Showing 93001 words to 96000 words out of 184891 words

Chapter 32 - DAURIN BOYE Complete Document by Safiya Abdullahi Huguma.txt

saba ganin qyama da kallon banza daga gun duk baquwar fuskar data zo gidan,abinda ke kwantar musu da hankali da sake basu qwarin gwiwar zama da mutanen gidan shine basu taba jin ko ganin maganar banza ba daga wajensu


Cikin minti goma kacal ta gama hadawa,atika duka na kallonta cikin mamaki
"Kai hajiya....ya akayi kika iya wannan hadin kamar ma yafi nawa kyau?" Murmushi kawai ayshan tayi ba tare data bata amsa ba,kusan tasan magunguna sosai,saboda inna yelwa tayi sana'ar saidasu kala kala,kuma babu maiyin wahalar sai ita,wani lokaci ma ita ke shiga jeji ta sassaqo abinda ya kamata,ta gada ne itama daga wajen mijinta wato kakan ayshatu bayan rasuwarsa,wanda ya rasu ne tun kafin a haifi umminta.




Tana aje jug din rahama na shigowa cikin kitchen din,ta tsuke cikin shirt da dogon skert tana takawa dai dai,ganinta duk sai su atika suka nutsu,suka soma gaidata tana amsawa dai dai tare da cewa
"Ku samamin wani abun,duka abinda kuka dafa din yau bana jin cinshi" kai aysha ta daga tana dubanta cikin mamaki,a qalla an dafa abu yakai uku kuma duka tace babu na cinta a ciki?,idanunta ne ya sauka kan ayshan,ta dan kalleta na minti biyu,yanayin halittarta tayi mata sosai,ta yabawa tsarinta saidai tana kishinta
"Amaryarmu...ya da fitowa da safe haka?,ke daya kika bar angon naki?"
"Tare muka fito nina rakota saboda ta damu taga anni,komawa nayi in dauko wasu takardu dana manta" muryar khalipha ta ratso kitchen din a sanda take takowa zuwa kitchen din,cikin yadin kufta baqi wanda iyakar rigar qasan gwiwa sai dogon hannu da take da shi,aikin sarauta aka yi masa sosai wanda ya dace da hula dara dake kansa,ba qaramin kyau suka yi masa ba,sai ya tashi tamkar wani jinin sarauta,kwarjininsa ya qaru sosai,sunkui da kansu atika sukayi sannan suka rusuna suna gaidashi,ya amsa musu suka lalubi qofa suka fice,kitchen din ya rage saura su uku,hannyensa harde a qirji ya zubawa rahama ido,wanda a take ya ladabtar da ita,ta dauke kanta tana basarwa
"Princess" yayi qarfin hali fada yana duban aysha,sai tayi wuri wuri da ido cikin mamaki da tambayar kanta dawa yake,hakan sai yayi kama da kamar ta kada mishi idanunta ne a ganin rahama,hannunshi ya miqa mata yana cewa
"Muje muyi break anni tace na kiraki" dubanshi take,ta fuskanci abinda yake nufi,amma sai take jin ba zata iya ba,har yanzu kallonta yake yana fatan ta dago abinda yake nufi ko don rahaman,iya matakin da zai dauka a kanta kenan ta rage sawa rayuwarsa ido da matsanta masa,ganin ayshan nason karya plan din sai kawai ya saqalo tafin hannunta ya janyota zuwa kusa da shi tamkar zasu hade,sannan ya soma takawa ba shiri itama tabi sahunsa yana fadin
"Rahaman kike jin kunya....idan baquwarki ce toni ba baquwata bace...muje kici wani abu na lura bakison cin komai,bana son wannan baquntar taki fa" da idanu rahama ta bisu ranta na suya,bata taba sanin haka khalipha yake ba sai yau,ashe duk sauqin kanshi da take gani da sakin fuska ta wani fannin baida kirki,ita zaiwa haka?"qwalla ce ta cika mata ido tayi hanzarin maida ta,a hankali ta soma takawa tabi bayansu,ta fasa canza abun karin,zama taci ko meye.




