Showing 141001 words to 144000 words out of 184891 words
Chapter 48 - DAURIN BOYE Complete Document by Safiya Abdullahi Huguma.txt
kusantarsu dangin ubansu basu isa suyi ba,saidai uwa ta gari da Allah ya basu ya santa zakayi zaton komai bai faru ba,mus'ab na girmama haidar kamar yadda haidar ke bawa khalipha girma,yana game a wayarshi ya isa wajen yaja plate ya zubo musu ya sauko dashi,da yake sau tari sukanci abinci kwano daya idan lokacin cin nasu yazo dai dai,annin ta riga ta saba musu da haka tun lokacin quruciya.
Da d'ai d'ai amal da rahama suka dawo wajen bayan sun gama cin abincinsu,banda maryam data wuce daki tana amsa waya
"Tashi mu wuce" khalipha ya fada bayan ya miqe tsaye
"Tun yanzu?dare baiyi ba da yawa" Rahama ta tambaya idanunta na kansu
"Mun dawo daga tafiya akwai gajiya da take buqatar a wareta" khaliphan ya fada yana hade fuska kamar ya manta anni na wajen,aysha kaman ta zura da gudu haka taji saitaja mayafinta ta sake rufe kanta
"Anni sai da safe"
"Allah ya bamu alkhairi,mu tashi lafiya ayshatu"
"To anni" haka kawai taji kallon da suke binta dashi bai mata ba,tana sane tace
"Anty rahama,sister amal saida safe.....kinsan ya khalipha da son jiki tausa yace yana so" aysha ta fada can qasa saitin rahama wanda tafi kusa da ita,ta yanda idan ba rahaman da amal dake kusa da itaba babu maijin abinda tace,saidai ta makaro,tuni khalipha dake tsaye ya jiyo abinda ta fada din,wato itama ta iya tsokana kenan da cusa haushi ko?,dukkansu zuciyoyinsu kamar zasu fito,basu sake magana ba har suka ida fita daga
Shi ya fara shiga sashen,ya fada saman kujera ya ware hannayensa kan makarin kujerar yana dubanta sanda take shigowa,gab da zata wuceshi ya sanya mata qafa take ta harde tayo kanshi gaba daya,hannunshi yasa ya tallafeta cikin jikinsa
"Me zaki wuce ciki kiyi?,kefa kika ce tausa zaki yimin ko?" Cikin mutsu mutsu ta girgixa kanta tana son qwatar kanta saboda riqon tsauri da yayi mata
"Ohk,yanxu kuma don kinga babu idanunsu zaki canza magana kenan?"
"Kai ka sani na dinga musu haka"boyayyen murmushi ya saki
"Over act kikayi,tunda kuma kika sakamin rai saikin yi,dama am too tired" dage mata yayi kan sai tayi masa idan ba haka ba shi zaiyi mata,da qyar ta kubuta bayan data fake masa da bata karanta komai ba,bedroom ta gudu,ta jima zaune a can sai data dai daita mode dinta sannan ta fito,kanta na a qasa tace
"System dina pls ta rannan..."
"Wadda na kamaki kina kallon fina finan soyayya?" Ya tambayeta ba tare daya dubeta ba,saita kasa amsa mishi
"Nayi seezing,bana so ki sake amfani da ita" mamaki ne ya kamata,me tayi da zai mata seeizing na system?,itakam bata sani ba,saidai koma meye yafi gaban haka saboda haka batace komai ba kawai ta juya ta samu wani guri can daban ta xauna tana duba abinda ya kamata ta karanta.
Sha biyu saura na dare ta tura qofar bedroom din,ga mamakinta saita sameshi zaune dirshan saman gadon da system a gabanshi,tayi tsammani yayi bacci ne,taqi shigowa da wuri don kada abinda ya faru jiya wanda batasan ya akayi ya faru ba ya sake maimaituwa,ta farka ne kawai ta ganta cikin jikinshi,wanda kuma da alama itace ta baro side dinta ta dawo nashi.
