Showing 153001 words to 156000 words out of 184891 words
Chapter 52 - DAURIN BOYE Complete Document by Safiya Abdullahi Huguma.txt
sace cike da baqinciki kishi qyashi da kuma hassada,maryam ce taja tsaki tana gyara kwanciyarta
"Shi abba yasan khalipha zaiyi kudi ya kasa taimakonsa,ai gashinan yanzu suna ganin arziqi saidai asan mana" take fada cikin zuciyarta
"Ya isheki haka malama,ya muna zaune muna hutawa zaki damu mutane da tsaki ne?,wai shin dawa ma kike ne?"
"Da uban wanda ya tsargu" ta fada tana gallawa zeenart harara,ai kuwa saita aje kwanon hannunta ta miqe tayo kan maryam din
"Ni kike zagi ko uba na?"itama tsaye ta miqe
"duk wanda kika zaba,aikin banza kawai,da kike wannan haqiqancewar wani kika fi har da zaki yiwa wani iyaka dayin yadda yaso,kin isa ki hanani tsaki ko cika gidan nan zanyi da tsaki?,ina cewa babu wanda gidan yake mallakinsa a cikinmu bare wani ya damu wani" nan fada yaso kacema tsakaninsu,sai suka hau 'yar gore gore,rahama ce ta leqo ta gansu sunayi,kallon banza ta watsa musu sannan taja tsaki ta juya ta koma dakinta ta maida qofar ta rufe,ita yanzu duka ba wannan ne yake damunta ba.
Aysha kam bata masan me suke ba,sanda ta fita gidan ba driver ko daya,duk sun tafi rakiyar anni kuma babu wanda ya dawo,malam shehu kuma ya tafi kasuwa cefane,hakanan ta taka zuwa bakin daya daga cikin motocin nata,ta tsaya gaban qaramar ciki tana dan dubanta,bismillah tayi ta saka muqullin ta bude ta shiga mazaunin driver,sai take jin fargaba,tana jin kamar ba zata iya ba,karon farko da zata soma driving,duk da ta jima da iyawa amma bata taba tuqi ba,saita rufe idonta ta karanto addu'ar hawa abun hawa,hakan yasa mata nutsuwa,ta maida qofar ta rufe,ta tashi motar ta daidaitata ta dan danna horn,mai gadi ya bude nata gate din ta fice a hankali cikin nutsuwa.
Sanda take fita su haidar na shigowa,mus'ab ne ya nunawa haidar ita,mamaki ya kamasu,suka dinga yi mata dariya mus'ab na fadin
"Wai yau anty da driving?ko ina zata oho,bari ta dawo yau zata sha tsokana"
"Ni kaina naso muna nan zata fita" haidar ya fada yana dariya,don basa manta yadda take da tsoron driving da kanta,taga shigowar motocin,sai taji kaman ta tsaya ta yiwa daya daga cikin direbobin magana su kaita,sai kuma kawai ta wuce abinta.
Tun daga harabar gidan haidar ya soma jin kaman hayaniya,saboda haka yabar mus'ab anan ya shige zuwa ciki,sanda ya shiga sa'insa tayi nisa,cikin fusata ya katsa musu tsawa nan take kowacce tayi shuru
"Wannan wanne irin iskanci ne da zaku maidawa mutane gida gidan karnuka?,toko wacce ta shiga taitayinta bana cike da rashin mutunci,ku bace ku bawa mutane guri da'alla ko kowacce ta wuce gidansu" hakanan maryam da zeenart suka wuce zuwa dakin suna qananun maganganu da gunguni,amal ya duba wadda ke zaune duk taqaddamar da ake
"Ke ba zaki tashi ba kenan sai nayi quli quli dake!" Ya fada.mata a zabure,ba shiri ta miqe itana ta wuce daki,don tasan halinsa sarai idan ya juye kaman khalipha haka yake komawa ba sauqi,dogon tsaki yaja sanda mus'ab ya shigo yake tambayarsa abinda ke faruwa,yana shafa tsakiyar kanshi yace
"Wadan nan mahaukatan yaran mana,ni na tsaya ma tambayarsu neke faruwa na kora kowacce,zasu zo suna mana hauka kaman gidan su" yana fadin maganar yana wucewa kitchen.
