Showing 108001 words to 111000 words out of 184891 words

Chapter 37 - DAURIN BOYE Complete Document by Safiya Abdullahi Huguma.txt

alqasim ne idan kayan sunzo ya kawo miki,zama babu sana'a babu kyau,Allah ya wuce gaba"
"Amin daddy" ta fadi tana addu'a cikin ranta karya furta wata kalmar da zata sa aysha ta gane komai,haka sukai sallama aysha na mata ta gaida gida,da qyar ta amsa tana jin kishi da qyashin ayshan cikin ranta,batasan me yasa kamar ta fita sa'a ba a rayuwa,miqewa.mummy tayi ta bita bayan ta saka an kwashe mata kayan an bita da su ta barta ita da daddy a falon suna hira,hira suke sosai abinsu gwanin sha'awa,yana jin dadin yanayin daya ga ayshan,yasan cewa da ikon Allah ta sake samun ci gaba ne a rayuwarta,a duk sanda ya tuna yadda ya daukota daga qauye su saiyaji tausayinta,ya kuma sake binta da addu'ar ci gaba da samun dacewa a rayywarta,nan haidar ya samesu,shima ya shiga hirar tasu,sun jima kafin daga bisani suyi haramar tafiya,sai a sannan ta kuma ganin mummy,ta danqa musu tsarabar data yi musu daddy ya amsa yana murna bawai don baifi qarfin abun ba,a'ah,saidon yadda kyauta take da girma da kima koma kafi qafin abinda aka yi maka kyautar da shi,yayin da mummy ta karba kadaran kadaham,duk da cikin ranta tayi farinciki,don wata sarqa ce fashion sabuwar shigowa mai tsadar gaske,ko ita bata kai ga siyanta ba har yanzu,anni ce kuma ta bata tace ta bata a zuwan ita ta saya matan,da biyu kuma tayi hakan tasan saqon zaije yadda ya kamata har cikin jiki da zuciyar mummy,ya kuma je din.


🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶




Washe gari da safe suna breakfast anni ta dubi aysha
"Ni kuwa ayshatu jiya zuwa shekaran jiya kunyi magana da khalipha?" Daga kai tayi ta dubeta gabanta na faduwa,tunda ya tafi baifi sau biyu daya ya kirata,batasan me zata ce mata ba,bata so tayi wata magana kuma batasan me khaliphan yace da anni ba karta warware masa,saita gyada kai kawai
"ke kika sakarma khalipha har haka kenan ya jima bai waiwayo gida ba?"gabanta ne ya fadi,sai tayi qoqarin tattara nutsuwarta,ta hade hannayenta waje guda bayan ta aje spoon din hannunta
"Tunda ya zauna anni akwai uzuri,idan baida wani uzuri na tabbatar bazai zauna har haka ba,zai zo da zarar ya samu dama in sha Allahu,aci gaba dai dayi masa addu'a" sosai kalamanta da amsar data bata ta kwanta mata a rai,sake shiga ranta tayi,tana yaba nutsuwa hankali da kuma haqurinta,wanda hatta yaran 'yan uwanta da dangin mahaifinsu khalipha masu zuwa dama wadanda basa zuwa bata ga masu hankali da nutsuwarta ba
"In sha Allahu aishatu,Allah yayi muku albarka" duka suka amsa da amin.




Bayan ta kammala ita ta soma tashi,saboda yau takeson ta yiwa anni gyaran dakinta kamar yadda ta saba duk sanda tazo weekend din qarshen wata,abun na damun amal sosai,amma ba yadda ta iya,kuma ita din ba iya yi zata yiba,hakan ya sanya duk weekend ita kuma take tafiya wajen mamanta har sai ayshan ta koma makaranta.




Haidar ne ya sauke ajiyar zuciya yana duban anni
"Anni....nifa ya khalipha bana ganin yana kiran anty...anya ko da gaske ne abinda ta gaya miki kidai bincika"
"Na sani haidar,ina sane na tambaya din,babu wani cikinku da zai layancemin wani abu,na san halayen kowannenku dai dai gwargwado,amma zan sake tambayarta don na tabbatar din"
"Nikam anni kimin addu'a Allah ya bani matar aure kaman takwararki" haidar ya sake fada yana dan murmushi,itama murmushi tayi tana dubanshi
"Aysha tana da nagarta aliyu,nagarta mai yawa,tana da tarbiyya wadda dai daikun yara a yanzu keda irinta,duk da tarbiyyarta daga indallahi ce,ina maka fatan samun mace kamanta"
"Allah amin" ya amsa yana daga hannu,bata rai mus'ab yayi
"Nifa anni?"
"Kaima haka auta" ta fadi tana murmushi gami da shafa kanshi,sai ya saki dariya yana jin dadin annin ta mishi haka gaban aliyu don yaji haushi fadansu na sako da sako,saidai wannan karon dauke kai yayi kaman bai gani ba.


