Showing 96001 words to 99000 words out of 184891 words

Chapter 33 - DAURIN BOYE Complete Document by Safiya Abdullahi Huguma.txt

dubeta ba koya kula da kukanta yace
"Ina abinci na?" Shuru tayi masa da fari har na tsahon minti uku
"Ina abinci na!" Ya sake tambayarta karo na biyu cikin qaraji da fushi wanda ya kada mata 'ya'yan hanji ta soma qwallawa rebacca kira
"Ohkey.....wai na tambayeki mana?,na kawo mai aiki ne donta kula dani ko don ta tayaki aiki?"
"Duka gaba daya" ta bashi amsa cikin bacin rai,cike da fushi yake nuna kanshi
"Ni kike baiwa amsa haka kai tsaye?"
"Waikai hamid me yake damunka ne?,ya za'ayi mu rabu lafiya da kai sannan kazo kana min wasu abubuwa kaman dan qwaya?" Dariya ya saki
"Au bakisan dam qwayar bane ni?,yau zakisan ni cakken dan qwaya ne tunda baki iya zama da miji ba" ya fada a sanda rebacca ta gama jera abincin ta fice,don kusan duk a kunnenta ake komai,zama yayi ba tare daya sake dubanta ba ya take cikinsa da abinci sannan ya miqe yasa kai zai fice,har yayi gaba ya dawo da baya
"Ina canjin cefanen da lado yayi dazu?" Cikin mamaki take kallonshi,a arziqinsa bata taba tunanin zai tambayi wani canji cefane ba wanda baifi dubu daya ba,ita a wajenta dubu daya ba komai bace
"Dubu dayan kake tambayata?"
"Ita ba kudi bace?...ko satowa nakeyi?,tashi malama ki dauko min" bacin ranta da mamakin sauyawar hamid dare daya suka sake yawa
"Bazan bayar ba,wannan wane irin nuna talaici ne?,dubu daya kawai?" Mari ya kai.mata Allah yasa tayi gaggawar kaucewa
"Ni zaka mara hamid?"
"Na nuna miki kadan daga abinda zan iya yine idan har na dawo baki nemo min dubu dayata ba duk inda kika kaita" daga haka ya juya ya fice abinsa,da kallo ta bishi hadi da hawayen takaici,a rayuwarta tunda taje ta taba daukar koda dubu dari ta riqe hamid zai magana akao bare dubu daya?,tunda take rayuwar gidansu ta taba baiwa dubu qwaya daya wani muhimmanci mai yawa?anya lafiya ko hamid yake?,kanta bazai iya daukar wannan abun ba haka ya sanya kai tsaye ta soma kiran lambar mommynta



Tana dagawa mummyn ta fashe da kuka,a rikice mummyn ke cewa
"Ke...lafiya asma'u,me ya faru?"
"Mummy hamid ne..."
"Hamid?,me ya sameshi?" Nan ta kwashe duk abinda ya faru ta sanar mata,take mummyn ta cika tayi fam
"Lallai yaron nan mugun dan iska ne,ce masa akayi baiwa aka kawo masa da zaice zai dakeki?,to wallahi daga yanzu ba yarda ba,duk sanda ya sake yunqurin dukanki ki tattara ki taho gida,idan yaso babanki ya masa jan kunne mai qarfi"
"A'h mummy,basai na taho ba,kinsan ma halin daddy baya yarda da irin wannan"tasan sarai ba wai daddyn take dubawa ba kawai,tsabar son miji ne
"Karki sake ki yarda dai ya dakeki wallahi ban lamunta ba,duk abinda ya sake faruwa ki sanarmin don bazan lamunci wannan iskancin ba" da haka suka rabu da mummyn ta aje wayar tana dakon dawowar hamid din.


🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶


A hankali ta turo qofar falon tamkar wadda ke sanda,idanunsa ya dago daga saman screen din system din da yake aiki akai,qwayar idanunshi wanda suke cikin farin gilashi da yake aiki da shi lokaci zuwa lokaci idan zai jima yana kallon screen ta fito tarwai,saidai ta danyi ja kadan gami da lumshewa saboda gajiya da kuma bacci da yake ji,a hankali ta janye tata qwayar idanun kamar yadda shima yayin ya maida kan screen din,cikin muryarta mai sanyi tayi sallama tana takowa cikin falon,tun dazun ya shigo don shi baima zauna ba a falon bayan sun gama cin abinci ya yiwa anni sallama yace yana da aiki da yawa yau,a can ya barta tana jin caftar su haidar tana kwasar dariya a ciki,ta sake sosai yau saboda rahama bata nan ta tafi gidan qanin anni zata musu kwana uku
"Zo" taji ya fadi sanda take shirin gifta shi,saita dawo da baya ta samu waje nesa kadan dashi ta zauna bayan ta nade qafafunta a qirjinta ta rungumesu kamar wata 'yar mage,bai dago ba har sai daya kammala tura wani saqo sannan ya rufe cumputer din ya zare gilashin fuskarsa yasa handkherchief ya goge idanun nasa sannan ya dubeta,kusan a tare suka kalli juna kowa kuma ya janye idanunshi,baisan me yasa sau da dama sukan kalli juna lokaci guda ba su kuma janye lokaci guda
"Meye babban burinki yanzu a rayuwa?" Ya jeho mata tambayar kai tsaye,shuru ne ya ratsa dakin tamkar ba kowa a ciki,ya kafeta da idanu yana karantarta,yayin da ita kuma take kallon tafin hannunta tana matsawa kamar wadda yakewa ciwo,abu biyu,abu guda biyu ne yake mata kai kawo a ranta,burinta na farko a duniya ta samu kusanci yarda da aminci na mahaifiyarta,burinta na biyu na biyu shine ta samu ilimi mai zurfi,ilimin da zai sauyata,ya zamewa rayuwarta garkuwa,karatun da tayi har yanzu bataji ta qoshi ba,har yanzu tana da qishirwarsa,har yanzu bata jin ta cimma gaci.




"Mahaifiyata....ina da burin naganni ni da ita tamkar kowacce 'ya da uwa" sai tayi shuru tana hadiyar zuciya kadan kadan,tana son danne mikin daya taso mata
"Bayan wannan fa?"
"Karatu" shuru ya sakeyi yana nazari,kafin daga bisani ya jawo wata paper ya danyi rubutu ya ninketa
"Kina da jamb?" Kai ta gyada da sauri
"Eh last year nayi,ta na nan"
"Good,kina da zabin makarantar da kikeso?"kai ta kada
"Duk wadda na samu inaso,matuqar dai makaranta ce" kai ya jinjina na tsahon wasu mintuna kafin yace
"Is ohk,zakije wudil?" Kai ta jinjina itama da sauri murmushi na qwacewa daga fuskarta,ganin mafarkinta na nesa na shirin zuwa kusa,burinta na gab da cika
"Ba damuwa" ya fada ta sigar dake nuna ya sallameta,da hanzari ta miqe tayi daki,cike da farinciki ta dira saman carfet din dake gefe guda wanda ta maidashi makwancinta,don ko da wasa bata taba hawa gadonshi ba,murna take sosai ita kadai a dakin,ba don dare yayi ba da ba shakka saita kira aliya ta shaida mata,don ba'a boyewa abokin kuka mutuwa.




Sai data gama dararta sannan ta soma sauya kayan jikinta zuwa na bacci masu kauri da taushi,ta saka dan qaramin hijabin da take kwana da shi wanda iyakarsa qirji ta shiga toilet ta daura alwalar kwanciya bacci(yana da kyau mu kasance cikin alwala a duk sanda zamu kwanta bacci,domin hakan ba qaramin kariya bace a garemu daga sharrin shaidanun mutane da kuma shaidanun aljanu,bama lokacin bacci ba kawai,a wuninmu gaba daya yana da kyau mu dinga zama da alwala,Allah yayi mana tsari,yasa mu dace duniya da lahira amin summa amin).




Tana zaune tana karanto addu'ar bacci taji ana knocking qofar,sai a sannan ta tuna bata rufe ba,tsuru tsuru tayi da ido ita batayi magana ba hakanan bata miqe ba,jin shuru yayi yawa yasanyashi turo qofar ya dubeta yana kauda kai
"Am sorry zan dauki blanket ne" sai kuma ya dawo da kanshi inda ya ganta,zai magana sai kuna ya fasa,ya isa ma'ajiyarsu ya dauki daya hadi da pillow sannan yace
"Me yasa kika zabi kwana a qasa?"
"Babu komai" ta fada a sanyaye,baice komai ba ya juya ya fice daga dakin,ta qarasa addu'arta ta koma ta kwanta ranta fari qal idan ta tuna batun ci gaba da karatunta.



