Showing 171001 words to 174000 words out of 184891 words
Chapter 58 - DAURIN BOYE Complete Document by Safiya Abdullahi Huguma.txt
soma zamewa,saita dan rintse ido kamar yadda ta saba,yana kallonta saidai wannan karon dariya ta bashi,ya qunshe abarsa yana kada kai ya shige toilet din.
Kaman yadda ya saba aqalla yana daukan minti talatin sannan ya fito,tayi wuf ta shige bandakin ganinsa daure da dan guntun towel yau sabanin da da yakan sanya rigar towel,sanda take qoqarin rufe qofar ya sanya hannu ya tokare qofar ya rufa mata baya
"Ya khalipha....don Allah" saita gaza qarasawa ganin ya cimmata ya kaita bango,ya mata rumfa gaba daya,tsoronshi da kwarjinsa wanda bata taba jiba yau ya kamata,so yake lallai ta kalleshi amma taqiya,nunfashinsu ya dinga cakuduwa da juna,murya can qasa yace daita
"Wannan saurin da kike kika fada toilet duk na meye,to sai kin nunamin abinda kike tsoro" kamar zata sanya masa kuka take masa magiya
"Babu komai don Allah kayi haquri,nidai babu komai" wani murmushi ya saki wanda shi kadai yasan ma'anarshi ya janye baya yana cije lips dinshi,saiya nufi famfo ya sake daura alwala sannan ya juy ya dubeta,har yanzu tana tsaye inda ya ritsata
"Kiy sauri ki fito na baki minti goma,idan ba haka ba,zan shigo na daukoki ko baki gama ba"murmushi tayi a kunyace,juyawa yayi ya fice sannan yaja mata qofar toilet din.
Sanda ta fito tuni yana saman abun sallah,sanye da jallabiyya fara qar har daukan ido take,kansa saye da hula tashi ka fiya naci baqa,dakin ya bule da wani irin sassanyan qamshi,wani kyau taga yayi mata sosai,don karta shagala da kallonsa saita kauda kanta,riga ta gani aje ta bacci da kuma after mai kauri gefanta,girgiza kai tayi sanda taga yadda rigar take,amma data tuna zata dora after din saita dauka ta koma bandaki ta shirya acan,ta mulke jikinta da wani turare daya aje mata wanda qamshinsa da dadinsa ya dinga sanyata kasala.
Binta yayi da kallo sanda ta fito daga bandakin,sai yayi mata nuni da gefansa,matsawa tayi ta saita sahu yadda ya dace ya kabbara sallah cikin mamakin sallar meye itama ta tayar,raka'a biyu sukayi sukayi sallama,yaja doguwar addu'a sosai wanda ke tattare da roqon dukkan alkhairi sannan ya shafa,jiyowa yayi ya zauna yana fuskantarta gami da tanqwashe qafa,janye idanunta tayi daga nashi tana jin zuciyarta na bugawa,wata fargaba na shigarta,sunanta ya kira wanda ya sanya ta daga kai ta dubeshi,a nutse yake mata tambayoyi game da abinda ya shafi addininta,sallah tsarki da wanka,kada kai kawai yake yana gamsuwa da bayaninta,kai karantse wata malama ce,sai data kammala sannan ya dora hannunshi ya karanta addu'ar nan da annabi ya umarcemu ga duk wanda Allah ya horewa yayi wani sabon abu,ko mata ko abun hawa,har ya gama tana saurarenshi,hannunsa ya sanya ya janyo ledar dake gafansa wadda suka siyo kayan ciye ciye a ciki,ya fidda komai ya aje a gabansu,itadai nata ido jiki a salube,donta shinshino wani abu,da kanshi ya dinga ciyar da ita,duk da taso ta turje da farko yayi kicin kicin ya nuna yayi fushi,cikin hikima ya dinga janta da hira wanda ya sanyata ta sake,sai gata tana qyalqyala dariya,bayan sun gama ita ta gyara wajen kafin ta kammala ya haye gado abinshi
"Malama a cire hijabin nan da after din mana haka?,banfa ga kwalliyar ba" sai ta dan diririce kadan saboda tuna yanayin rigar dake qasa,girarshi ya dage mata
"Yes....ko so kike nayi asarar kudina?" Ya fada yana zuba mata idanu,hakanan ta dinga fidda kayan kunya na saukar mata,sai daya ragw saura rigar baccin kawai,zuwa sannan numfashinsa ya soma masa nauyi,tunda Allah ya halicceshi bai taba ganin sura irin haka baka,ashe ayshan ta zarta dukkan yadda yake tunani,hannunshi ya miqa mata yana daga zaune saman gadon,bayanshi jingine da fuskar gadon qafafunshi miqe
"Kai zo nan muga wani abu....ya maqale miki a gashi meye haka kamar qadangare?"gaba daya basirarta ta tafi,dama atsorace take haka kawai,sai ta kwasa tayi wajenshi babu shiri,batasan cewa wayo yayi mata ba sai data ji ta shigo hannu,saqonni yake aika mata masu wuyar bijirewa,masu nauyi a qwaqwalwa,masu rikita lissafi,sai daya warware mata dukkan wani lissafinta sannan ya rada mata
"Zanso darenmu na farko ya zama cikin wannan garin mai albarka kamar yadda na jima ina burin haka a rayuwata a duk sanda Allah ya bani matar aure,saboda kwadayin albarkar dake cikin garin,kin bani damar cika wannan buri nawa uwaisha?" Kai ta gyada mishi tana rufe idanunta,tana son ta yaqi tsoto da fargabar dake taso mata
"Na gode,na gode" ya dinga maimaita mata yana cusa kanshi tsakanin wuyanta da sumar kanta ta sauko tayi musu rumfa duka su biyun.