Gab da zasu isa qofad da zata sadasu da ainihin falon taso ta zame hannunta,turasu yayi ita da shi cikin wani daki wanda sai da suka shiga taga store ne na kayan abinci,idanu ya tsareta da shi sannan ya soma cewa
"Na gaya miki tun ranar farko ni dake,karkiyi wani abu da zai saka baqin fuskar dake yawan zuwa gidan nan su dora ayar tambaya a kanki ko akanmu,ke matata ce wadda na aura saboda ina sonta,ta aureni auren 'yanci da soyayya kuma akan radin kanta,a haka kike a idon family na....kiyi qoqarin ci gaba da kasancewa a haka,bana son ki bada qofar zargi" kalma ta qarshe data shiga kunnen rahama kenan wadda tazo wucewa,tsai tayi tana jira ko zata sake jin wani abu,saidai ba abinda khaliphan ya sake cewa,illa handkherchief daya ciro daga aljihunsa ya miqawa ayshan yana cewa
"Goge hannunki da kyau,baki tsaya kin wanke ba muka fito,ga gefan fuskarki ma ya dan baci kadan" a sanyaye ta saka hannu ta karba ta goge duk inda yace din,gefan bakinta ne kawai bai gama goguwa da kyau ba,dole ya karba ya sake matsawa gabanta kadan yasa handkherchief din akan yatsanshi ya soma goge mata,numfashinsu ne ya soma gauraya da juna saboda kusancin da hakan ya kawo tsakaninsu,idanunta ta daga saita saukesu fes cikin na khaliphan,ja baya yayi da sauri kaman wanda aka jonawa shock,cikin aljihunsa ya saka handkherchief din sannan ya juya ya soma yunqurin ficewa,hakan ya sanya rahama qara wuta tabar wajen kafin su fito su cimmata.




Duk kowa na saman tebur din kusan kaman qarasowarsu ake jira,ja mata kujera yayi ta zauna kafin shima ya zauna,hakan ya yiwa anni dadi sosai,yayin da amal ta dauke ido zuciyarta kaman zata fito,rahama kam hararar khalipha take a fakaice,wanda ko giyar wake tasha tasan bata isa ta harareshi ba gaba da gaba,haidar ne ya soma gaidata sannan mus'ab,dukkansu ta amsa cikin fara'a da jin kunya,don dukkansu sun girme mata amma suke girmamata kamar itace gaba da su,shikam haidar ganin qimarta yake tun waccar rana a capteria,abinda tayi ya tabbatar masa ita din nutsatstsiyar macace,sai gata a amatsayin matar wanshi hakan ya masa dai dai,a nutse ake cin abincin babu yawan surutu kaman jiya,tsakiyar shurun muryar rahama ta ratso
"Ya kamata amarya ki fadi abincin da kika fiso tunda kin shigo cikin iyalin da kowanne lokaci ake daukar abincin da kowa yafiso a girka"
"Karki damu....abun mamaki duka choice din anni akan abinci irin na aysha ne...." Ta wutsiyar ido aysha take satar kallonshi,itadai tasan basu taba magana makamanciyar haka ba,hasalima koda za'a titsiyeta batasan choice din anni ba a yanzu,dan sauya fuska rahama tayi sannan tace
"Haba ya khalipha...ka barta ta fadi da kanta mana...,wai haka ne?"murmushi ta saki wanda dan fitar sautinsa yasa khalipha daga kai ya dubeta sannan ya maida kan plate din gabanshi yaci gaba da juya abincinsa
"haka ne"ta bata amsa a taqaice,kafada ta daga tana tabe baki
"sai kace mutuniyar qauye?...."
"Suba mutane bane?,abincin da suke ci duka yafi namu lafiya,mu kusan duk kame kame muke,ko a qarfi idan kija hada yaron qauye saiya kada na birni guda uku shi kadai" anni ta bawa rahama amsa tana murmushi tare da son nusashsheta,sosai amsar ta yiwa aysha dadi ta kuma qarawa anni qima da martaba a idonta,khalipha ma yaji dadin hakan,saboda baison aysha tayi wani abu da zaisa rahama ta dauki haske kan wani abu daya shafeta ko ya shafi rayuwarta,daga haka bata qara tankawa ba kowa yaci gaba da cin abincinsa.
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*


********************** ⬇ **************************
********** Ai Hausa Novels ****************
*************************⬆ **********************


DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.


Visit > https://www.aihausanovels.com.ng


Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post.

