Showing 126001 words to 129000 words out of 184891 words

Chapter 43 - DAURIN BOYE Complete Document by Safiya Abdullahi Huguma.txt

plate din ta soma ci kamar dole,yayin da basma ta tashi daga falon da gudu ta shige daki tana sakin kuka,ta jima tana tausayin anty indo,tun batasan ciwon kanta ba har zuwa yanzu,da kallo ummi ta bita,cikin zuciyarta takewa inna yelwa Allah ya isa,har zuwa yanzu bata daina ganin illar matar da sharrinta ba har ya zuwa yanzu?,saita danne abinda ke taso mata ta zubawa yarn ido dake cin abinci kamar dole,a haka babansu yayi sallama,dukkaninsu suka miqe suka taryeshi,saidai ba yadda suka saba ba,tunda yaga hakan yasan lallai akwai abinda ya faru,ko kuma ta tuna da ayshan ne kamar yadda aka saba,zama yayi saman kujera bayan yaran sun koma sun zauna ya tambaya yana dubam fuskarsu daya bayan daya
"Me ya faru?" Sai suka soma kallon kallo aka rasa mai bada amsa,yusrah ce tayi qarfin halin cewa
"Anty indo ce tazo gidan nan dazu ita da mijinta" zumbur ummi ta miqe tabar falon,saiya bita da kallo har ta shige dakinsu,sake duban yarab yayi yana sake tambayarsu,yusrah ta kwashe komai ta gaya masa,ya jima yana nazari kafin daga bisani yace
"Shikenan kuci abincinku,kar wanda yasa damuwa a ranshi,zanje naga umminku" ya fadi yana miqewa suka amsa da to abba gaba dayansu.


*************************


Zaune take saman kujerar dake cikin dakin hotel din wadda ke daura da gadon baccinsu,tana sanye cikin kayan bacci masu kyau da kauri kanta yana da mayafi,tana nade saman kujerar idanunka kan t.v da suke hasko wani wasa,saidai kusan fiye da rabin hankalinta ya karkata ne kan tunanin abinda ya faru da ita dazun da safe tsakanina da umminta,shawarar da basma ta bata tana mata yawo cikin qwaqwalwarta,khalipha ne yayi clapping hannunshi gaban fuskarta wanda ya dawo da ita daga tunanin data tafi,yana tsaye a kanta yana dubanta
"Kin saba alqawarinmu,kin manta?" Dan siririn murmushi ya subuce daga lebanta,sam ta mance da maganar daya gaya mata kafin ya shiga wanka,saita maxe kawai,yanayin yadda ta basar din saiya burgeshi,ta tsuke dan bakinta waje guda ba tare data sani bama,agogo ya kalla yaci ace sun kwanta bacci saboda haka ya qarasa ya kashe kayan kallon yana fadin
"Time for sleep" maimakon ta tashi ta hau gado saita gyara zamanta a saman kujerar alamar anan take shirin kwana,dubarta yayi sai baice komai ba yaci gaba da shirin kwanciya barci,sai daya kammala komai zuwa sannan tana zaune idanunta nakan system dinshi daya kunne ya aje a wajen zaiyi aiki,tanata nuno hotunan dake cikinta daya bayan daya,takawa yayi ya kashe qwan dakin ya kunna mara haske,a nutse ya qarasa gaban kujerar ya zauna gab da ita har kafadunsu na gogar juna,ta jishi sarai amma sai taqi nuna hakan,tadanja wani littafi dake gefan system din din bataso ya fuskanci kamar tunani taci gaba dayi,system din yaja gabanshu yana dauke idanunshi daga kanta ya soma aikinsa,wanda galibi na office ne wanda ya kamata ace a matsayinsa na shugaba ya dubasu da kanshi.




Idanunta nakan littafin tana bin pages bayan pages tana dubawa,duk rubutun dake cikin littafin yana dauke da kwanan wata da time kowanne rubutu,duk layi daya data karanta mamaki ne yake kamata,bata fahimtar komai saidai rubutun kamar yana bada labari ne kan wani abu daya faru lokaci zuwa wani lokacin,buron hannunshi ya aje ya jingina da kujerar da yake kai gami da hade hannayenshi waje guda,ya lura da yadda ya shiga rudu kadan da mamaki,zuwa yanxu yana ganin ba wani boye boye tsakaninsu,ya kamata tasan su su wayesu duk da bata taba tambayarshi ba,tamkar ma bata damu ta sani ba
"Wanene khalipha?" Ya furta cikin sanyi yana ci gaba da kafeta da idanunsa,da hanzari ta daga kai suka hada idanu,sai taji tambayar tazo mata a banbarakwai,abinda ta jima tana tambayar kanta da kanta kenan,abinda ta jima tana son sani,saidai koda wasa bata taba gigin tambayarsa ko wani nasa ba,saboda tana ganin a matsayin wadda kamar alfarma akayi mata karanta baikai tsaikon ta tambaya din ba,sake dubanshi tayi wannan karon idanunshi nakan biron hannunshi dake jan wasu layuka saman farar takardar dake gabanshi


