Showing 9001 words to 12000 words out of 184891 words
Chapter 4 - DAURIN BOYE Complete Document by Safiya Abdullahi Huguma.txt
tun yanzu" cike da rashin damuwa ta nunawa mommyn inda kayan suke,don tunda aka soma dramer tasan akwai abinda zai biyo baya shinyasa ma bata debe kayan ba,asma'un ita taje ta birkita kayan ta dauko wayar tana jifan ayshan da harara kamar ita ta cewa daddyn ya aikata hakan ko tana da masaniyar zai aikata din
"A'ah dawo ki debi sauran kayan mana ya zaki barsu nan?" Mommy tace da aysha wadda take niyyar komawa dakinta,bata ce komai ba ta dawo ta kwashesu tana fadin
"An gode".
" ke kawo....zonan mu ga"asma'u ta fada cikin hargagi,ba musu ta dawo da baya ta sake zube kayan a gabanta,hannu ta saka ta bibbirkita ta ciro doguwar riga guda daya wadda bata da kalarta cikin wadda daddyn ya raba musu,gefanta ta jefa tana cewa
"Jeki wannan ta yimin,kamar ma tafi tawa tsada,ina da wata idan na shiga daki zan dauko miki a amadadinta" Tsaki asma'u taja bayan ayshan ta shiga dakin
"Rigima ce fa kawai irin ta daddynku,ita kanta yarinyar na fuskanci rayuwa bata dameta ba,yarinyar data taso a qauye saika dinga siyan kaya na manyan kudi kana bata,harda abinda batasan darajarsa ba ma....miqo min wayar" mommy ta fada tana miqawa asma'u hannu,saita noqe
"Namecy zan bawa ita mommy please" dan zare ido mommy tayi
"Ke bana son sakarci bani nace" cikin shagwaba tace
"Habba mana mommy,kinsan 'yar waye ne cikin garin nan?,wallahi nasan na bata wannan wayar as a gift ba qaramin daga min aji kyautar zatayi ba" harara mommyn ta watsa mata
"Yar banza,sai shegen son suna da tara qawaye"
"Thank you my mommy,i love you so much" ta fada tana tsalle hadi da faduwa saman kujerar cikin farinciki,ta tabbata gobe zatayi abunda kowacce saita kalleta cikin qawaye,haka nan husna zata sake ganin darajarta da yadda da irin kudin nasu gidan,duk da qawaye ne amma gasa ce sosai a tsakaminsu,kowacce so take tayi abinda zata burge daga,kowacce so take 'yar uwarta taga ta fita,kowacce so take ta ganta itace a gaba ta baro daya a baya,su kansu basu san cewa abota suke mara ma'ana ba,har hassada da qyashi da kishi ya shigo cikin tarayyarsu yayi kane kane ba tare da sun sani ba,abu daya ne ya hana mommy amshe wayar jin cewa 'yar wani za'a bawa,kasancewarta mace mai son mu'amala da manyan mutane,tana son a ganta tana mu'amala da wani,wanin ma da yayi suna ya kuma shahara,haka dabi'arta take a jininta take,kusan ba'a qasa yaranta suka dauki wannan dabi'a,za'a iya cewa duk cikinsu mutum daya ce ta banbanta da su,halayenta kusan irin na mahaifinta ne,hakan ya sanya babu jituwa ko alaqa mai qarfi tsakaninta da asma'u,saboda banbancin ra'ayi da hali.
A hankali yake kurbar lemon dake cikin tambulan din qarau na glass sake gabanshi,yayi kyau cikin shigar da yafiyi shigar suit musamman idan ranakun aiki ne,yanayin zamanshi a wajen da yadda yake kai lemon bakinsa lokaci lokaci kadai ya isa ya gaya maka nutsuwar da yake sa ita uwa uba aji da kyau da Allah ya bashi,kusan babu budurwar da zata shigo wajen bata kalleshi ba,masu rawar kan cikinsu kanyi sha'awar dosar sa su taya hajarsu saboda alamun malasa da suke hangowa tattare da shi,saidai basu iya qarasawa saboda kwarjinin da yake da shi suke karya kwana su sauya hanya.
