Showing 135001 words to 138000 words out of 184891 words

Chapter 46 - DAURIN BOYE Complete Document by Safiya Abdullahi Huguma.txt

mala,halinka na gari ya bika,Allah yaci gaba da kulama da iyalinka kar ya barsu su tozarta har abada" taso haduwa da khalipha amma Allah baiyi ba harta koma qasar,saidai lambar waya da sukayi musaya ita dashi suke gaisawa,ta tafi tana kewarsu bayan tayi musu alkhairi mai.yawa,cikin 'yan uwanta ba wanda ta waiwaya,haka suka di.ga mata zarya suna zaton samun abun duniya daga gareta,saidai yadda tazo da abinta haka ta koma dashi,abinda sukayiwa zuri'ar sa'id bata jin zata iya baiwa kowa komai nata.




Da wannan kudin ne khalipha ya gina rayuwarshi,ya gina mahaifiyarsa,ya gina 'yan uwanshi,Allah ya albarkacesu ya bude company nashi na kanshi,duk da kamfaninsa bai fasa hulda da wasu kamfanunuwan da yasan sunfi nashi suna ba,bai raina duk wanda ya nemeshi,kafin wani lokaci Allah ya sanyawa dukiyarshi albarka,rayuwarsu tayi kyau,suka manta da duk wata wahala ta rayuwa,fili ya siya mai azabar girma,ya ginawa anni gida na gani a fada,saboda yayi alqawarin dukkan wata wahala data sha a rayuwarta saiya mantar da ita,bazaiyiwu dan adam ya manta sharri ko alkhairi ba,amma tabbas anni ta manta da wata wahala ta rayuwa data sha a baya,haidar da mus'ab kuwa dukkansu saida suka zabi makarantar da sukeso a duk qasar da sukeson yin karatu,ya wadatasu da duk wani abun buqata na rayuwa.




Abu daya ne anni ke fama da khalipha akai danginta na niger,kamar yadda ya gaya mata ne har yau yaqi sakin jiki dasu,duk yadda suke nuna musu qauna da kulawa,yana jin cewa suma suna da tasu gudunmawar da suka bada wajen tabarbarewar rayuwarsu da halin da suka fada,saboda watsar da anni da sukayi da duk lamuranta tunda suka aurar da ita tamkar ba jininsu bace ita,dole daga bisani don babu yadda ya iya ya sauko suke gaisawa da su.




Rahama jikar wannan yayan annin ce,wanda kusan lokaci daya akayi aurensu da anni da babarta,kusan sa'anni suke da khalipha,tunda taga hoton khalipha take mayatar sonshi,saidai shi ko kadan bai taba sonta ba,asali ma cikin dangin nasa baya jin zai iya aurar wata.




Cikin shekara biyu suka zama tamkar basu ba,saika rantse cewa basu taba dadanar zafin talauci ba,Allah ya sanya albarka mai yawa cikin rayuwarsu,ya duba zuciyarsu basu nufin sharri ga kowa,hakanan basu zalunci kowa ba,har lokacin basu manta da hajar ba,shuru shurunta,haqurinta,kawaicinta da yanayin kyawawan dabi'un da take dasu,hakanne ya sanya khalipha ya gina masallatai da.islamiyyu rijiyoyi da borehole borehole duka da sunanta kan Allah yakai mata ladan,hakanan bai manta da mahaifinsa ba,shima yayi gine ginen masallatan juma'a dana kamsusu salawati sadaqatul jariya a gareshi (a nan dan jan hankalin da zanyi ga wadanda Allah yayiwa iyayensu rasuwa kafin suyi arziqi,idan arxiqi yazo musu daga baya suyi qoqarin yin wani abu da Allah zai dinga kaiwa iyayen nasu ladan,koda baka da arziqin gini ko qur'anai ka siya kakai masallaci duk wanda ya karanta Allah zai kai ladan cikin mixanin mamacin,koda qur'ani daya ne,koda rijiya daya ce,koda borehole daya ne,Allah ya jiqan iyayenmu wadanda suka rigamu gidan gaskiya,wadanda ke raye kuma ya qara musu lafiya da nisan kwana mai amfani)


Lokaci guda sunan khalipha ya soma fantsama cikin al'umma,ya soma shuhura tauraruwarsa ta fara haskawa,duk wani mai kudi so yake ya qulla alaqa dashi,duk wani dan kasuwa so yake yayi hurdar kasuwanci dashi,a sannan ne su kawu hamza hankalinsu yadawo kansu,wanda tun bayan rasuwar hajar basu sake ganin gilmawar wani daga cikin iyalin sa'id ba,hakan babu wanda ya nemesu ko ya tambayi ba'asi,ko yabi dalilin shurunsu,sabgar gabansu sukaci gaba dayi,dare daya suka tashi sukaji an fara ambatar sunan khaliphan cikin jaridu gidajen t.v dana redio,nan fa kowa ya kade babbar rigarsa,kowa ya kade tsohon zumunci da suka bunne suna alfahari da dansu ne,suka bazama zuwa gidan khaliphan donsu sabunta kusancin dake tsakaninsu.




