Showing 162001 words to 165000 words out of 184891 words

Chapter 55 - DAURIN BOYE Complete Document by Safiya Abdullahi Huguma.txt

tafiya nabar mai ita ba" dariya yaso bata,haka ya iya soyayya?,dama haka masoya suke ji cikin zukatansu?,haka ya tsaya daga bayanta yana tayata qananun abinda zai iya,duk da kusan wayo yayi mata morewa kallonta kawai yake,idan ya kasa daurewa yadan matsa kadan ya rage zafi da haka suka kammala komai tare.




Wani irin wuni ranar sukayi tare da juna yana sake bayyana mata kanshi,hakanan itama,kowanne na sake jin dan uwanshi cikin niki da zuciyarshi,so yake ya cire mata dukkan wata kunya tashi da nauyinsa,ya gaya mata soyayya yake da buqatar ta nuna mishi zalla babu algus,qunahe qunahe ko 'yar kunya,yana son ta zama shi ya zama ita,yana son su zama sirrin juna kamar yadda Allah S W T ya fada cewa
_"Su(mata)tafafi ne a gareku,haka kuma(maza)taufafi ne a garesu"_ hatta da wayoyinshi duka a kulle suke,bai bude ba sai bayan sallar la'asar,mahmoud ne mutum na farko daya soma kiranshi
"Haba haba boss,ya za'ayita nemanka amma a rasa ka?,ka bace sama da qasa" murmushi ya saki idanunsa na kan aysha dake hada masa system dinshi
"Kai mahmoud,na gaji wallahi,daga dawowata?,ina buqatar na huta shi yasa,zan hau yanzu zan duba dukkanin saqonnin"
"Alright....mutumin nan fa ya matsa min daga jiya zuwa yau?"
"Wa fa?" Khaliphan ya tambaya
"Alj kutama mana" dogon tsaki yaja
"Rabu dashi don Allah,mutumin banza,ya bani mamaki wallahi,irinsu ne ke amfani da damar da Allah ya basu suke ruguza rayuwar matasanmu ta hanyar shigo da miyagun qwayoyi,bazan qyaleshi ba mahmoud saiya d'an d'ana kudarshi,sai ya dawomin da dukka kudade na cikin kwana uku"
"Banga laifinka ba,koni iya mutuncin da zan iyayi masa kenan,sam mutane basa yiwa kansu da rayuwarsu adalci,ta yayaAllah xai albarkaci bayan irin wadannan?"
"Ka gani" cewar khalipha yana jan tsaki,nan suka kammala tattaunawarsu kafin suyi sallama daga bisani.




Kwanansu uku cikin gidan yana koya mata wani darasi mai wuyar mantawa,wata wutar qaunarshi yake rura mata azuciyarta,soyayya mai tsayawa a rai,tamkar zata zauce wani lokaci haka take ji,yasan dukkan wani salo da matakan gina soyayya cikin zuciyar abokin rayuwa,badon yajin aiki daya ratso musu suke zaune a gida ba ta tabbata mawuyacine taci gaba da fahimtar karatu idan ta koma makaranta,duk wannan abun khalipha na baya baya ne saboda komai ya tafi dai dai da plan dinsa.




Cikon kwana na hudun da wani yammaci tana kitchen tana hadawa khalipha salad,ta baroshi a falo yana kwance yana hutawa,wanda da qyar ya yarda ya zauna don cewa yayi sai yazo ya tayata,tayi kyau qwarai cikin wani lace mai kyau daya zaba mata yau yace shi zata sanya mishi,ba zafi yau garin sai hadarin daya hado,ruwa bai samu sauka ba saiya juye yake bada wata iska mai sanyi da dadi,haka yake kullum a rana sai tayi masa kwalliya uku hudu,bata masa qasa da hala,ta fuskanci mutum ne shi maison mace mai ado,sai Allah yasa ra'ayin nasu ya kusan zuwa daya,ko a baya rashin sukunin rayuwa ne yake hanata kwallia,a yanzu kam duk wanda yasanta ya santa da ado,abin ya mata dai dai,sao kawai ta baje kolin kwalliyarta so ranta.




