Showing 15001 words to 18000 words out of 184891 words
Chapter 6 - DAURIN BOYE Complete Document by Safiya Abdullahi Huguma.txt
dakin suka afka jikinta suna rigima kan wani abun wasa,sai sannan ta dagonta rungume wanda ya fado jikintan tana duban babban dake tsaye
"A'ah,a'ah abba yaya?,bana hanaku irin wannan guje gujen bane wai?"
"Ummi....."
"Kul na sake jin wannan sunan a bakinka"
"Mami nawa ne fa,ya bar nashina gida tun shekaran jiya da zamu taho na sakoshi cikin trolly na,shine yanzu ya dauke yace wai nashi ne"
"Shine zaka biyoshi haka?,bana son sakarcin banza...oya maza wuce daki kaje ka canza wadan nan kayan daka bata" ta fada tana ware masa idanu,haka nan ya juya ya fita yana cuno baki,shi kuma wanda ke jikintan yana ta dariya abinsa alamun ya samu nasara.
Idanunta ta maida kan basma daketa kallon aysha dake takure gefe guda kanta a qasa tana son yi mata magana amma tana shakkar ummin tasu,tsawa ta katsa mata
"Fice a gun,kar na sake ganin qafarki tsaye a wajen nan"
"Amma mami......"
"Ubanki nace....kama hannun yusra ku wuce daki ki gyara sauran kayanku da baki gama hadawa ba" kamar zata fashe da kuka haka basma matashiyar dake da shekara goma sha hudu ta kama hannun qanwarta dake da shekaru goma suka fice,sai data ga ficewarsu sannan ta daga yasir dake jikinta ta kama hannunshi suna niyyar ficewa a dakin,sai a sannan aysha ta daga kanta tana duban mahaifiyar tata da idanunta dake cike fal da qwalla,cikin rawar murya tace
"Ummi....ki yafemin don Allah duk abinda nayi miki...wanda na sani da wanda ban san......"
"Idan kika qara yimin magana Allah ya isa ban yafe ba" ta fada cikin tsawa sannan taja hannun yasir,cike da tsantsar tashin hankali ta bita da kallo qwalla na silalo mata suka ratse inna yelwa dake tsaye da kwano a hannunta
"Kuma ga naman naki binta"cewar innar
"samin a daki na" ta fada tana yin gaba,haka nan ta juya kuwa tabi bayanta.
Sanda ta dawo har aysha ta gama cin kukanta ta gode Allah,sai tuquqi da zuciyarta ke mata kadai,muryarta a shaqe suka gaisa da inna yelwa,ta kuma tambayeta jikin kawu ta sanar mata da sauqi,ko kadan bata tada zance abinda ya wakana tsakaninta da umminta ba,wannan ba shibe karo na farko ba da irin hakan ta taba faruwa ba,shi yasa sam aysha batayi mamaki ba,inna kulu na haka ne saboda ba ita ta haifi umminta ba?,koko tana haka ne saboda alkhairin da take samu daga wajen ummin nata kada ta yiwa kanta sanadi,saboda ta sani tsaf zata yanke duk wani alkhairi da take mata matuqar zaka shiga maganar data hada da ayshan,biyayya kusan duk wanda yaga yadda take mata za'a ce takewa binta,wanda hakan kusan kowa ke ganin bai rasa alaqa da abun duniya da take samu daga wajenta,zuciya da jikinta duka babu dadi hakan ya sanya bata iya tsaiwa taga dawowar kawu ba bare ta dubashi tayi sallama da inna yelwa da zummar ta dawo gobe.
