Showing 168001 words to 171000 words out of 184891 words
Chapter 57 - DAURIN BOYE Complete Document by Safiya Abdullahi Huguma.txt
tafi,kukan da take yaqi tsayawa har a cikin mota,tun khalipa na daurewa har ya gaza
"uwaishah,ki taimakeni kiyi shuru,har cikin qirjina nakejin ciwon kukan da kikeyi" bata son bata masa rai ko qanqani,hakan ya sanya dole tayi shuru gami da yin luf a qirjinsa,kusan ranar wuni tayi a sanyaye,tunanin daddy fal zuciyarta.
🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶
Washegarin ranar jirginsu ya daga sai saudiyya,a garin makka suma soma sauka,suna sauka a masaukinsu dukkansu sukayi wanka suka dauki harama,saboda tsabar murna da zumudi ma ta rigashi kammalawa,ji take kaman tayi tsuntsuwa ta ganta bakin ka'aba,tana da abubuwa da yawa da zata roqa,tana da mutanen da takeso ta yiwa addu'a sosai,idanunta a kanshi sanda ya kammala daura hiraminshi,idanu suka hada sai suka sakarwa juna murmushi a kusan tare,kowa da abinda yake saqawa cikin zuciyarshi.
Sati guda sukayi a garin makka,iya ibada kam sunyita saidai fatansu Allah ya amsa,bata taba sanin khaliphan ta fannin ibada jarumi bane sai a wannan karon,duk nacinta da son ibada sai taga ashe ya kere mata,sau tari idan ta gaji tayi kaman zata huta sai taga shi a sannan ya saka qaimi,sai ya sake zaburar da ita,tabbas ta yarda ta kuma amince cewa kowacce mace halayenta idan zama yayi zama na kamanceceniya dana mijinta,kota debi wasu dabi'u nashi koshi ya debi nata,idan akayi katari na gari ne sai nagartarta ta ninku,idan kuma akasin haka ne walau ya rinjayeta ta ko ta koyi kaso mafi yawa daga cikin halayensa,shi yasa akeson ko aboki zakayi ka aboci na qwarai,don annabi ya kwantata aboki na qwarai da misalin mai saida turare ne ko.baka siya ba idan ka zauna dashi dole wataran zai san maka,kaima zakayi qamshi,hakanan nara gurbin aboki tamkar abota da maqeri ne,kana zaune feshin wutar zai dinga sauka atufafinka yana bata maka sutura,hakan shike nuna auren miji na gari shine babbar sa'a hakanan abu mafi muhimmanci da gata da mace zata yiwa kanta da zuriyar da zata samu a nan gaba.
Randa suka cika sati guda a garin makka suka wuce madina don suyi ziyara,musamman ya samu motar da zata zagaya dasu duk wani wajen da tarihi yazo dashi a addinin musulunci,farincikin data dinga ji ya zarce wanda taji a garin makka,jinta take fes,zuciyarta qal,kamar babu wani abu daya taba samunta a rayuwa na bacin rai,kullum tana maqale da masallacin ma'aiki tana yiwa kanta khalipha daddy da anni addu'a,dama duk wanda ya ratsa rayuwarta,idan na neman shiriya ne ta nema masa,idan na fatan alkhairi ne tayi masa.
Randa suka cika kwanaki hudu a garin madinan,da wata safiya sun fito zuwa masallaci ita da khalipha,irin wannan yanayin yana mata dadi qwarai,takan jita wata ta daban ta musamman,zuciyarta da ruhinta kan cika da farinciki,tabbas garin madina dabanne,hatta da yanayinsa ma daban yake,tayo bangaren mata shi yayi bangaren maza taji sabuwar wayarta daya siya mata tana ruri,tana dubawa taga sunanshi ne,cikin mamaki ta kara a kunnenta
"Ta wacce qofa zaki shiga?" Ya tambayeta,gaya mishi tayi sai yace ta sauya ta shiga ta daya qofar,bata kawo komai ranta ba ta amsa mishi ta kashe wayar sannan taci gaba da takawa donta wuce zuwa cikin masallacin.
A hankali take takawa cikin zuciyarta tana ta istigfari kamar yadda ta saba tunda suka zo,bata minti daya cikakke bakinta babu ambaton Allah,tana son ta ribaci lokacinta da dimbin falalar da garin yake dashi,dukkan aikin da kayi cikin garin walau na alkhairi kona sharri kana da ninkin lada ko zunubi.
