa kuwa ana shirin yanka abun suna,ta gaisa da 'yan uwan mero dake rumfarta ta tsallake uwar daka inda meron take tana shiryawa,mero na dariya tace
"Indo baki manta da al'ada ba,na zaci birni tabi jikinki ai ba zaki iya wannan asubancin ba" dariya tayi ta amshi yaron da tuni anyi masa wanka an shiryashi tsaf cikin daya daga cikin rigunan da khalipha ya sako masa,kyau yaron yayi sosai dama kuma kyakkyawa ne,ya debo babarshi xam,sai taji ya bata sha'awa
"Tushiya masomin dawa mero,ta yaya zan manta usulina"
"Wannan gaskiya ne,aike indo kam Allah ya baki,duk yadda akaso ayi da rayuwarki Allah bai nufa ba,gashi da yake ke din 'yar qwarai ce irin halak daular da kika samu bata sanya kin manta da tushenki ba,bakya qyamatar kowa cikin 'yan garinku,kowa sanbarka yake dake" cewar iyalle kishiyar babar mero wadda ke shigowa dakin ta tsinci zancan da sukeyi,murmushi mero tayi kaman yadda yasha itama shi tayi,tana zaunw suna hira da mero harta kammala shiryawa,tayi kyau cikin atamfa abinta,tanajin an shigo da abun sunan za'a soma gyarawa ta ajiye yaron tana cire hijabin jikinta ta rataye
"A'ah ina zaki kuma?" Maro ta tambayi aysha tana dubanta
"Aiki mana"
"Wanne aiki duk ga mutane nan,kiyi zamanki muyi hirarmu karki bata jikinki,inake ina bakin murhu ma" dariya aysha tayi,duk basusan irin uban aikin data tashi ta saba dashi bane,hakanan bata taba samun sararawa ko salamar aiki ba sai bayan data auri khalipha
"Mero kenan,aikin kuma ai da yana kisa da ban kawo iwar haka ba,bata jiki kuma mero idan a kanki ne ba kayana ba har fatata zan iya batawa,idan kin manta halaccinki a gareni ni bazan manta ba,ke kadaice wadda ta tsaya dani a sanda duniya ta juyamin baya,kin manta randa muka fara qawance,ranar da 'yan uwana suka taddani bakin rafi zasumin duka kika qwaceni daga hannunsu?" Dariya mero kawai take tana girgixa kai,ba shakka alheri danqo ne baya faduwa qasa banza,ita ta mance yadda abun ya kasance amma har yau gashi ita indon bata manta ba
"Tunda sai kinyi jeki kiyi ki dawo muyi hirar" aysha na dariya ta fice,ko su sunso hanata amma ta karbe hanjin ta gyarashi fes ta kuma dorashi kan wuta,sai data gama suyar a sannan rana ta dan fito tacewa meron bari taje ta dawo ta duba baquwarta.
Sanda ta koma ta tadda hanan a bararraje ita da inna yelwa suna kwasar hira kamar sun jima da sabawa,har tayi wanka abinta ta kuma karya da lafiyayyen kunun gyada daya sha madara da kuma qosai,idanun inna yelwar a kanta tunda ta shigo take kaffa kaffa da ita,kiran daya daga cikin surukanta ta kira ta hadawa ayshan ruwan wanka
"Jeki abinci inna karima,zan iya hadawa da kaina" ta fada tana zare hijabin jikinta
"Banda abinki indo da kin bari ta hada mikin,inake ina jan ruwa yanzu" dariya ma maganar ta inna yelwa ta bata,bata mantawa akwao sanda take wani azababben zazzabi haka ta tasota gaba kan sai taja ruwan,data gaya mata tana jin jiri ne tace ko zata fada cikin rijiyar sai taja,haka kuwa akayi wanda da qyar tayi guga uku,tana cikin na hudun jiri ya debeta gugan ya koma rijiyar,ita kuma Allah ya kawo mero a dai dai lokacin ita ta riqeta,bata tankawa inna yelwar ba ta daura zani da hijabi ta fice abinta ta debi ruwanta cikin babban dakin girkin da aka yi musu taja ruwa ta sirka ta shiga bandakin da aka yi cikin daya daga cikin dakunan dake falon inna yelwar,wanda ta shaida mata shine nasu da zasu dinga sauka a ciki.