Duk wanda yaje gidan a cikinsu saiya jima a qofar gidan yana qarewa gidan kallo cike da mamaki da tambayar kanshi ya akayi khaliphan yayi kudi?,ba shakka ya taka sahun mahaifinsa,babu ko kokwanto arziqi ajininsu yake kenan?,duk cikinsu ba wanda baiyi wannan tunanin ba.




Da fari sanda suka soma zuwa anni qin saurar kowa daga cikinsu tayi,saboda dukkansu ba wanda abinda sukayi musu bai tsaya mata a rai ba,kwantar da kai ban haquri da magiya gami da zirya haka suka dinga yi,daga bisani ita da kanta taga meye riba idan ma ta riqesun?,kafin ita dubu nawa aka yiwa irin haka yau ina suke?,haka ta haqura ta yafe musun.




Duk abin nan da ake khalipha bai qasar yayi tafiya,sanda ya dawo ya taras da abinda ke faruwa ba qaramin tashin hankali yaso yi ba anni ta dakatar dashi,a qarshe ranat bai iya kwana a gidan ba,saboda ganinsu da yayi ba abinda yake tuna masa sai halin da suka jefasu a baya,ba abinda yake tuna masa sai hajar dinsu,ba qaramin daga anni tasha da khalipha ba kafin ya sassauto,duk da haka bai qaunar haduwa dasu kada ma kawu idris yaji labari,domin shi ya sani yanda basu so mahaifinsu ba,basu sosu sanda suna cikin halin ha'ula'i ba,basuso su sanoda duba maraicinsu ba to babu yadda za'ayi a yanzu su sosu fisabilillahi saidon wata manufa.




Ai kuwa ganin sun samu afuwa sai kowa ya soma yunqurin yadda zai samu fada mai girma a wajen,abu na farko da suka soma fafutuka akai shine cusawa khalipha 'ya'yansu ko Allah zaisa ya kamu da soyayyar wata daga ciki ya aura,duk abinda suke kallon takunsu kawai yake,yasan manufar kowa a cikinsu,abun ya sake baiwa khalipha tsoro da mamaki yadda kowa ya koma yana haba haba dashi mahaifiyarsa da 'yan uwansa,kowa so yake ace na hannun daman khalipha ne,kowa 'yarshi yakeso ya bashi,hakanan suma yaran kowacce burinta yace yana sonta,kama daga 'yammatan danginsu dama wadanda bana danginsu ba,kowacce zalamarta ta fito muraran,abinda ya sake tsoratar dashi kenan,yana tsoron ya dauko wadda zata soshi ba don Allah ba,wadda zata zama silar rabuwar kawunanshi shida 'yan uwanshi,wadda zata hana 'yan uwanshi su mori wahalar da suka sha,ta cire duk wata qauna da shaquwa a tsakaninsu,ta cutar masa da mahaifiyarsa shima qarshe ta cutar dashi,dalili kenan daya sanyashi bin hanyar daya bi domin gwajin samun soyayya ta domin Allah.




Qatutuwar ajiyar zuciya khalipha ya sauke yana ci gaba da jan layukan da zuwa yanzu sun qaru kan takardar babu adadi,aysha dake jingine jikin kujera idanunta alumshe hawaye na ratsowa saita rasa abinda zata ce,tsakanin ita dasu khalipha batasan wanda yafi wani fuskantar qalubale matsatsi da wahalar rayuwa ba,batasan wanda yafi wani fuskantar qalubale ba,wacce iriyar rayuwa muke ciki a yanzu?,me yasa zuciyoyinmu babu kyau?,me yasa muka watsar da zumunci muka wulaqanta shi?,muke jin jininmu ahalinmu?,muka fifita mai dukiya akan mara shi?,ashe haka shima ya fuskanci rayuwa?,ashe haka suka sha fama da gwagwarmaya?,zuciyarta karyewa tayi baya ga hawaye sai sautin kukan ya fara fitowa kadan kadan
"Humairahh" ya kira sunanta a tausashe duk da yadda zuciyarsa ke zafi sakamakon tabo wani ciwo da yayi da yake zuciyarsa,saita bude jiqaqqun idanunta akansa ba tare data motsa ba sautin kukanta nason qwacewa,bude mata hannayensa kawai yayi batayi wata wata ba ta isa inda yake ta fada ya maida hannayen nasa ya rufe,kuka sosai ta saki,saiya dinga hadiyar wani abu mai tauri wanda idan ka kalli adam's apple dinsa dake motsawa sama da qasa zaka fuskanci hakan.