37


Ta kammala gyaran dakin anni tana shirin fitowa annin ta shigo
"Sannu da aiki ayshatu,Allah yayi ma rayuwarki albarka" sunkui da kai tayi tana murmushi ta amsa da amin,ko yaya annin ta gwada jin dadinta kota yabeta kan wani abu dadi take ji,saboda lafazi ne da bata saba jinsa ba a bakunan al'umma a kanta,cikin karamcin ma da suka yi mata batajin tana da abinda zata saka musu dashi
"Amm...aysha" waiwayowa tayi tana amsawa
"Kikace kuna waya da khalipha?" Kai ta gyada gabanta na faduwa
"Kin tabbata?" Kai ta sake gyadawa kawai ba tare data furta komai ba
"Shikenan jeki,Allah ya dafa mana"
"Amin" ta bata amsa tana ficewa,yayin da annin ta bita da kallo,ta sani cewa samun kaman ya aishan a wannn zamanin abune mai matuqar wahala,sosai take qaunar ayshan tare da fata da kuma addu'ar Allah ya nuna mata wani lokaci da take muradin gani.




Dakinta dake nan sashen anni ta koma tana jujjuya maganar cikin ranta,kaddai ace anni ta dago wani abu ne?,da wannan tunanin ta shiga wanka,bayan ta fito ta shirya,tana son ta debo wasu kayanta daga can sashen khalipha,wanda tunda ya tafi itama ta tafi bata sake leqa sashen ba koda wasa,muqullan ma tunda ta ajesu a locker bata sake bi ta kansu ba,bude locker din tayi ta dauki keys din ta fice zuwa sashen nasu.




Gab da zata shiga wayarta tayi ringing,saita dakata tana dubawa,hanan ce,dariya ta dan saki tasan cewa akwai wata a qasa tunda ta kirata,dagawa tayi da sallama ilai kuwa karadin hanan din ya cika kunnenta,ko gaisawa bata tsaya sunyi ba tace
"Nida saddiq...yace na cikashi da zancan aysha naqi na hadaku ku gaisa,na gaya mishi ba laifi na bane,ke din ce kifin rijiya ce baki zuwa ko ina" dariya aysha tayi
"Bani shi mu gaisa" miqa masan tayi ya amsa suka soma gaisawa,sosai yake da so jama'a kamar hanan din,sun dan taba hira kadan kana daga bisani ya zolayeta kan ta kula mishi da gimbiyarsa,sannan zayazo a raba gardama kan wanda yafi wani son dan uwanshi,shi yace ya fi sonta ita tace shi,da dariya aysha ta katse kiran jin musu na niyyar barkewa tsakanin hanan din da saddiq,tana dariyar abin ta bude sashen ta shiga,abu na farko data soma cin karo da shi daya daga cikin window size na hoton khalipha wanda ya fito tarrr kamar kayi masa magana ya amsa ka,fuskarshi qunshe da murmushi wanda hakan ya sake bayyana kyanshi,gabanta ne yadan fadi,sai taji kaman shine a gabanta yake kallonta,dauke kai tayi taci gaba da shiga sai kuma ta kasa,sake maida kanta tayi zuwa ga hoton,ta soma takawa a hankali zuwa sashen da hoton yake.




Ta jima tsaye gaban hoton tana kallonshi,sai ta sanya hannunta a hankali ta shafi qafafunsa,hakanan tausayinsa taji ya kamata,yabar gida yabar ahalinsa duk saboda ci gaban familynsa,tsahon watanni baiga mahaifiya mafi soyuwa a gareshi ba ko wani dan uwansa,cikin ranta ta soma jera masa addu'ar samun dacewa da nasara a rayuwarsa,ba shakka khalipha wani babban jigo ne a rayuwarta,yana daya daga cikin shika shikan da komai nisan rabuwa komai tsahon lokaci ko zamani bazaiyiwu ta manta da wanzuwarsa ba,iyakacin zamanta a gidan ta shaida jatumtarsa a rayuwa,jarumi ne kuma tsayayye na gaske,zata so taji wani abu daga tarihin rayuwarshi daga bakinsa,ta tabbata akwai gwagwarmaya ba qarama ba,a hankali ta sauke hannunta ta juya,sai hanan da saddiq suka fado mata a rai,murmushi ta saki tana ayyana dadin da soyayya ke da shi,sai ta dinga gwada kanta a matsayinsu,wani tunani ne ya fado mata a rai wanda ya tilastata daga kai ta dubi daya hoton khalipha dake gabanta,wanda yana zaune ne saman wata irin kujera ya dora qafarshi daya kan daya,kai ta girgiza tana gayawa kanta bamai yiwuwa bane,khaliphan?,da hanzarin ta watsar da tunanin ta shiga nazarin sashen,akwai 'yar qura bamai yawa ba,wanda hakan ke alamta ana shigowa a share lokaci lokaci,sosai ta gayara wajen tsaf,take komai ya koma fes,ta rurruf abubuwan da tasan zasu qara qura ta sake dauraye jikinta ta debi kayan da take buqata tabar sashen.




🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶




"Wayyo bayana" aysha ta furta bayan ta dago daga durqushen da tayi tana hada kayanta,ajiye littafin hannunta hanan tayi tana dubanta
"Wai karkicemin wannan satin duk sai kin rigamu tafiya gida?da alama ma dai ni kadai zaku bari,don maman hunaifa ma jiya najita tana waya da abban hunaifa abuja zatayi weekend" Sai data samu gefan gadonta ta zauna tana miqe qafarta sannan ta amsa mata
"Wallahi haka kawai wannan karon duk hankalina yayi gida....ki shirya don Allah mu wuce wajen wankin kan nan sai nayi zan wuce"mirginawa hanan tayi daga kwancen da take zuwa daya bangaren
"Wallahi yau kasala nakeji da gajiya...anya zan iya zuwa kuwa?" Harararta ayshan tayi
"Baki isa ba kuwa,ki tashi kawai ki shirya" hakanan hanan ta miqe a kasalance ta shiga wanka ta fito ta shirya suka fice.




Tare suka jero suna 'yan hirarrakinsu jifa jifa,idan sunga wanda suka sani su tsaya su gaisa wani lokaci har sukan dan taba hira kafin su wuce.




Dab da zasu wuce wata mota hanan ta taba aysha
"Gafa mutumin can,kinga mota zai bude amma ya tsaya satar kallonki"
"Wafa?" Ayshan ta tambaya tana duban hanan
"Waye banda daddy huguma,kinsan Allah gayen ya hadu,a nan makarantar yake geology ya karanta suka riqeshi suka bashi lacturing,da qyar ma idan ba zuwa sabuwar semester ku hadu da shi ba,ki bashi dama kawai aysha wallahi,ya hada komai fa" kallonta ayshan tayi taja tsaki tana kauda kai,gabanta taji yana faduwa
"Kekam hanan kinga dacewar haka?,kinsan wayeshi ne?,pls karki sake wannan maganar" dariya da mamakinta take boyewa,batasan me yasa ayshan ta tsani ayi mata zancan wani ba,ta tsani ace wani na sonta
"Allah ya baki haquri,amma maganar gaskiya karki bari wannan damar ta subuce miki,ina miki sha'awarsa"
"Toh naji" ta fada da alama ta qosa da zancan
"Aysha sai yaushe zaki bawa mutane dama?,waikekam soyayya bata burgeki?,kinsan bakasan dadin rayuwa ba harsai kaso kaima ansoka?,rayuwar da babu soyayya nikam ina tunanin wace iriyar rayuwa kenan?" Hanan ta fada da alamun da gaske take magana,shuru aysha tayi tana saurarenta,saita dinga jujjuya maganar hanan din cikin ranta.




Gab da zasu fice daga makarantar motar saddiq ta sako kai,ja hanan tayi ta tsaya tana dubanshi cikin murmushi sanda yayi parking ya fito
"Wato ba zata kayi niyyar yimin kenan?"murmushi yake yana dubanta
"Tuba nake ranki ya dade,na kasa zama ne kawai naji inason ganinki"
"Yayi kyau,kaman kasan tunaninka nima nake"
"Zuciya daya"
"Ruhi daya" sai suka sanya dariya shi da ita,aysha na gefe tana kallonsu,burgeta suke sosai yadda suke son junansu
"Ranki ya dade" saddiq ya ce da aysha
"Tare da naka..Allah yasa ba zuwa kayi ka hanata rakani ba"
"Ni na isa,ina zuwa?"
"Zamu wankin kaine"
"To bismillah ku shigo nayi rakiya" ba musu suka qarasa jikin motar,hanan ta shiga gaba aysha na baya yaja suka tafi,cikin motarma hirarsu suke,ba komai aysha keji ba,wani lokaci saidai taji dariyarsu har suka isa wajen,cewa yayi zai jirasu,saboda haka tabar hanan cikin motar ita ta shiga aka soma yi mata.