Tana zaune tana karyawa jifa jifa tana duban inna yelwa,wadda ta taqarqare tana faman jansu da hira,ita a yanzu bata yadda ba qaunarta take?,haka aysha kewa kanta wannan tambayar cikin mamaki,data gama tare suka fice da hanan,wannan karon maimakon gidan mero gidan inna kulu suka nufa,shima dai gidan tun daga waje tasan tabbas aikin khalipha ya sauka ta kanshi,sanda ta gansu ita dinma da yake ba baya bace wajen son abun duniya kamar zata goya ayshan,itadai kallon kowa take
"Mamarki kuwa ina zaton yau zata shigo garin" cewar inna kulu,da mamaki take duban innan,tunda suke bata taba sako mata zancan innarta a tsakaninsu ba sai yanzu,bata ce komai ba wanda hakan yadan sanyayar da jikinta saita sauya hirar,awa biyu kawai sukayi mata suka wuce gidan sunan,a can hanan ta sake abinta,ta dinga yiwa mejego da 'yan suna hoto,ita abun qayatar da ita yake,da yake su iyaye da kakanni 'yan haifaffun cikin gari ne,kusan bata da wani qauye da zata nuna tace na kakanninta ne.
Duk hidimar nan da ake hankali da tunanin aysha na kan khalipha,tana shirin tada sallar la'asar taji shigowar saqo,cikin hanzari ta sanya hannu ta dauko wayar tana dubawa
_ina cikin aminci da kulawar ubangiji,na gode qwarai da kulawa_
Haka kawai taji amsar bata gamsheta ba,amma don kada ta takura shi saita haqura ta tada sallarta.
A ranar suka koma makaranta da yammaci lis,wanda motocin daukarta ma su sukayi jiranta,tana jin zuwan umminta garin a sanda suke shirin ficewa daga takai din,saidai ko kusa ko alama bata kwantanta dosarta ba bare taje wajenta.
Koda wani satin ya kewayo taje gida weekend kuma gida taje wajen daddy,tayi sa'ar samunshi a gida kuwa,sun jima suna hira dashi sosai,wanda hakan ya baqanta ran mummy,irin ci gaba da sauyin da take gani tattare da ayshan ya soma tabata,saita tuna asma'unta,wanda kusan rabin wahalarta ta dawo wuyansu,bata tabaji aysha tace ehmmm dazai nuna tana cikin wani hali ba bare takai ga furtawa har duniya ta sani.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Qarfe biyar ne na yammacin ranar,suna zaune ita da mummyn ta a falon samanta,kayanta ne da suka zo daga lagos a bude suna lissafi ita da mummyn na kudaden kayan da sunan wadanda za'a rarrabawa.
Saman ya hawo yana amsa waya da alama shigowarsa gidan kenan,baiyi ko sallama ba ya ratso falon,suka hada idanu da mummyn,baiko nuna alamun ya santa ba ya samu daya daga cikin kujerun falon yayi zamanshi yana ci gaba da wayarshi,dif asma'u sukayi ita da mummyn ganin ya sanyasu gaba yana waya,sai daya kammala sannan yace
"Barka da yamma" yayi maganar yana latsa wayarshi ba tare daya nuna da mummyn yake ba,hakanan ta amsa saboda tasan da ita din yake,irin gaisuwar da ada idan yazo wajen asma'un yake maya kenan,banbancinta da waccar kawai yana kallonta yake gaidata,a sannan data danyi qorafi sai asma'un tace yanayinshi ne haka,haka mummyn ta qyale maganar ta biyewa son ran asma'un.
Mai aikinsu ya soma qwalawa kira,cikin mintina qalilan sai gata ta shigo,cikin girmamawa ta risina masa ya gaya mata abinda zata kawo mishi,dole mummy ta yiwa asma'u sallama,ganin abun na hamid ba girma ba arziqi.
