Showing 12001 words to 15000 words out of 184891 words
Chapter 5 - DAURIN BOYE Complete Document by Safiya Abdullahi Huguma.txt
da shi kasancewar tafiyar da yayi bai samun isashshen baccin da ya kai awa hudu ko biyar
🧶🧶🧶🧶
Tunda suka shigo siririn titin da zai sadaka da ainihin qauyen nasu tunaninta ya rarrabu kashi kashi kaman yadda ta saba kowanne lokaci,ina zata sauka?,a wanne gida zata fara yada zango?,gidansu mahaifinta ko gidansu mahaifiyarta?,ko kuma gidan gwaggwo lami?,ason ranta gidan gwaggwo lami tafi sha'awar ta sauka,saidai hakan ka zama tamkar ta aikata wani laifi ne aduk sanda labarin zuwanta ya iske gidansu mahaifiyarta harma dana mahaifin nata,zasuyita mata fassara daban daban kaman yadda suka saba,duk da cewa ada bawai sun damu da rayuwarta bane,saidai a yanzun suna son nuna sun damu da rayuwar tata ko don dan qaramin alkhairin da take riqowa tazo musu da shi,wanda hakan ya dan sauya yanayin mu'amalarsu da dangantakarsu,sauyin da bai taka kara ya karya ba,sauyin kuma da bashi da wata ma'ana ko alfanu a gareta.
Itadai a baya tasan ba wanda ya damu da rayuwarta,babu wanda ya damu data rayu kota mutu,ba wanda keson ta rabeshi,kowa gani yake rab'uwarta da shi wani kayan nauyi ce,idan kuwa ya zama dole ta rabi mutum din yana ganin ya yiwa rayuwarta gagarumar alfarma ne,koda kuwa babu wani abu da yake iya tsinanawa rayuwartata
Umarni ta baiwa mai motar da ya daukota tun daga tashar takai saboda asma'u ta fice da motar da daddy ke fadin wai ya basu,wai mana tunda bata taba shigarta ba itakam,hakan kuma bai dameta ba,mommy kuma ta kasa bada koda qarama cikin motocinta biyu a kawota kasancewar babu idon daddyn,tun da sassafe ya sallameta sukayi sallama ya fita,tace drivan ya sauketa qofar gidansu mahaifinta,tunda duk tsiya da uba ake ado,yaran da sukayi tsaye gaban motar su suka daukar mata jakarta zuwa cikin gidan,sai data biya direban sannan tabi bayan yaran zuwa cikin gidan,lokaci lokaci gabanta na faduwa tare da tunanin me kuma zata taras wannan karon.
Kamar ko yaushe,kamar kuma kowanne lokaci irin wannan,dukkan matan sassa sassa dake gidan na gindin qatuwar bishiyar dake tsakar filin gidan,wadda kusan itace ta zama wajen hutawarsu a duk sadda rana ta qwalle a sararin subhana,nan ne dai wajen zaman,masu sana'a nayi,masu gulma da sa'ido ma duka suna yi,masu ayyukan gida ma duk sukan jibge a nan,wasu bisa shimfidar tabarmar kaba,wasu kan kujera 'yar tsuguno,yayin da wasu ke a tsaye suna surfe ko wani aikin ma daban,bishiya ce da Allah ya mata yalwar inuwa da kuma iska,har wani bai takurawa wani,wajen zaman ya ishesu a wadace.
Tunda aka shigo da jakarta yanayin hayaniyar dake wajen ta ragu,kowa ya maida hankalinsa kan ganin shigowarta,mata ne a qalla sun kusa su goma kowacce idanunta a kanta tana qare mata kallo,ta saba da wannan kallon tun a sanda yake muguwar guba ce a rayuwarta,balle yanzu da kaifin wannan gubar ya ragu saidai abinda ba'a rasa ba,fuskarta a washe ta zauna gefan tabarmar da tatuwa take kai ita da faccalarta karime ke kai suna irga soyayyar tunkuza wadda da alama basu jima da kammala aikinta ba,saboda yanayin maiqon dake jikin zannuwansu da rigunansu,kowacce da yanayin data amsa mata,zuciyar kowannensu da abinda take saqawa.