Qarfe shida na safe ta gama shiryawa tsaf cikin lafaya,ta nade jikinta sosai kamalarta ta fito,fatarta data sake kyau da qyalli sakamakon isashshen hutu ta sake bayyana sosai cikin kalar tufafin dake jikinta,ranta fari qal,yau ita daya tasan farincikin da take ciki,duk zumudi ya cikata sakamakon screening da zata wudil,a haka ta fito parlourn ta tadda shi tsaye yana kurbar ruwan dumi a cup,wanda sabonshi ne hakan duk safiya kafin yaci komai,don yana wanke duk wani system na jikin mutum tare da inganta lafiya,ido ya dan xuba mata ganin yadda take ta faman zumudi,fara'ar fuskarta tafi tako yaushe,wanda hakan ya sake bayyana mishi irin yadda take qaunar karatu a rayuwarta,gaidashi tayi ya amsa taci gaba da tsaiwa tana jiran jin me zaice,sai daya gama shan ruwan sannan ya aje cup din
"Ban sanarwa da anni ba....bansan ya zata dauki zancan ba"duk sai taji daukinta ya tsaya,kuzarin data fito da shi ya ragu,dan soma takawa yayi ya nufi qofa a sanyaye tabi bayanshi.




A parlour suka tadda haidar riqe da muqullin mota kamar yadda khalipha ya tsara shi zai kaita,da alama magana suke da anni,dubansu take har suka qaraso cikin falon,aysha ce ta soma gaidata sannan haidar itama ya gaidata,daga bisani ta koma gefe ta lafe tana ji suna gaisawa da khalipha
"Me zasu yi a wudil da safiyar nan?"
"Screening zasu....zan miki bayani anni"
"Screening?" Ta maimaita tana danyi shuru kamar mai nazari,kada kai tayi daga bisani sannann tace
"Haka zaku tafi kenan baku karya ba?"agogo haidar ya duba sannan yace
"Zamu karya a hanya karmu bata lokaci,amma ban sani ba ko anty zata ci wani abun"
"Na qoshi" ta fada da sauri wanda har hakan ya sanya khalipha waiwayowa ya dubeta,yayin da anni ta saki murmushi saboda ta karanci zumudin da takewa tafiyar,duk da bata gama fahimtar tafiyar ta meye ba
"Allah ya kiyaye hanya,saikun dawo" anni ta fada suka juya suka fice khalipha na jawa haidar kunne kan tuqin ganganci.




Dubanta ta dawo dashi kanta,filon dake saman kujerar ya janye mata alamun ta zauna,babu musu ta zauna din tana hade hannayenta waje daya,shima ya zauna daura da ita kansa na dan kallon qasa
"Kiyi haquri anni,naso muyi maganar dake kafin wannan lokacin amma na sha'afa saboda yawan hidimomin dake shigo min.....na samu wata dama ne daga wani kamfani dake da reshe a mafi yawancin qasashen duniya....to amma wannan dama daci gaba ba zasu tabbata min ba har sai na sake qaro karatuna,wanda hakan zai zamemin kamar jifan tsuntsu biyu da dutse daya ne,zan kai wani mataki mai girma cikin reshensu dake qasar nan,sannan namu kamfanin zai sake samun ci gaba da daukaka da yardar Allah,karatun duka zai daukeni ne tsahon shekara biyu....mun dauko humaira daga ainihin inda suje ruqonta don mu samawa rayuwarta nutsuwa jin dadi da kuma ci gaba,sai na tattauna da ita game da meye burint,ta sanarmin karatu ne,hakan ya sanya nayi tunanin me zai hana na maidata makaranta yadda take da buqata,nq bata zabi ita da kanta ta zabi waccar makarantar,tunda dama can ta cike first choice da second choice dinta,dalili kenan da yasa na tura ta can din....amma nasan hakan bai kamata ba,ya kamata na fara yin magana dake kafin duka na yanke wadan nan abubuwan" kai ta jinjina,ta tabbatar duk abinda khalipha zaiyi yana zurafafa tunaninsa kafin yanke komai,hakanan baya aiwatar da komai saida dalili,sannan tunda suke ita da shi bai taba yanke wani hukunci ba tare daya shawarceta ba,bai kamata don an samu akasi a wannan karon ta manta baya ba ta tuhumeshi
"Tunda har haka takeso babu damuwa,Allah ya bada sa'a ya taimaka,saidai kai din kar ka manta cewa da da yanzu ba daya bane,zaka tafi har tsahon shekara biyu wata uwa duniya?"
"Zan dinga zuwa duk sanda aka samu chance...."shuru ta sakeyi sannan daga bisani tace
"Shikenan..amma dai kayita istikhara ka barwa Allah zabinsa,idan alkhairi ne dukkan abubuwan daka zayyana Allah ya tabbatar da su,idan babu alkhairi kuma ina roqon ubangiji yayi maka musaya da mafi alkhairi,sannan kayi shawara da matarka"
"Amin ya Allah anni na gode...Allah ya jiqan magabata"
"Amin amin"
"Zan shiga ciki inason na sake hutawa kafin goma na wuce office..."
"Allah ya nuna mana" har ya miqe ya soma taku ta kira sunanshi,dawowa yayi da baya ya zauna hannun kujerar daya tashi a kai
"Khalipha...na baka shawara?" Cikin mamaki ya daga kai yana duban annin,lafazin nata ne ya dan bashi mamaki,kai ta kada
"Qwarai kuwa shawara,domin kuwa abinda ya shafi rayuwarka ne kai kadai" sai ya samu kanshi da kada kai
"Ka riqe aysha da kyau,don ina tsammatar ita din matar aure ce ta gari irin wadda kowanne namiji yakeso" iya abinda ta fada kenan taja bakinta ta tsuke,ya tabbata ta fadi hakanne ta bar mishi saura yaje yayi nazari a kai
"In sha Allahu" kawai ya fada yayi mata godiya ya miqe ya fice.




