Showing 117001 words to 120000 words out of 184891 words
Chapter 40 - DAURIN BOYE Complete Document by Safiya Abdullahi Huguma.txt
kammala abinda take tashiga wanka wanda bata samu yi ba saboda gyaran kayan sawarsu datayi,harda na khalipha wannan karon nata qyake ba dui da batasan ya zai dauki abinda tayin ba,bata gane kurenta ba sai data fara gyaran don batasan haka kayan keda uawa ba,hakana komai nashi a tsare yake a muhallinsa,kamar side sin tie socks boxers da sauransu kowanne daban daban,dole ta maida tsarin yadda ta gashi.
Tana shirin shafa mai wayarta tayi tsuwwa,murmushi ta saki ganin maman hunaifa ke kira
"Mutuniyar nan anya ba wani ne ya riqe mana ke ba?,kin riga mu tahiwa gashi har yau baki dawo ba koni gashi na haqura na dawo duk da baban hunaifa bai koma ba?"
"Kinga barta dawowar tata duk a suna ne,sun maidani abin tausayi ita da mijinta,a gabana take fecewa mijinta kwalliya duk sanda basu da lactures su fice yawo abinsu,yanzun ma kin ganta gaban kayan kwalliya tanayi" cewar hanan wadda ta amshe wayar ba tare data bar mmn hunaifa ta qarasa fadin abinda takeson fada ba,dariya aysha ta saki,duk sai taji tayi missing nasu,batasan me yasa khalipha ya tsaidata daga komawar datayi niyya ba dazun da safe
"Allah aysha saimun rama,Allah yakai damo ga harawa bari muna muyi auren nan saita ri ga rufe idonta"
"Idan ban wa mijina ba nikam duk banga amfanin ma kamfanin sutura da kayan kwalliya ba,kuma idan yazo kanku ban yadda ku saurara ba" mmn hunaifa dake gefe ta fadi,dariya suka sa gaba daya sannan suka soma gaisawa tare da tambayatta lafiya,sa kawai tace musu basu da lacuters ne dalili kenan amma tana kan hanya,hira suka yi sosai sai data ji kiranabban hunaifa na shigiwa alamar ya iso sannan sukayi sallama,aysha na dariya ta aje wayar,a hankali ta dora idonta kan fuskarta data bayyan a gaban mudubi,murmushi taci gaba dayi tana tuna yadda ma'auratan ke bawa junansu kulawa,abun na mtuqar bata sha'awa da burgeta kaman yadda yake burge hanan,sai kawao ta sami kanta da yin kwalliya sosai duk da cewa a yanzun mawuyacine ka ganta ba kwalliya koda lite ce.
Sosai tayi kyau uta kanta ta gani,siririyar sarqa ta saka da dan kunenta tana hade da zobe mai kyau ta feshe jikinta da turare sannan ta yafa yalolon mayafi daya dace da adon nata,gurin anni takeson shiga sai ta dauki litattafanta ta fita dasu tana son ta duba.
Ba kowa a falon sai rahama dake faman waya,wani kallo tabi aysha dashi tun daga sama har qasa,sauyawar yarinyar na bata tsoro,dudud wata nawa amma kaman an maya wankan engine,amal ce ta shigo daga wata qofa wadda zata kaika bayan gidan,itama kallo tabi ayshan dashi,duk ta lura dasu saita rasa na meye kallon?,a baya sam bata taba tsayawa dubawa ba bare ta tantance,saidai zuwa yanzu rashin jituwa tsakanin amal da rahama ke bata mamaki da tambyar kanta meye sila,uwa uba yadda amal din ta sake ja baya da ita ta rasa daliki,koma meye dukansu ba damuwarta bane,tana qoqarin sauke nauyin da musulunci kawai ya dora mata,haka nan taji zaman falon bai gamsheta ba,saboda haka ta jiya kawai ta fuce zuwa can bayan gidan inda ya wadatu da yawan shuke shuke,ta bude takardunta ta soma dubawa daya bayan daya.
Bata nima da zama ba taji shigowar motocinsu haidar,da alama daga office suka dawo,saitaqi tashi zuwa cikin gidan,don karatin ya soma mata dadi,duk da cewa akwai ma'aikatan dake gayafn flowers din wajen dake wucewa jifa jifa,amma da yake ba hayaniya suke ba basu dameta ba.