Cikin zuciyarta take hamdala sanda take shigowa layin nasu,sai kuma ta sakarwa kanta murmushi tana dariyar tsoro irin nata,yadda ta dauki abun ma duka ashe baikai haka ba,horna tayi cikin minti daya mai gadin gidan daddyn ya bude mata qifa ta sanya motar tata ciki,tana cikin rufe motar bayan ta fito adaidaita ta shigo gidan,saita daga kai cikin mamaki tana duban adaidaitan,asma'u ce ta fito daga ciki tana miqawa mai adaidaitan kudinsa,canji ya miqo mata saita watsa masa wani kallo
"Kai bana son iskanci yanzu zan saka ayi ma duka kana dai ganin cikin gidanmu ka shigo,yaya za'ayi ka dauki dubu daya daga inda ka daukoni zuwa nan,ko an gaya maka satar kudin ake?"
"Amma dai hajiya aiba haka mukayi dake ba ko?,drop kika ce bakyason na dauki kowa,a qa'idama kudinki sunfi haka,kuma wallahi kibar ganin gidanku na shigo baki isa ki dakeni akan haqqina ba" ashar ta maka mishi tana fadin
"Yau zakasan ubana waye zakaga qaryar iskanci" shi kuwa ganin haka saiya fito daga adaidatan nashi yana fadin idan ta isa tasa a dakeshi din saiya farke mutun wallahi ko waye,kallo daya aysha tayi masa ta karanceshi,irin matasan nan ne masu zuqe zuqe,askin kanshi kawai ya isa ya gaya maka wayeshi,a hankali ta tako ta saitin matashin tayi sallama,saiya tsaya da hayagagar da yake yana dubanta cikin dan layi,kwarjini tayi masa,haka shigarta ta banbanta data asma'un,amsawa yayi ta bude jakarta ta ciro dubu biyu sabbabi kar,wanda tun wancan satin ta ciro su a atm ta yiwa anni siyayyar tafiya a matsayin tata gudunmwar,duk da babu abinda ta rasa amma ance gaida mai gaidaka,miqa masa tayi sannan tace
"Kayi haquri don Allah malam,dauki motarka ka tafi" saiya amshe yana cewa
"Allah dai ya biya,kinga inda akasan arziqi,da alama wannan ba matsiyaciya bace irinki,ke ina jin ma ke 'yar riqo ce ko mai aiki a gidan don irinku sunfi kowa yin haka,matsiyaciya mai qaryar arziqi" ya shuga babur dinsa zai tayar,saita yunqura zata biye masa da sauri aysha ta damqe hannunta,qamshin turarenta da laushin tafin hannunta ya sanya asma'un waiwayawa tana dubanta
"Ba girma da mutuncinki bane anty,bakiga a yanayin da yake ciki ba?" So tayi ta wanke ayshan tas,saboda maganganun daya yaba mata sun qona mata rai sosai,to amma da wani abu ya fado mata a rai wani quduri da ayau takeson ta cimma saita hadiye komai
"Da kin barni na nunawa dan iska iyakarsa ai,basu da mutunci 'yan adaidaitan nan,koda yake ke dakike hawa saikinfi kowa sani ai"murmushi kawai ta saki
"Ki qyaleshi kawai,mun yini lafiya?" Ayshan tace da ita sanda suka soma takawa zuwa ciki,da qyar asma'un ta hadiye abinda ke damunta ta dan saki fuska ta amsa,wanda hakan yayi mata dadi
"Indo motarnan bata rufu ba fa" cewar usama wanda ta barshi yana duba motar daddy data yi parking kusa da ita
"Oh,ohkey,ina sauri ne zanwa mai adaidatan can magana naga kamar a buge yake,don Allah dan rufemin usama idan ba damuwa ka miqo min key din cikin gida"
"Toh ba matsala" ya karba yana yin gaba,su kuma suka cu gaba dayin cikin gida,saidai asma'u ta kasa cewa komai,mota kuma wacce iri?,ina ayshan ta samu mota?,kasa haqura tayi sai data waiwaya taga motar sanda usman ke rufeta,daskarewa tayi wani malolo ya taso mata wanda ta kasa hadiyeshi
"Mota kikayi aysha?"murmushi tayi
"a'ah,tunta lokacin bikina khalipha ya bani,bana hawa ne dai kurum" kan uba,wanne irin kudi wai gayen nan ke da shi ne?,asma'u ta furta cikin ranta,kaman baisan ciwonsu ba?,ko baisan nawa motar take ba,lallai ba shakka ya zame mata dole tayi wani abu,ita ya kamata ace tana cikin wannan yanayin ba aysha ba,taya zata zamewa aysha tsanin da zata taka ta cimma wani abu a rayuwarta?,da wannan saqe saqen zucin suka isa falon,wanda asma'u bata samu damar sake cewa komai ba.