Email > aihausabooks@gmail.com


******* FOLLOW US ******


Facebook: Ai Hausa Novels


Twitter: Ai Hausa Novels


Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels


WhatsApp Number: 08138873799




Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.


********************** ⬇ **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** ⬆ **************************
*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_


*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_


*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_


*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_


*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_


*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
08030811300


*KO KUMA*


07067124863




*DB*


33






Bayan sun kammala break din hira ta balle,wanda kusan haidar da mus'ab ne suka hada rudun,sun saka rahama gaba sai cakar da ita suke,itakam tayi kicin kicin don bata son raini,nan ma saida khalipha ya tsawatar,qarshe tashi tayi ya basu waje,amal itama ta miqe tana sauka qasa don zuwa kitchen ta samu ruwan da zata sha.


Mus'ab kewa anni qorafin motarsa tare da roqarta ta bashi daya cikin wanda ya khalipha ya bata,wasa qasa yake maganar saboda yadda khalipha ke harararshi "Shikenan....a baiwa diyata dayar,kai kuma ka dauki daya,amma fa aro..." Ta qarashe fada tana dubanshi,dan tsalle yayi kadan saboda yasan ta fadi ne kawai qarshe dai ta zama tashin halak malak
"Yes my anni!.....thank you" hannunshi khalipha ya saka a aljihu ya ciro muqullan mota yana fadin
"Kin tunamin kuwa anni....ina haidar...idan kun samu lokaci ko zuwa dare ne kuje ku dauko motarta dake wancan gidan...wacce zata yi amfani da ita kenan anni?"
"A debosu duka ta dinga hawa wadda takeso ko 'yata" kunya ce sosai ta kama aysha da wani irin nauyi,ita dako rage hanya ba'a qaunar ayi mata a rayuwa yau ita ake cewa ta dinga hawa mota bama daya ba har guda biyu?,itakam wacce irin qauna mutanen ne ke mata ne
"Allah ya saka da alkhairi ya jiqan magabata ya qara lafiya..na gode"
"Amin...amma babu godiya saboda tamkar 'ya kike kema,ku bata muqullanta ta soma hawa duk sanda takeso" dan dubanta khalipha yayi sannan ya maida dubanshi ga anni yana miqewa
"Banjin ta iya driving...."
"Faduwa tazo dai dai da zama....sai na koya mata kawai" mus'ab yayi hanzarin fada,harara khalipha ya maka masa wadda ta sanyashi ya nutsu sannan ya dubi anni
"Zan fita amma bazan jima ba zan dawo"a dawo lafiya suka yi masa gaba dayansu.




Ranar a nan ta wuni gaba daya,ko da su atika zasu shiga girkin dare a lokacin bata jima da gama sallar la'asar ba binsu tayi kitchen din,kusan ranar gaba daya ita tayi girkin daren sai tattaimaka mata da suka dinga yi da wasu abubuwan,da fari qin sakar mata sukayi suna tsoro suna dari dari,daga bisani dole suka sakar mata din ganin yadda take komai cikin qwarewa,a nan suka saba sosai dasu atikan kamar sun jima tare,qarfe shida suka gama ta baro kitchen din ta koma sashensu ta shiga wanka.




A hankali ta tura qofar dakin kaman yana nan duk da tasan baya nan din,gefan akwatunanta ta nufa ta bude,doguwar riga ta ciro ta ajeta saman akwatin sannan ta shiga bandakin ta tura qofar ta sama tara ruwan dumi,ba jimawa ya cika ta soma wankan tana jin dadin dumin ruwan da yadda yake bada qamshi shi da kansa ruwan,ita kadai cikin ranta take jinjina gayu irin na khalipha da son qamshi.




Shida saura ya shigo gidan kamar yadda ya saba sai daya biya yaga anni kafin ya wuce sashensa,annin tana ta qorafin wunin da yayi yauma a waje,dariya kawai yake yana jinjina yadda anni keso ayshan,ya sani duk don saboda ita yayi hakan,tabe baki rahama tayi bayan ya wuce wadda ke zaune gefan annin tana latsa waya ta kalleta
"Nikam wannan auren soyayya akayi?,ango da sai kayi satima kuna gida daya baka ganshi ba amma shi kwana biyu kacal ya soma fita yana wuni?,kodai bata iya kula da miji bane?"
"Banda abinki rahama wannan ai zancanku ne keda yayan naki" anni ta fada tana miqewa don da wuri take daura alwala kafin a kira sallah ta shige toilet abinta,hada ido sukayi da amal,saita saka dariya wadda tayi ne kawai don ta qular da rahaman itama ta miqe ta bar falon ta shige dakinta