Sosai ta duquf tana duba wata paper dake hannunta,sai hancinta ya dinga jiyo mata wani qamshin turare nadaban wanda kamar ta sanshi,hat ta basar taji qamshin na sake daduwa cikin hancinta,saita daga kanta,khalipha ke dosowa inda take,bayanshi yaro shi nasir na biye dashi dauke da wasu fikes,juyawa taga yiyi yayi mahana kadan da shi saitaga yadan rusuna cikin girmamawa ya juya yabar wajen,shi kuma yaci gaba da qarasowa inda take,faduwar gaba tasamu wadda ta zame mata jiki aduk sanda ya kalleta ko suka kadaice daga ita saishi
"Sannu da zuwa" ta fada a yangance wanda ita batasan tayi din ba,idnunshi a kanta ya amsa shima cikin nashi salon.
Ticket din dake hannunshi ya miqa mata guda daya tana duban kwalliyar da tayi ta yau wadda tayi masifar burgeshi,buba ce da zani saidai kuma an danne gefe da gefanta dai dai jikin mai ita,sosai qirar jikinta ta fita,dan siririn mayafin data yane kanta bai rufa asirin gashinta ba da yasha gara yake qyalli,hakanan qamshin jikinta bai bar buso mishi ba tare da iska mai sanyi irin ta la'asar din da akayi dace aka samu raguwar yanayin zafin da ake ciki,fararen qwayar idanunta ta saka tana karanta ticket din,legos?,me zasuje yi a legos din?,kamar ya karanci abinda yake kai kawo a zuciyarta yace
"Gobe zamu wuce,kada ki damu da abinda zamuje yi" ya qarashe maganar yana bin yatsunta da kallo da har yanzu jan lallen dake jikimsu yake ci gaba da burgeshi hakanan
"Toh" ta furta a sanyaye tana ninke ticket din,haka kawao jikinta yayi sanyi take jin fargaba,hannunshi cikin aljihun wandonshi ya juya ya fara takawa,sai kuma ya tsaya cak yana duban gilmawar masu ya kan fulawar dake gyara a wajen,haka kawai yaji wani abu ya taba ranshi,saiya dawo da baya a sanda take ci gaba da rubutun assigment dinta
"Ko zaki koma ciki?,nan din maga bake kadai bace" kai ta girgiza tana shakkar hada ido dashi,batasan me yasa sau tari idan yana gab da ita take yawan jin hakan ba
"Duka bamu takura ba babu komai" bai sake tanka mata ba ya duqa ya soma tattare takardun,saita soma binsa da kallo,baiko dubeta ba har ya gama,hannunshi ya sanya ya zare biron dake tsakiyar yatsunta sannan ya juya ya soma tafiya,ta fahimci me yake nufi dole ta sauko daga saman lilon ta zira takalmanta ta biyo bayanshi.
A fakaice take qarewa tafiyarshi kallo,idan baka sanshi ba sai kayi tsammanin yana sane yake irin tafiyar,kamar saraki ko mai jinin sarauta a jikinsa haka yake takawa cike da nutsuwa
"Kinsan idan namiji ya amsa,sunanshi yanayin tafiyarsa ma kawai abun kallo ce" ta tuna kalaman hanan data sakata a agaba tana koya mata yadda zata gane ta fada soyayya da wani,da kuma siffofin qasaitaccen namiji wanda ba lallai sai mai kyau ne yake da su ba,duka shirme take daukan abun,sai gashi a yanzu batasan dalilin da yasa daya bayan daya komai yake dawo mata ba aduk sanda khalipha yayi wani motsi.
40
Tunda suka doshi sashen anni suke jiyo muryar rahama,hira suke da mus'ab amma kamar musu musu haka,anni na gefe bata sa musu baki ba tana sabgar gabanta,suna shiga ta bisu da idanu,idonta kan litattafan dake rungume hannun khalipha,duk wata walwalarta ta bace tsaf kunnuwanta da idanunta dukka suna kansu,idanu suka hada da aysha ta daga mata gira bayan ta sakar mata murmushi,ta mata sign na toya kika gani? Da idanunta,saita dauke idonta ta basar tamkar bata gani ba,saidai har yanzu kunnuwanta na wajen
"Gobe zamubi jirgin qarfe biyu anni in sha Allahu"
"To Allah ya bada sa'a,Allah ya nuna mana goben"
"Amin" ya fada cikin hikima yana karantar yadda hankalin rahama ya raja'a a kansu,littafi daya ya zaro cikin wadanda suke hannunshi ya dan buga ma ayshan kadan
"Wuce muje ki qarasa aikinki" kunya ce ta kamata,amma ya riga yayi warning dinta tun jiya,idan ma bata bishin ba zaiyi abinda yafi haka ne gaban annin kamar yadda yace mata,dole ta miqe,ya tasata a gaba suka fice.