Tsahon mintuna tayi a cikinsu tana tattambayar 'yan uwanta dake gidajen aure da iyayenta maza wasanda dama ta tabbatar suna goba suda yaransu maza wadanda suka tasa sai qananu da aka bari a gida,matan kuwa matasan da basuyi aure ba na wajen talla,kana daga bisani ta tambayi kakarta wadda take mahaifiya ce ga mahaifinta hafsatu wadda suke kira da inna yelwa
"Tana rumfarta tana hutawa" cewar lami wadda ta maida tabaryarta cikin turmi bayan ta watsa dawar da zata surfa,tasan dama a rina,kasancewarta mace mai shegen mulki ga duk wanda ke qasanta da nuna isa,bata cas bata as cikin gidan,yawanci irin wannan lokutan tana rumfarta zaune saidai ta wurgo umarni kuma dole abi,walau 'ya'yan nata ko matansu ko su kansu jikoki.
Ilai kuwa a sanda ta daga labulen dake rumfartata sai ta sameta zaune saman tabarmar karauninta,falon nata a share qal wanda tasan aikin daya daga cikin surukan nata ne,wanda duty duty suke,qafafunta miqe abinda,haule daya daga cikin surukanta tana murza mata goro a magogin qarfe tana watsawa bakinta,bawai don bata da haqora ba a'ah da saura,tsabar mulki ne da ganin dama.
Fuskarta a sake tayi sallama yayin da inna kululu ta dago kai tana dubanta
"Hala kinji zuwan waccar uwar taki shine kika kwaso qafa kika taho,bayan kin san babu abinda zai sauya,zuwanki banza zamanki banza" sosai kalaman suka soki zuciyarta,duk da cewa ta jima tana jin ire iren wadan nan kalaman daga bakin inna kululun,saidai har yau ta kasa sabawa,ta rasa sai yaushe wannan DAURIN BOYEN zai warware?,sai yaushe komai zai gyaru?yaushe zatayi dariyar farinciki da zata ratsa har qasan zuciyarta kamar kowacce 'ya?.
Bata amsa mata ba har ta zauna gefan tabarmar da take kai tana gaida haule,ta amsa tana miqewa tare da gyara daurin zaninta da alama ta gama murza goron,kallonta inna kulu tayi
"Ki kiramin karime"
"Toh" ta amsa tana ficewa,sai data fitan sanann innar ta maida kallonta kan aysha
"Uwarki kika biyo ko?" Ta sake maimaitawa bayan ta amsa gaisuwar da ayshan ta mata,kai ta kada ranta na tabuwa
"Kibar wannan maganar inna yelwa,ni baffa nazo dubawa ance min baida lafiya"
"K'nnnnn,lallai Allah yasa da gaske kike,ya kika baro su sa'adatun,ince dai bakya musu wani mugun halin naki ko?" Ta fada tana tsareta da ido,ya ilahil Aalamina,daga durowarta?,ba'a tambayeta komai daya shafeta sai zancan su mommy?,koda yake hakan ba komai bane,abinda yafi hakan ma zata iya gani
"Suna lafiya lau,tana gaisheki"
"To madalla".
Shiru ne ya biyo baya kaman wadansu baqin juna,ita innar bata ga damar sake magana ba har karime ta shigo ta fita,yayin da ayshan ta rasa abun cewa saboda ba wani sabo bane tun fil'azal tsakaninsu,bugu da qari tunanin daya rinjayi zuciyarta ta gefe guda najin mahaifiyara dake aure a lagos wai tazo,ba zata iya tuna yaushe rabon data sanyata a idanunta ba,idan zata tuna tun sanda zata bar qauyen zuwa gidan daddy rabonta da ita,shekara aqalla kusan takwas kenan,rabuwar da har yau tana tuna yadda suka yita,a duk sanda ta tunada lokacin sai qwalla ta cika mata idanu
Ta tafi tana roqon ta kalleta sau daya,ta tafi tana kukan ta kira koda sunanta sau daya taji da kunnenta,ta tafi tana kwadayin taji tayi mata addu'a ko sau daya ne tak a rayuwarta,saidai dukka wannan burin nata bai cika ba.