Har ya nufi sashensa sai ya sauya akala zuwa sashensu haidar,ya tura qofar ya shiga ya ratsa falonsu sai ya wuce dakin mus'ab,yana kwance dai dai saman abun sallah yana kwasar bacci abinshi,da alama yau baije masallaci ba a daki yayi sallah,hannu khalipha yasa ya daka masa duka a qeyarsa,miqewa yayi a zabure da har zai soma masifa ga zatonshi haidar ne sai kuma yaga khalipha tsaye a kanshi hannayensa harde a qirjinsa yana dubanshi,kai ya sadda yana gyara zamanshi
"Wato duk fadan da nake maka kan salla bisa jam'i baka ji ba ko?"qeya ya soma sosawa cike dajin nauyi da kunya
"wallahi ya khali...."
"Shutup.....kasan muhimmancin sallar asuba da isha'i a jam'i kuwa?,annabi S A W yace idan kaga sallolin nan guda biyu sune mafiya nauyi akan munafukai,suna yiwa munafuki wuya da nauyi, sallar asuba da isha'i,sannan ya sake cewa da mutane sunsan me yake cikinsu da sunzo musu koda dajan gindi ne...ka shiga taitayinka,karka sake ka shiga sahun wadancan mutanen,annabi S A W a lokacinsa yace badon mata da yara dake cikin gidajen wadanda basa halartar sallah asuba ba,da ya umarci wani yaja mutane sallah,shi kuma ya dauki itace ya zagaya gidajensu ya kunna musu wuta,ibn ummu makhtum mai yiwa annabi kiran sallahn farko makaho ne,ya nemi uzuri wajen annabi S A W kan bashi da d'an jagora,sannan hanya akwai kwazazzabai a hanya shin ya iya zama a gida yayi sallar asubarshi?,har annabi ya bashi daman ya zauna har ya tafi yayi kiranshi ya dawo,ya tambayeshi daga gida yana iya jiyo kiran sallah?,yace masa eh,yace to lallai lallai dole ya taho masallaci ya halacci sallah cikin jam'i,saikai da baka da wuni uzuri?,saika kai sha biyu na dare kan waya daya na dare,ka kasa tashi sallar asuba wace hujja zaka gayawa Allah" sosai jikinsa yayi sanyi,a hankali yace
"In sha Allah hakan bazai sake faruwa ba ya khalipha nayi alqawari"
"Ka kiyaye karna sake ganin irin haka ya faru,kada na sake zuwa masallaci ban ganka ba"
"In sha Allahu" ya fada cikin nadama
"Ka tabbatar ka fito qarfe goma zamu fita ni da kai,haidar ya wuce wudil,karka sake na rigaka fitowa" ya fadi yana bude qofar fita daga dakin
"In sha Allahu yaya" daga haka ya fice zuwa nashi dakin.




Koda ya shiga ya cire jallabiyyar jikinsa ya kwanta don ya sake ri tsawa sai ya kasa,maganganun anni ke dawo masa,ya kasa gane ina ta dosa,duk wata kulawa da yayi alqawari yana baiwa ayshan,ba wata takura cikin rayuwarta sam,ya kasa gano komai haka bacci yaqi daukarsa,dole ya haqura ya miqe ya sauya kayan jikinsa zuwa wanda yake amfani da su idan zai shiga gym dinshi ya fice zuwa dakin motsa jikin.