Agogonsa ya sake dubawa ya yarfar da hannu gami da jan tsaki,banda haduwarsu da mas'ood yau ta zama dole baiga abinda zai sashi zaman wajen ba,sam wajen baiyi masa ba,akwai yawaitar cakudedeniyar maza da mata abinda yafi tsana,yana da kishi qwarai duk da cewa kuwa baida qanwa mace,a zahiri zaka ce bai damu da motsin dake faruwa a wajen ba,saidai a badini yana zaune ne yana sake.nazarta da karatun halayyar 'yammatan zamani,abubuwa da yawa sun faru da suka bashi mamaki suka kuma sake sa mishi tsanar zaman wajen,yana mamakin yadda yammatan ke shigowa,wata tsakiyar maza biyu wata namiji daya,ba wani kunya ko takatsantsan da aka san diya mace da ita,ta zauna cikinsu suci abinci ko abinsha suna hira kaman zasu tafa,wasunsu ma sukan kebe can baya suje susha shisha,wanda shi a wajenshi bata da maraba da taba wiwi da sholisho,hakan take ko a wajen malaman lafiya,zuqa daya ta shishar dai dai yake da ka zauna kasha karan taba sigari guda dari biyu,yana da yaqinin mafi yawansu ba nan suka cewa iyayensu zasu ba,suna iya qarya da sunan mabanbantan wurare da sunan cewa can suka nufa,su binne iyayen har su zo su koma basu fuskanci komai ba.
Dogon tsaki ya kuma ja yana niyyar dauke kanshi wata mota ta shigo wajen,hakanan yaji ta dauki hankalinsa,bawai don kyanta ko bai taba ganin irinta ba,a'ah,hasalima shekararsa uku da hawanta,duk da ba ita yake kallo kai tsaye ba amma hankalinshi na wajen.
kaman a mafarki yaga khadija na fitowa daga gaban motar bayan matashin dake tuqa motar ya zagayo ya bude mata,yana iya ganin sanda ta sauya hijabin jikinta da mayafi sannan ta fito,tare suka jero har zuwa kan daya daga cikin kujeru da teburan dake wajen suna wa juna magana.
Sosai mamaki ya kamashi,don bai tsammaci ganinta a ire iren guraren nan ba tare da wani namiji,da kuma shiga irin ta jikinta,aljihunsa ya laluba sai yaji wayarshi da yake kiranta da ita,yaji dadin hakan,don dama ya taho da ita ne saboda yana da plan din daga nan ya leqa wajenta.
Miscal wajen hudu yana hangota daga inda yake,tana ganin kiran take dauke kanta,daga bisani ta soma tsaki,yana hango saurayin na mata magana kan ta daga,sai a kira na shida sannan ta daga din,sallama ya soma mata ta amsa da qyar tana wani basarwa
"Hala na katse miki wani abu mai muhimmanci...."
"Kusan haka ne,don bacci nake...na dawo daga makaranta na gaji ina buqatar hutu don Allah....ko kudin sun samu ne?"
"A'h...muryarki dama kawai nake da muradin ji"
"Ohk....idan sun samun zaka iya kirana saika gayan ranar da zaka zo" ko kafin ya kashe tashi wayar tuni ta datse nata layin,yana iya hango yadda take yatsina fuska sannan daga bisani ta wurga wayar jaka ta sake tattara hankalinta ga saurayin.
Yana shirin dauke idanunsa ya hangi sanda ya amshi jakarta ya saka mata kudi a ciki,kanshi ya kawar sannan ya miqe tsaye bayan ya ciro wayarshi yaba laluben number mas'od ranshi a bace,shi yasa ya tsani jira,badon mas'ood din ya tsaida shi da alqawarin yana hanya ba da bai zauna wajen har idanunsa sun gane masa abinda ya gani din ba
"Afwa boss,afuwa don Allah"
"Is too late....nayi cancel schedules dina na yau na zauna jiranka duk da muhimmancin da lokacina yake da shi.....saidai wani lokaci kuma idan na samu chance....na kiraka ne na gaya maka karka qaraso baka kuma sameni ba" ya qarashe fada yana shigewa bayan motarshi da jibril ya bude masa sannan ya kashe wayar ya ajeta gefanshi,idanunshi na kansu har sanda driver ya soma jan motar suka soma barin wajen,idanunsa ya lumshe sanyin A.cn dake cikin motar yana ratsashi,sosai zuciyarsa na zafi...dukkan wani hope nashi yana sake raguwa sosai fiye da kowanne lokaci,sunayen Allah yake jerowa daya bayan daya cikin zuciyarshi kamar yadda ya saba duk sanda yaji bacin rai,bai yadda ya zauna zuciyarshi na soyuwa hakanan ba tare daya kira Allah ba.