Sai qarfe biyu saura ta miqe daga zaman kuramen ta rataye mayafinta ta dauki butar inna kulun ta zagaya don kama ruwa da daura alwalar sallar azahar
🧣🧣 *DAURIN BOYE*🧣🧣
*NA*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
HASKE WRITERS ASSO
(Home of expert and perfect writers)
0⃣7⃣
Bayan ta kammala sallar tana zaune saman abun salla,yaran gidan na shigowa da daya da biyu,wasu tana nan aka haifesu wasu bata nan,wasu ta tafi a sanda suke da qananun shekaru wanda zuwa yanzu sun girma,sa'anninta kuwa suka taso tare wanda taci wuya wajensu yanzu babu kowa cikinsu,kowacce tayi aure tana gidan aurenta da yaranta,duk yaron daya shigo bata rasa dan abinda zata bashi,a haka har uku na rana ta kusa ba wanda yabi ta kanta,sai bayan ukun sannan innan ta tura mata wata langa wadda ke dauke da shinkafar hausa fara qal da man gyada da yaji,ta dan soma curewa waje daya saboda tayi sanyi sanyi,bata damu ba ko dama can ita ba mai damuwa bace taja ta tsakura ba da yawa ba ta rufe kwanon,inda Allah ya taimaketa a halittarta ita din ba ma'abociyar son cin abinci bace,lamarin daya taqaita wahalarta qwarai da gaske a shekarun baya da suka shude.
Mayafinta ta rataya tare da maqala 'yar jakarta bayan tasha ruwa ta wanke hannunta tana duban innar
"Inna zan qarasa gidansu inna kulu" wani kallonta watsa mata sannan tace
"Zaki dai je ganin uwarki ko?,uwar da bata damu da rayuwarki ba" Kanta ta kada can qasar zuciyarta tana jin babu dadi,komai lalacewar uwa uwace,sam bata jin dadin kalaman dake fitowa daga bakin inna kulu ko yaushe akan mamanta,batasan wanne irin rashin jituwa bane haka a tsakaninsu tsahon shekaru tun tasowarta amma har yau bata sauya zani ba
"Bansan ma sunzo ba inna,zanje na duba jikin kawun ne" baki innar ta tabe tana ci gaba da abinda take ba tare data tanka mata ba,har ta gaji da tsaiwa haka nan taja jikinta a hankali ta fice daga dakin ba tare data sake cewa komai ba itama.
Wannan karon tsakar gidan nasu babu jama'a sosai sai yara jefi jefi,kowacce tayi sashinta masu wankan da ba'a yiba tun safe nayi,da masu shara da wanke wanke,ba zasu sake hallaraba wajen ba kuma sai bayan sallar la'asar,hakan shinya bata damar ficewa hankali kwance daga gidan ba tare data sake jin wani abu da bazaiwa kunnuwanta da zuciyarta dadi ba,tun tasowarta haka taga gidan nasu,wannan zaman dai sai an yishi a kulli yaumin.
Da gudu yaron ya biyo tayarsa da yake garawa wadda bata tsaya ko ina ba sai gaban aisha,dafe tayar tayi ta daga kanta tana duban yaron,kallo daya ta masa ta tabbatar jininsu ne,don yana kama da umminta sosai,kana dubanshi kasan daga duk inda ya fito ba waje bane na wahala,sanye yake da wando da t.shirt wadda ta dace da kayan nashi,duk da sun debi qura da jar qasa kadan sanadiyyar wasan da yake faman yi babu ji babu gani amma kana kallonsu kasan masu tsada ne,kallonta yayi sai ya dauke kai yaci gaba da gara tayarsa alamar bai santa ba,ita dinma bata sanshi ba,amma bata tantama shine yaron data ji labarin ummin nata ta haifa bayan shekararta daya da komawa gidan daddy zuwanta na farko ziyara qauyen
"Laaaa,anty indo" taji an ambata qasa qasa,waiwayowa tayi tana duban mai kiran sunan nata,wanda tasan masu kiran nata da wannan sunan wasu kebantattun mutane ne.
Basma ce wadda a qa'idance zata kira da qanwarta,saidai a zahirance kai ba zaka ce qanwar tata bace musamman a shekarun baya da suka shude,gwara a yanzun da yanayin rayuwarta data basman ta saje,mutane da dama wadanda basu sansu ba kan sheqe da dariya idan ta nunata tace qanwarta ce saboda banbancin yanayi na rayuwa da tazara mai tarin yawa a tsakaninsu,saidai a yanzu da rayuwa ta soma zuwa mata da wasu daga cikin sauye sauye zaka gasgata cewa qanwarta ce karon farko saboda yanayi na daidaikun kamanni data dan debo nata.
Fuskar yarinyar qunshe da murmushi kamar yadda fuskar aysha ki cike da fara'a ta qaraso gabanta ta kama hannayenta
"Anty indo dama kina nan?,yaushe rabon dana ganki anty?,tunda kika koma inda kike sai a dade ba'a ganki ba me yasa?"