Zube litattafan yayi saman kujera sannan ya harde hannunsa a qirji,ya zuba mata ido kaman yadda ya saba,baisan me yasa idanuwanshi suke qawatuwa da kallonta ba,amma har yanzun yaqi yarda da hakan dari bisa dari
"Ki sauya wasu kayan kafin mu sake fita" ya fadi yana sauke hannayenshi,kayan jikinta ta kalla,duka duka nata wuce awa daya da sanyasu ba,saboda ta riga data dauki corse wajen maman hunaifa,ba zaka taba rasata cikin tsafta da qamshi ba ko daga bacci ta tashi bare da ranar Allah,ya fahimci me take nufi tsaf,sai ya soma takowa zuwa gabanta wanda bata ankara da shi ba sai daya zo gab da ita,cikin hanzari tayi niyyar ja baya saiyayi caraf ya riqo hannunta,idanunshi cikin nata yace
"Kwalliyarki tayi kyau,qamshinki yana tashi zuwa ko ina,kawai inason ta darsa a ranta cewa akwai dalili na sauyin kayan da kikayi daga shigowarmu na awanni biyu kacal" wayyo,ji tayi kamar qasa ta tsage ta shige,gashi yaci gaba da kallonta ne bayan ya gama maganarshi ba tare daya sakar mata hannu ba,fatanta daya ya sakar mata hannun saidai yaqi
"Ko baki ji ba?" Ya fada yana murza yatsunta wanda hakan ya haifar mata da wani yanayi cikin jikinta da nashi gaba daya,gaba daya jikinsa ya amsa shi yasa ta samu damar zare hannunta saboda kasalar data saukar masa
"Naji....toh" ta fada da sauri tana zamewa ta nemi wajen zama,sai ya juya kawai shima ya wuce cikin bedroom.
Yatsun nata take lanqwasa idanuwanta na a rufe,tana son tantance wane baqon yanayi ne haka take ji cikin jikinta sa zuciyarta,idanu da fuskar khalipha na mata yawo cikin tunaninta,yaba kwalliyarta zuwa qamshinta da yayi sai take jin kanta na kumbura,baqin kalamaine a duniyarta,sai take jin kamar hira ce irin ta tsakanin masoyi da masoyi,murmushi ya qwace mata tana hasaso gata ita da khaliphan kamar yadda take ganin hanan da saddiq,kamar wadda aka tashi a barci ta gargadi kanta,saidai ire iren wannan tunanin ya kasa barin kwanyarta,a haka ya cinye duk awoyinta har ta soma jiyo kiran sallar magariba sannan ta miqe ta zauna sosai tana tattara nutsuwarta waje daya.
Sanda ya fita sallah ita kuma ta shiga ta shirya hadi da dauro alwala,taga shigar da hayi na qananun kayan marron and black,tana sane ta gidda wata gown maras nauyi saidai tana da duhun kala wadda take guda biyu ta ciki marron mai dogon hannu tana hade sarqar wuya saita sama baqa armless,tayi rolling da maroon vail,kwalliya kadan tayi ta gogawa tausasan lips dinta lipstick marron,hakan sai ya sake fidda kyanta ya kuma fitar da shape din qaramin bakinta,dan siririn abun hannu mai guda daya da zobe ta sanya a hannunta sannan ta yiwa kanta ruwan turaruka masu sanyin qamshi,ba qaramin kyau shigar tayi mata,kafin ta gama sallar magariba taji shigowarsa,bata fita ba saboda tasan sai sunyi isha'i zasu shiga,ana idar da sallar isha'i kuwa ta fito daga dakin.