52
Anty halima,anty kubra da anty lubabatu na zaune a falon,da fari sun soma hayaniyar ganin asma'u ganin shigowar aysha ya sanyasu rage hayaniyar tasu,dukkanin idanunsu na kan ayshan,kowa da irin kallo da yake mata,musamman anty halima da komai na ayshan ya tsone mata ido
"Ashe ana ganinku?" Cewar anty luba tana duban ayshan,tana neman abun fada,murmushi ayshan tayi
"Ana ganinmu mana anty luba,makaranta ce kawai ke sakawa wani zubin bana zama available koda yaushe,sai weekens nake dawowa gida" tabe baki anty halima tayi
"Kuma a haka ake zaman auren?" Dubanta aysha tayi,ta karanceta tsaf,ta kuma gogu da zama dasu hanan
"Eh...ba wata damuwa bace ko matsala ai idan akwai fahimtar juna tsakaninka da abokin zamanka"toh baki yasan abun fada baisan me za'a maida masa ba,sai maganar ta dan yiwa anty halima zafi,tunda suke da aysha wannan ne karon farko data soma maida mata amsa dai dai da maganarta,ta fuskanci amsar ta shigeta dai dai yadda ya kamata,don haka saita miqe tana cewa
"bari na qarasa na duba jikin daddyn" ba wadda ta amsa mata.
Da sallama ta shiga falon daddyn,yana zaune qasan carfet ya jingina da kujera,mummy na gefanshi tana hada mishi abinci,a ladabce ta qarasa gabanshi ya zube tana gaidashi da dubashi da jiki,fuskarshi fal da fara'a yake amsa mata,sannan ta waiwaya rana gaida mummy,da qyar take amsa mata,itakam a rayuwa ta rasa me ta yiwa mummyn,idan ma har zamansu ne tare bataso a baya ai zuwa yanzu yaci ace ta aje komai tunda tabar musu gidan,zata tashi daddyn ya tsaidata,hira suke sosai wadda suka jima basuyi irinta ba da daddyn,taji dadin hirar tasu ita kanta ba kadan ba,daga bisani tayi sallama da daddyn bayan ta aje masa kudi masu yawa,da fari qin amsa yayi yace shime bata ne ai
"Nasani daddy kafi qarfinsu,amma abinda kayimin a rayuwa kafi qarfin komai a wajena,badon baka dashi ba na baka,saidon bansan me zan baka din ba,amma wannan ka amsa daddy kasa min albarka ka nuna jin dadinka wannan shine kadai zai faranta min ,ya kuma tabbatarmin da kaji dadin kyauta ta"
"Shikenan indon baffale,Allah yayi miki albarka ya albarkacu rayuwarki,jiyan ma munyi waya da maigidan naki ya dubani da jiki,Allah yayi muku albarka"
"Amin daddy" ta amsa kanta a qasa tana jin wani abu cikin ranta,yaushe khalipha ya kira daddyn amma ita ya shareta,toko laifi tayi masa?,da wannan tunanin ta baro sashen daddyn ta dawo sashen mummy,asma'u ta tadda kawai a falon,sai anty halima dake dakin mummy tana bacci,saura duka sun tafi,da murmushi kan fuskarta ta dubi ayshan
"Ina mai gidan ya kika barshi?"
"Yana lafiya" ta bata amsa fuskarta a sake,saidai zuciyarta cike fal da mamaki,dama akwai sanda asma'u zata tambayi lafiyar khaliphan,tsaki asma'un taja wanda ya katse tunanin ayshan ta sauke wayar data kanga akunne
"Pls aysha bani aron wayarki don Allah zanyi wata waya,bashi nake bin wata mata idan na kira taga numberta ce sai taqi dagawa" wayar tata ta ciro daga jakarta ta miqa mata sannan ta miqe,alwala dama takeso ta daura zatayi sallar la'asar ,don haka ta shige toilet din dake parlour din donta daura alwala.
Cikin hanzari ta dauki abinda zata dauka a wayar sannan ta fita ta aje mata wayar tana murmushi cikin ranta,sanda ta fito daukar wayar tayi ta sanya cikin jakarta sannan ta tada sallah,bayan ta idar ta yiwa mummy sallama ta baro gidan.
Tana cikin revers zata fice daga gidan taga anty halima da asma'u sun fito,da alama wani waje zasu je,hakan ya sanya ta dakata har suka qaraso gab da ita,cikin murmushi tace
"Anty naga kamar wani waje zaku"
"Eh ya akayi?"