Kamar a mafarki kamar wasa sukayi kacibus da umminta tana shirin fita daga masallacin itama,kallon kallo suka fara yuwa junansu tamkar wasu baqin juna,dukkan wani tashin hankali da fargaba da aysha takeji a sanda suka hadu a yanzu fes take jinta,zuciyarta a taaye take kyam,idanunta cikin na umminta
"Assalamu alaikum"aysha ta furtawa ummin tana dubanta
"wa'alaikumussalam"ta amsa mata itama tana dubanta,idan batayi kuskure ba qwalla take gani cikin idanuwan ummin fal,saitadan gotata kamar zata shige,da sauri aysha ta riqe tsintsiyar hannunta,tsahon minti daya suna a haka kowa ya kasa motsawa,sai ta jiyo sheshsheqar kukan ummin nata,abinda yayi masifar tayar mata da hankali,da hanzari ta sakar mata hannu tasha gabanta,batayi auneba taji ummin ta rungumeta tsam tana sakin kuka sosai
"bazan iya ba,bazan iya ci gana ba"
"Kiyi shuru ummi don Allah" saiga ayshan dake bata bakin tayi shuru itama ta saki kukan,duk yadda taso daurewa ta kasa,kuka suke sosai,ganin masu wucewa zuwa cikin masallacin na kallonsu ya sanya ayshan janye ummi gefe.
"Naja'atu" dukkaninsu suka waiwaya jin an ambaci sunan ummin,wani mutumine wanda aqalla zaikai shekara hamsin da biyar,gefanshi kuma khalipha ne tsaye suna dubansu,kuka ummin ta sake saki tana kauda kanta daga garesu baki daya,takawa mutumin yayi har zuwa inda take tsaye ya riqe hannayenta
"Idan kowa bai isa alfarnar garin nan,da wanda kabarinsa ke cikin wannan waje mai albarka sun isa su sanya ki amshi diyarki"
"Abban basma.....bana so...." Sai maganar tata ta harqe
"Bana son maganar da suka fada ta tabbata akan aisha,banason ta silata wani abu ya sameta" ta fada tana sake barkewa da kuka
"Dukkaninmu ba zamu fahimci abinda kike magana akai ba idan ba bayani kika yi mana ba"
"Ammm....abba,me zai hana mu samu wani waje su zauna a can" cewar khalipha,kai abban ya gyada masa sannan ya riqe hannun ummi naja'atu dake ta kuka.
Shuru kowannensu yayi kafin abba ya daga kai ya dubi aysha
"Khalipha ya cancanci zama yaji kowanne irin abu da naja'atu xata fada,fita kice ya shigo" a sanyaye aysha ta miqe don zuwa kiranshi,saidai duka hankalinta nakan ummin,gani take kaman kafin taje ta dawo xata rasa ummin,kamar kafin taje ta dawo ummin xata sauya ra'ayi,zata fasa fada mata komai,zata fasa karbarta,itama ummin nata idanun nakan ayshan,ita kadai tasan me take hadiyewa a haka harta dawo tare da khalipha,kujerar dake daura da aysha abba ya nuna masa yace ya zauna,da fari baiso zaman ba,saboda yana ganinnkamar wani sirri ne da bai shafi yaji ba,amma abba yace ko daya,miji shine babban sirri na farko wajen matarsa,haka ya zauna kanshi da idanuwanshi a qasa yana harhada cukurkudaddiyar rayuwarsu shida ayshan waje daya
"A ranar dana bar gidan baffale a daren ba'a kwana ba akace ana sallama da baffana,yana fita baifi minti biyar ba muka jiyo hayaniya cikin zauren gidanmu,sai gashi ya dawo yace na fito ana son magana dani,ban musa ba na miqe na fito,saidai wadanda na gani a wajen inda ya gaya min su sukazo tabbas bazan fito ba,gefe daya na samu na tsaya ina dubansu,dukkan yayye da qannem baffale ne mazan sai inna yelwa
"halaa ma dai bakasan abinda ya faru ba?"cewar saya daga cikin yayyen baffale yana gayawa baffana,kai ya jinjina yace kai nake sauraro
" to mudai muna da tantamar indo diyar baffale ce gaba dayanmu,tunda cikinta bai tashi bullowa ba sai da yabar garin nan gaba daya"nan fa ran baffanmu ya baci sosai,duk haqurinshi kuwa,saidai ya hadiye yana dubansu kawai
"Me kukeson ku gayamin,nafi ku sanin wace naja"
"Ai ka tsaya malam duka na wannan ba,abu daya shine zai tabbatar mana da aisha jinin baffale ce kuma jininku" shuru kowa yayi nida baffa gaba daya muna sauraronsu,inna yelwa ce ciki izgili nuna isa da taqama tace
"Daga nan har shekaru goma dai dai da rana daya idan naja ta koda kalli indo kota sake ta nemeta toba jininmu bace,ba baffale ne mahaifinta ba,matuqar jininmu ce to babu ita babu ita,ba ruwanta da ita jininta zasu kula da ita..." Ban tsaya na qarasa saurarenta ba kawai na juya cikin gida na barsu nan da baffa na,maganar ta inna yelwa ta yimin ciwo qwarai,sharrin zina ba abinda ya kaishi muni,na shiga bacin rai sosai a sannan,na sake tsanar inna yelwa da ahalin gidanta gaba daya.
