Showing 69001 words to 72000 words out of 184891 words
Chapter 24 - DAURIN BOYE Complete Document by Safiya Abdullahi Huguma.txt
abun na bata haushi da takaici gami da mamaki,tamkar sake rabasu akayi bayan wancan dalilin daya zama silar wanzuwar komai
"Na roqeki gwaggo ki fiddani daga duhu izuwa haske,ki warwaremin wannan DAURIN BOYEN,na jima cikin zullumi tashin hankali tsoro da firgici saboda irin qiyayya qarara da nake ganowa daga idanun mahaifiyata....me yayi zafi gwaggo?" Ta qare da sigar tambayar kamar zata shide numfashinta zai tsaya
"Yau xan baki labari indo...yau in sha Allah ba zaki sake kwana da tunanin kin aikatawa mahaifiyarki wani laifi ba" ta fada tana sauke ajiyar zuciya,mero da ita tayi saura a dakin saboda karime tana waje bata shigo ba,saboda kusan itama tabi sahun 'yan takaici da jimami,dubanta gwaggo asabe tayi
"Zauna mero.....baki zama wata bare ba ko baquwar al'amarin"komawa tayi ta zauna tana tattara hankalinta wajen gwaggo asabe kamar yadda aysha tayi,shuru ne ya ratsa dakin kafin daga bisani gwaggo tace.
"kamar yadda kika sani cewa dangin mahaifinki fulani ne gaba da baya,yayin da mu dangin mahaifiyarki muka kasance manoma ne,har kakanki kafin Allah yayi masa rasuwa ya kasance sarkin noma na qauyenmu,fadan manoma da makiyaya fada ne daya jima yana wanzuwa tsakanin wadan nan mutane guda biyu,fada ne daya janyo asarar rayuka da dama,ya janyo asarar dukiyoyi rashin kwanciyar hankali da lumana,ya kuma janyo gurbacewar mu'amala tsakanin manoma da makiyaya,to wannan abu ya shafi qauyenmu,duk da cewa mu ba'ayi kashe kashe ba,amma rashin jituwa ya shiga tsakani da sabani mai girma,kowa ya tsayawa bangarensa,kowa yana goyan bayan dan uwansa da yake jin labari a can wani yanki an kashe ko anci zarafinsa,hakan ya kawo silar daya zama manoma da makiyaya basa ga maciji a tsakaninsu,a irin wannan ne Allah ya hada soyayya tsakanin mahaifinki baffale da mahaifiyarki,suna tsananin son junansu qwarai da gaske,sam basuyi duba da abinda kaje ya kawo ba,basuyi la'akari da abinda ke faruwa tsakanin jinsin biyu ba,soyayyarsu kawai suka saka a gaba,sanda soyayyarsu ta bayyana,kowa cikin gidansu sunja daga kan daya bazai auri daya ba,duk wata hanya ta rabasu anbi amma sunqi su rabu,junansu kawai suke so,bana mantawa mahaifiyarki ansha jibgarta a gabana amma bata sauya zani ba,a haka suka ci gaba da gudanar da soyayyarsu ba tare da sun yarda da qudurin raba su ba.
Sanda suka tada maganar aure gagarumar rigima ta barke cikin qauyenmu,abu har ya kai gaban alqali,inda yaja kunnen iyayen da su qyale yaransu suyu aure tunda suna son junansu,mai yiwuwa hakan ya zama silar kawo zaman lafiya a tsakani.
Toh tun asali mahaifiyarki macace mai zafi fada da kuma fushi,tana da wuyar saukowa a fushi idan ranta ya baci,hakanan bata yarda a take haqqinta ko waye zata qwaci kanta a hannunsa,tana da riqo idan ka bata mata,saidai takan sauko idan ka nemi yafiyarta,dalili kenan daya sake taka rawa wajen kawo hatsaniya tsakaninta da matar babanta inna kulu,kowa cikin fadin garin yasan ta da wannan hali,hakan ya sanya kaf 'yan matan qauyenmu ba yarinyar dake kawo mata wargi,mahaifiyar baffale ta miqe ta fadi wannan halaye nata,ta kuma ce ko donsu ba zata bari danta ya aureta ba,ba zata hada jini da ita ba.
An buga sosai kafin daga bisani Allah ya qaddara cewa sai baffale ya aureta,biki akayi sosai kasancewar tana da dangin mahaifiya a nan cikin birni,an mata komai na gata,jeran da babu tamkarsa,hakan ya sake hura wutar kishi a zuciyar faccalolinta tun kafin ta shigo,don duk cikinsu ba wadda ta samu irin gatan data samu,hakanan yadda baffale ke take take a kanta babu wadda ta samu irin wannan soyayyar.