Sanda mummyn ta fita mai aikin ta shigo ta shirya masa komai sannan ta fice,wata sabuwa kuma ya samo don tuni ya sallami wacar farkar tasa ya gaji da ita,idanunsa nakan kayan da salma ke lissafawa ba tare data ko dubeshi ba,lissafi yake cikin ranshi,so yake kawai ta kulashi suyi wani abu ta yadda zai samu damar cewa ta masa asarar wani abun ya debi lesunan gabanta ga kaiwa budurwarshi.
Tana sane taqi kulashi,don a yanzu ta gaji da hamid ta gaji da aurenshi,kamar ita asma'u tana ganin bai cancanci ta rayu da hamid cikin irin wannan uqubar ba,tana da kyau,tana da gata tana da usuli,ba shakka hamid bai cancanci ci gaba da zama da ita ba.
"Ke...wato saboda wuyanki yayi kauri kina ganin mutane baki iya musu sannu da zuwa ba ko?,kuma saboda rashin tarbiyya a gaban babarki amma bata tsawatar miki kota nuna miki rashin dacewar abinda kika aikata ba" abinda bai sani ba shine,ita kanta asma'un dama hanya take nema,saboda hama ta miqe a fusace cikin daga murya tace dashi
"Dakata hamid,karka sake kiran uwata saboda ita din ba sa'arka bace,sannan rashin tarbiyya aikao za'a tambaya wannan,tunda baka iya zama da matarka ba kaga kuwa daga wajen tsoho aka...." Bata kai aya ba ya wanketa da wani lafiyayyen mari
"Karki sake ki qarasa,wanda kike shirin zagi shi ya bada kudin da kika gani kika maqale min"
"Ni ka mara hamid?,...."
"An marekin ko kina da abinda zakiyi?"kai take kadawa kuka kamar zai qwace mata
"wallahi zakasan ka mareni,ka mari aurenka,yau saika sakeni,saika bani takardata" wata wawiyar dariya ya saki yana jan tsaki,komawa yayi ya zauna saman kujerar daya tashi a kai yana kwance agogon hannunsa mai tsada ya sanya hannunshi cikin abincinsa
"Aikin auru kenan har abada,idan ma kina mafarkin zan sakeki ne to kinyi kuskure,don ni ba shashasha bane,nasan ciwon kudina" daga haka yakai abincinsa baki ba tare daya sake bi ta kanta ba.
Dakinta ta shige cikin kuka ta dauko jakarta da mayafinta ta fito,ko kallonta baiyi ba,itama hakan yayi mata dadi,saidai bata gane manufar sharetan da yayi ba sai data je bude qofa taqi buduwa,sai daga bisani ta gane muqulli ya saka mata,dawowa tayi gabanshi cikin hargagi ta tsaya
"Ka tashi malam ka budemin qofa,don wallahi daga yau na gama aurenka na gaji"
"Ni kuma yanzu na fara aurenki wlh,don ba more komai cikin abinda na kashe miki ba" wani qululun baqinciki ne ya taso ya tokareta,me yake nufi kenan?,yana son yayi mata qwalelen rayuwar da ta shiryawa kanta samu a gaba?,yana nufin fa bazai saketa ba,wanda hakan dai dai yake da cewa haramiyarta rayuwar da takewa kanta hasashe.
51
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
A hankali yake ratsawa ta cikin layin nasu har zuwa qofar gidan da yake mallakinshi ne,kuma a halin yanzu yake zaune a ciki,yayi kyau sosai cikin qananun kaya wanda ya dira jibgegiyar rigar sanyi a kai,yana saka key yana shirin bude qofar gidan wayarshi tayi qarar shigowar saqo,basu jima da gama waya da anni ba wadda ta tashi zuwa saudiyya don tayi umara,wayar ya zaro daga aljihunsa yana dubawa,murmushi ya saki a hankali yana karanta abinda saqon ya qunsa,a qalla ya dauki wasu kwanaki bai.maida.mata da amsa,yayi kuma hakanne saboda ya auna yadda ta damu dashi,shin abinda zuciyarsa take raya masa haka ne?,wani irin yanayi da bai taba hasashen shiga irinsa ba akanta ya samu kansa,bashi da shakku kuma ko kokwanton cewa wannan ba komai bane soyayya ce,yadda yake ji din ya tabbatar da cewa ba qaramin kamu tayi masa ba,yaushe hakan ta kasance duka bazaice ba,yana tsoron kar yayi zurfi da yawa abun ya zame masa matsala,ya kasa samun goyon baya yadda ya kamata daga gareta.