Ana tsaka da wannan saiga inna sailuba,qawar inna yelwa ce sosai,saidai ikon Allah Allah ya hada jinina da ita tana qaunata qwarai,batasan aurena ya mutu ba saboda ba'a garin take auren ba,saidaga bisani tazo ta biyo ta yimin jaje tare da nuna rashin jin dadinta akan aninda inna yelwa tayi,ranar sai gata hankalinta a tashe,ban taba ganinta cikin tashin hankali ba irin ranar,ita take gayan maganar data sake sakawa na janye jikina da.aysha,na nuna mata qyama,na farko ta gayamin inna yelwa ashe ta rabani da baffale tasa aka sanya qiyayyar juna atsakaninmu,har ya mutu yana ambatona yana neman gafarata,sannan yanzu kuma sunyi wani shiri saboda basa son hada jini dani,duk ranar dana yiwa aysha wani kallo na tausayi ko jin qai a ranar ba zata sake kwana a duniya ba,saboda suna da yaqinin babu uwar da zata daurewar azabar da suka shirya suna gana mata iri iri,banso na rasa aisha diyar dana fara samu a duniya,tilas na koyawa kaina kyararta da tsangwarta,duk da a sannan na shaidawa baffa na kafin rasuwarshi yayi addu'a sosai da rubutu,idan baki manta ba mero na baki wani rubutu kisha waina tsari,shike aikawa meron ya bata yace ta baki,koya manta wani lokaci da kaina nake dauka na aika a zuwan baffa ne ya bayar,duk halin da kike ciki aysha ina sane labari yana zuwarmin,na hana 'yan uwana su daukoki kosu karboki ne gudun kada wannan abun da suja qulla har a lokacin yana nan ya zama silar barinki duniya,silar barina qauyenmu bazan iya zama ina nuna miki qiyayya sauran jama'a na nuna miki ba,sai naga gwara nayi aure a nesa,gwara nayi nesa dake,wataqila idan bakya ganina zaki haqura dani,wataqila abinda kike ji cikin zuciyarki zai ragu,kullum ta Allah sai nayi kuka akanki aysha,sai nayi kuka saboda tausayinki,kullum addu'a nake Allah yasanya duk randa zamu hadu wannan mugun abun ya warware,haduwarmu a nan zuciyata ta bani yaqinin duk wani mugun abu bai isa yayi tasiri a waje mai tsarki irin wanna ba,ki yafemin aysha....dukkan abinda ya faru ya farune bawai don ina sane ba ko inajin dadin faruwar hakan....."sai kuka ya qwace mata(a nan ina nemawa wadda ke cikin halin tsana da kyarar mahaifiyarta kamar aysha addu'a,ku sanyata a addu'a Allah yaye mata ya karkato mata da hankalin mahaifiyarta).
Rungumeta aysha tayi itama ummin ta rungumeta tsam suna kuka,sai khalipha ya kasa dauka ya miqe a hankali ya fice daga wajen,ganin haka ya sanya abba miqewa shima ya basu waje.
08030811300
57
Dukkan abinda ya faru a rayuwar aysha daga wanda ta bashi lbr kama da wanda ya faru yanzu ya dinga tariya cikin kwanyarsa,jinjina kai kawai yake,sai yaji yana son magana da anni wadda satin da zasu zo ta gama tata umarar ta wuce dubai inda ruqayya da take aure saboda haihuwa da tayi,shima yana saka ran daga nan can zasu wuce da aysha suga juna,don bata taba ganinta ba,ta kuna takura tana son ganin nata.