A hankali take takowa har zuwa bakin gadon,ba abinda zata yi sai kwanciya kawai,don haka ta aje litafanta kan bedside din dake daura da ita,ta zauna a side dinta ta hada tafukan hannunta ta soma addu'ar kwanciya bacci,bayan ta gama ta hura ta shafe jikinta sannan ta maida duka qafafunta saman gadon,gyaran murya taji yayi wanda ya danja hankalinta,saidai bata juyo ta dubeshi ba
"Bacci zakiyi?" Ya tambayeta yana ci gaba da aikinshi,kanta ta gyada sannan tace
"Eh"
"Gobe zaki koma,hira ya kamata muyi" ya furta a dake kaman bashi yayi maganar ba,dan boyayyen murmushi ta saki
"Cikin wannan satin nima zan koma so ba lallai mu sake haduwa kafin sannan din" ya kuma yin maganar yana kashe system din,rasa amsar sa zata bashi ya sanyata yin shuru,bai sake cewa komai ba shima sai daya kammala komai ya dauke daga wajen sannan ya jingina bayanshi sosai da fuskar gadon bayan ya kara pillow
"Dame dame kike da buqatar tafiya dashi?"
"Babu komai,ina da komai" ta fada cikin sanyin muryarta data bada wani amo da salo ma daban saboda shurun dare da yanayin duhu duhun dakin,wanda hasken wayarshi daya haske fuskarshi mai saye da gilashin qarawa ido gani ya haska fuskarshi sosai,dan yatsanshi ya saka ya gyara glass din sosai sannan yace
"Come closer" daga kanta tayi ta dubeshi,yanzun ma kamar bashi ne yayi maganar ba hankalinsa nakan wayarshi,tsahon sakan goma kafin ta matsa kadan ta rage tazarar dake tsakaninsu ba mai yawa ba can,pillow din dake gefanshi ya dauko ya maida side din da take sannan ya nuna mata inda yake nufi da yatsa ba tare da yace komai ba,a hankali ta zauna inda yace din,tana gab dashi don tana iya jiyo fitar numfashinsa,wanzuwar pillow din a wajen kawai shiya hana cinyoyinsu gogar juba,wayar hannunshi yayi mata nuni da ita saita maida kallonta kai,tana kallonshi ya tafa (www.rahamalls.com) ya shiga,ba dadewa link din ya bude,jerin kayan da store din na rahamalls suke saidawa ya bude,kaya ne babu wanda babu a kai,yaci gaba da dubawa har yazo bangaren computers
"Dubamin...wacce ce tafi kyau?" Ya fada yana scrolling down,da ido ta dinga bin hotunan system din tana kallo,dukka bata banxa ba wadda batayi kyau ba,dai dai kan wata ash tace
"Irinta maman hunaifa...."sai kuma tadan kame bakinta batasan cewa a fili ta fada ba
"ohkey"ya fada yana shiga page din gaba wanda dinkakkun kayan maza suka bayyana,yayi order din wanda zaiyi ya kashe data dinsa,har a lokacin tana zaune a wajen
"bayan na tafi?,me zaki dinga tunawa dani?" So take ta daga kanta ta kalleshi tada da wanne yanayi yayi maganar,amma nauyi da kwarjinin idanunsa dake bisa kanta sun hanata dagowa,a sanyaye tace
"Babu"
"Ni kuma akwai" ya fada kana yayi shuru yana ci gaba da dubanta,batasan sanda ta furta lafazin
"Mene shi?"
"Yanzu nake so ki barmin abu daya da idan na tuna zaici gaba da debemin kewa duk tsahon lokaci" hannunshi ya miqa mata sannan ya kafeta da idanunshi sai ta dan tsaya tana kallon hannun nashi,ya qagu yaji dumin jikinta mai dadi,tunda ya taba dandanashi sau daya har yau feelings din yaqi barin jiki da qwaqwalwarsa.
A hankali ta dora tafin hannun nata itama saman nashi kamar yadda ya buqata,sosai ya rintse hannun kafin ya jawota ta fada jikinsa yasa hannayensa ya rufeta ruf yans jin dumi gami da shaqar daddad'an qamshin turarenta dake tashi a jikinta,dukkaninsu kowanne yana iya jiyo bugun zuciyar kowa,ba wanda yake wani qwaqwwaran motsi a cikinsu kowa yayi luf jikin dan uwanshi.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
A kunyace take hada dan abinda tasan tana buqata wanda dashi zata tafi wudil,ta rasa me ya fisgeta jiya har ta amsa tayin khalipha,duk inda yabi saita kaicewa ganinsa,har ya kammala uzurinsa cikin dakin ya rigata fita,batasan meye manufarshi ba akanta shima me yake nufi?,abu guda ta sani har sukayi aure suna kallon juna ne a matsayin wa qanwa.