"Ku shigo saina rage muku hanya" ta fada tana bude musu qofar motar
"A'ah,jeki kawai" anty halima ta fada tana yin gaba asma'u ta bita a baya,sai dataga sun wuce sannan ta tashi motar itama ta fice a gidan tana girgiza kai kawai cike da mamakinsu,har yau ace jiya iyau alqarasu?,Allah ya kyauta ta furta a sarari sanda take hawa saman titi.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Duk yadda yaso daurewa cikin kwanakin gaba daya juriyarshi ta qare,ya tabbatar wa kansa da cewa soyayya ce ta kamashi,soyayya aysha ce ta masa kamu bana wasa ba,irin soyayyar da bai zaci zai bawa wata diya mace irinta ba,cikin daren ya kasa bacci gaba daya sai juyi da yakeyi,ji yake idan har baiji muryarta ba wani abu xai iya faruwa dashi,dole ya janyo wayarshi yayi kiran layinta.
A lokacin itama tana cikin falon sashensu tana karatu,don tun sanda annin ta tafi bata fiya zama a wancan falon ba,don gaba daya ta kame kanta itama saboda su rahama,sai taso ma sannan suke ganinta,tayi qoqarin dai killace duk wani abu daya kamata,tun randa aka rasa atamfar anni daya cikin ukun data bayar akai mata dinki,idanunta ta daga kawai ta dubi wanda ke kiran,sunanshi ta gani saman screen dinta yana yawo,wani abu mai kama da jan aji ya motsa mata,saita share kiran har ya katse,sake kiranta yayi karo na biyu,nan ma tana sane ta basar da kiran,don ta tabbata cewa lafiya lau ya daina kiranta da replying saqonninta.
Zama yayi daram kan gadonshi sanda yake sake kiranta karo na uku,jikinsa har dan rawa yake yana addu'ar ta amsa ba tare ma da yasan yana yi ba,baisan cewa haka ya damu da ita ba,baisan cewa haka yayi kewarta ba,baisan cewa haka soyayyarta ta kamashi da zafi ba sai yanzu,bata daga din ba sai gab da zata yanke ta kara a kunneta hadi da yin sallama,wata ajiyar zuciya ya sauke da qarfi a sarari wadda ta ratsa dodon kunnen aysha,saita lumshe idanu tana jin muryarshi yana amsa sallamarta
"Uwaishah...." Sai taji sunan yayi mata dadi qwarai har data lumshe ido
"Ya Allah,what a nice name" ta fada cikin zuciyarta,tana jin zuciyarta na mata nauyi dauke da wani abu mai wuyar fassara,gaidashi ta soma yi ya amsa murya can qasa sannan yace
"Uwaish bakya kewata ko?,duk yadda naso na daure na kasa,wannan abun ba lafiya ba" idanu ta zaro don bata fahimci kalmarsa ta qarshe ba
"Me ya sameka kuma ya khaliphah?" Yadda ta ambaci sunanshi karon farko saida murmushi ya subucr daga lebansa
"Asiri kika yimin ko ayeesha?" Gabanta ne ya fadi sosai,tsoro ya kamata,sai zuciyarta ta karye,tuni hawaye suka tsattsafo cikin idanunta
"Ya khalpha?,asiri fa?,na rasa wa zan yiwa asiri saikai?,don Allah ka yimin bayani waya gaya maka haka?" Ta qarashe muryarta na rawa,dariya sosai take cinsa saiya kanne
"Ki jirani zan gaya miki" ya fadi yana katse wayar saboda ya kasa boye dariyarsa,baiso kuma taji,wayar na hannunshi yana jujjuyaya yana kallonta,iya muryarta kawai daya ji ta kwantar masa da.hankali sosai,hakanan cikin jikinsa yaji ayshan kuka take,saboda haka saiya rubuta mata texs
_idan kikayi kuka toki tabbatarwa kanki da kanki baki da gaskiya,hakanan idan kika damu to shima baki da gaskiya,just in kin yarda da.kanki fell free kawai,ki tanadi abinda zaki kare kanki idan nazo tuhumarki_
Saqon nashi ta dinga maimaita karantawa,saita samu kanta da share hawayen fuskarta,ta dinga maimaita karanta saqon nashi,ta wani bangaren yana mata kama da gaske,ta wani bangaren kuma yafi mata kama da wasa da tsokana,to amma yaushe suka fara haka da khaliphan?,sai taji matuqar kewarshi,tana son ganin fuskarshi mai kyau da kwarjini,hakan ya sanya ta ture litattafanta ta jawo system dinta ta shiga inda ya adana mata hotunanshi ta hau kalla daya bayan daya.
Nishadi yake ji sosai cikin zuciyarshi,saiya sauka daga saman gadonshi ya soma duba abubuwa masu amfani a wajensa ya fara hadasu waje guda,bayan ya hau net ya duba idan zai samu jirgin da zai tashi gobe zuwa nijeria ya sayi ticket.