Suna soma magana da annin ayshan ta fito,saita koma gefa daya tana kallonshi hannayenta sarqafe da juna,wani iri so nashi da qimarshi na hauhawa cikin zuciyarta,sai yanzu ta fahimci shiya shirya komai,shiya shirya haduwarta da mahaifiyarta kamar yadda ya biya musu umara suma ya biya musu donsu hadu a nan,wanne irin mutum ne shi wanda bai gajiya da alkhairi?,wanne irin so yake mata da har kullum yake bibiye da lamuranta da dukkan mutumin daya rabeta yana aikin faranta musu?,bata dawo daga duniyar tunani ba saidaya miqa mata waya yana cewa zasuyi magana da anni,ta amshi wayar zata kai kunneta can qasa yace
"Ki rage wannan kallon da kikemin idan baso kike ki qarasa zautani ba" murmushi ta saki mai sanyi wanda yasa kumatunta lobawa,saiya shagala da kallonta sanda suke magana da anni,harta gama ta miqo masa bai sani ba
"Nima zaka zautani dinne?" 'Yar qaramar dariya ya saki yana karbar wayar
"Na gode,kin rama munyi one one ko?" Ya fadi yana dage mata gira,wani murmushin ta sake saki
"To yaya?,komai yayi normal?" Ya fada yana wara hannayenshi,kai ta gyada,sai hawaye ya soma bin fuskarta
"Ashe haka uwa take sa dadi ya khalipha?"kai ya shiga girgiza mata
"nooo...kuka kuma dai?,ashe zaki sanya na fasa barinki ki kwana wajenta da nayi niyya" idanu ta fiddo tana share hawayen
"Da gaske zaka barni?" Girarsa ya daga
"Yes,kwana daya zakiyi,amma kiyi alqawarin tanadarmin dukkan wani farinciki a sanda kika dawo ko?" Bata gane me yake cewa ba,saidai tunda yace zai barta ta kwana wajen umminta ya gama mata komai,haka kuwa akayi,ya dauki abba suka wuce nasu masaukin,suka bar uwar da diyarta suka kwana babu bacci suna hira
"Bansan irin qaunar da basma take miki ba,tun daga ranar da kikazo naqi kulaki ta daina walwala har yau" murmushi aysha tayi
"Ki barta,zanyi magana da ita da kaina gobe zan kirata" ranar haka suka kwana dungurgur a zaune aysha na bata labarin yadda ta rayu,kuka wiwiwi ummin ta dinga yi,ta rasa inda zata dora ranta,tayi alqawarin yafewa inna yelwa ne aduk sanda ta gane kurenta ta nemi afuwa banda haka data yi mata Allah ya isa,ta kuma nemi Allah ya fitar mata da haqqinta,ranar ko masallaci basu sake komawa ba,haka suka kwana tare,duk wani motsin ummin aysha na biye da ita,ko hijabinta bata bari ta dauka da kanta,yayin da ummin kebin ayshan da kallo duk inda ta motsa,tausayinya na ratsata,ta goge qwalla a boye tafi sau nawa,itakanta a karan kanta idan ta tuna yadda tabar ayshan tun batasan kanta ba sai taji dama ta tariyo baya ta goge komai,me yasa tabar musu 'yarta bayan tasan basa qaunarta?,me yasa bata tafi da 'yarta ba kome zasu ce suce,da duk wani shiri nasu bayi tasiri ba,data rayu da 'yarta tasan gatan uwa,saidai qaddara ta riga fata,hakanan bawa baya iya gujewa qaddararta,mai yiwuwa data tafi da ita din da a yau ayshan bata samu khalipha ba,da wataqila bata samu matsayin da take dashi na rayuwa ba a yanzu.
Washegari khalipha ya dawo bayan sallar azahar,don abba yazo tunda safe ya gansu ya wuce masallaci,a sannan aysha na ramuwar bacci ummi ta tasheta tace maza taje,haka ta dauraye fuskarta ta fita harabar wajen da yake zaune,idanu ta zuba mata wani abu na tsirga masa harta qaraso inda yake,ji yake kaman ya sureta,yana kallonta yasan bacci take aka tasota,saiya narke mata tun kafin tayi magana
"Wato an samu ummi an manta dani ko?,ba saqon saoda safe,ba saqon barka da safiya,babu na barka da rana,shikenan na gode...kice kawai ba zaki iya kula dani ba tunda kin samu ummi na auro wata kawai" har cikin ranshi da wasa yake,amma abun mamaki saiga qwalla aisha ta fara,abunma kamar yayi dariya amma ganin da gaske kuka zata mishi saiya daure,bai taba zaton yadda ake cewa masu suna aysha nada kishi sosai gaske ne ba kamar yanzu,da qyar yasha kanta,saiya koma seriouse dinshi sosai
"Ki shirya anjima zanzo ki rakani inyi wata siyayya" kai ta langabar
"Ya khalipha....ban gaji ba da ganinta"
"Rakiya nace zakimin ai ko?" Kai ta gyada
"Shikenan" kadan suka taba hira ya wuce shima masallaci,saboda addu'a yakeso yayi yau sosai kan rayuwarsu shida ayshan,harkokin kasuwancinsa,iyaye da 'yan uwanshi.