"Kowanne dan adam yana tare da nashi qalubalen a rayuwa,karki zaci ko tsammaci ke daya kike fadawa matsala ko kika fada,dukkan tsanani yana tare da sauqi haka ubangiji ya fada cikin qur'aninsa" sai yayi shuru yaba ajiyar numfashi,tunaninsa ya luluqa ya koma can baya wasu shekaru da suka shude.




*_muhammad khalipha_*




"Cikakken sunan mahaifinsa shine muhammad sa'id mai goro,haifaffen garin kano dan kasuwa wanda ya shahara da sana'ar saida goro a fadin qasar nan,kusan ya gaji sana'ar ne daga wajen mahaifinsa,wanda yake da mata biyu,uwargidansa ita ta haifa masa yara maza guda biyar ta shidan autarsu mace anty ruqayya,idris shine babba,hamza,habibu,munzali,sai saminu,matarshi ta biyu har ta koma ga Allah yaronta daya wato mahaifina muhammad sa'id,a sannan dukkansu suna ganin babu wani abu da mutum xai iya xama cikin sana'ar saida goro sai duka suka qita,mahaifinsa shiya karbeta hannun biyu ba tare da rainata ba,hakan ya yiwa kakana dadi saboda dama duk cikin yaran sa'id halinshi daban,sai Allah ya sanya yafi qaunarshi,dalili kenan daya saka ya dinga fuskantar qiyayyar 'yan ubanci mai zafi,sai ya tashi a kyare a tsangwame,gashi kome za'ayi masa mahaifiyarsa khadijah da ake kiranta kubra bata daga kai kotace wani abu saboda mutum ce mai tsabar haquri,haka rayuwarshi ta kasance a tsakanin 'yan uwansa,babu wata qauna sai tsabar yan ubanci da nuna banbanci,ruqayya wadda ita ta kasance qanwa gareshi kuma me binsa ita kadai take sonshi,a irin haka Allah ya yiwa mahaifin nasu rasuwa,mahaifin khalipha da innarshi suna gani akayi rabon gadon rashin gaskiya,saidai innarshi bata ce komai ba kamar yadda shima baice ba,suka rungumi abinda aka raba aka basu,sa'id bai zauna ba ya koma kasuwa,wajen abokan arziqi da sukayi zaman lafiya da mahaifinshi masu irin sana'arshi,sanin halayensa na gaskiya da amana,hankali da nutsuwa yasa suka karbeshi yaci gaba da sana'a a qarqashinsu,wato babu maraya sai rago,hakanan babu nakasashshe sai kasashshe,kyau da samartakar sa'id ko daya basu sanya masa girman kai ba ya kama sana'arsa ka'in da na'in,hakan kuwa yayi matuqar taimakawa don nasu raba abincin ci ko suturar sanyawa ba,yayin da a bangaren su hamza kuwa komai ya tsaya cak,rigima ta dinga tashi tsakaninsu,kowa yana ganin shi ya cancanci a baiwa gadonshi dana 'yan uwanshi ya juya,kowa yaja ya kafe kan ra'ayinsa,tilas aka sake gutsuraws kowa aka miqa masa nasa kason,inda mahaifiyarsu daga qarshe ta karbi nata itama dana ruqayya 'yarta,saiyw zamana komai nasu ya soma lalacewa saboda hadin kai,kowa ya tasamma cinye dukiyarsa ba tare da yasan ina tayi ba,hakanan suka dinga fada tsakaninsu kamar zasu yaqi junansu,a haka rayuwa taci gaba da garawa kowanne bangare.




Cikin shekarun da suka biyo baya Allah ya sanyawa dukiyar sa'id da innarshi albarka,yayi kudi mai ban mamaki,yasha fada cewa gaskiya da riqon amana sune ginshiqi kuma matakin nasararsa,sai abu na farko tsoron Allah da kuma bin iyaye,kuma haka yake,duk wani dan adam dake neman cimma wata nasara a rayuwarshi to yayi riqo da wadan nan matakan da taimakon ubangiji zaikai inda yasa gaba.