Riga da skert ne a tamfa a jikinta,qafarta plat takalmi ne mai igiya wanda mahadi ne da jakar hannunta mai azabar kyau da tsari,hijani ta sanya mai hannu iya gwiwa,wanda yake hade da niqab,saita saka glass din da kanyi amfani dashi lokaci zuwa lokaci domin ado,harabar gidan take takowa bayan sunyi sallama da anni,yau duka cikin mutanen nata babu wacca ta gani,kodon da wuri ta fito oho.
Motocin khalipha ta gani jere a harabar gidan,tayi zaton wani guri zashi shima,saita dan tsaya tana duba ta inda zata hangi malam shehu,don wani lokaci shi ko haidar dama wani ke kaita.
Dai dai lokacin khaliphan ya fito da dan sassarfa daga sashen ma'aikatan gidan,da alama wata 'yar ganawa yayi dasu,yana tafe yana duba agogonshi,caraf ya kamata tana satar kallonshi,ta kalleshi ita kanta batasan yakai sau nawa ba,shigarsa ta yau ba qaramin kyau tayi masa ba,haka uwa uba take jin wani ba dadi gami da wassafa adadin kwanakin da zata dauka kafin ta sake ganinshi.
Dauke kanta tayi ita ala dole saita tayi pretending kan cewa bashi take kallo ba,wani sashen na gidan daban ta maida kanta tana kalla,saidai haka kawai zuciyarta taqi biyota,ji tayi an riqe jakar hannunta,abinda ya sanyata waiwayo kenan ba tare data shirya ba,yana tsaye gabanta ita yake kalla,saidai fuskarsa a dinke take,ya mata kwarjini sosai,hakan ya sanya gabanta faduwa,da hannu ya mata nuni data wuce,jakar daya riqe ta kalla alamun ya sakar mata,sai ya dage kafadu yana gaya mata ina ruwanta,sakin jakar kawai tayi tayi gaba,da sauri nasir yaronshi dake riqe masa muhimman abubuwanshi duk sanda zasu fita ya matso da sauri zai karba saiya dakatar dashi.
Gab da zasu isa wajen motocin haidar ya faka tashi motar ya fito,tuni ya riskesu,cikin girmamawa ya gaida khalipha
"Barka da safiya yaya"
"Barkanka....ina fata ka kammala yadda ya dace?"
"In sha Allahu" ya amsa yana murmushi yana duban aysha sai ya kallo khalipha
"Na fito da motane na kaita?"
"Na hutashsheka yau" ya fada yana bude mata murfin motar da kanshi
"Yaya ni nake kaita dama ai,yauma bansan da wuri zata koma bane shi yasa na fita" tsayawa yayi da abinda yake ya zubawa haidar ido,shakka ta dan shigeshi,don khalipha ba daga nan ba wajen kwarjini,ko dan uwanshi namiji ya zubawa ido sai yaji ya a jikinsa
"Sorry yaya...." Ya fada yana hade hannyensa waje guda
"Anty Allah ya kiyaye hanya,asha L....." Sai ya juya da sauri yana dariya zuwa cikin gida,cikin zuciyarshi yana tuna hirat da sukayi jiya shida anni bayan barinsu khalipha wajen
"Haidar....kayi a hankali"
"Me ya faru anni?" Ya tambayeta yana tsayawa da bare bayan wayarshi da yake
"Yayanka ya fara kishinka ne" idanu ya zaro
"Kishi anni akanme?" Murmushi ta saki
"Akan matarsa" idanunsa a waje yaci gaba da duban annin yanason yaji qarin bayani
"Ya kamata ka janye jikinka zuwa yanzu,saboda ya fara soyayya,kasan kuwa illar da soyayya kewa wanda ya fada cikinta ba tare daya sani ba ba kdan bane,zaiyita abubuwa gq zaton na wanda yake kallonsa ko yana cikin hayyacinsa,saidai ina lamarin ba haka bane,shi sha'anin soyayya ya wuce duk tunani" ta qarashe maganar tana tubawa kanta da nata masoyin alhj sa'id,da irin gwagwarmayar da suka fuskanta kafin su cimma gaci
"Lalle ya khalipha ya hau network,ni anni kawai ina respecting din anty saboda na jima banga mai shekaru irin nata dake da hankali da nutsuwa kamar haka ba,sannan tausayinta nake ji tun daga randa na fuskanci tayi shigen tamu rayuwar,uwa uba ina taya yaya kishi ne saboda nasan halin sa'o'inmun nan,suna qyalla ido suka ganta ita kadai ba wani gefanta tsaf zasu iya yiwa ya khalioha shigar burtu....hajjaju anni da alama an tuna da,ya kamata na sanarwa mus'ab harma da ya khalipha muzo mu kwashi darasin soyayya...." Ya qarashe yana dariyar zolaya,daquwa ta watsa masa
"kaci gidanku,tashi ka bani waje ja'iri" yana dariya ya bar wajen yayin data bishi da kallo,na shakka soyayya bata tsufa,don har kwanan gobe bata fasa son sa'id dinta ba,da wannan tunanin haidar ya qarasa cikin gida,lallai zancan annin ya tabbata,tunda suka taso da yayan nasu basu taba ganinshi yana soyayya ba,ah lallai abun zaiyi matuqar armashi,zaiso yaga ya za'a buga wannan game din mai qayatarwa.