Tunda ta fito a kitchen din ya zuba mata ido yana kallonta,kullum sabuwa take a wajensa,kullum tayi masa ado sai yaga na yanzu yafi na dazu kyau,sai yaga kamar bai taba ganin kwalliya iri tata ba,tana isowa kusa dashi ta aje tray din hannunta saman teburin gabanshi,batakai ga gama ajewar ba ya miqe ya zauna sosai yana murza ido,murmushi ta saki,tasan da walakin tana fiddo idanunta waje tace
"Uhmmm..."
"Ji nake kamar na hadiyeki na huta wallahi,kinga indai hakan ta faru ba wanda ya isa ya sake ganinki saini kadai" murmushi ta saki mai taushi,harga Allah kalaman khalipha ko da yaushe na sake dilmiyata ne cikin kogin qaunarshi,koda yashe kalamansa na sake nuna mata itama cikakkiyar macace wadda ta cancanci taso kuma a sota
"Ina godewa Allah koda yaushe daya qaddara zaka wanzu cikin rayuwata" shima murmushi yake mata,yana jin kaman ya janyota jikinss,saidai yana tsoron kada qiluta jawo bau,duk da yana fata komai yazo qarshe,saiya daga pillow din kujerar da yayi matashin kai dashi,ya ciro passport ya buda sannan ya miqa mata,hannu ta saka ta amsa,gabanta na faduwa zuciyarta na dukan uku uku,addu'a take Allah dai yasa ba cewa zaiyi zai koma ba,idanunta takai kai,visa ce ta shiga qasar saudiyya,wadda bata kowa bace face tata,idanu ta fiddo zuciyarta kamar zata fito,babban burinta a duniya?,mafarkinta ne zai zama gaskiya koko dai?,kai ta daga tana dubanshi da alamun tambaya,shima ya tattara dukkan hankalinsa da nutsuwarshi akanta,farinciki na ratsashi sakamakon farincikin daya sanyata a ciki
"Ya khalipha....da gaske?" Kai ya jinjina mata
"Da gaske ne uwaishata,rana ita yau in sha Allahu zamu tafi,kije ki gayawa Allah dukkan matsalolinki da damuwarki tsakaninki dashi,sannan mu roqawa kanmu samun dukkan wata rayuwa ta farinciki da ma'aurata kewa kansu fata,ya bamu zuriyya ta gari,yasa zamu fara rayuwarmu a sa'a" rungume passport din kawai tayi a qirjinta ruwan hawaye na bin kuncinta,abinda bata taba tsammatarsa ba cikin rayuwarta,dubanshi kawai take ta rasa bakin magana,idan ta bude baki ma me zata mishi?,dukkan wata kalma da zata fada ya riga daya saba jinta,walau a bakinta ko a bakunan al'umma,ya fahimci haka,saboda haka saiya ware mata dukkan hannayenshi alamar ta taho,ba taba lokaci kuwa ta kwasa zuwa gareshi ta zube a jikinsa tana sheshsheqar kuka,hannunshi ya sanya ya zame dankwalinta wanda tun dazu dama yaso zamewar ta hanashi,ya dinga shafar gashin kanta kawai yana shaqar qamshin jikinta,ganin ta kasa shuru sai ya soma rada mata
"So kike ki fasamin zuciyata kenan" idanunta dage jiqe da hawaye ta dago ta dubeshi dasu,saiya kanne mata ido daya yana murmushi
"Eh mana,kinsan abu mafi muni da kunnuwana zasu ji shine sautin kukanki?" Jin yace haka saitayi qoqarin hadiye kukan,ta kwantar da kanta saman qirjinsa tana goge hawayenta
"Na rasa me zance maka ne,na rasa me zanyi,dukkan wata kalma da zan fada gani nake bata gamsar ba,ka zamemin fitila a rayuwata,ka zamarmin haske mai kore duhu,kai daya ka bani farinciki da daruruwan mutane suka kasa bani,dame zan saka maka nikuwa aysha bayan bani da komai ban mallaki komai ba"
"Ke kike da komai,kuma kece kika mallaki komai" saitayi shuru tana sauraronsa gami da tunanin abinda yace
"Zuciyarki rayuwarki da gangar jikinki nakeso ki mallakamin,ki bani dukkan wata yardarki,ki soni ki qaunaceni,kici gaba kuma da sona domin Allah kamar yadda kikayi a baya" cikin sanyi da kwantar da murya tace
"Indai wannan ne ka gama samunshi har gaban abada"
"Kinyi alqawari?" Saita zauna sosai tana dubanshi cikin ido,wanda hakan ya sanyashi shima gyara zamanshi yana dubanta
"Duk duniya babu wanda ya cancanci samun wannan matsayin sama dakai,idan ma akwaishi bana fatan Allah ya nuna minshi har abada,zan rayu dakai cikin kowanne irin yanayi,bana fata na saba maka dai dai da rana guda kona sauya maka matsayi daga wanda na doraka akai a yanzu,idan wannan yana cikin qaddarata shima ina roqon Allah ya dauki raina kafin lokacin" wani murmushi ya saki,yana jin wani farinciki na ratsashi,tabbas baiyi wuyar banza ba,addu'a bata faduwa qasa banza,hakanan dama Allah yake lamarinshi,haka ya fada cikin qur'aninsa _sau da yawa zaku qi abu amma alkhairi ne a tare daku_ gashinan tabbas hakan ya tabbata a kanshi,saitin zuciyarshi ya dafe da d'aya hannun nasa
"Karki kasheni ni mana tun yanzu,idan kika mutu uwaisha in zauna dawa?" Yadda yayin ya bata dariya,saita saki murmushi mai sauti tana dubanshi sanda yake cusa hannunshi cikin aljihun wandonshi ya ciro wani dan qaramin akwati mai kyau,tana kallonshi ya bude,ya ciro wata nannadaddiyar dubu daya da aka yiwa ninki mai kyau,saiya dagata yana dubanta sannan ya dubi ayshan
"Kin tuna wannan?" Kudin hannun nashi sosai ta kalla kana ta dubeshi tana dan tabe baki gami da girgiza kai,wani kishi take ji yana dan sukarta,tana tunanin ko wata budurwarshi ce ta bashi?,murmushi ya saki yana maidata ciki sannan ya dubi ayshan
"Tun daga ranar da kika bada ita a matsayin biyan bashi a gareni na tabbatar da cewa akwai banbanci mai tarin gaske tsakaninki da asma'u,sannan akwai wata boyayyar halayya da baiwa da kike da ita data sha banban data sauran mata,yau bari na baki labarin da baki sani ba" daiya gyara zamanshi yana daukar cup din coffen data zuba mishi ya kurba,sannan ya soma bata labarin dukkan 'yammatan daya tabayi da yadda suka qarke dasu,mamaki.ne ya kama ayaha,tsoron duniya da mutanen cikinta ya sake kamata,kowa ya lalace?,kowa mai kudi yakeso?,idan a familynka ne sai.kana dashi kake sa wata babbar daraja?,idan saurayine kai ko qur'ani kake hadiya saboda sanin Allah da tsoronshi ba mai baka aure idan baka tara koka aje ba koda kana da sana'ar rufawa kai asiri?,wannan wacce iriyar rayuwace mukeyi?,tunaninta ya katse mata sanda ya tura mata system dinshi gabanta yace
"Duba" ba musu taja ta soma dubawa,order ne da yayi mata daga store na rahamalls wanda tuni suka iso,har an bude katafaren wajen siyayya gashinan da hotunansu an tsara komai dauke da sunan UWAISHAH MALL
"Duk abinda kika gani a nan naki ne humairah ke na tanadarwa,na yiwa kaina wannan alqawarin tunda dadewa bawai yanzu ba,nayi alqawarin ninka miki dubu dayanki tun ba yanzu ba,wannan shine tukuicin da nayi niyyar yi miki a matsayin taimakon da kika yimin sanda ake bina bashin dari biyar kika sadaukar min da dubu daya duk da bakisan waye ba ni" kasa magana tayi wannan karonma,sai ta rufe bakinta kawai da tafukan hannayenta,kai ya girgiza yana jifanta da tattausan murmushinsa
"Karki ce komai,don bana buqata,na riga dana gaya miki abinda nake da buqata" ya fada yana ware hannayenshi,sai kawai ta rungumeshi tana sakin kuka.