Gab da magariba ya dawo,yayi kyau sosai cikin shigar larabawa jallabiyya baqa harda hirami,ita kuma ta sanya abaya maroon da baqin niqaf bayan ta nade kanta da mayafin abayar kai kace hijabi ta saka,kallonta yake saboda wani kyau data yi masa,idanuwanta da suka fito ta tsakiyar niqaf din kamar an qara musu girma da kyau,tun a lokacin jikinsa gaba daya ya amsa har cikin zuciya tuhi da gangar jiki,duk wani kuzarin daya taho dashi ya bace,a haka suka lallaba masallaci sukayi magarina da isha'i sannan yace ta fito su tafi.
Katafaren shagon saida kayan ado ne na mata,binsa tayi kawai da kallo sanda ya nufi bangaren kayan bacci bayan ya gama siyan turaruka masu dan karen kyau da tsada,tana kallonshi don yace ba ruwanta ya dinga zaben kayan bacci kala kala,sai daya dauki wajen kala goma dukkansu babu mai qaramin kudi sannan ya biya suka wuce.
Wani shagon suka sake tsayawa nan gaba da wajen kadan,gwalagwalai suke siyarwa,kana ganin yadda suke gaisawa da bashi qima kasan babban custumer ne,hakanan akwai alamun sabo sosai tsakaninsu,kujera yaja mata yace ta zauna,sample aka kawo mata kala kala na sarqa da dan kunne,zobe da banguls khaliphan yace ta tayashi zabe,ta tambayeshi guda nawa yace kowanne bibbiyu,tana zaton anni ko wani zai saiwa saboda haka ta zage ta zabi masu kyau,ita kanta sun bala'in burgeta,basu dade sosai ba ya biyasu sukayi sallama suka fita.
Daganan wajen saida kayan maqulashe ya tsaya shima,yayi siyayya sannan suka shiga motar suka wuce,ta dan gaji hakanan ga kewar ummi,Allah Allah take su isa ya ajeta ta ganta sannan ta huta,sai taga dirven ya dauki wata hanya daban,ba ha yar hotel din da suka sauka ba,hakanan ba hanyar hotel din su ummi ba,dubanshi tayi
"Ina zuwa kuma ya khalipha"
"Masauki zamu koma nayi kewarki uwaisha....kiyi haquri gobe saina maidaki wajen ummi,ni kadaine bana jin dadi" batason bata masa dai dai da rana daya,duk yadda taso ganin ummi saita kada masa kai kawai,sai a sannan ta tuna ma yace mata dama kwana daya zatayi,amma batasan ba zata dawo ba data sake magana da ummin.
Area ce mai wani irin kyau mai kwantar da zukata,hakanan hotel din shima kansa tun daga gininshi da tsarinsa kasan na musamman ne,bata sake tabbatarwa ba sai da suka shiga dakin,duk kayansu yana ciki a shirye,shi ya maida qofar ya sanya muqulli ya rufe,haka kawai a ji jikina yayi sanyi,ta daga kai ta dubi khalipha dake kallonta yana murmushi
"Dakin yayi miki?,ko mu sauya waje?" Murmushu tayi mai sanyi sannan tace
"Sosai ya khalipa"
"Wayyo Allah" ya fada yana aje kayan siyayyar hannunshi,don bai barta ta dauki komai ba kamar yadda bai bar wani ya dauka musu ba
"Wanka da alwala....wazai fara ni koke?" Idanu tadan fiddo
"Ya khalipha...nikam haka zan kwanta bana jin yin wanka"
"No...dole kiyi,so kike ki zama qazama?" Ya fada yana kada kanshi,haka kawai take jin fargaba,saboda kallon da khaliphan yake mata saitake ganin kamar ba wanda ya saba yi mata ba,saita noqe kafada
"Toka fara yi sannan ni" hannunshi ya ware
"Well,hakan yayi" jallabiyar jikinsa ya