48
Ajiyar zuciya ya sauke mai sanyi sannan ya dauke idonsa daga binta da yayi da kallo sanda ta gama shigewa cikin hostel din nasu,a hankalibya sauke hannauensa ya shige motar da tuni aka bude masa murfinta,sauran suma suka shiga tasu suka tashi motocin suka bar wajen.
A tsaye ta sameta a varender din dakunan nasu ita da wata maqociyar dakinsu surayya,da alama hira suke,saidai idanunta na can farfajiyar harabar da motocin khalipha sukayi parking kafin su tashi
"Idonki kenan?" Hanan ta fada tana murmushi gami da jifan ayshan da hararar wasa kafin daga bisani ta nufota
"Kedai bari kawai hanan....sabgogi ne suka sako kai sai godiyar Allah" karbar daya daga cikin qaramar jakar dake hannunta tayi
"Dakin ba dadi gaba daya,kullum hunaifa na bakin gadonki"
"Allah sarko daughter na,yau dai zan ganta" ayshan ta fada tana zama gefan gadonta
"Inafa zaki ganta uwarta ta maidata wajen kakanninta saboda tsabar cin zali,idanu aysha ta zaro
" kai hab,badai yaye ba ai bata rufa shekara biyu bafa"
"Hmmm,kefa mmn huanifa dadi miji" dariya suka saki baki daya kafin daga bisani hanan ta tsagaita
"Ke tsaya....idanuna sun gano gulma fa,wanne handsome dinne ya ajeki haka da jerin motoci?,ko zancena ya tabbata ne?" Murmushi aysha ta sani tana tuna khalipha,yadda da fari yayi kaman baisan sunzo ba,bai bude mata qofa ba bare shima ya fito sun jima zaune a haka
"Yaya na ne" idanu hanan ta zaro
"Da gaske?,....kai amma ma sha Allah,hala dai duka gidanku kyawawa ne" ta tambayi ayshan tana dariya,tsaki ayshan taja itama tana dariya
"Ban sani bani,naxo baki bani komai ba kin cikani da tambaya?,me zan samu" dariya hanan ta saki
"Kinzo a sa'a kuwa,dazu saddiq ya tafi,ungo ci iya cinki" ta fada tana miqa mata wata leda daje saman drower dinta.
Hira suke sosai a haka mmn hunaifa ta dawo daga lacture ta taddasu
"Saura qiris na biyo sahu ko zancan hanan ne ya tabbata wani ya qwamushe mana ke" dariya sosai aysha tayi
"Harda ke mmn hunaifa?"
"Eh to ai gaskiya ne,budurwa mai kyau da aji kamar ke ai dole a samu 'yan takara da yawa" ta fada itama cikin raha,sun jima zaune a nan suna hirar yaushe gamo,aysha nata yiwa mmn hunaifan qorafi kan baro hunaifa gida da tayi
"Yana iya,abbanta yace na barta itama kakartata tafison haka"
"Ai shikenan" aysha ta fada tana dan bata rai.
A hankali ya tura qofar falon sannan ya kunna qayayen wutar haske ya gauraye wajen,takawa ya dinga yi a nutse har ya isa cikin falon ya zube saman kujerar cike da gajiya.
Hakanan yake jin sashen duka ya masa wani iri,sai yaji ya masa girma,a hankali idanunsa suka kai kan takardunta da tayi amfani dasu jiya dake aje a wajen,sai yaji kamar shi daya yake rayuwa,idanunsa ya lumshe yana futar da iska akai akai daga bakinsa,dalili kenan daya sanya ya dade sosai hira wajen anni,a haka ya shafe wasu lokuta kafin ya miqe ya tarkata ya shige bedroom dinsa.