Awa uku aka gama musu komai har lallen,yayi kyau kuwa fiye da ko yaushe ita kanta taga haka,kaman wata amarya haka tayi fes tayi kyau,wannan karon haka tabar gashinta,maimakon daa da ake mata manya kalba guda biyu ko uku,ta saki jelarta kota hadeta da ribbom.


Da suka dawo ma tare ta barsu ta shige hostel din,ta taras maman hunaifa ta dawo harta musu abinci,sallah kawai tayi ta zauna suka ci abincin suna hirarsu har zuwa sanda hanan ta shigo.


🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶




Qarfe goma drivern gidan anni ya iso
"Toh sai Allah ya kaimu monday kuma"
"Anya ko zako ma dawo monday din kuwa?" Hanan ta fada tana tsokanarta,waiwayowa tayi tana kallontq cikin harara
"Me kika gani?" Dariya tayi
"A'ah babu komai,wannan zumudi haka,kodai kinyi kamu ne?"tsaki ta saki tana dariya
"baki da amsa"
"Idan tayi wari maji" hanan ta fada tana qyalqyalewa da dariya,har bakin mota hanan din ta rakota sukai sallama,don maman hunaifa tun safe ta fita.




Cikin girmamawa dirvern ya fito xai amshi kayan hannunta ta dakatar da shi
"Yi zamanka malam shehu" ba qarami girmansa take gani ba,saboda a qalla ya kusa haifarta,haka shima ba qaramin girmamata yake ba saboda yadda take ganin mutuncinsa,cikin mota suna tafe suna hira jifa jifa,duk da rabin hankalinta na kan dan qaramin littafin dake hannunta,wanda duka lacture din jiya ce.




Da yammaci suka iso gidan,kaman kullum anni na zaune a falo tana kallon africa t.v 3,dukkansu fuskokinsu qunshe da murmushi,anni ta amsa sallamar ayshan
"Lale da 'yan makaranta"
"Anni sannu da gida" ta fada tana zama qasa kaman yadda al'adarta take yawanci idan annin na zaune kan kujera
"Yauwa ayshatu" gaisawa sukai cikin kewar juna annin na tambayarta hanya da sauran al'amura,daga bisani annin da kanta tace taje ta huta,ba musu kuwa ta wuce dakin ta,wanka tayi tana saman gado zata shafa mai a nan bacci yayi awon gaba da ita,bata farka ba sai la'asar,shi dinma kiran wayar aliya ya tada ta
"Kin dawo kenan"
"Tun azahar ma,wannan satin duka makarantar naji ta isheni gida nakeso"
"Da kyau,ina hanya to ki jireyeni" cikin zumudi ta amsa mata dan sun dan kwan biyu basu hadu da aliyar ba,alwala ta daura ta shafa mai da hoda ta sauya kaya ta tada sallah sannan ta fito falon.




Amal ce kawai zaune a falon da alama bata jima da zuwa ba don har mayafinta na kafadarta,hada ido sukai da aysha,ayshan ta sakar mata murmushi,yayin da gaban amal din ke faduwa,kullum rana ta Allah ayshan sauyawa take kamar wadda ake canzawa,komanta qara kyau da fitowa yake kaman ba ayshan data sani watannin baya da suka shude ba,duk sa cewa ko dacan dinma ayshan a hade take,saidai kanta ya bude sosai fiye da yadda ta santa
"Amal ce?"aysha ta fada tana murmushi
"wallahi" ta amsata a taqaice tana jin kishinta na ratsata,tana satar kallon yadda fatar ayshan tayi kyau,jan lallen yatsunta yayi matuqar zama ado a gareta.
"Kwana da yawa....sau wajen hudu ina zuwa weekend bana samunki"
"Nima makaranta na koma banda cikakken lokacin kaina"
"Ma sha Allah,abu yayi kyau Allah ya taimaka" ta fada cikin fara'a ba tare da ta kawo komai ranta ba ta wuce kitchen.