Cikin satin aysha ta soma koyan mota sosai ta hannun aliyyu,wanda sam khalipha ya hana mus'ab yace haidar din ya fishi nutsuwa,tun tana dari dari da su har ta soma sakin jiki,haidar nada kirki qwarai,yana da daraja mutum,yadda yake bata girma abun har kunya yake bata,idan taga yadda yake tsarewa rahama da amal gida idan baiga dama ba sai abun yayita bata mamaki,suna kamanceceniyar halayya da khalipha ta wani fannin,zamanta cikin gidan sai ya soma yi mata dadi,ta soma sakewa musamman idan tana tare da anni,duk wata kunya da surukuta anni ta soketa tsakaninsu,sukan zauna su taba hira duk da har yanzu bata iya bude baki sosai tayi magana yadda ya kamata mai tsaho,saidai tana qoqari matuqa wajen ganin ta saba dasu din.




Sati uku da biki ta soma warwarewa sosai,janta a jiki nuna mata ita watace da mu'amala mai kyau shi ya taimaka wajen samuwar wannan sauyin,saidai abu daya da bata jin dadinshi shine yanayin yadda rahama take mu'amalantarta,takan bata girma dai dai gwargwado,hakanan bata shiga sabgar da bata shafeta ba kamar yadda haka halayyarta take tun a gida,saidai duk wani motsi na ayshan a idonta yake kamar wadda aka baiwa gadinta,hakanya sanya itama ta iya takunta take matuqar taka tsantsan da ita.


🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶


Parlour din asma'un cike yake da qawayenta na makaranta wanda ta gayyacesu suzo gidanta kwanaki sati hudu da tarewarta,manyan qawayenta ne da take ji da su ko ince a kullum take qoqarin yin abinda zata burgesu su fahimci cewa ita din ba qaramar mace bace,a ranar ta baiwa yarinyar da aka kawo mata a matsayin 'yar aiki qwaya daya 'yat qabilar igbo umarnin ta dafa musu abinci har kala uki,baya ga snacks da lemuka da aka jibge tsakiyar falon,anaci ana kwasar shafta.




Gaba daya hankalinsu yayi gaba babu wadda taji kota lura da shigowarshi,fuskarshi tamke yake bin kowacce da kallo,sai a sannan suka ankara da shigowar tasa,nusaiba itace ta soma masa magana cikin wasa irin na qawar amarya
"Ango kace kana kusa da dawowa ma kenan.....dama kai muke jira ai" maimakon ya sake mata su gaisa kaman yadda suka saba yi a lokacin hidimar biki saitaji yaja tsaki tare da yin gaba ya haye sama,dukansu baki galala suka bishi da kallp har ya gama hawan
"Ke....haka naki mijin kuma yake?" Cewar daya daga cikin qawayen tana riqe da haba cikin mamaki
"Wannan ko anya asma'u?,kinga kallon raini da wulaqancin da yake mana kuwa?"dayar ta kuma fadi
" ni ban gaji wulaqanci ba wlh,oya ku tashi kawai mu wuce"cewar husna babbar qawar asma'un da take ji da ita,sai a sannan da taga suna shirin miqewa asma'u da wani baqinciki ya qumeta da azabar kunya ta magantu
"Babu wannan maganar don Allah kuyi zamanku ina zuwa....yana da fushi ne zai iya yiwuwa a waje aka bata mishi rai bari naje" ta fada da sauri tare da miqewa tayi hanyar stairs ranta na bala'in baci.