46




Misalin sha daya na safe yana tsaye gaban dressing mirrow din dake dakin yana daura agogon hannunshi,yayin da taje zaune daga gefe tayi kyau cikin material doguwar riga da mayafinsa,yatsun hannunta take murxawa,tayi nisa sosai cikin tunani,batasan da wacce fuska zata kalli khalipha ba saboda munana zatonta da tasoyi a gareshi,sai gashi rayuwarsu ita dashi din taso tayi kamanceceniya,anya kuwa zata samu wani kaman khalipha a rayuwarta?,anya kuwa ba dace bane wanzuwarsa cikin rayuwarta,ya fuskanci fiye da abinda takeso ya fuskanta,batajin akwai sauran abinda ya rage kuma,jarumi ne tun quruciya kawo girmansa,zaki ne da yake iya fuskantar duk wani qalubale dake gabanshi,mai qaqqarfar xuciya,kaifin hankali jumuri da juriya.




D'as d'as taji ya murza yatsunsa saitin fuskarta wanda hakan ya sanyata dagowa da hanzari hakan ya tabbatar masa lallai tayi nisa cikin duniyar tunani
"Madam tunanin me kike kuma haka?" Kai ta kada tana fidda qaramin murmushi daya fitar da dimple din fuskarta gami da dauke idanunta daga kanshi,saboda wani kyau da yayi cikin suit din daya tsuke a ciki
"So ya jikin naki?"
"Da sauqi" ta furta da muryar mai sanyi
"Ma sha Allah"
"Sauko muci abinci" sai tadan noqe kadan tana kallonshi,baibi ta kanta ba ya bude komai ya zauna dirshan a qasa yana lanqwashe qafafunsa,sai a sannan ya dubeta da lumsassun idanunsa wanda kullum suke cike da wani irin kwarjini,kasa musa masa tayi,sai ta janyo jiki ta sauko qasan itama tayi irin zaman da yayi,cup biyu ya hada tea ya zuba komai kuma cikin plate daya
"Bismillah" ya furta yana watsa mata kallonshi bayan ya saka chips a bakinsa yana taunawa a hankali,a sanyaye ta sanya hannu ta dauki ruwan tean din ta soma kurba a hankali,nashi cup din ya aje bayan ya zagaye hannayenshi a jikin cup din ya zuba mata idanunshi,yana son yasan dalili ko ya zaluqo abinda ya sanya kulli yaukin yake jin sabbin feelings game da ita,ya sani dai cewa da fari tausayinta ya soma ji,daga bisani sanyinta da yanayinta ya soma yi masa kama dana hajar,a yanzun kuma bazai iya tantance komai ba,baisan dalili ba baisan me yasa ba,bashi da amsar duka tambayoyin dayakewa kanshi.




"Zuwa yanzu ina fata kin gamsu da cewa ba yaudararki koda siffa biyu khalipha yazo miki ba,sannan kin fahimci khalipha shi dinma ba kowan kowa bane,irin rayuwar da kikayi shima ya dan dana ya kuma fuskanci makamanciyarta,ina fata na wanke dukan wani shakku da tarin tambayoyin da kike dashi a kanmu?" Ya qarashe maganar yana qoqarin kallon qwayar idanunta,dan qaramin murmushi mai gajeran zango tayi,saita kasa cewa komai taci gaba da kurbar shayinta
"Kinga na gaya miki gaskiya....koki tashi tsaye ki karbi mijinki ko su qwace miki shi" ya fada cikin idont care manner,ba don kuma hakan bane har zuciyarsa,saidai yayi hakanne saboda ya gwadata,hakanan ta samu faduwar gaba da kalamanshi,tana son ta kalleshi,tana son ta tambayeshi ya dauketa ne amatsayin mata,tana son jin ya canza mata matsayine daga wanka ya bata a baya amma ba zata iya tambayar tashi ba kada ya zaci wani abu.