Tafe suke a motarshi saidai kana duban fuskarta kasan tsantsar baqinciki da bacin rai ke cinta,a yanzu ba abinda ta tsana irin auren hamid,neman kawai hanyar da zata yakiceshi take,saidai ta lura da idan natayi takatsantsan ba haqarta ba zata taba cimma ruwa ba.




Daga barkar haihuwa suke wanda ita sam batasan ma wadda suka jewa barkar ba,saidai ta cika da mamakin uban kayan da hamid ya siya din yakai,dama shidin ba dai neman suna da son burgewa da gwaninta ba,tunda sukayi aure bai taba yi mata siyayya irin hakan ba,sai gashi yayi ya kaiwa wasu,dai dai nan wayarshi ta dauki kuwwa,ganin kiran babanshi ne ya sanyashi dagawa,bayanin da daddyn nashi yayi masa ya daga masa hankali qwarai,ya tabbatar cewa gagarumar matsala ce take fuskantosu
"Yanzu daddy meye mafita?,ya zamuyi?"
"Ya kamata mu soma dakatar dashi,yanzu haka ancemin yana gidansa,idan kana kusa ka sameni nan titin lodge road saimu qarasa mu bashi haquri,ko qafa ne muce ya daga mana sai muyi tunanin abinda zamuyi a dan taqin"
"Shikenan daddy ganinan zuwa yanzu,ina kundila amma bari na qaraso"
55