*mrs muhamma ce*👑*D B*
*0⃣6⃣
*Wannan littafin na kudi ne meso ya karanta ya nemi wannan number 08030811300*
Washe gari ita mommy ta baiwa tsaraban yaran nata dake aure ta hadata da driver ta kai musu,duk da cewa tana da makaranta amma ita sam wannan ba matsalarta bace,damuwarta shine ta idar mata da nata aiken koma ya zatayi ba matsalarta bace,hakan ya sanya a gurguje taje ta miqa musu,ba wani zama tayi ba,ko dama can ba wani sabo ke tsakaninsu ba,tsakaninsu da ita idan bautarsu da tashi,gidan anty safiyya kawai ta dan zauna har ta sha ruwa,kasancewar duk ta fisu sakin fuska da janta a jiki.
Ranar bata shigo gida ba sai qarfe biyar na yammaci,duk da haka bata zauna ba sai data shiga kitchen ta shiryawa daddy abincin dare da taimakon inna laraba,data gama dinma dai ba zama tayi ba,kayanta ta soma hadawa wanda zata je gida gobe da su,tsaf ta shirya kayan nata cikin matsakaiciyar jaka,kaman yadda ta saba ta tsinci wasu daga cikin kayan nata ta zuba daban da niyyar yin kyauta da su kaman yadda ta saba.
🧶🧶🧶🧶
Tafe suke shida drivansa cikin motar tasa baqa wul,wadda kallo daya zaka mata kasan ba qananun kudi aka sanya aka sayeta ba,yana lafe bayan motar sanyin raba na kadashi,sanye yake da suit suma baqaqe wadanda suka dace da kalar fatarshi wadda ainihin hutu da jin dadi suka ratsashi,dirarsa kenan cikin qasar,wanda a yanzu haka yana hanyarsa ne ta isa gida,lokaci lokaci yakan lumshe kyawawan idanunsa dauke da zara zaran gashin ido,hakanan yake jin kasala da gajiya sun masa dabaibayi,Allah Allah yake ya isa gida yaga anninsa ya kuma kwanta ya huta.
A hankali qaramar wayarshi da bai wuce mintuna goma da kunnata ba ta dauki qarar qaraurawa,ko bai daga ba yasan wacece,ita kadai zata kirashi ta cikin wannan wayar,saboda don ita kadai ya saka layin ciki,hakanan daya bude yaci karo da tarin saqonninta tun na kwanaki bakwai da suka wuce,wato kwananshi biyu kenan da barin gidansu,kwana daya kuma da ganinta da yayi a wancan eatery din,wanda yayi dai dai da tafiyar data kamashi zuwa china sai a yau ya samu dawowa,a kasalance ya saka hannu ya daga wayar gami da karata a kunnesa
"Na gode da wulaqancin da ka yimin,duk ni na saiqa kaina koma meye ka yimin khalipha" idonsa ya sake lumshewa ya bude yana jin yadda taratsin maganarta ke ratsa kwanyarsa
"Afwan dija na"ya fada cikin qarfi halida danne bacin ranshi a kanta wanda ya haifar da sanyi a muryarsa,sanyin muryar da ta kashe mata jiki tare da sauke kaso hamsin cikin darin bala'in data so yi
"Ni baka da abinda zaka gayamin,wannan wanne irin cin fuska ne,tun ranar da kazo gidanmu na qarshe gaba daya aka daina samunka a waya,kuma kai baka neme ni ba,haka ake soyayyar?"boyayyen murmushi kawai ya saki,shi yasan ba wannan ne maqasudin fadanta ba,a baya bata taba nemansa ko damuwa da duk kwanakin daya dauka baije gidansu ko ya nemeta ba,idan ya nemeta falillahil hamd,idan ma bai nemeta ba duk daya wai mamaci ya karye
"ai nace kiyi haquri ko?,wayar tawa ce ta samu matsala,sai yau na samu na karbo daga wajen mai gyaran" ya qarshe maganar yana istigfari cikin zuciyarshi,daga can bangaren khadija dummm tayi,tana sake ji cikin zuciyarta da jikinta lallai muhammad din bai dace da ita ba sam,baiwar kyau kawai Allah ya masa,wanda bazata bari kyansa ya rudeta ba ta shiga gidan da bashi take da buri ba,wanne irin gyaran waya fisabillilahi,wayar tashi da ko tata wayar ta fita tsada,don ranar farko data fara ganin wayar sai data sake kallonta,gaba daya ba zata wuce dubu goma ba
"Kawai ka fadi me ya hanaka dawowa,ko babu waya ai qafafunka zasu iya kawoka,ko kudinne ba zaka iya bani ba shi yasa ka janye jiki?" Maganarta ta bashi dariya,baisan murmushin da yayi ya fito fili ba sai data ce
"Dariya na baka?" Cikin waskewa yace
"A'ah....ba haka bane,gani nayi kin kusa canko abinda ya hanani dawowa.....kawai dai kudin ne basu samu ba,kuma ina kunyar nazo miki haka" ranta yayi qololuwar baci,a haka zata aureshi?,mutumin da ya kasa mata kyautar naira dubu talatin kacal ina zai samu kudin aurenta,a gabanta kowacce cikin qawayenta suka dinga karbar alert na kudade daga samarinsu,mai qaramin kudi cikinsu itace wadda aka turowa dubu talatin,sai ita zata tashi a tutar baya?