Sai daya gama komai ya haye gadonshi sannan ya rasa abinda yake damunsa,saiya juya daya side din idanunsa kan side din da take kwanciya ko yaushe,filonta da abun rufarta yana nan a wajen,hannu ya miqa ya janyo filon ya cusa kanshi a ciki,qamshin turarenta ya shaqa har cikin kanshi,qamshine mai sanyi da tsayawa a rai,sai ya mirgina ya koma side din nata,baisan me yake damunsa ba rashinta a dakin ya tsaya masa a rai,miqewa yayi ya zauna dirshan kan gadon,ya lalubo wayarshi ya kunna ya tafi nemo lambarta.
Dai dai lokacin da itama take kwance rub da ciki kan gadonta,dakin ya dauki shuru,mmn hunaifa tayi bacci,sai muryar hanan dake waya da take iya jiyowa kadan ladan,duk da bata jin me take fada,littafinta ne a gabanta tana haskawa da torch din wayarta son sun kashe wutar dakin tana duba amsoshin tambayoyin data amsa dazu.
Gida biyu hankalinta ke rabuwa,ko daya bata jin dadin kwanciyar bare karatun da takeyi,bata wuce sakan goma bai fado mata a rai ba,saita aje wayar da takardar hannunta ta qanqame filon da take kai tana sauke ajiyar zuciya.
Qarar wayar tata ce ta sanyata daga kai taga mai kiran,kamar tasan number,haka kawai gabanta ya fadi,ta kira sunan Allah sannan ta jawo wayar ta daga gami da karawa a kunne,sallama tayi cikin sanyin murya,boyayyar ajiyar zuciya ya saki sannan ya amsa mata ya dora da
"Idonki biyu?" Gyara kwanciyarta tayi zuwa rigingine tana sauke numfashi,muryarshi na ratsata
"Eh,baccin baixo ba"
"Saboda me?" Ya tambayeta kai tsaye
"Karatu nake"
"Uhmmm,ban yarda ba,wanne karatu ne har dare haka,kuma ma ai karatu bai hana barci ko?" Murmushi ta saki kadan,batasan wacce amsa zata bashi ba
"Ina anni?"
"Tana nan qalau,na barta zata kwanta"
"Nayi kewarta" ya sani cewa har cikin zuciyarta ta fada,yana alfahari da irin soyayyar dake tsakaninta da annin,ya sani cewa Allah ne ya masa baiwa da samunta,saidai yana ganin kamar a binda shi yake ji ko yake fata daga gareta babu shi
"Dazu ta gama zancanki...." Shuru ne ya ratsa tsakani kowa yayi shuru yana jin fitar numfashin dan uwanshi,shi ya kasa aje wayar kamar yadda itama ta kasa
"Anni kadai kikayi kewa?" Ya tambayeta da wani salo,'yar kunya taji,idan da kara kam baici tace anni kadai tayi kewa ba
"Harda su haidar..."
"Haidar?" Ya tambayeta yanayin muryarshi na sauyawa,take yaji kishin haidar sosai ya kamashi,itama sai data fada din sai taga kaman hakan baiyi tsari ba
"Harda kaima" tayi saurin fada,amma data duba kiran sai taga ya katse,duk sai taji babu dadi a ranta,ko babu komai akwai sadakinsa a kanta,shi ya soma tsamo ta ya kawota cikinsu,shi ya kamata ta fara nunawa damuwa da kulawa bayan anni.
"Ana soyewa ne,ban taba ganinki kina wayar dare ba sai yau,Allah yasa ta samu" inji hanan wadda ta sauko daga gadonta da niyyar shiga toilet saboda fitsarin daya matsota,murmushi ta mata duk da a duhu ne
"Ke kam Allah ya shiryeki hanan,jeki fitsarinki kawai"
"Aiko nayi zan dawo nabi qwawqwafi,ban yarda da wannan canzawar da naga kinyi ba,tun dazu naga kin saka waya a gaba kin kasa karatun arziqi,gwara naji labari tunda wuri na shirya qawata da kyau,don naga batasan komai game da soyayya ba" bilhaqqi hanan ke maganar,yayin data baiwa aysha dariya sosai,bata sake cewa komai ba ta wuce tana murmushi.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Qarfe takwas da rabi na safe tana shiryawa don tafiya lacture tana duba wayarta,hakanan hankalinta ya karkata data kirashi,rabuwar jiya bata ji tayi mata ba sam,har ta gama shiryawa ta hada tea a cup zallarshi ta kurba donta dumama cikinta hankalinta bai bar kan wayar ba.
Sanda zata