Zuwa sannan dukka yayyenshi sunyi aurensu,saiya zama babu da talauci ta saukar musu,ci da iyalin na neman ya gagaresu,ruqayya da suke ruqo dalilin mutuwar mahaifiyarsu saita soma passing passing daga hannun wannan zuwa na wancan,a nan ne suka soma rabowa wajenshi,kowa ya soma kwantar dakai dayi masa biyayya kamar zasu kwanta mishi,innar sa'id ita ta umarceshi da kada ya fasa taimakawa kowa a cikinsu ko bayan ranta,to shima mai sauqin raine da haquri,saboda haka sai ya zama shine lalurar duka gidajen nan gida biyar,yayin da sukaci gaba da nuna mishi soyayya da qauna ba don Allah ba,ko sau daya bai taba kawo komai a ran shi mara kyau game dasu ba,haka yaci ga ada taimaka musu har Allah ya kawo rasuwar innarshi,abinda bai sani ba shine a bayan idanunshi murna suka dinga yi da faruwar hakan,suna ganin abu mafi sauqi shine su aikashi lahira su cinye gadonshi,tunda a yanzu baida wani wanda zaici gadonshi tunda ba aure gareshi ba.




Zakaran da Allah ya nufa da cara,suna can suna nasu shirin a sanda Allah ya hada soyayyar sa'id da aishatu buzuwa daga niger,Allah shi yakai sa'id garin ta silar kasuwancinsa suka hadu da ita,soyayya suke da juna tuquru da gaske a lokacin da ayshan tuni yayanta kuma mariqinta ya bada ita ga wani dan uwansu,sam tama mance da wannan batun don bashi takeso ba,ba tsoro ta aika sa'id gaban yayan nata ya gabatar da kansa a wajensa,yayi mamakin yadda aysha ta manta da batun da sukayi da ita,amma ya kauda wannan yayi masa bayanin cewa an bayar da ita,aysha ta sakawa ranta sai sa'id yayan nata ya dage sai wanda ya zaba mata,duk da bata taba fito na fitodashi kan lamarin ba amma duk wanda ya santa yana kallonta yasan tana cikin damuwa,abinci na mata wuyar ci,da yaga dai da gaske take saiya amshi neman aurenta da sa'id yake,amma bisa sharadin idan ta tafi dadi ko wuya karya dawo musu da ita,tace ta amince da hakan,saboda dukka wata nagarta da mace ke nema wajwn mijin aure sa'id nada ita,wanda ko kwatan haka bata gani ba daga wajen wanda yayan nata ya zaba mata ba,duk da yake dan uwanta amma tasan yana da raunin nagarta,akan wannan sharadin akayi aurensu,ya daukota daga nijer zuwa nigeria,yayi mata dukkan wani gata,ya riqe anni da kyau cikin qauna da soyayya da kuma kulawa da juna,itama ta riqeshi da irin biyayyar nan da akasan matan aure nada dashi.
[26/02, 8:54 PM] +234 810 044 6653: 43


Soyayya suke gudanarwa mai kyau da tsafta,ya karbo ruqayya daga hannun 'yan uwanta ya dawo ma da anni ita,hakan ya yiwa anni da bata da kowa dadi,saitake kallon ruqayya a matsayin 'yar uwa,suna zamansu lafiya,yayin da daga gefe guda 'yan uwan sa'id nacin dunduniyarshi duk da cewa shine komai nasu,cinsu,shansu,suturarsu,karatun yaransu,kuka da lafiyarsu da sauransu duk yana wuyanshi,haihuwar farko anni ta haifi muhammad khalipha,nan fa hankulansu suka sake tashi saboda suna ganin sun rasa damarsu,tunda har ya haifi da namiji tasu ta qare,suna ji suna gani suka haqura,suka ci gaba da tatsarshi da tatsar dukiyarshi ta hanyoyi daban daban,yaki halal yaki haram,haihuwa ta biyu anni ta samu mace,ruqayya nata murna ta samu 'yar uwa amma ana yayeta ta rasu,a haihuwa ta uku ma sai aka sake samun namiji haka ta hudu,sai ata biyar Allah ya kawo hajar.......,har a sannan daga dangin anni ba wanda ya nemeta,ita kuwa kullum zancansu na cikin bakinta,saidai tasan bata isa ta matsa kusa da inda suke ba saboda sun mata sharadi tun farko.