Cokalin hannunshi ya karkada cikin cup din tangaran din dake hannunshi,wanda shi ya bada sautin daya dawo da hankalinta kanshi
"Daga yau ina buqatar amsar duk wata tambaya ko magana dana miki,shurun kin nan bana buqatarsa alright?"
"Toh" ta furta,sai yaci gaba da kallonta,tayi laushi sosai akan sanda suka taho daga gida da kuzarinta harda tsokanar fada wa rahama,yana ganin tana da buqatar shan iska,saboda haka a take cikin ranshi ya soke tafiyarsu anjima da yayi niyya,saiya buda wayarshi ya tura saqonni sannan.ya rufe ya miqe tsaye yana duba agogon hannunshi.
"Hudu dai dai ki shirya zanzo ki rakani waje waje" tana daga zaune ta daga idanunta har ta kalleshi tana jin faduwar gaban kada dai yace gidan ummi zasu koma,yanayin yadda ta kalleshin sai daya dan sanya bugun zuciyarshi qaruwa,saboda yadda idanun nata suka sake haske da girma
"A dawo lafiya" tace dashi sanda yake fita,ya amsa mata cikin kulawa sannan yaci gaba da takawa har ya fice




Tana kammala sallar la'sar ta isa gaban mudibi ta tsara kwalliya mai kyau da burgewa,tayi kyau cikin atamfa riga da skert wanda kalarta take mai duhu,dalili kenan daya sanya ta sake mata kyau ta haska fatarta mai haske da qyalli,tsaiwa tayi gaban mudubin tana kallon kanta,duk da cewa ranta akwai damuwa amma bai hana kwalliyarta yin kyau da tasiri ba,ita kanta tasan zuwa yanzu ado da kwalliya yabi jikinta,ya zame mata jiki,koda inda zata ko babu ba zaka rasata cikin kwalliya ba.




Tunda ya shigo yake kallonta,komai nata yayi masa kamar tasan ra'ayinsa da tsarinsa game da kwalliya,har ya kammala shiryawa ta tsone masa ido,wannan karon shima cikin shadda ya shirya,cikakkiyar shigar kanawa zam,badai iya sanya sutura ba dama,yana gaba tana binshi a baya zasu fice daga dakin ya juyo cikin wani irin zafin nama,hannunta ya cafka yadan rage tazarar dake tsakaninsu har tana jin saukar numfashinsa,kamar mai rada yace
"Bazan iya daurewa ba,kinyi kyau humairaaah" ya fada saitin kunnenta wanda hakan ya sanya tsigar jikinta tashi,kunya taji ta kamata bugun xuciyarta na daduww,saitayi hanzarin sake ja baya gami da zare hannunta daga nashi,kai ya girgiza mata ya nufarta kamar kuma wanda aka umarta saiya tsaya cak sakamakon tuna wani abu da yayi ya juya ya fice,sai dataga fitarsa sannan ta bishi a baya.




Wata tafiya ce ta alfarma cikin rakiyar motocinsa wanda bata sani ba biyoshi sukayi daga kano ko dama yana da wasu a nan lagos,tafiya suka yi mai dan dama kafin su iso bakin wani beach,wajene mai kyau da tsari,tun daga saukarsu ya burgeta,tana zaune a mota sai da yayi mata magana sannan ta fito,su biyu suka dinga takawa suna zagayawa bakin wajen,wanda daga qarshe suka qare a boat,su biyu ya biyawa saboda haka iyasu ya dauka,ya biya dukka awannin da zasu kashe cikin ruwan.




Iskar dake tasowa daga cikin ruwan mai dadi ce da kuma wani irin sanyi mai armashi,idanunta ta lumshe tana sheqar iskar har cikin zuciyarta take sauka da sanyinta tana wanke duk wata damuwa da qunci da yayi saura a ciki,wani lokaci idan wani jirgin yazo giftasu fallatsin ruwan kan tashi har kan fuskarta saboda tana daga gaba gaba,har lokacin idanunta na lumshe sanyin ruwa yayi mata yadda takeso,murmushi ta saki sanda ta tuno wani scene data gani cikin film din da khalipha ya dage sai ya tayata gani,yadda masoyan ciki suka gabatar da wata zazzafar soyayya cikin jirgin ruwa,saita fara imagination wanda ya sanya murmushinta fadada.