Tana tafe tana share hawaye,sam bata ka biyo ta hanyar da jama'a suke wucewa sosai ba don bata da buqatar tsayawa tayi magana da kowa,kasancewar tunaninta bai tare da ita hakan shi ya bashi nasarar shan gabanta ba tare data lura ba,sai jan baya da tayi da sauri sabida ganin inuwar mutum a gabanta ta hasken farin wata,a nutse ta qare masa kallo haqoranshi a waje kamar yadda ta sansu yana washe mata baki shi a dole fara'a
"Indo matata.....yau a gari?" Kalma mafi muni data tsana taji ta kenan daga bakin dan ladin tun a shekarun baya zuwa yau,bata taba ganin dan akuya mara kunya irinsa ba,tun a baya neman tsari take da shi balle a yanzu da ta soma samun sa'ida da sauqin wahalar rayuwa,ta kuma san inda duniya ta dosa,bata iya amsa masa ba illa ce masa da tayi
"Dan matsa min malam na wuce sauri nake"
"Haba indo,yanzu fusabilillahi ke ba zaki haqura ki karbeni a matsayin miji ba kije ku zauna tare da 'yar uwarki,naga dai 'yar uwarki ce,abu shekara da shekaru amma kin kasa haqura,duk abinda na dinga yi miki sharrin shaidan ne da zuciya" bacin ransa da wanda ta qunso ya taso ya tokareta,cikin zafin nama da zafin zuciya ta kewayeshi fuu tayi gaba,binta yaci gaba da yi yana magiya saidai banza ma ta fishi a wajenta,don sam bata masa kallon mai hankali,ta sani cewa tsantsar kidahumanci da jahilci kadai sun isa su maidashi mahaukaci tuburan,bare ga shegiyar mai saurin tarwatsa rayuwar koma waye wato qwaya da yake afawa lokaci lokaci,bata taba zaton inda yana da cikakken hankali zai iya tararta ya dubi qwayar idonta ya mata magana ba,bai qyaleta ba sai da yaga shigarta cikin gida sannan ya haqura ya juya yana jin takaicin rasa indon da yayi,tana qiyasta yadda tayi kyau ta goge da tuni yana can yana mora,yanzu gashi yana can yana fama da ladidi.
*_WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA KI TUNTUBI WANNAN NUMBER ( 08030811300)_*
*DAURIN BOYE*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
0⃣8⃣
Kebantaccen waje ne da yake ganawa da muhimman mutanensa,wanda a siffa yafi kama da lambu.
Waje ne mai kyau daya qawatu da shuke shuke da kujeru irin na kaba,daga gefe guda wani magangarar ruwa akayi mai kama da qorama,zakayi zaton ba cikin companyn yake ba saboda yadda aka tsarashi,kallo daya zaka ma wajen ka fuskanci dan qaramin taro aka gama yi a wajen,saboda yadda grass carfet din wajen ya baci da robobin kayan ci da na sha,khalipha na tsaye cikin mutanen wanda baqi ne daga qasar waje wanda zasuyi hadin gwiwa wajen bude wani kamfani,da sauri daya daga cikin yaranshi wanda ke riqe da wayoyinshi ya matso inda yake tsaye,ya tsaya daga bayanshi kadan cikin girmamawa
"Sir,ana kiranka" hannunshi kawai ya miqa ya amshi wayar yana ci gaba da magana da mr james,vivo dinsa ce yasan mai kiran koda bai duba ba,amma duk da haka saiya duba screen din,khadija ce kamar yadda ya zata,bai samu damar daga wayar ba har sai da suka kammala maganarsu da su mr james sukayi sallama da su suka shiga motocinsu suka fice daga companyn baki daya.
Da sauri daya daga cikin yaran ya sake matsowa da niyyar amsar wayar ya adana ta,daga masa hannu khalipha yayi sanda ya danna kiran khadija sannan yaja baya jikin wasu flowers da aka yiwa ado mai kyau
"Muhammad...ni kake qin dagawa waya?" Abinda ta soma fada kenan,kadan ya cije lips dinsa kana yace
"Afwa....ina wani uzuri ne....mun tashi lafiya?"sai data ja iska kafin ta amsa masa
"Lafiya lau.....ya ake ciki ne wai?,gaskiya jiran fa yayi yawa...har yau kana nufin kudin basu samu ba?" Danne bacin ranshi yayi cikin dakiya yace yana kada kai tare da tabbatarwa kansa itama khadijan ta fadi,bata kai labari ba,bata kuma cinye jarabawar ba
"Su naketa qoqarin hadawa basu samu ba....dubu goma ce kawai ta samu" can qasa yaji ta ja tsaki tana qunquni sannan tace
"Ka kawon dubu goman na toshe wata kafar,da babu gwara babu dadi"
"To shikenan"
"Kar ka wuce qarfe hudu saboda inason in fita"
"To babu damuwa" qit ta kashe wayar,ya cirata daga kunne yana kallonta gami da kada kai,har yau dai jiya iyau,dukkansu kaman tare aka haifesu tsabar kamanceceniyar hali,ya talaka yake wanda baida komai kafin ya samu macen aure a wannan zamanin?,ya talaka mara abun hannunsa yake kafin ya samu soyayyar gaskiya?,da wannan maganar zucin ya miqawa jibril wayar,ya amsa yana miqo masa daya daga cikin kebantattun wayoyin nashi wanda kira yake ta shigowa tun dazun,bai bashi bane ganin wata wayar yake amsawa,karba yayi ya kara a kunnesa kana ya soma takawa yana barin wajen,yana fita ma'aikata suka shigo suka soma kintsa wajen da kawar da duk wata dauda ko shara komai qanqantarta.