Dukkan wani qauna tattali da soyayya tamu tana kan hajar mu duka baki dayanmu,kasancewarta auta kuma mace a cikinmu,hatta da anni na qaunar hajar,yarinyar hallayyarta daban take,tana da haquri,sanyin hali shuru shuru da rashin surutu tun tana qaramarta,tana da biyayya bata da rashin kunya sam.




Hajar nada shekara goma aka aurar da anty ruqayya,mijinta ma'aikacin gwamnatin tarayya ne,tu a alokaci. Gwamnati na tura ma'aikatanta qarin karatu qasashen waje aka turashi ya dauki ruqayya suka tafi,wata hudu da tafiyarsu babban tashin hankali ya samu iyalin muhammad sa'id mai goro,Allah ya daukeshi sakamakon jinya da yayi wadda batagi ta wata guda ba,tashin hankalin da matarsa da iyalansa suka shiga a sannan bazaiyiwu baki ya musaltashi ba,da qyar aka samu kan iyalin nasa saboda kowa a cikinsu a dimauce yake,ruqayya batasan da wannan ba sam saboda a lokacin wayar tafi da gidanka bata yawaita ba ba'asan number ko layin da za'a sami mijinta a sanar masa ba.




Ba yadda bawa ya iya da hukuncin Allah,haka daga bisani suka haqura suka dauki dangana.




Kwana uku kacal 'yan uwan alhj sa'id suka soma zirya kan dukiyarsa da abinda ya bari,yau suce a bada muqullin kaza,gobe suce meye password na safe dinshi,jibi suce a bada muqullin mota,gata suce ina takaddun kaza,a lokacin anni da kallo kawai take binsu,kasancewar har yau batayi normal ba,saboda mutuwar tayi mata duka bana wasa ba,alhj sa'id shine gatanta uwa kuma uba a gareta,ko mutuwar iyayenta bata shiga wannan yanayin ba saboda a sannan bata da wani shekaru duka duka bata wuce shekara uku a duniya ba,haka suka dinga karbar abubuwa d'ai d'ai da d'ai d'ai ba tare data ce musu komai ba,uwa uba bata da kowa bare yace zai tsaya mata,khalipha da yake shine babba a sannan bazai wuce shekara goma sha shida ba,duk da haka yaso tasowa da nuna rashin amincewarsa kan abinda ke faruwa,to amma qarancin shekaru da kuma duk sanda ya doshi anni da maganar maimakon ta bashi hadin kai sai kawai ta saka kuka,tana ganin kamar ta dukiya kawai suke bayan wanda suka rasa yafi dukiyar da duk abinda ke cikinta,hakan yasa ya janye ba mataimaki babu mai qwarara masa gwiwa.




Kafin kace meye wannan sun kwashe duk wata kadara daya mallaka,suka debo kauyoyin bogi da sunan duk dukiyar alhj sa'id banki sun karbe saboda bashin daya cicci kafin barinsa duniya,abinda ya rage musu kawai shine gidan da suke ciki sai motar hawanshi guda biyu,wanda shima easa muqullin akayi,muqullan kuma khalipha ne ya kwashe ya boye sanda suka haukace da nemansu,basu da tsayyaye gakan ya sanya dole suka haqura da qaryar da suka yanka musu,ko a sannan khalipha sai daya qaryatasu ya kuma yi maganganu son ransa saboda yasan duk abinda suka fada qarya be,basu ji kunya ko nauyin idon mahaifiyarsa ba,basuji tausayin maraicinsa ba suka mishi duka suna zqginsa kan bashibda mutunci baisan darajar na gaba dashi ba,yarin dasu kansu sun shaida sanda mahaifinsa nada rai ko kallon banza basa iya masa,bawai don wani abu ba A'ah,duk sharrinka da hassadarka idan kaga iyalan sa'id kasan sun samu tarbiyya fiye da duk wani yaro dake cikin danginsu,basu fara ji a jikinsu ba saida kowa ya watse ya kama gabanshi,aka barsu saisu yasu,suka soma cin abinda tayi saura daga kudin hannunsu da kuma store din gidan,don ko daya alhj sa'id ya gatanta anni bai barinta ta saida komai(kira a garemu mata,kada gata da dadin da miji yake baki yasa ki rungume hannunki kiqi sana'a komai qanqantarta,saboda ba wanda yasan ya rayuwa zata kaya mishi,ko babu talauci akwai mutuwa akwai tsufa).