*mace nayin soyayya da dukkan zuciyarta,yayin da namiji keyin soyayya da dukkan qarfinsa*

34










Kwance take saman doguwar kujerar falonta tana kallo,tun dazu ta aika drivern gidan tare da hamid zai taho mata da shawarma don ita take kwadayin ci,saidai ta tashi babu kudi a hannuna,kasancewar ko naira biyar hamid bai bata a hannunta,hakanan ko cefane akai zaibi ba'asin ragowar canjinsa,kudinta dake accnt dinta takeso taje ta cira a atm saboda kwata kwata bata saba zama babu kudi a hannunta ba,batasan babu ba sam,mummynta ta tsaya mata bata taba neman abu ta rasa,har gwara daddy wani lokaci yakan hanata ko ya bata ba yadda ta buqata ba(qalube gareku iyaye,bawai burgewa bace ace komai yaro ya nema saika bashi,irin haka akwai matsala mai yawa a rayuwar yaro,baka da tabbas na cewa zaka ci gaba da rayuwa da shi har abada,koda kaci gaba din baka da tabbacin zaka dawwama cin wadatar da zaka dinga yi masa duk abinda yakeso,irin haka takan fara ne tun daga sanda yaro yake qarami,bani biyar bani goma bani ashirin,randa baki bashi ba ya zauna yayita yi kiki kuka,ba zaki barshi ba yaci kukansa har ya haqura saboda ya gane ba duk abinda kakeso kake samu ba,A'ah,sai kice ya isheki da kuka ungo ni ka barni na huta,daga ranar ya gane haka duk randa kika hanashi kuka zai saka miki har sai kin bashi din,diya mace 'yar gudan wani ce,idan ta saba duk abinda ta buqata zata samu kina da tabbacin wanda zata aura haka ne?,kina da tabbacin zaku rayu tare kici gaba da yi mata yadda takeso?,don Allah iyaye muyi qoqari mu gyara,kaza tana taka danta ne badon bata sonshi ba,a'ah saboda ta koya masa darasin rayuwa,yana kukan bakiso bakijin dadi har cikin ranki amma saiki danne don mi koya masa lallai abinda kikeso shiza'ayi ba abinda shi yakeso ba,Allah ya shirya mana zuri'a baki daya amin).




Driver dinne yayi sallama hannunshi riqe da baqar leda wadda taketa maiqo,miqewa tayi daga kwancen da take ta zauna sosai tana yatsina gami da cewa
"Miqo" ya qarasa ya miqa mata dariyar mugunta fal cikinsa yana dannewa,budewa tayi maimakon shawarma sai ta hangi wainar fulawa wadda ko wadataccen manja babu a ciki bare albasa,wurgi tayi da ledar cikin fushi
"Meye wannan malam zailani?,wannan wanne irin iskanci ne da rashin mutunci?,nace shawarma ka kawomin wainar fulawa a qaqqandare?" Cikin kwantar da murya yace
"Hajiya ba laifi na bane.....wallahi Allah muna cikin tafiya da shi muka biyo ta wani layi yaga ana soyawa,da kansa ya bada umarnin na tsaya naje na siyo miki....ita kanta yarinyar da ganin motar har kyautawa tayi ta sako gyara" miqewa tayi cikin fushi ta soma zazzageshi da masifa kamar zata cinyeshi danye ko kamar shi yayi mata,sake kwantar da murya yayi duk da dariya na cinsa a ciki,wulaqancin data taba yi masa rannan har yanzu bai manta ba yace
"Haka zaki haquri hajiya kici tunda duka da wancan da wannan din duk dangin fulawa ne"
"Malam zailani,ka tashi ka fiya ka bani wuri tun ban zagi uwarka ba" hannu yasa ya rufe bakinsa cikin tsananin mamaki,don bai zaci isgilancin nata yakai har nan ba
"Allah ya baki haquri" ya fada yana miqewa gami da ficewa daga dakin,komawa tayi saman kujera ta zauna kamar zata saka kuka tsabar baqinciki
"bari daddy ya aikomin da kudin da yayimin alqawari,naga wanda ya isa ya hanani cin abinda raina keso"gaba daya hamid ya sauya kamar bashi ba,a baya duk abinda tace masa tana da buqata kona miliyan nawa ne yi mata yake babu musu,sai gashi yanzu biyar tashi sai tayi da gaske take cinta,hatta da cima ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login