Jin kaman ana shirin rungumota ta baya ya sanyata saurin waiwayawa,khalipha ne tsaye hannayensa goye a bayansa yana kallonta,ya bude baki zaiyi magana wayarta ta dauki tsuwwa,saita juya tana dubawa,aliyace ke kira,latsawa tayi ta kara a kunnenta,dai dai sanda a sake jin ya matso gab da ita fiye da da,don a yanzun ko qwaqwqwaran motsi tayi zata iya fadawa jikinsa,hakan yasa ta hadu tsam ta hada hankalinta waje guda,saidai hakan bata samu ba,don duk yayin da ruwan yayi wasa da jirgin saita gogi jikinsa,hakanne ya sanya ta danna handsfree ba tare data sani ba
"Bakya jina?" Tajiyo muryar nan ta aliya
"Ina jinki sashen,ya gida yasu mama"
"Lafiya lau sashen,na shiga ta wajenku na tadda baku nan,tace min kunyi lagos?,hala amarci aka tafi shahh hh...." Ta qarashe maganar da sigar zolaya tana bayyananniyar dariya,kunya ce ta kama aysha,saurin katse aliyan tayi,duk da tasan idan aliya ce tayi ta banza saita gama amayar da abinda ke cikinta
"Banason iskanci aliya meye haka ne?" Dariya ta sake yi
"Au na manta fa yayanki ne ko?,to ai ba laifi yayanma ai girma ne,amma dai abi a hankali kada komawa wudil ya gagara"
"Dama abinda kika kirani ki gayan kenan aliya koko me?" Ta fada tana dan hade rai kaman tana gabanta,don ji take kamar ya jefa wayar cikin ruwan dake gabanta tsabar kunyar da aliya ke bata,gashi tana iya jiyo yadda khaliphan ke turo kai da alama kunnensa yakeso yaji abinda aliyan ke fada sosai,dariya ke taso masa yana danneta ganin yadda mode din ayshan ya sauya,bai manta abinda mahmoud ya gaya masa ba kusan hakan yace mishi ana ya gobe zasu tafi,da alama bakinsu daya
"To aini kaman qarar ruwa nakeji,ciki kuka kwana ne?"
"Sai anjima,ki gaida mama da kyau" aysha ta fada tana shiriin katse kiran
"Ayyah sashen kiyi haquri,nikam kira nayi na baki saqo wajen boss....abokinshin nan wallahi ya fiya matsa lamba da yawa"
"Zan gaya masa,ki gaida mama bana ji sosai" ta fada tana katsewa saboda kada aliyan ta baarota,don tasan kadan daga aikinta ta fadi maganarta,kuma ita babu ruwanta ita zata bari da jin kunya.




"Mu haka muke,bama kama abu da wasa,idan muka soma sai mun cimma gaci,jarumtarmu a nan take" ya fada yana nuna saitin zuciyarshi da yatsa,saita zame jikinta dake tsakanin qarfen jirgin da khalipha daya katangeta ta baya,kamar hadin bakintana tsaka da takwa don barin wajen kiran hanan ya shigo,shima tana zaune kan wani dan tebur da aka ajiye musu coffe da kayan motsa baki zata soma amsawa taji an zare wayar daga hannunta,handsfree ya maidata sannan ya aje saman teburin ya zagaya kujerar dake fuskantarta ya zauna bayan ya harde hannu ya zuba mata idanunshi,hakanan ta dake ta soma amsawa
"Anya lafiya ko ayshat,kodai wani ya riqe mana ke ne?" Idanunta dan fiddo
"Haba mana hanan,kada muyi haka dake mana ya zaki fadi haka" dariya ta sanya cikin nishadi
"Ah to ni na sani,kinsan soyayya ba abinda bata haifarwa,sauyawar hali da tsarin rayuwa na lokaci guda....wai da hakan zata faru kuwa da nafi kowa murna"
"Me yake faruwa a makaranta?"
"Labiba ta shigo dazu nemanki,tace jibi kuna da C.A" idanu ta zaro don shaf ta mance labiban ta gaya mata dr mahadi ya fadi cewa zaiyi CA din cikin sati duk da bai tsaida rana ba
"Ya salam,ina hanya in sha Allahu"
"To Allah ya kawoki lafiya,kinga matar nan ma tabi mijinta taje tayi bulunbuqui da ita" tasan sarai da maman hunaifa take
"Ba ruwana,maman hunaifa ta waje na ce"
"Hademin kai zakuyi kenan?,zaki dawo ki sameni" ta fada tana dariya dariya da haka sukai sallama.




Cikin narkewar da batasan tayi ba ta langwabar da kai tana duban khalipha,kallon data masa sai ya zama kamar da manufa tayi,gaba daya ya kashewa khalipha jiki,yasan me takeson cewa makarantarta,da qyar ya bude bakinsa yace
"Baki da damuwa".




Sun jima kafin subar nan,daga nan dinma wani wajen suka qara nufa,sai da sukaje waje uku kafin su koma hotel.




Washegari da daddare ma ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login