Cikin wannan sassanyan daren,khalipha da ayshan suka zama abu guda,khaliphan ya samu ayshan fiye da yadda yake tsammani duk da cewa shi din farin shiga ne,ya bita a sannu yanda ya kamata saidai hakan bai hanata jin jiki ba,tunda ita dinma baquwa ce a fannin,saidai yanayin yadda ya riritata ya taqaita mata wahala qwarai da batasan yadda zata kaya mata ba.
Hakan gaba dayansu bai hanasu tashi sallar asuba ba,tare sukayi jam'i,ya waiwayo yana kallonta sanda suka idar cikin tausayawa da wata tarin qauna,saidai taqi yarda su hada idanu,wata kunyarsa mara misali take ji,murmushi ya saka a sirrance don yasan kunyar me take
"Khalipha zan mutu,ashe dama baka sona?" Ya fada a hankali,sarai ta jishi kuma tasan ita yake tsokana,saitayi banza dashi saidai bakinta data dan zumburo
"Ina sonki mana my uwaisha,Allah sai yanzu ma nake sake jin wani sabon shauqi game dake,uwaishaahhh zan iya mutuwa saboda ke..." Salon yadda yayi maganar cike da tsokana da shagwaba ya sanyata sakim dariyar dole,shima tayata yayi kafin daga bisani yayi nasarar sanyata cikin jikinta yana shafar gashin kanta,addu'a ya dinga jero mata godiya da fatan alkhairi tana amsawa can qasa kanta na saman qirjinta,a haka har bacci yayi awon gaba da ita,shimfideta yayi a wajen yana gyara mata kwanciya idanunshi a kanta,ya jima ahaka yana kallonta kafin ya miqe yana shawagi kadan kadan a dakin kamar mai gadinta,zuciyarsa fes qal,wani farinciki na musamman na ratsashi,ashe da can ba rayuwa yake ba gashinan ne dai kawai?,ya godewa Allah da tasahon shekarun ya tsareshi ya kuma kare ayshanshi,duk irin gwagwarmayar rayuwar da suka fuskanta hakan bai sanya sun fada gonar daba tasu ba.
Bai taisheta ba sai dayaga lokacin sallar azahar yayi,tana zaune inda tayi sallar yana aukin kallonta yace
"Ko zaki shirya na kaiki wajen ummi?" Kai ta girgiza alamun a'ah,don tana ganin kamar idan taje ummin zata gane wani abu daya faru.
Da la'asar ta sanke wanka da ruwa mai zafo don taji dadin jikinta,taji din kuwa,har ta dan samu tayi mishi kwalliya,tana daura dankwalin kanta taji hannunshi a wuyanta,sarqar gold din da suka siyo ce wadsa duk ciki tafi kowacce kyau da tsafa,bata ce komai ba itadai tana tsaye tana kallonshi,yasanya mata dan kunnenta sannan ya kama hannunta ya zira mata awarwarayen,baya ya danja yana kallonta
"Kamar yadda na zata kin haskasu sosai" ido ta zare tana daga gira alamun neman qarin bayani
"Eh,kin haskasu,don kinfi qarfin su haskaki aysha basu da wannan kyan saidai ke haskasu" tilas ya sanyata dariya,idan yana yabonta wani lokaci yakan sanyata dole taji kanta ya kumbura,taji duk duniya babu macen da tayi sa'ar miji kamar ita
"Wannan shine dan qaramin tukuicin da zan baki kan farincikin da kika sanyani daren jiya" ya rada mata wanda kunya ta sanyata saka tafin hannunta ta rufe fuskarta,kamar yadda ya saba ya hanata godiya yace amma wannan karon ta adana godiyarta sai haduwa ta biyu,murmushi ta saki kawai,khalipha na sata jin kunya shi kuma babu ruwanshi.