Yana tsaka da wannan kira ya sake shigo masa,sai yabar abinda yake ya duba kiran,salim ne saboda haka ya tabbatar kiran mai muhimmanci ne
"Ya salim ya ake ciki"
"Am sorry boss,zarginka ya tabbata kan mutumin nan....yana amsar kudaden ne yana safarar miyagun qwayoyi,idan ya samu ribar yake dauka ya dawo maka da kudadenka,yanzu haka a rahoton da na samu sunyi niyyar fitar da wasu qwayoyi an kama yaransu,suna kuma gab da fadin sunayen su waye" idanunshi ya runtse sosai,dama ya jima yana tantamar bawa mutumin bashi,banda anni ta sanya baki tun a wancan lokacin da bazai bada ba,lallai ya zama dole ya samu mutumin
"Good job salim,ku jira zuwa ne gobe,but bana son kowa ya sani"
"Thank you boss,Allah ya kawoka lafiya"
"Amin" ya amsa yana katse wayar,ya cillata gefa yana furzar da iska mai dumi daga bakinsa,lalllai bazaiwa mutumin nan ta sauqi ba duk tsufarshi saiya gane baida wayo,ya bata mishi rai qwarao,amma daya tuna chaptershi da ayeeshanshi sai ya saki murmushi yaci gaba da shirinsa yana imagining haduwarsu gobe.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Kwance take saman gadonta,wanda a sannan kusan sha daya da rabi na dare,har a sannan hamid bai dawo ba,ta riga data saba da rashin dawowar tashi wani lokacima sai tsakiyar dare,a da tana damuwa saidai a yanzu sam babu abinda ya shafeta dashi,neman hanyar rabuwarsu kadai ya rage mata donta cimma muradinta.
Cikin shakku da tantama ta soma kiran number khalipha ta farko,nan na'ura ta sanar mata number a kashe take,hakan ya sanya ta tafi kiran daya layin nashi.
Sha daya da rabi da minti biyar wanda yayi dai dai da sha biyu da rabi da minti biyar a cyprus,kwanciyarshi kenan saman gadonshi,kaman bazai daula ba,amma ganin kiran daga nijeria ne ya sanyashi dagawa bayan tayi kamar zata tsinke,jin muryar mace sai ya bashi mamaki,muryar da bai santa ba
"Amincin Allah ya tabbata a gareka"
"Wa'alaikumussalam warahmatullah" ya maida mata da yaren larabci
"Ina fatan kana lafiya kamar yadda nake,duk da ni din sai a hankali tawa lafiyar"
"Amm,idan babu damuwa da Allah zan iya sanin dawa nake magana"
"Kasha kuruminka,ba wata bace illa asma'u,tsohuwar masoyiyarka"
"Asma'u?,asma'u?" Haka ya dinga nanata sunan a ranshi yana son tuna wacce asma'u,asma'un ce ta fado mishi,saidai ita din a yadda ya sani matar aure ce,akanme kuma zatayi kiranshi a irin wannan lokaci?,hasalima bata da numbersa
"Idan baka gane ba bari nayi maka dalla dalla,asma'u dai wadda ka fara cewa kana so tayi kuskure da gangancin hadaka da aysha bayan ita tafi kowa dacewa dakai" gaba daya sai yaji kaman yana magana ne da zararriya,kodai ba cikin hayyacinta take ba?
"Am lafiya kike kuwa?," yana nufin cikin hankalinta take,amma fuskanci maganarsa ba
"Lafiya nake,amma ba lau ba" zuciyarshi ce ta bashi shawarar sauraro kafin yanke hukunci,saboda haka yace da ita
"Uhmm....me yake faruwa?,ina kika samu numberta?"
"Khalipha kenan...."
"Point of correction..." Yayi saurin katseta
"Yaron oga dai" a shagwabe tace dashi
"Haba don Allah,na baka haquri fa tuni,amma bai wuce a wajenka ba?kuna yanzu ma kira nayi na sake baka wani haqurin don Allah ka yafemin komai ya wuce" Tsaki yaja a bayyane wanda ya isa kunnenta
"Me kika yimin da zaki bani haquri?,idan ma kina tunanin akwai wani laifi da kika yimin ma to babu,nikam khalipha saidai nayi miki godiya ma,domin duk abinda kike zaton kinyi alkhairi ya zamewa rayuwata da ita wadda kikayi nufin cutarta,karki sake kirana daga yau,don ni bana magana da matan mutane" yana kaiwa nan