ko duban asma'u baiyi ba ya dauke kan motarshi ya canza hanya
"Wai malam ina zaka dani ne?" Banza yayi da ita donshi kadai yasan tashin hankalin da yake ciki
"Kaga malam ka saukeni ina zaka dani nina gaji fa"tsawa ya daka mata sannan yace
"kiwa mutane shuru,ke bakisan abinda yake damunsu ba zaki cikasu da surutu,koma meye kema kin taimaka wajen faruwar abinda ya farun,dole muje dake kema ki saka baki" ganin yana yi kamar zai daketa ya sanyata yin shuru kawai tana huci,haka suka ci gaba da tafiya har suka cimma daddy,cikin tasu motar ya shiga suka tafi yabar motocinsa nan wajen wani cin abinci dake lodge road din.



Qararrwar falon daketa kadawa ya sanyashi miqewa don zuwa duba wanda ke neman izinin shigowa
"Kinga yanzu kikai alqawari ba zaki sake kuka ba,karki karya" kai ta gyada mishi tana binshi da kallo,har cikin ruhinta tana jin wani alfahari na kasancewarsa miji a gareta,daya tamkar da dubu.




Daya daga cikin masu tsaron qofar gidan ne yake shaida masa yayi baqi,baisan su waye ba hakanan suma sun gaya mishi cewa baisan da zuwansu ba
"Qyalesu su shigo" ya bawa mai tsaron qofar umarni,falon ya koma yana dubanta
"Kinga duk kinsa coffen yayi sanyi,dan sake hadamin wani zanje naga wasu baqi,nasan ba jimawa zasuyi ba tunda banyi dasu zan gansu ba,nan da minti biyar zan sallamesu saiki kawomin coffe din a can zan sha"amsa mishi tayi yayin daya dan sunkuya ya sumbaci goshinta sannan ya zura takalminsa ya fice.




Tunda suka shigo gidan gaba daya ya tafi da imaninta,tasan cewa za'a rina hakan,don tun a mota ta fuskanci wajen uban gidan mijin nata zasu je,sai take ganin gidan kamar ta sanshi,sai taga yana mata zubi da gidan aysha da aka kawota,girgiza kai tayi wani bari na zuciyarta na gaya mata
"Haba wane mutum,ta ina khalipha yake da kudi kamar na mutumin nan,ta inama zai ginawa ayshan gida har haka?" Ko kusa bata ankare da khaliphan ba har suka gama parking suka fito,saboda idanunta nakan jerin motocin alfarma dake pake a inda aka tanada saboda ajiyar motoci na gidan.




Hamid da daddy suna gaba tana binsu a baya,zuciyarta cike taf da qyama da dana sanin auren hamid,bata taba tunanin kudin da suke tinqaho dashi ba nasu bane na rance ne ba sai yau,da zasu kula da ita da kyau ta baya kallon wulaqanci take jifansu dashi,gab da zasu isa wani guri datake hango wani mutum can zaune hamid ya dakata ya jata gefe
"Ki tabbatar da cewar kin bude baki kin bada haquri,idan ba haka ba wallahi Allah kinji na rantse miki duk wani abu da nasan na siya miki ke har motar da kike hawa saina saidata,saboda duk da kudin da muka karba da bikinki na cire wani abu a ciki na siya miki" dubanshi kawai take,a fuska gashinan mutum iya mutum,saurayi dan gaye maiji da kanshi,saidai a ciki duka hoto ne kuma kango ne,sam hamid baya burgeta yanzu dai dai da qwayar zarra,hakanan mamaki ma suke bata shida ubanshi duka a yanzu,koda zata bar gidan hamid batason ta rasa abinda ta shigo da shi,ta koma gida a tsiyace,wannan ne dalilin kawai da zai sanyata ta bada bakin,saidai bata ce masa uffan ba har suka qarasa wajen.