♦♦♦♦♦
Kusan jiran da ya saba yi mata na yau ya wuce na ko yaushe,bai damu sosai ba saboda maganar da yake cikin waya tun dazun ta dauke masa hankali,ya jima tsaye qofar gidan sanye da wani yadi mai sauqin kudi wanda aka yiwa dinkin riga iya gwiwarsa da gajeran hannu,irin yadikan nan ne da ake saidawa kan farashi mai sauqi,duk da haka yadin ya masa kyau saboda baiwar qira da Allah yayi masa,daga takalmin qafarsa har zuwa hularsa masu qaramin kudi ne duka baqaqe,mota uku ce ta masa rakiya saidai yau sun shigo har cikin layin,amma suna tsaye bayanshi qofar wani gida wanda a qalla daga gidan zuwa gidansu khadijan gidaje hudu ne a tsakanisu,waya ya daga ya kirata
"Gani nan" ta fada sannan ta kashe tana jan tsaki
"Kaman wani kudin arziqi ya kawo min,sai kyau iya kyau amma babu abokan tafiya,wannan da kyan da yake da shi da shine kudin shi kuma mummuna da da sauqi,kyau ba kudi ai wahala ce tunda ba dashi zaku rayu ba,ba kuma kyan zaka loqa a goshi kayi yawo da shi ba" ta fadi ita kadai tana mita sanda take gyara yafen mayafinta.
Babu wata cikakkar fara'a a fuskarta haka ta iso
"Mun yini lafiya"
"Lafiya lau ya mutanen gidan"
"Suna lafiya....." Ta amsa ciki ciki
"Ina saqon?" Ta buqata kai tsaye saboda tana tantamar idan ka ya kawo din
"Gasu nan" ya fada hannayensa na harde a qirjinsa ba tare da ya motsa ba yana karantar yanayinta lamarin na sake bashi tsoro da mamaki,sai ya cire hannunsa daya ya saka cikin aljihun wandonshi,ganin haka ya sanyata tadan saki ranta sannan tace
"Ok....mu shiga daga ciki mana" ta fada tana duban qofar gidan sannan ta maido idanunta kanshi,kafadunsa ya daga duka biyun yana ci gaba da qoqarin zaro kudin,ba tare daya dubeta ba yace
"Ba sai na shiga ba,abinda kika fi buqata na kawo miki kawai muyi sallama na wuce" bata fahimci komai ba haka bata ce komai ba,saboda hankalinta dukka yana kan kudin daya ciro a aljihunsa,wanda kai tsaye bata ce ga adadinsu ba,bandir bandir ne sababbi kar a miqe na 'yan dubu dubu guda biyar,sai 'yan dari biyar biyar kuma daban,wadan can ya maida aljihunsa ya irga 'yan dari biyar biyar din dubu goma ya miqa mata yana kallonta
"Lissafa kiga sun kai?" Amshewa tayi,cike da zumudi qasan ranta tare da fatan samun qari ta lissafa cikin qwarewa sannan tace
"Sun cika" sai ya kada kai ya sake ciro wadancan bandiran yana dubanta yace
"Nawa kika ce kina buqata a baya?" Farrrr tayi da ido dadi na ratsata,addu'arta ta karbu cikin zumudin daya kasa boyuwa tace
"40k kawai nake buqata,ina zaton zata isheni komai da komai" sai ya miqa mata dukkan kudaden hannun nasa yace
"Zaki iya gane nawa ne nan ko?" Cikin zumudi bakinta a washe tace
"Yes,duk bandir daya dubu dari ce,duka wannan five hundred thousand kenan"kai ya gyada hannayensa soke cikin aljihunsa,ya dan shaqi iska sannan yace
"ki riqe duka na baki" idanunta ta waro baki daya tana jujjiya kudin cikin rudewa tace
"Kai muhammad please da gaske kake?,dama ka samu kudin kake ta min wasa da hankali haka,oh my god sweetheart na gode na gode,dama ni na sani ba zaka barni naji kunya ba,dama ashe wasa kake min"
"Eh....gwadaki nake.....kuma kinyi failing....baki ci wannan jarabawar ba khadija,kin fadi warwas har abada" sai kuma ta dan saurara daga murnar da take tana dubansa cikin mamakin kalamanshi