"Kana nufin duk jiran da nayi ya tashi a banza kenan bazan samu ba?" Sake gyara kwanciyarshi yayi bayan motar sanyin A.C na ratsashi,cikin kwantar da murya kaman gaske yace
"Ni bance ba zaki samu ba,ai Allah shine mai bayarwa,shike kuma azurta bawa a duk sanda yaso,ina nan ina qoqari cikin satin nan ina saka ran Allah bazai hanani ba" shiruuu tayi bacin rai na ratsata
"Ai shikenan" abinda ta iya fada kenan ta katse kiran,wayar ya cire a kunnensa yana kallonta,ya sake sakin murmushi kawai yana girgiza kai,baiyi ko yunqurin nemanta ba ya aje wayar gefanshi saboda baison sauran hayaniya hutu yake nema kuma,har suka isa gida yana tunanin rayuwa da irin darussan daya samu masu tarin yawa dangane da halayyar 'yammatan zamanin nan.
A nutse yayi sallama cikin parlourn alfarma wanda yake mallakin mahaifiyarsa,parlour ne daya wadata da dukkan wani nau'i na kayan morewa rayuwa,dattijuwa anni na zaune cikin daya daga cikin kujerun tana sauraron hadisai saga tashar talabijin ta saudi sunna tare da kallon masallacin ma'aiki da suke nuno lungu da saqonshi,a hankali ta cira kai tana amsa sallamar tashi fuskarta qunshe da fara'a,yayin da bakinta ke furta masa marhaban lale,cikin qauna irin ta d'a da mahaifi ya iso gabanta,suka shiga gaisawa cikin nunawa juna kulawa
"An dawo lpy"
"Lpy alhmdlh anni cike da nasara"
"Alhamdulillahi rabbil Aalamin" ta fada tana hade hannayenta waje daya kaman mai addu'a,kansa ya sake dagawa ya dubi saudi sunnah sannan ya kuma duban anni cikin murmushi
"Ko yaushe cikin shauqin wajen nan kike anni" murmushi ta sake masa mai sanyi irin na manyan dattijai sannan tace
"Banda abinka khalipha wannan waje ko sau nawa musulmi zaije ai bazai rabu da shauqinsa ba,ba zaiqi ya dawwama a nan ba har ranar mutuwarsa"
"Gaskiya ne,inaga ki soma shiri zan sa khalid ya shirya miki komawa can cikin watan nan,ko sati hudu kije ki sake yi" murmushi ya sake yalwata kan fuskarta,farinciki tare da alfahari da tilon dan nata ya sake mamayarta,bai wasa da duk wani abu data nuna tana muradi ko da iya kan fuskarta ya fuskanci haka,kwata kwata watanta uku cikin na hudu da dawowa daga umrar
"Ba matsala khalipha?" Murmushi ya saki
"Har abada anni ina fata mun tserewa matsala,ko sau nawa mike da buqatar zuwa ki fadi kawai,yaronki a shirye yake da ya kaiki,uwace ke da ba kowanne d'a yake dace sa irinta ba,har abada bazab manta sadaukarwarki garemu ba"
"Alhamdulillahil lazi bi ni'imatihi ta timmus salihat,Allah yaci gaba da yiwa rayuwa albarka,ya tsareka ya maka jagora,Allah ya zama gatanka kaida 'yan uwanka,ya hadaka da mace ta gari"
"Amin ya Allah anni,Allah ya qara lafiya da nisan kwana"
"Amin amin" ta fada tana murmushi,ya bude bakinsa zai sake magana yaga shigowarta falon,hannunta riqe da wani kyakkyawan kwando kwanon tangaran,tana sanye cikin shadda gezner ruwan hanta wadda aka yiwa dinkin buba da ado mai kyau tun daga sama har qasa,tayi daurin zamani tare da buga kwalliya sosai,suna hada idanu ta soma jifansa da murmushi,janye idanunsa yayi a hankali ya maida kan anni yayin da take qarasowa kusa da su,ta aje kwanon gaban annin sannan ta zauna tana fadin
"Barka da dawowa ya khalipha"
"Yauwa,sannunki amal"
"An dawo lpy ya hanya?" Ta fada tana murza yatsunta kanta a qasa alamun jin kunya,ya sake dubanta ya dauke kai sannan ya miqe yana cewa
"Alhamdulillah,yasu momma?"