Tura qofar dakin tayi,saita sameshi yana tsaye ya kwabe rigarshi saura singlet yana shirin cire dogon wandonshi ta shigo,cikin nuna bacin rai da fusata ta kalleshi
"Haba hamid....ya zaka kunyatani gaban qawayena don Allah?,me suka taba yi maka zaka yi musu wannan wulqancin?,so kake suje gaba su samu abin bada labari?" Bai tankata ba har sai daya cire wandon saura gajeran wando kawai sannan ya dago ya dubeta cikin qanqan da idanu
"Ke,an gaya miki bansan ciwo kudi ba?,ko an gaya miki tsintosu nake?,ohk kin zaci za'a ci gaba da yadda aka saba ko?,toni ba haka nake ba,nasan ciwon kudi nasan mutunci da darajarsu,haka kawai ki taramin garadan qawayenki ki kwaso abinci da abun shan da a qalla zamuyi sati muna ci ki jibge musu don tsabar burga?,to wallahi kiyi gaggawar zuwa ki sallameshi ki kuma kwashemin kayan abincina ki maida store" tsantsar bacin rai da mamaki ne qarara ya bayyana a fuskar asma'u,tana jin ya xama lallai ta nunawa hamid bacin ranta qarara saboda gaba
"Me kake nufi hamid?,qawayen nawa?,to wallahi babu inda zasu,kayan abinci kuma da kake magana ai daga gidanmu aka hadoni da shi ko?" Dawowa yayi da baya maimakon daa da yayi gaba zai shiga wanka
"Haka kika ce?,don an kawo wadan nan matsoyatan kayan abincin kike gaya min haka?,ohk fine....ki gayamin nawa na kashe miki wanda sunyi ninkin baninkin kudin kayan abincin da aka kawo min?,koni na gayawa iyayenko ina da buqatarsu ma?,a matsiyaci kika aureni?,tunda ba zaki iya sallamarsu ba ni zan iya" ya fadi yana nufar qofa,da mamaki ta soma tsaidashi saboda singlet da gajeran wandon dake jikinsa amma ko juyowa baiyi ba bare ya saurareta.




Kaf dinsu saida kowacce ta miqe tsaye a tsorace ganin mijin qawar taso a haka,dubansu yayi sannan ya soma magana
"Kafin na qirga biyar kowacce a cikinku ta kwashi matattun qafafunta tabar min gida tunda yunwa ce ta kawoku,kada wadda ta sake zuwa min gida tasha min koda ruwa ne bare abinci,ku cika cikinku a gidajen ubanku kafin kuxo" cikin bacin rai husna da take jin tafi qargfin wulaqanci ta soma maida masa martani,kanta yayo wanda hakan ya sanya suka qarasa ficewa a guje ba shiri ba tare da sun tsaya daukan kayayyakinsu ba,bayansu yabi cikin daga murya yake baiwa inyamurin mai gadinsu umarni cikin karyayyen turanci
"Maza ka sakar musu karnukan nan su qarasa rakasu" jin abinda yake fada ya sakasu qara mai,taimakon da Allah yayi musu daya motar da suka zo cikinta tana qofar gidan basu shigo da ita ba saboda motocin hamid guda uku dake harabar wajen data asma'u daya data zo da ita ta cike wajen.




A tsaye a falon ya tadda asma'u tana qwallar takaici tare da tunanin anya kan hamid daya kuwa?,lafiyarsa qalau?,kodai ya soma bin hudubar yayyensa mata randa sukazo da sunan sunzo ganin amarya da sukaji suna gaya masa
"Wannan matar taka sai kayi da gaske,makarantarsu daya da nabihat,bata da kirki batason talaka,dagawa gareta da girman kai,hakanan kudinka takeso tosai kayi tsayin daka idan ba haka ba rainaka zatayi wallahi" abu daya ne bata sani ba,hamid mutum ne mai shegen son abun dunuya,yana da dukiya amma ta cinsa ne iya shi kadai,ko sanda yana gida wani abun sai ya rataya a jikin mahaifinsa yayi masa bazai taba qwandala tashi ba,irin yaran nan ne dako.iyayensu basa iya taimakawa banda Allah yasa mahaifin nasa yana da wadata shima,saidai matsalarsa daya mahaifin nasa,mutum ne da bashi da tattali,yana da son nunawa duniya shi wani ne ko nawa zai kashe akan haka zai iya,ya kuma yi nasara don sunansa ya dan fita,sakamakon yadda yake nuna qaryar arziqi don baikai nan ba.




A parlour ya taras da ita zaune tana gunjin kuka,kota kanta baibi ba ya wuce zuwa sama abunshi ya dauki wankanshi.




Minti talatin ya sake saukowa,ya tsuke cikin qananun kaya,yana dannan waya ba tare daya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login