Zara bata barin dami,sannu a hankali komai nasu ya tasamma qarewa,a nan anni ta shiga tsantsar tashin hankali,yaranta basu saba da wahalar rayuwa ba cikin qaramin lokaci saiga talauci na bayya a jikinsu,makaranta aka korosu ganin anci tearm biyu ba kudin makaranta ba dalilinsa suka koma zaman gida,duk wanda tasan suna huldar arziqi da maigidanta ta nemi taimakonsa amma kowa ya janye hannunshi yaqi tabuka komai,masu ragowar imanin ciki ne zasu taimaka daya biyu suma saisu watsar(irin rayuwar da muke ciki kenan a yanzu,kaci arziqin mutum amma bayan qasa ta rufe idonshi kana kallo iyalinsa su shiga halin ni 'yasu ba damuwarka bane,bamusan cewa kukan maraya cikin al'umma musifa da bala'i bane a cikinmu,kina ko kana katanga daya da maraya zai iya kwana baici abinci ba amma ke washegari kina da sauran da zaki zubar a bola,bamusan tashin hankalin dake jiran duk mutumin da zai kwana a qoshe maqocinsa ya kwana da yunwa ba koda kuwa ba marayu bane,ta yaya zamu rabu da ganin musifu da bala'i a rayuwarmu d'aya nabin d'aya?,ga cin dukiyar maraya data zama ruwan dare,Allah S W T yana fada cikin qur'aninsa mai girma , *_wadan nan da suke cin dukiyar maraya da zalunci haqiqa suna cin wuta ne a cikinsu,da sanju zasu shiga wutar sa'ira_* ,bama dukiyar maraya ba kawai,hatta da haqqin wani idan kaci ranar gobe qiyama duk abinda kaci din haka zaka zo dashi a kafadarka gaban zatin Allah komai girmansa komai qanqantarsa saika dauko shi,gaban mutane da aljannu qwari da dabbobi,tun daga zamanin annabi adamu har zuwa zamanin annabi muhammadu a gaban idanunsu za'a maka hisabi,Allah da kanshi yace *_haqiqa ubangiji baya zalunci dai dai da qwayar zarra_*
Allah ya shiryemu yasa mu gyara dabi'unmu,ya rabamu da cin haram da cin haqqin daba namu ba Allahumma amin.)






Duk wani fadi tashi ba kalar wanda bata runguma saboda farincikin 'ya'yanta da walwalarsu,Duk wannan abun yasan tana yine saboda farincikinsu,tun quruciya yaro ne mai son iyaye da son faranta musu,shi yace ta daina saida komai nata,zai fita yaga yadda zaiyi ya dinga sama musu abinda zasuci din,sam ta hana shi tace bata amince ba,abata haquraba anni sai data qarar da duk wani abu nata mai daraja.




Abu na gaba daya kunno musu kai shine yawan hauro musu gida da aka shiga yi,ga zaton masu haurowar tarin dukiyar da alhj sa'id ya tafi ya bari tana narke a gidan,wannan abun shi ya tsoratasu,musamman anni da take tsoron mutuncinta dana diyarta hajar,hakan ya sanya suka tattara kayansu sukayi balaguro zuwa gidan babban wansu alhj sa'id din wato saminu,wanda dukansu tare suka rabe dukiyar a tsakaninsu.


Sanda suka je matar gidan damai gidan dukansu basa nan,sanin su waye a wajen masu gidan ya sanya mai aikin ta saukesu sauka mai kyau,saidai tana mamakin suturar dake jikinsu,anan suka zauna sukaci suka sha cimar da suka jima rabonsu da ita.




Kafin wani lokaci hajar ta lafe jikin anni bacci ya dauketa saboda sanyin acn dake busowa,wanda rabonta dashi ta jima,a haka matar gidan damai gidan suka dawo tare da alama taren suka fito,tun shigowar saratu ta soma binsu da kallon banza kamar taga kashi,matar da ada kamar zata yiwa ummi sujjada,shima mai gidan abinda ya soma ce musu shine
"Kai yaya?,ya akayi ne mu kukazo yi" da qyar ya amsa gaisuwarmu,ummi tayi masa bayanin abinda ke tafe damu
"A gaskiya gidana babu wajen zamanku,saidai kuyi haquri aisha kuje koda gidan hamza wataqila shi yana da daki spare,ni yarana ma so nake kowa nayi masa nashi dakin daban,saidai ga wannan kwa sayi abinci don wataqila harda yunwa ma ta saku shirya wannan qaryar" ya fada yana ciro dari biyar ya miqa musu,mus'ab zai karba zuciya ta ciyo khalipha

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login