Haka sukayi zamansu yana jinyar abarsa yana lelenta,saida sukayi kwana biyu cur sannan suka fita,zuwa sannan ta samu sauqi bata jin komai a jikinta,don ya bata tazara bai sake neman komai daga gareta ba,ranar tare da ummi suka wuni a masallaci,don suna saka ran a satin zasu bar saudiyya.
Cikin satin kuwa khalipha ya dinga daukarta suna zuwa siyayya,har gajiya tayi da siyayya,ya dinga sanyata tana diban kaya kamar banza,batasan cewa ba nijeria zasu wuce ba sai ana ya gobe zasu tafi,ya shaida mata suma zasu suga ruqayya ne,langabe masa tayi tana kallonsa
"Nayi missing din anni pls ya khalipha...."
"Na sani nima haka,amma inaso muje mata ne da babbar tsaraba" sam bata gane ne yake nufi ba sai tace
"Akwai tsarabar dana siya mata,kuma abinda tafiso shi na siya mata,nasan zataji dadinta" bakinsa ya tabe yana kada kai
"Duk tsarabar da zaki kai mata bata kai wanna ba,so nake ki samar mata jika....." Ai bai qarasa ba ta saki ihu tana rufe fuskarta,yayin daya bita ya danneta yana qoqarin saita bude fuskar ya qarasa gaya mata ita kuma ta qiya,daga qarshe shi yayi nasara dole sai rintse idanunta tayi tana saurarenshi a haka.
Karon farko da suka soma haduwa da ruqayya tayi aysha ta kwanta mata sosai,kamar yadda itama anty ruqayya ta kwanta mata,ta rasa inda zata saka ayshan,ta lura akwai sabo da qaunar juna sosai tsakaninta da khalipha,yaranta kamar aysha ta qwacesu,yara masu kyau da tarbiyya.
Tun anty ruqayya na mata hira kan dabarun zama da miji tana jin kunya har daga qarshe ta haqura,a nan ta samu sirrika masu tarin yawa a wajenta,dauka mata wannan tasha,dauko mata wancan ta lasa duk wasu hadin na larabawa ne,sai data tsima ayshan da kyau cikin dabara,donta lura da take taken khalipha wanda ta fuskanci ayshan sam batasan me yake nufi ba,ana sallar magariba ta sanya ayshan tayi wanka da kyau cikin ruwan turaruka,ta bata wata rigat bacci mai kyau saidai tana da dan kauri wadda tasha turaruka kala kala,bayan ta gama shiryawa suna gefan gadon anty ruqayyan ayshan na sauyawa qaramin yaron anty ruqayyan pampers khalipha ya shigo dakin wanda dakin spare ne na baqi mata dake cikin gidan,dubanshi anty ruqayya tayi samda yake tsaye ya tokare bango da qafarsa guda daya daya yana tsaye a kanta,hannunsa harde a qirji ya dan shagala da kallon aysha wadda antyn ta gyara mata kanta yayi kyai qwarai
"Ya ne alhj halifa?" Saiya saki ajiyar zuciya a boye ya maida kanshi gunta
"Zuwa nayi ki bani matata,tunda na fuskanci so ake a qureni ana zaton bazan iya magana ba" dariya ta saki
"Allah ya baka haquri,aysha tashi ki bishi tun bao daukeki da kanshi ba" sauke qafarshi yayi yana tattare hannun rigarshi
"Kamar kuwa kinsan abinda nake nufi kenan ba?"kafin suce meye su duka ya daga ayshan cak yana fadin
"Allah ya bamu alkhairi saida safe anty" kunya kamar aysha tayi me?,sauqin abun daya duka yaran antyn na dakinsu suna assigment,tun daga hanya qamshinta ya soma rikitashi,suna zuwa daki ya qarasa birkice mata,ranar ya more angoncinsa qwarai,taso tayi dauriya amma daga qarshe saidata nuna raki,duk da akwai sauqi akan karon farko,shikam ji yayi kamar ma ranar yake ango.