"Inda na koma din ba cikin garin nan bane basma,kuma makaranta nake zuwa bako yaushe nake da lokacin zuwa ba....yaushe kuka zo?"tayi dukka maganar tata cikin fara'a
"yau kwananmu uku,gobe ko jibi abbu zaizo ya daukemu" cike da zaquwa tace
"Harda ummi?" Kai basma ta kada
"Harda ita,tana cikin gida ma,shigo muje ki ganta"ta fada tana dan jan hannun ayshan, faduwar da gabanta yayi shi ya tilasta mata lumshe idanunta kafin daga bisani ta budesu,Allah ya sani tana sonta,tana son ganinta,tana son ta rabeta,amma bata san me yasa duk bata da wannan damar ba,batasan me ya haifar da wannan babban gibin da baraka dake tsakanin dangantakarta data mahaifiyarta ba da kuma gidansu mahaifinta,a hankali ta bude idanun ta dafe hannun basma dake cikin nata
"kije zan shigo,kinsan me zai biyo baya idan ta ganmuntare aiko?" Fuskarta a bace ranta a hade ta kada kai
"Shikenan,amma don Allah anty karki koma ki shigo din"
"Yanzun nan kuwa kada ki damu,zan leqa gidan mero ne".
A haka suka rabu ta shiga layin gidan meron,tayi hakanne kuwa don tana jiyewa basma hukuncin da zai biyo baya idan ummin ta gansu tare,ba qaramin aiki bane a wajentan ta lakada mata dukan da zata ji a jikinta,tunda tun kafin takai hakan take dakuwa wajenta matuqar zata gansu tare,ko zata ga ta bata wani abu,wani lokaci idan ta tsawaita tunani kan wadan nan cakudaddun al'umaran takanji kanta tamkar zaya tsage,bata da amsa bata kuma da mai bata amsar,sai tarin tsana da tsangwama da take fuskanta aduk sanda tayi yunqurin tambayar wani makusancin lamarin kan meya faru a baya?,meye sanadi?,mai ya haifar da haka,wasu sukanyi gaba su barta a nasu tunanin tasan komai,tsabar rainin wayo ko wahala ce ta soma taba qwaqwalwarta,da wannan tunanin na tsohon shafin rayuwarta ta qarasa gidan qawarta ta quruciya wato mero.
Cikin farinciki suka rungume juna ita da mero,da qyar suka samu wajen zama kowa na zumudin ganin dan uwansa,abota ce da ba zasu taba mantawa da ita ba,abota ce data yiwa aysha rana,abota irin wadda ta kasa samunta daga yan uwanta a wancan lokacin
"Indo....ashe komai na rayuwa mai wucewa ne...kin ganki ko indo kin zama matar birni,don ma har yau babu qibar da kika qara" mero ta fada tana kama habarta,qaramar dariya aysha ta saki tana kada kai
"Mero har yau halayyarki ba zata sauya ba kenan....komai na rayuwa mai wucewa ne mero,amma banda abu guda,wanda bana tsammanin zai wuce" ta qarashe maganar fara'ar fuskarta na raguwa,da alamu maganar da take cikin zuciyarta ta taba ranta sosai,hannu meron ta aza bisa kafadar aysha tana cewa
"Ba abinda ke tabbata a duniya sai ikon Allah indo,kici gaba da sakawa ranki salama,kici gaba da sawa ranki cewa watan watarana zai zama labari tamkar ba'a yiba,umminki mutum ce kaman kowa,zuciyarta na hannun ubangiji,kuma yana da ikon sata ta sauya aduk sanda yaga dama koda bata so yin hakan ba" cike da gamsuwa take gyada kanta gami da sanya yatsunta ta dauke qwallar data sauko mata,zuciyarta na samun nutsuwa da kalaman mero
"Haka ne,na gode qwarai Allah ya qara zumunci"
"Ba wannan tsakaninmu indon baffale,yanzu mutuminki zan dafa miki ko kuwa?,yau ban dora sanwa ba a gidan nan duka yaran suna gidan gwaggwan habu shi yasa ban dafa komai ba" dariya indo ta saki saboda tuno wani abu da tayi
"Hoooo,meron habuwalle,bada kanki a sare...waima yana ina" dariya mero ta saki
"Zaku taba diramar taku ne?,yau tun safe ya tafi hungu ina jin kuma bazai shigoba sai gefin magariba,amma ai tunda kina nan zaku hadu ne" ta fada tana yunqurin tashi
"Kinga yi zamanki karki wahal da kanki,ban jima da cin abinci ba na fito" komawa tayi ta zauna tana dubanta
"Wanne abinci ko muna abinci,sun baki wannan busashshiyar shinkafar tasu da ke kika jima da yin bankwana da cin irinta,ni bansan meke damun jama'ar gidanku ba,ga arziqin abinci gar abinci amma su basu raba kansu da cimar da kowa cikin karkarar nan ke fatan bankwana da ita ba" dariya aysha tayi kawai tana jin mitar mero,itadai indai aka taba indo tofa za'aji kansu da shi koda waye ma,zata iya cewa su biyu ita da aliya bata taba samun soyayya kamar tasu ba,tabbas idan wani ya qika wani zai soka haka rayuwa take.