Yana tsaye gaban t.v batasan me yake dubawa ba,yadan bawa qofar fitowa daga dakin baya,takun takalminta duk da plate ne ya sanyashi juyowa,baisan ya akayi ya tsinci kanshi da kallonta ba,wannan karon muraran ko alamun kunya bare ya waske babu
"Hi....na shirya",aje remote din hannunshi yayi ya nuna mata hanya da hannunshi alamun tayi gaba,ko sau daya bai dauke idonshi daga kanta ba sanda take takawa,kamar wadda ake busawa sarewa haka take takawa,gab da zasu shiga sashen taji an riqo hannunta ta baya ya janyota baya,saura kadan ta fada qirjinsa,ta daga kai tana dubanshi,qwayar idanunsu suka hadu da juna,saiya saukar da idanunshi zuwa kan dan qaramin bakinta daya qawatu da jambaki ya qara masa taushi,yatsanshi ya saka ya lakaci jambakin yana ci gaba da duban fuskarta
"Kinsan yadda jambaki ke miki kyau kuwa?,Allah yasa bakya sakawa a makaranta"abinda yakeosn fadi mata kenam don iya gaskiyarsa kenan,saidai kuma baiso ta fassara maganar da wata siga ta daban,a daidai lokacin rahama dake zaune ta cikin falon tana hangosu,ranta yayi qololuwar baci,tana ji a yau saita nunawa aysha iyakarta,sai ta miqe tsam kawai ta isa saman teburin,wanda tun dazu mus'ab ke mata magana tazo bata taso ba,don yau anni ba zata samu saukowa ba saboda ciwon da qafarta ke dan mata.
Dauke kanta aysha tayi tana jin wani nauyi na ratsata,shima saiya basar yaci gaba da riqon hannunta har zuwa cikin falon.
"Ina anni?" Khalipha ya soma tambaya sanda suke tsaye shida ayshan bayan sun gama gaidashi
"Tana sama qafartace tadan matsa mata"
"Ohk bari mu ganta" ya fada yana danyin gaba aysha zata bishi mus'ab din ya sake cewa
"Ammm....yaya,tace idan kunzo ku fara cin abinci tukunna" yasan ta fadi haka ne saboda tasan halin kowanne cikinsu
"Anty ko wata fita ta musamman zakuyi da yaya?" Haidar ya fada yana murmushi yana duban aysha,itama sai tayi murmushin tana cewa
"Me ka gani?"
"Wannan kyau haka?"khalipha dake zuba ruwa a cup yana daga tsaye ba tare daya zauna ba ya daga kai ya dubi haidar din,haka kawai yaji wani iri,itakam ayshan bata lura da haka ba tayi murmushi
"Bana son zolaya haidar"
"Allah ko,ga guri ki zauna dama inason muyi wata magana dake" ya fada yana nuna mata kujerar dake daura dashi,duk da cewa akwao empty chair guda daya a tsakaninsu
"Zauna nan" khalipha ya fada a kausashe yana ja mata kujerar da yake tsaye a bayanta,yanajin wani irin ba dadi cikin ranshi wanda baisan dalili ba,bai ankara ba sai da yaga suna kallonshi shida rahama,don mus'ab ya duqufa danna waya wanda bai wuce charting yake ba,yayin da amal ta maida hankali wajen zuba lemo tana sha wanda idan ka qare mata kallo hankalinta ba wajen yake ba itama,sai data zauna shima yaja ta kusa da ita ya zauna
"Amal,zuba min abincin" ya fada a dake,dubanta takai ga amal din,sai taga fuskarta ta washe ba kamar dazu ba,ta aje cup din hannunta ta miqe tsaye tana dauko platw wamda yake daga gaban ayshan,haka kawai taji haushi ya kamata,me kenan me yake nufi,raini yakeso yaja mata ko kuwa,dafe hannun amal tayi suka hada idanu,saita sakar mata murmushi
"Yi zamanki,shi ala dole yau bazanyi komai ba,bayan ya sani idan ina kusa dashi lokacina duka nashi ne" ba amal kawai amsar ta taba ba,hatta da rahama dake gefe taba karantar kowa d'ai d'ai dashi kanshi uban gayyar daya tsokani abun,wanda shi kansa baisan me yasa yayi hakan ba,yasan dai baiji dadin yabawar da haidar ya yima adonta ba
"Love is...."sauri mus'ab yayi,yayi yayi gum da bakinsa daga sunutar bakin dayaso yi,saiya soma zungurar haidar yana masa gulma,
"uhmmm...kya fadi gaskiya idan ma kishi kika ji,tunda dai shi ita yace ta zuba mishin ko?" Rahama ta fadi tana qarashewa da dariya duk da cewa dariyar bawai har cikin ranta ita kenan ba da biyu ta fadi hakan
"Babu damuwa idan ma kishin ne,ai na isa ne" itama ta maida.mata rai kwance kai kace wasa take mata,sai taja plate dinta rahaman ta soma juya abincin tana cewa
"Namiji dai mijin mace hudu ne"
"Is enought....kici abincinki kawai" yace da rahama,sai ya dubi aysha
"bani abinci naci" ya fada yana zubawa aysha ido,shi kadai ya gano bacin rai kwance a fuskarta a bayan murmushin dake kan fuskarta,fushin na meye?,abinda bai taba gani tattare da ita ba?,miqewa rahama tayi tabar abincin nata ta sauka daga wajen ta fuce daga falon ma baki daya,tsit wajen yayi,cikin nutsuwa ta zuba mishi komai ta tura gabanshi sannan ta samu waje ta zauna bayan ta zuba kunun gyada cikin cup wanda anni aka yiwa shi tasha ta rage mata saboda kusan ita da annin sunfison cima daya,haidar da mus'ab ne suka miqe a tare suka bar gun cin abincin suma
"Wannan sanya idon na rahama ya soma yawa,ya kamata yah khalipha ya dauki.mataki fa" haidar ya fada cikin jin haushi
"Idont know why suka addabi mutane ma,kowacce ya zauna gidansu ta kasa" mus'ab ya amsa yana jan tsaki.