Atika ta samu a kitchen tana yunqurin hada abincin dare,da fara'a ta tari ayshan
"Habawa,shi yasa tun yau naji gidan ya saki,ashe uwar masu gida ce ta iso" dariya tayi tana zama kan kujerar dake kitchen din
"Baaba atika kina kaini inda banje ba"
"Ai gaskiya ce,na jima banga mutum kamarki ba,Allah ya baki dama kina gida kamar wannan amma baki dauki kanki a bakin komai ba,magana ta Allah ba ganin ido ba halayenki masu kyau ne"idanu ta lumshe,tana qissima inama ace ita da mahaifiyarta ke wannan hirar?,inama ace itace ke yabonta kamar haka?
"Allah ya sanyani na zama mafi alkhairin abinda kuke zato,kuma ina roqon Allah karya kamani da abinda kuke fadi....me zan samu baba banci komai ba"
"Yau dai sinasir na yiwa hajiya,kinsanta da son sinasir,zakici ko a dafa miki wani abun?" Kaita kada
"A'ah baba karki wahal da kanki,kai bawa duk abinda ka samu aici kake,bani sinasir din" murmushi baba atika ta saki ta soma zuba mata,halayyar aysha na burgeta qwarai,kusan tayi gadon anni(kira da jan hankali a gareku masu 'yan aiki a gida ko gurin aikin da kake da wasu a qarqashinka,abinda ke qarawa mutum girma farinjini da kwarjini shine ka nuna qasqantar da kai dakai da tawali'u a inda ka isa kuma kake da girma ka nuna kai ba mai girma bane dai dai kake da kowa dake wajen,wannan abun na qaramin qara soyayyarka yake a zuciyar na qasa da kai ba,kuma dabi'ace mai kyau,koyi ne da halin ma'aiki,yadda yaje zama cikin sahabbansa kai bakace shine ba banda haiba kwarjini cikar zati da kyan da babu mai yashi da Allah S W T ya bashi,Allah yasa mu dace).




A kitchen din ta cinye abincin tas,tana ci suna hira,muryar Aliya data jiyo a parlour ya sata fitowa,tana zaune suna hira da anni da alama bata jima da shigowa ba,amal na zaune gefensu tana chart saidai rabin hankalinta na kansu,bayan sun gama gaisawar anni ta miqe ta koma samanta ta basu waje,dab da aliya aysha ta zauna tana dala mata duka a cinya
"Autar mama....kinga yadda kika koma me mama ke baki kina cinyewa ke kadai saboda rashin amana koki ragen?" Dariya aliyan ta saki
"Wai don karna tambayeki shine kikai riga malam masallaci,me kuke ci a wudil,koda yake nasan aikin anni ne wannan,wannan ai saikisa angon ya kasa shaidaki idan ya dawo" baki aysha ta rufe da hannunta
"Wallahi sashen masharranciya ce ke"
"Errrrhmm....nikam inason tambayarki dama wanne mai kike amfani da shi yanzu,naga kanki kamar ba haka yake ba sanda kikazo gidan nan" cewar amal bayan tayi gyaran murya,duban jelar gashin ayshan take har tasa aliya ta kalla itama
"Ba wani mai,kawai na samu gidan gyaran gashi mai kyau ne"
"Kuma ma dai abun sa'a ne" aliyan ta fada ba tare data dubi amal ba,tunda aysha taga haka tasan neman magana ne ya motsa da biyu aliyan ta fada,kama hannun aysha tayi
"Muje ciki don Allah kisha labari" miqewa tayi suka wuce dakin ayshan,suna shiga aliyan ta dubeta
"Wai har yanzu wannan 'yan zaman kisan daben suna zuwa dama?" Baki ayshan ta tabe
"Eh,ina ruwanki dasu?" Dariya ta saki,tasan halin ayshan sarai da rashin son yin zancan wani
"Tabdi,ai wallahi da nice da tuni na saita musu hanya,suna zaune ina da miji kamar khalipha yana giftasu?" Dariya ta bata sosai saboda yadda ta gwada da hannunta,jan hannunta tayi ta zaunar bakin gado
"Ce miki akayi mijina ne,yayana ne" wata harara aliya ta watsa mata taja tsaki
"Kici gaba da fadin haka,kina zaune zw'a farauce miki shi zakice na gaya miki" dariya ce ta subucewa aysha ganin yadda aliyan ta haqiqance bilhaqqi,aliyan zata maida mata amsa ta katseta ta hanyar daga mata hannu
"Yi haquri anty aliya ina zuwa" ta fada tana dariya sannan ta fice ta samo mata abin motsa baki ta dawo
"rannan naje imam wali dubiya....kinsan wa na gani?" Kai aysha ta girgiza tana zubawa aliya lemo sannan ta miqa mata,amsa tayi tana qunshe dariya
"Wai asma'u a third gate tana jiran adaidata sahu,dama tana hawa motar haya a rayuwarta?" Aliya ta qarashe tana bushewa da dariya,kallonta aysha take sosai,labarin bai mata

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login