Washegari qememe ya hanata fita sai daya sake morewa,kunya tasa ma ta kasa fita gaba daya,'yar halak anty ruqayyan saiga aiken breakfast ta turo babban danta ya kawo musu,koda yamma da suka fito zai zaga da ita gari antyn fuskewa tayi kamar ba'ayi komai ba,wanda hakan ya sanya aysha itama ta sake.
Kwanansu bakwai a dubai suna amarci sosai,randa suka dawo daga wani mall tana fitowa daga wanka saiga kiran wayar hanan,ta tsaya da tsane ruwan kanta da take ta amsa wayar,ta gaya mata an dawo daga yajin aiki,suka dan taba hira sannan sukayi sallama ta aje wayar tana duban khalipha dake ninke kayan da suka cire shi da ita,haka yake baida qyuyar aiki,wani lokaci har mamaki yake bata,baida girman kai ko kadan,baya jin yiwa iyalinshi aiki ko wata hidima,wani abunma kafin tayi musu shi yayi
"Komawa gida yazo kenan,kaga hanan ce ta kirani tacemin an koma strike" kanshi kawai ya daga ya kalleta,saiya maida yaci gaba da abinda yake ba tare daya ce mata uffan ba kamar ma baiji abinda tace ba,dubanshi kawai take,ta tabbatar yaji din,amma batasan me yasa yayi banza da zancan ba,saitaja bakinta itama tayi shuru taci gaba da sabgarta,saidai jikinta gaba daya a sanyaye yake.
Har sukazo kwanciya jikinta a mace yake,yayin da shi kuma har a sannan baice da ita komai ba,sai daya gama addu'at kwanciya ya shafa itama ya shafa mata sannan ya janyota jikinsa,a hankali can qasa yace da ita
"Karki wani zafafa da yawa,kar ki saka buri da yawa,Allah ya sani ni kadai nasan me nakeji a zuciyata a kanki,kici gaba kawai da addu'a kan ci gaba da karatunki a wudil,idan babu alkhairi Allah ya zaba miki abinda yafishi alkhairi"sosai gabanta ya fadi tana tsoro da fargabar fa yace ba zata koma ba,amma duk da haka saita danne kawai,tunda shine sila na komai hatta da karatun nata ma.
Cikin dare ta tashi a firgice sakamakon mafarkin da tayi,gidan daddy ya cika anata kuka,shi kuma yana zaune yana ta bin mutane yana basu haquri,ita kuma waisai ta shigo ta fadi tana kuka,saiya dagata yana cewa ta fada kan maciji,sai macijin ya sareshi shima ya fadi anan sai kuma akayo kanshi anata jijjigashi amma ya daina motsi,tana cikin bawa khalipha labarin kawai saita saki kuka,harga Allah zuciyarta tayi gida a sannan,da qyar ya lallabata ya nuna mata sharrin mafarki ne,shi ya sanyata tayi alwala shima yayi suka dasa sallar nafila har asuba,bayan tayi sallar ne bacci ya dauketa.
Tana farkawa kuwa layin daddyn ta soma kira,babu jimawa ya daga,wata wawiyar ajiyar zuciya ta saki sannan ta soma gaidashi,a sake yake amsawa ta tambayeshi jiki yace jiki da sauqi sosai,don bai taba jin dadin jikin nasa irin yau ba,hira sukayi mai tsaho sannan sukayi sallama tace ya gaida mutanen gidan,yace zasuji don safiyya ma mutuniyarta nakan hanya tace saitazo ta kawo masa wani dahuwar nama,tana dariya tace idan tazo daddy kace ta ragemin,yayi dariya yana fadin
"shikenan kuwa zata ji,sai wani lokacin kuma"
"Zan sake kira daddy anjima in sha Allahu"
"Allah ya bamu aron rai"
"Amin" da haka suka rabu,khalipha na tsaye saman kanta yana kallonta yana dariya
"Yar daddy,kin kirashi dai kinji dadi ko,kuma kinji lpy lau yake sharrin mafarki ne,haka kawai jiya kika wani birkice,ina shirin da asuba adan sanmin na d'ana duka aka hanai" juya qwayar idonta tayi cikin kunya tana murmushi
"Hankalina ya tashi ya khalipha,ina son daddy" gefanta ya samu ya zauna
"Mutum ne na qwarai sosai" daga haka hirar daddyn ta balle a tsakaminsu,kowannensu na tuna alkhairinsa gareshi.