daga idonta tayi ta dubi amal,sai taga tana satar kallonsu,yau duka sai tayi maganin masu shegen sa ido,sai ta dire cup din hannunta ta janyo plate din dake gaban khaliphan ta amshe cokalin hannunshi ta debo lomar abincin
"Uhummm" ta fada tana gyada kanta,cikin mamaki yake kallonta saita bude mata dukkan idanunta wanda hakan yasa suka sake girma suka fito sosai
"Karbi mana,kacemin dazun kana jin yunwa" ta fada a shagwabe wanda hakan ya taba zuciyarshi sosai,murmushi ya sakar mata idanunshi cikin nata,tana jin nauyinsu sosai a kanta amma ta dake
"Dont bother pls,zanci da kaina,banaso ki wahala" ya furta cikin wani irin salo da ya kusa tarwatsa zuciyar amal wanda ya tilastata barin wajen da hanzari,yayi tasiri mai girma cikin zuciyar aysha daya sanya jikinta yin laushi,sakar masa tayi ganin amal tabar wajen,cikin sauri ya kamo hannunta ya riqe gam cikin nashi
"Baki isa ba saikin qarasa abinda kikayi niyya,kinsan akwai 'yan sa ido dake shige da fice ko?" Haka dole ya hanata tashi daga wajen duk da taqi yarda ta bashin,saiya ci gaba daci da kanshi jifa jifa idanunshi a kanta,yana mamakin me yakeson sauyashi daga ainihin halayyarsa haka.
Ita ta soma gaba taje ta gaida anni,bata tsaya jiranshi ba ta wuce,hakanan yau takejin haushin amal da rahama gaba daya wanda batabtaba jin hakan ba kamar yau.
Tunda wuri tayi shirin kwanciya saboda tafiyar da yace mata zasuyi gobe wanda batasan ta mece ba,ko cikin gida bata qara shiga ba,kuma dama bata da sha'awar shiga din,don ta tsani kallon qwaqwqwafi da rahaman ke mata,ta dinga binsu da kallo ita da khaliphan kaman wanda ke zaman dadiro,tsako taja saboda tuna hakan da tayi,ya kamata ta yiwa tufkar hanci,koma meye fa khalipha ya biya sadakinta no need a samu wasu mutane da zasu dinga sanya musu idanu,tayi kyau cikin red night gown ta lullube kanta da farin mayafi,saika rantse ba shigar bacci tayi ba sabida yadda kayan sukayi mata kyau,qaramar jakarta ta bude ta zuba kayanta kala biyu da duk wani abu da zata buqata,duk da batasan adadin kwanaki ko kwana nawa zasuyi ba,ta hada komai tsaf,saita ciri tashi jakar mai kyau ta buda kayanshi shima ta zabi kala biyu ta shirya masa komai da komai a ciki,sai data kammala duk wata sabga tata sannan ta dauki system dinta da haidar ya siya musu su biyu shi da ita kala daya ta fito parlour,tana son kallon wani film da ta taba ganin tallanshi ta baiwa haidar ya mata downlod dinsa.
Saman doguwar kujera ta miqe abinta ta dora system din saman cinyarta ta