Ya amsa musu sallamarsu saidai ya maida kanshi kan wayarshi yana turawa aysha tex kamar ba yanzu ya barota cikin gida ba,baiyi tsammanin su bane da bazai bada damar su shigo ma cikin gidan ba,qamewa asma'u tayi yayin da take qare masa kallo,wani tashin hankali taji yana gewaye ilahirin qwaqwalwarta,wai dama khalipha ne wanda sukazo roqa?,dama alhj kutama surukinta da hamid mijinta dukkansu a wajen khalipha suke amsar bashi?,dama da dukiyar khalipha aka aurota?,take dukkan wani qaimi da kwadayin rabuwa da hakid ya sake ninkuwa cikin zuciyarta,taci gaba da qarewa khalipha kallo tun daga zara zaran yatsun qafarshi zuwa kanshi,tana kuma tantance banbanci tsakaninsa da hamid wanda ya yiwa kanshi mazauni daura da khaliphan,karon farko data soma jin haushin kanta da kanta a rayuwa,tun daga siffa khalipha ya gama cinye hamid murus,me ya kaita yin wannan ragon azancin?,wai me yasa ma batasanya daddy ya nashi jari gida da mota ba asanda take tunanin talakane ta aureshi ba?,inuwar daya gani kusa dashi ya sanyashi dagakai,sai yaga asma'un,yayi mamaki don baisan meye alaqarta da alhj kutama da kuma hamid ba,Allah yasanya ba son kudinta ya kaita qulla alaqa dasu ba,ya furta cikin zucuyarsa
"Ki zauna mana,ya zaki tsaya qerere kan mutane?" Hamid ya fada cikin fada fada,saita ja kujera a kunyace ta zauna,a mutunce ba wulaqanci ya gaida daddg sannan suka gaisa da hamid,duk da bai bashi hannu ba,don a yanzu qyamatarsu yake,yana mamakin yadda kana musulmi zaka iya saida abinda zai zama cutuwa ga al'umma,infact ma ruguza al'umma gaba daya kayan shaye shaye yake,saboda matasa sune qashin gadon bayan al'umma to an ruguzasu me yayi saura?.




Daddy shi ya soma bada haquri sannan hamid,murmushi kawai khalipha yayi sannan kai tsaye ya kira sunan daddyn
"Aikin Allah kayi da kudin da kake tunanin samun sassauci daga gareni?,idan na sassauta maka ma na bada goyon bayan kaci gaba da aikata dukan abinda kake aikatawa kenan?" Gyaran murya asma'u tayi wanda ta gyara zama gami da lanqwasa muryarta ta sona zayyanowa khalipha maganganu,wanda kusan rabi hannunka mai sanda take masa a karan kanta,yadda ya hade yatsunsa waje guda yana kallonta yasa ranta yayi fari qal taci gaba da magana tana juya idanu,sai data gama yaja wani.matsiyacin tsaki sannan ya juya ya dubi alhj kutama bayan ya kira sunanshi
"Kada ka sake nemana idan ba kudina ka kawomin ba nan da kwanaki uku,idan ka tashi kawomin kuma ka daure ka dauko mutane masu hankali su rakoka" ganin yana niyyar miqewa yasa hamid zungurar asma'u kan tayi magana,don iyaka saninsa da khaliphan yana da tausayin mata qwarai,ta fuskanci abinda yake nufi itama kuma ko banza batason rasa dukiyarta,saboda haka ta soma roqonshi,daidai sanda aysha dake dauke da wata butar shayi mai kyau da qananun kofuna,saita soma takawa a hankali ganin kamar baqin nashi basu bati ba,bata ma gane su waye ba,shi ya soma ganinta,saiya miqa hannunshi yana cewa
"Kawo my uwaishahh" cikin nutsuwa take takowa ta dora yalwataccen mayafi mai kyau saman kayan jikinta,qamshin turaren data sake fesawa jikinta na kadawa zuwa ko ina,maganar khalipha ita taja hankalinsu kanta,take kowanne tunaninshi ya banbanta,alhj kutama na farinciki tare da jin dadin ganin fitowar uwar gidan,ko banza yasan idan ya roqeta ta sanya baki wala'alla khalipha ya dage musu qafa ko ya qyalesu,ya danganta da yadda yake jin maganarta,hamid mamaki ne ya daskarar dashi a wajen,dama aysha muhammad khalipha mai goro ta aura?,ya akayi haka?bayan asma'un tasha bashi labarin irin mijin da ayshan zata aura ta qyalqyala dariya tana fadin shi ya dace da ita ai,ya tabbatar asma'u bata da masaniya da tabbas ba zata qyalewa aysha shi ba,idan ko aysha ce matarshi lallai abubuwan zasu zo da sauqi,tun ba yauba ya santa da tausayi da sanyin hali,ba shakka mai yiwuwa tasha musu kan khalipha.




Ta gefan asma'u kuwa wani dan banzan kishin aysha shi ya taso mata,komai na ayshan ya sauya,dukkan wani jin dadi da hutu ya gama bayyanar mata,babu shakka ayshan nason tsere mata tayi mata fintikau a rayuwa,lallai ba shakka ya zame mata tilas tasan dukkan mai yiwuwa ta samu cikar burinta a rayuwa,cikin salo da kwainane asma'u ta sake lanqwasa murya tana roqar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login