A ranar da yamma tana tare da anty ruqayya suna hira khalipha ya shigo yana shaida.mata ta shirya nan da wa daya zasu wuce nigeria,cikin mamaki anty ruqayya kanta take kallonshi bama ita ayshan ba
"Lafiya daiko?" Ta tambayeshi
"Lafiya,aikime kawai ya taso min a kamfani kiran gaggawane ya samu"
"Auto,har naji dadi" ta fada tana sakin ajiyar zuciya,itakam.aysha ba wani zumudi dataji wanda ta tsammaci zataji duk randa zasu koma gida,saita miqe zuwa dakinsu da zummar hada musu kayansu.
[16/03, 11:11 PM] +234 806 544 7089: 58
Wani jiri taji yana niyyar kayar da ita sanda taga tarin al'umma da rumfuna tun daga qofar gidan daddy zuwa cikin harabar gidan dake a wangale,kusan tunda tazo gidan ta gama rayuwarta ciki bata taba ganin an wangale qofar gidan irin haka ba
"Ya khalipha?,me yake faruwa?,me ake haka a gidan?" Ta tambayeshi cike da tsoron amsar da zata fito daga bakinsa
"Kinga saukarmu kenan nace bari na kawoki kiga jikinsa don hankalinki yafi kwanciya,wataqila maqota ke wani sha'anin koma daurin aure ake ne,amma kinsan me za'ayi?,shiga ciki ina nan ina jiranki idan kun gaisa saiki fito mu tafi"
"To" tace tana fitowa bayan ya bude mata murfin motar da kanshi,haka kawai ta dinga jin kamar zata fadi qafafunta sunyi laushi kamar ba'a jikinta ba haka ta dinga takawa har cikin gidan.
Anni ta soma cin karo da ita,mamaki dukka saiya kamata,meya kawo anni gidan to me akeyi?,ko dama ta sansu?
"Allah ya jiqan alhj,ba shakka anyi babban rashin da aka jima ba'ayi irinsa ba" kunnenta ya dauko mata muryar wani daga can wata rumfa dake bayanta da yazo gaisuwa,bata gama wannan ba ta dinga jiyo ihun asma'u tana kiran sunan daddy,da hanzari ta taka don shiga tabi ba'asin meke faruwa sai taji gangar jikinta ta kasa daukarta,ji tayi tana sulalewa zuwa qasa,daga haka bata sake sanin abinda ke faruwa ba.
Sanda ta farka dakin ta dinga bi da kallo sai daga bisani ta gane a asibiti take,a hankali abinda ya faru ya dawo mata kanta,saita fashe da kuka tana fadin
"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" a hankali wanda hakan shi ya fargar da khalipha dake saman abun sallah cewar ta farka,gaba daya hankalinshi a tashe yake cikin hanzari ya isa gabanta anni dake zaune can kan kujera ta taso itama,ta dakatar da khalipha dake shirin dagata ta zauna,saiya fasa ya tsaya saitin kanta yana shafa sumar kanta a hankali yana tayata fadin innalillahin,har tsahon wani lokaci bai hanata kuka ba hakanan basu fasa maimaita innalillahin ba tare dashi,daga bisani ne ta saki ajiyar zuciya tana cewa
"Da gaske ya khalipha daddy ya mutu?,dama sallama jiya mukayi dashi kenan a waya?" Ganin shima ba wani a nutse yake can ba saboda yanayin da ayshan ke ciki ya sanya anni matsowa
"Allahn daya haliccemu shi ya fimu sonshi,ya kuma fimu sanin dalilin daya sanya ya dauke abinshi,kada mu yiwa Allah daya bamu shi butulci"
Kai kawai take gyadawa tana ci gaba da ambaton sunan Allah,wanda shi ya dafa mata ta samu nutsuwa,sai da anni ta tabbatar ta nutsu sannan ta taimaka mata ta tashi ta zauna,khalipha ya sanya daya daga cikin yaranshi suka yiwa likitar magana,macace likitan dalili kenan ma daya sanya khaliphan ya kawota wannan asibitin,ta tabbatar mishi komai ya koma normal,saidai ta kiyaye damuwa da bacin rai ta rubuta sallama.
Gidan anni suka wuce kai tsaye tayi wanka,saidai har a sannan hankalinta bai jikinta,ta matsa sai an kaita can gidan makokin,haka