"Kamar yaya wacce iriyar jarabawa?"murmushi ya fidda mai kyau wanda ya sake fitar da kyan surarshi,sai taga yau taga yafi kullum yi mata kyau,ya zaro wayarsa yana dannawa wadda khadijan ta bita da kallo,idan bata manta ba wancan satin ta taba tambayar kudin wayar taji tafi qarfin kanta,don har saurayinta ta tamnaya ya siya mata ita a sannan yace bata da hankali,ashe ba qananun kudi ta baro masa ba, cikin burgewa take bin wayar da ido,idanunsa na kan screen din wayar yace
"Kudi kike so khadija bani ba,kudi sunfi miki soyayyata,sune gaba da komao a wajenki....gasu nan na baki su a madadina...as from today ki saka a ranki baki taba sanin wani mai suna muhammad ba a rayuwarki ko mai kama da shi,kisawa ranki kamar a mafarki alaqarmu ta taba wanzuwa....." Ya qarashe maganar yana kashe wayar tare da maidata aljihunsa fuskarsa qunshe da murmushi wanda take cakude da mamaki,haushi al'ajabi da takaicin halayyar 'yammatan yau,yayin data saki baki kawai tana binsa da kallo saboda lissafinta dake neman dagulewa lokaci guda.
Kunya da tsoron rasashi a sanda ta fahimci wayeshi suka dabaibayeta,tsoron subucewarsa daga hannunta a sanda ta gane cewa type dinta ne shi suka cikata,cikin qoqarin kare kai ta bude baki da niyyar bawa kanta kariya,saidai isowar motocinsa wajen yasa ta kasa furta komai,a gabanta ilyas daya daga cikin yaranshi ya bude masa bayan motar ya shige ba tare da ya sake koda waiwayarta ba,tana kallo suka janye motocin suka fice daga layin suka barta tsaye riqe da rafas din kudi.
Har suka bace daga layin tana tsaye tana bin kyawawan baqaqen motocin da kallo mamaki ya daskarar da ita,da gaske wannan shine ainihin muhammad ba wanda ta sani ba?,shin mafarki take ko gixo idanunta ke mata,saita maida idanunta kan kudin tana jujjuyasu tare da qare musu kallo,qwaqwalwarta a daure take tamau,ta rasa me zata aiwatar,takai hancinta ta shanshanasu,wani irin lallausan qamshi suke fitarwa irin mai kwantar da zuciya,take nadama da dana sani suka lullubeta,ya akayi ta kasa boye zalamarta?,ya akayi ta kasa gane cewa muhammad ba qaramin mutum bane?,iya motoci kawai data gani na biye da shi da kyautar daya mata a yanzu sun isa bata amsar cewa shi din wani ne,shi din isashshe ne,sam bata jin zata iya haqura da shi,asarace da ba zata iya jurewa ba,samun irinsu muhammad a wannan zamanin tamkar gudun yada qanin wani ne ga 'ya mace,mai rabo ke samu,zata san yadda zata lallabashi ta dawo da shi cikin rayuwarta,tabbas sai ya zama mallakinta cikon burin rayuwarta kenan,jiki a salube ta juya ta shige gidan tana gyara riqon kudin a hannunta zuciyarta cike da zulumi da fargabar kada ta rasa muhammad daga rayuwarta.
*_WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA KI TUNTUBI WANNAN NUMBER (08030811300)_*
*DAURIN BOYE*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
09
A gaggauce ta tsame hannunta daga cikin flour din da take kwabawa ta dauraye hannunta ta goge jikin towel sannan ta fita a kitchen din don amsa kiran da mommy sa'adah keta qwala mataba tare da tayi la'akari da aikin data sanyata take yi ba
Cikin bedroom dinta ta taddata,tana zaune gefan gado,daga daura da ita kayan turarukan wuta ne lodi guda da alama lissafinsu takeyi,yar lelen nata kuma na gaban madubi tana ta shafe shafe da qalqale qalqale,saboda yau fita ce ta musamman zatayi,dinner ake na wata cikin qawayenta na makaranta da take aure,qawaye ne irinta 'yan ji da kai da daukar duniya da fadi,su kansu kayan da zata sanya a ranar order dinsu aka yi mata bayan an musu dinki na musamman,ba'a maganar jaka da takalmin da zata sanyawa qafafunta na kudade masu yawa.