Sosai saqon yayi masa dadi,don har ya shiga parlour din gidan maimaita karanta saqon yake yana murmushi kafin daga bisani ya samu wajen zama.
Daga bangarenta kuwa tana zaune gefan gadon anni bayan sun dawo daga rakiyarta airphort,wadda ta bar mata muqullin dakin nata a hannunta saboda ta tashi ne ran asabar sanda ayshan ke zuwa gida hutu,kasa aje wayar tayi daga hannunta sai juyata take tana jin wani iri babu dadi a ranta,batasan me yasa a duk sanda ta tura mishi saqo take kasa samun amsar sa ba,batasan dalili ba tana jin babu dadi sosai cikin ranta,ko wani laifi tayi masa?,damuwarta tana ganin ko bata rasa nasaba da qoqarin kyautata matan da yake yasa batason itama tayi masa wani abu da yake ba dai dai ba?,duk dai bata sani ba.
Gauruwar ajiyar zuciya ta sauke,jiki a sanyaye ta miqe ta soma kintsawa annin dakinta gami da gyara duk wani da tasan zai iya samun matsala kafin dawowarta,a qalla ta kusa kashe minti ashirin qwarara sannan ta sanya key ta kulle dakin ta sauko zuwa falon gidan.
Rahama,amal maryam harma da zeenrat dukkansu na zaune darshe darshe a falon,kowacce na sabgar gabanta kamar wadda ta samu gidan gyatuminta,hannun ayasha harde a qirji tabi kowaccensi da kallo ba tare da sun ankara ba,dukkansu mamaki suke bata,baya ga wani abu mai kama da haushi haushinsu da yake tasiei gami da mintsinarta can qasan ranta,saidai babu wadda ta taba nunawa haka cikinsu,saboda tana ganin nata da wannan hurumin.
Bata cewa kowa komai ba ta ratsasu zata shige,saboda kacokam amanar gidan anni ta danqa a hannunta ne,wanda hakan tasan ya bata ransu duk da basuyi magana ba,saidai fuskokinsu sun nuna,wani tsaki taji rahama ta ja,bata waiwayo ba bare ta nuna tasan da ita take,tunda suke sallama da annin take wani cika tana batsewa.
Cikin lambun gidan ta samu waje ta zauna,tana son yanayi da iskar wajen,ita kadai wajen shuru,jifa jifa tana tunanin rayuwa da abubuwa da dama da suka shude daga cikin rayuwarta,tun wancan sati taso ta sake zuwa gida taga daddy har ta gayama khalipha saidai bata samu zuwa ba,sabida wancan karon tun ranar lahadi ta koma makaranta saboda monday takwas na safe tana da lacture,ajiyar zuciya ta sauke ta soma danna wayarta,number din anty safiyya ta nema ta kirata,don sukanyi waya duk bayan wasu kwanaki,ko bata kira ta ba ita zata kira,bugu uku aka daga,murmushi ta saki saboda kukan al'amin daya fara yi mata sallama
"Me aka.yiwa dan gida na anty?" Cewar aysha tana murmushi
"Hmmm,rigima kawai yakeji aysha wannan dan gidan naki sai a hankali"
"A lallabamin shi al'amin baya kukan banza" dariya antyn tayi sannan suka soma gaisawa
"Kin shiga wajen daddy ne?jiya ban ganki ba inata tambayarki mummy bata cemin komai ba"
"A satin nan nakeson shiga"
"A'ah,karki cemin bakisan baida lpy ba,jiya fa a asiniti muka wuni daxu da safen ya koma gida" idanu ta fiddo cikin mamaki,don ita ba wanda ya gaya mata
"Me ya sameshi anty?,wallahi ban sani ba ba wanda ya gayamin"
"Wani irin zazzabi ne mai naci wlh sai da aka qara masa ruwa"
"Subhanallah,ai kuwa yau ba sai gobe ba zanje na ganshi,wallahi anty banda na kiraki mummy bata gayamin ba" ajiyar zuciya anty safiyya ta saki,wato har yau mai hali baya fasa halinsa kenan
"Allah ya kyauta,shikenan idan na samu dama nina zan shigo,idan ban shigo yau din ba sai gobe"
"To aunty,Allah ya bashi lafiya" suna kammala wayar ta miqe,hankalinta duk sai taji yaqi kwanciya,tana qaunar daddy kamar nata mahaifin,shine mutumin daya soma saka maqullin alkhairi ya budewa rayuwata dukkan wata qofa da a yanzu ta samu kanta a tsaye,kai tsaye cikin gida ta nufa ta isa sashensu,cikin qanqanin lokaci ta shirya tsaf,kana dubanta kasan ta samu dukkan wata dama ta rayuwa,duk aninda ke sanye a jikinta mai aji da tsada ne,har yau tana jin gajiyar kayanta dake jibge ne cikin gidanta wanda ita ka ta batasan iya adadinsu ba,saidai ba makeup ko daya a fuskarta.