"Lafiyarsu qalau suna gaidaka"
"Ma sha Allah,anni zan shiga nayi wanka na huta" daga kanta amal tayi da sauri tana dubanshi
"Ya khalipha ga abinci can na shirya maka fa" ta fada a narke tana dubanshi
"Am ok,nafi buqatar na huta" ya fadi yana soma motsawa alamun zai wuce ne
"A'ah ai ba'ayi haka ba,kaje kayi wankan saita miqo maka ko a can sai kaci" cewar anni wadda bata so amal din taga kaman ya gwasale qoqarinta ne,saboda tunda ya kira annin yace mata sun taso take rawar qafa
"Ba damuwa anni" ya fada yana daukar safarshi daya cire yayi gaba.
Sai daya kashe wayoyinshi kaf sannan ya rage kayan jikinsa ya fada bandaki,mintina talatin yayi sannan ya fito,ya shirya cikin jallabiya mai gajeran hannu,yana cikin fesa turarensa ya jiyo knocking daga can qofar falonshi,ya aje turaren yana daukar wayarsa qwaya daya ya kunnata sannan ya fita zuwa falon.
Amal ce ita da mai aikin anni raliya,wadda ke dauke da kwanukan abinci,sakin qofar yayi,amal ta amshi kayan abincin daga hannun raliya ta shigo ciki,kasancewar ta sani baiso kowa na shigo masa bangare barkatai,a gabanshi ta dire kwanukan abincin a sanda yake waya da P.A dinshi,kafin ya kammala harta gana zuba masa komai ta samu gefanshi daya daga cikin kujerun ta hakimce tana satar kallonshi,ba qaramin so takewa khalipha ba,ji take kaman ta bude ido taga ya zama nata,komai nashi yayi mata,sak irin mijin data sha zanawa a mafarkinta,kyakkyawa mai qirar qarfi,mai aji mai kudi kana mai dimbin ilimi.
Hada idanu sukayi sanda ya dauki plate din data cika da fried rice da gasashshiyar kaza a gefe,daga cikin dabi'unsa sam baison kallo,a nutse yana juya abincin yace da ita
"Akwai wani abu da yayi saura ne amal?,kina iya tafiya" shagwabe masa tayi tana noqe hanci
"Haba ya khalipha,wanne irin na tafi bayan hira nakeso na tayaka?yaushe rabon da mu hadu don Allah,amma kai ko irin nunawa ma baka yiba" fararen idanunsa ya watsa mata yana tauna abincin bakinsa a hankali,sai daya hadiye sannan yace
"Indai zaman hira kika zo yi yanzu kam bazan iya ba,kinsan ban iya cin abinci ana min surutu ko?"kai ta sadda qasa
"Kayi haquri to" sai ta dan bashi tausayi kadan,banda ya riga ya gama da farke layarsu ita da mahaifiyarta bai tunanin zai iya tsallakewa tarkon ita yarinyar a yadda take binshi sau da qafa
"Is ok,kije ciki idan nayi bacci na tashi zan shigo,sai muyi hirar ko?"
"Tohm" ta fada tana miqewa tare da ficewa daga parlourn bayan ta ja masa qofar,kai ya girgiza yana ci gaba da cin abincinsa a hankali,har yau bai manta da mahaifiyarta ba wato momma zinat,har yau bai mance irin kyara tsana tsangwama da kallon qasqanci da ta dinga jifansu da shi shida mahaifiyarsu ba a wani zamani baya can da ya shude,sai gashi cikin qanqanin lokaci momma zinat din ta koma daya daga cikin gagga gaggan masoyansu,abun da mamaki da kuka daure kai a wajenshi,saida ga duk wanda baisan abinda ya faru shekara kusan goma sha biyar baya ba zaiyi zaton soyayyace daga Allah momma zinart din ke musu,da wannnan tunane tunanen ya kammala,a nan kan doguwar kujerar da yake kai ya miqe,kan wani lokaci bacci yayi awon gaba