"Mommy gani" aysha ta furta tana rusunawa gefan mommyn,wayarta ta aje sannan ta dubeta
"Saura me da me ki kammala ne?,qarfe shida na yamma fa zasu soma taron,kuma nasan tana can tana jira"
"Mommy na gama komai da komai,doghnout din ne naga kamar bazai isa ba shine zan dan qara yawanshi"
"Zaikai kamar nan da minti nawa?" Ta tambayeta bayan ta kalli agogo
"Awa daya ko minti hamsin"
"To kiyi sauri ki gama din,saboda ke zan aika ki kai matan"
"To mommy" ta fadi tana miqewa tare da qoqarin ficewa daga dakin
"Idan kin gama ki debi komai kimin packaging,ki hada masa dambun kazar nan da kika ma daddy last week,yau nake xaton hamid zai dawo gobe zai shigo waje na" cewar asma'u dake goga jambaki kan lebanta,wanda ta bada umarni ne kawai ba tare data waiwayo ta dubi wadda ta bawa umarnin ba
"Toh" shine abinda aysha ta fada tana ficewa daga dakin cikin ranta tana fadin autan maza,hamid shine saurayin asma'u data zaba cikin dubban samarin da Allah ya bata a matsayinta na budurwa 'yar qwalisa wadda har ranta takejin duniya na damawa da ita,me ji da kyau aji ado da gata takowanne fanni,hamid ya yiwa asma´u dari bisa dari,tana jin ya dace da tsarinta ya kuma yi dai dai da ra´ayinta,hamid matashin saurayin dan kasuwa ne maiji da gata da kuma dukiya,mutum ne shi mai shegen son girma,son matsayi da qyamatar mu'amala da duk wani wanda baikaishi arziqi ba,tafiyarsu tazo dai dai da asma'u saboda katarin hali da akayi yazo guda,soyayya ake bugawa sosai,wani irin so asma'u take masa wanda yake baiwa kowa mamaki,irinson da ba'a taba ganinta ta yiwa wani d'a namiji shi ba,saboda ta jima tana jan maza a qasa,tana daga musu kai da hura musu hanci saboda baiwar kyau da Allah ya bata da iya kwalliya,uwa uba gata data samu daga wajen uwa da uba kasancewarta auta a gidansu,saidai tashin farko ta matowa hamid,ya rushe duk wani plan nata ya tafi da zuciyarta,a yanzu haka babu wanda baisan da zaman soyayyarsu ba,haka nan ta tsaidashi a matsayin wanda zata aura,saidai iyaye duka basu shiga ciki ba,saboda tana da plan din sai ta gama degree dinta sannan a soma maganar aurensu,shi dinma hakan ya masa shi yasa komai ke tafiyar musu dai dai,suke kuma gudanar da soyayyarsu hankali kwance.
Sam jinin aysha da hamid zan iya cewa bai hadu bane ko kuma banbancin halayya ya sanya hakan,tsakaninta da shi gaisuwa,sai ko idan yazo ta miqa masa kayan maqulashen da asma'u ke sawa ta hada masa ta kama gabanta,yana da ji da kai girman kai da kuma daga kai da jin shi wani ne,wannan halayyarsa ce a jininsa.
Cikin awa gudan ta kammala komai ciki harda wanka,ta shirya tsaf cikin lace bayan ta nannade jikinta da laffaya wadda ta dace da shigarta,ita ba ma'abociyar son kwalliya bace,hakan ya sanya kaso hamsin na kyawunta ke boyewa idan ba ka mata kyakkyawan kallo ko kyakkyawan sani ba,ita dai barta da qamshi,tana son qamshi,kuma dukkan turaren da take amfani da shi ba mai hayaniya bane,saika matsa kusa da ita zaka dinga jin tashinsa,kuma a hankali,yawanci tafi ta'ammali da turaren kaya haka sai rollon body spray masu kyau da dadi tamkar wata babarbariya.
A parlour ta tadda