Daya daga cikin muqullan motarta da anni ta damqa mata ne sanda zata tafi take mata fadan ajiyesu da tayi bata taba hawan ko daya ba,saita gangaro zuwa sashen annin,zuwa yanzu daga maryam sai amal da zeenart a falon,amal na kwance tana charting,maryam.na zaune tana kallo,yayin da zeenart ke riqe da kwanon farfesun kayan ciki wanda yake a mazaunin abinda za'a hada cikin anincin dare aci amma tsabar zalama da son zuciya da aka saba ta kasa jira,sam ta kasa zaman gidansu duk da jan kunnen da babanta yayi mata na kada ya sake ganin qafarta gidan annin tunda har khalipha ya wulaqantasu amma ta kasa jurewa,don tace ko dadin da take ci gidan annin ai babu a gidansu,ko iya shi ta samu ai ta more,qasa qasa amal ke kallon ayshan,tayi mata kyau komai nata mai aji da burgewa,duk abinda tayi saiya nuna maka ita din ta dabance mai ilimi da kuma aiki dashi,kitchen ta wuce ta tadda bara'atu daya mai aikin tasu,don inna atika da ita aka tafi umarar wannan karon,da fari anni cewa tayi yayi visa din mutum biyu bayan ita,ko amal da zeenart,ko amal da maryam din,ya amsa mata da to kawai,amma harga zuciyarshi baya jin zai iya cire kudinshi ya biyawa wata daga cikinsu zuwa saudiyya,kosu ko iyayen nasu,saboda haka kawai sai passport din ya aiko mata dashi da komai da komai na baba atika,dama ya jima yana son kai matar,saboda yadda anni kejin dadin zama da ita,uwa uba riqon amana da gsky,hakanan annin bata taba kuka da ita ba,itama annin data gani bata ce masa komai ba bare tayi qorafi,tasan wannan abubuwan da suka faru shekarun baya har yau ke tsikarinsa,ba abu bane na mamaki,dafi ne ko ace gubace da duk sanda ya tuna take taso masa,tama godewa Allah da yakanyi musu alkhairi lokaci bayan lokaci na abinci da sutura,don da fari yadda ya birkice bata zaci tsinkensa zai bari su mora ba,shi kuwa yayi hakane saboda darajar annin da umarnin data bashi wanda bazai iya tsallakewa umarninta ba,da shawara ce da da sauqi.
"Kardai fita zakiyi?" Bara'atu ta tambayeta
"Eh wallahi zanje dubiya ne....don Allah saqo zan baki,idan haidar ko mus'ab wani daga cikinsu ya shigo kice masa ina gidan daddy,amma bazan jima ba can zan dawo,akwai tamfofi da anni ta bayar za'a dinka guda uku tace telanta zasu kaiwa su sun sanshi"
"To a dawo lafiya,Allah ya tsare"
"Yauwa amin" nan ta juya ta fice,koda tazo fita itama bata bi takan kowa ba,sai kallo da kowacce take binta dashi a