Ledar data zabo mata atamfofi cikin nata ta miqa mata,ta daga tana ta murna da godiya,duk da cewa bata rasa komai gidan mijinta ba,habu mutum ne mai zuciyar kula da iyali wanda irinsa daidaiku ne cikin karkara a halin yanzu.
Sun dan jima suna hira sannan sukayi sallama da alqawarin gobe idan bata samu taje gidan gwaggwo asabe zata dawo susha hirarsu.
Tamkar mara gaskiya haka ta dinga taka dogon soron gidan kakannin nata,ba komai ya haifar da hakan ba illa tunani da zaton mahaifiyarta a halin yanzu na cikin gidan,tsakar gidan fetal yake babu kowa,bata ji motsi ko hayaniyar kowa ba,hakan shi ya sake bata qwarin gwiwar kutsa kai cikin gidan bakinta dauke da sallama,inna kulu dake qasan rumfar da suke girki ce zaune gaban murhu tana ta aza wuta bisa dukkan alamu wani abu mai buqatar wuta da yawa take dafawa,waiwayowa tayi tana amsa sallamar kafin daga bisani ta dan washe fuskarta tana fadin
"Indo....yaushe kika shigo garin?"
"Wallahi inna dazu dazun nan"
"To maraba,qarasa daki nima gani nan tasowa"
"Toh" ta amsa idanunta na satar kallon kebantaccen dakin da tasan cewa mahaifiyarta na sauka ciki duk sanda tazo garin,dakin a bude yake saidai an dan karashi hakan yasa ba zata iya gane da mutum ko babu ba da haka ta sanya kanta cikin dakin inna kulu dake falle daya dauke malale da leda da labulaye gami da lailayayyen gadon qarfe da doguwar kujera qwaya daya wanda dukkan wannan gyaran aikin ummin nata ne.
Tana shirin zama gefan gadon inna yelwan qamshin turaren ya ziyarci hancinta,qamshi ne data san cewa ba irin wanda inna kulu ke amfani da shi bane,hakan ya sanya ta soma baza idonta cikin dakin,tashin farko jikinta ya soma rawa har ta kasa hayewa saman gadon qarfen mai tudu wanda ya sha katifa,ta zame baki daya zuwa qasan ledar dakin ta zube ragwaf cikin rawar jiki,umminta ce zaune kan kujera qwaya daya dakin,sanye take cikin wani legos lace mai kyau da tsada peach wanda aka yiwa dinkin buba qarama da plain zani,hannunta sanye da awarwaro da zobe,haka wuyanta da kunneta sanye da sarqa da dan kunne,tayi fresh tayi kyau fiye da yadda ta santa ma ashekarun baya,tunda aqalla yanzu ta kusa shekara biyar rabon data sanyata a idanunta,daurin dankwalinta dai dai da zamani,idanunta na kan wayarta qirar samsung torching dake hannunta tana shafawa,cikin rawar murya ta hada lafazin
"Ina wuni ummi...." Shiru taji kamar yadda ta zata,tamkar babu wata halitta a dakin bayan ita,ko motsi ummin bata yi ba bare ta saka ran amsawarta,kai ka rantse da Allah bata san akwai halitta cikin dakin ba
"Ummi bar....ka da yamma....an yini lpy?" Ta sake maimaitawa,saidai kaman waccan karon wannan karon ma ko motsi bata yiba bare ta amsa,abu guda ne ya banbanta yanayin shigowar 'yan matasan yara maza guda biyu a guje daya yana bin daya cikin