To wani irin zama zance tayi cikin gidansu mahaifinki,tsakaninta da mijinta salamun salamun,zaman lafiya suke da qaunar juna,hakanan yana nuna mata qauna ko a gaban waye,nan fa qananun maganganun cikin faccalolinta da gutsiri tsoma suka soma yawa,kowacce kishi take da ita,saidai sunsan halinta duk wadda ta tareta gaba da gaba ta gaya mata maganar banza tofa itama ranta sai ya baci,ba zata qyale mace ba,suka dinga gutsura magana suna yiwa surukar tasu nuni data saka ido a rayuwar gidan baffale,suka karanta mata da alama ta mallakeshi,kasancewarsa shine qarami hakan yayi tasiri a ranta nan da nan,sannan uwa uba ga kuma kallon da take mata na yarinya mara kunya mara dagawa kowa qafa fitsararriya,nan fa aka fara sa toka sa katsi tsakanin su,mahaifiyarki ita kadai tsakanin faccaloli da uwar miji,amma da yake jarumar gaske ce duk ta iya da su,ta tare iskancin kowa,kuma bata fasa nuna soyayya da kulawa mijinta ba,tana matuqar sonshi hakanan tana kiyaye duk abinda baiso gami da bashi amanna,ta bashi yarda ta sakankance kan cewa bazai taba tozartata ko wulaqantata ba,mu kanmu a sannan mun jinjina mata da irin qoqarin zaman da tayi,a haka ake zaune har tsahon shekara guda,bata taba haihuwa ba sai bari da take yawan yi a kai akai,da wannan kuma suka samu dama suka tasa ta a gaba da habaici da gori,ba uwar mijin ba ba faccalolin ba.
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*
*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_
*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_
*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_
*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_
*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_
*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
(08030811300)
26
*DB*
Duk wadda ta gaya mata baqa kan rashin haihuwarta saita maida masa martani,inna yelwa kawai take dagawa qafa,itama randa ta gaji ranar ta maida mata,daganan cacar baki ta barke a tsakaninsu,har baffale ya dawo ya taddasu haka
"Na gaji da zaman wannan yarinyar mara mutunci a cikin zuri'ata,yarinyar kamar 'yar fata,kamar 'yar Allah bani?,to lallai lallai saidai ka saketa ta koma gidansu,yau dai ba zata kwana cikin zuri'ar modibbo ba" kai baffale ya kwantar yana bata haquri amma sam inna yelwa tace batasan wannan zance ba,tace saidai ya zaba ko matarsa ko ita,hakanan baffale yana ji yana gani yayi mata saki daya,tana kuka ta tattara kayanta ta dawo gida
Zaman nata a gida nan ma ba wani dadi ne dashi ba,saboda adawa suka dinga sosai da inna kulu,kusan ta wani janibin idan aka karanci halayyar mahaifiyarki lafiya lau za'a zauna da ita,duk da tana da wuyar sha'ani amma tana da dadin zama,duk da baffale ya saketa sai ya zamana kamar ba'a rabu ba,kullum suna tare kusan idan baida wani uzurin da zai gabatar to suna tare da ita,tuni ya maidata da baki,gidanne kawai bai maida ta ba,sanda labari ya kai kunnen inna yelwa tayi tashin hankalin rabasu amma ina sam haqanta yaqi cimma ruwa,a sannan ma ashe tana da ciki tun kafin ta baro gidan mahaifinki,bai bayyana kansa ba sai a sannan.
Tofa sai sabon rikici ya kunno kai,inna yelwa ta kafe kai da fata kan cewar ciki bana danta bane,yayin da mero ta kafe itama ciki na baffale ne,a sannan baffale baya nan,ya tafi neman kudi garin legos,rigima taqi ci taqi cinyewa,inda alqali ya sake shiga karo na biyu,yace a jira har sanda Allah zai dawo da baffale aji ta bakinsa,hakanan mahaifiyarki ta dinga rainon cikinta a gida,har sanda cikinta ya isa haihuwa baffale bai dawo ba,da yawa suna cewa zaunar da shi inna yelwa tasa akayi don kar ya dawo sabo da ita,haka dai zance keta yamadidi.
Wata tara da kwanaki ta haifeki,kama ta bayyana ta zahiri,kama irin ta ahalin gidan moddibo,ran kwana bakwai aka saka miki sunan aishatu,ba ragon suna ba rigar sakawa,babu kuma wani daga gidansu mahaifinki,a sannan naja'atu bata damu ba,tasan cewa da masoyinta ya dawo komai zai dai daita.
Watanki takwas sannan mahaifinki ya dawo,ranar daya dawo bai zarto ko ina ba sai wajen naja'atu,yayi murna matuqa da samunki sannan ya sake jaddadawa naja'atu cewa zata dawo dakinta ranar juma'ar da zata zagayo,a haka suka rabu,daga bangarenshi ba wanda yasan da wannan magana,ita kuwa tuni ta shaidawa 'yan uwanta ta kuma soma shiri,labari yakai kunnen inna yelwa,ta kuma ci alwashin daukar mataki,wanda shi ya kaita ga barin garinmu na kwana biyu sannan ta dawo,ba wanda ta gayawa me tayi,babu kuma wanda ta gayawa imda taje,ta dai dawo ta ja bakinta tayi shiru.
Ranar juma'ar kuwa aka yi mata rakiya,saidai inna yelwa ta tsare qofa ta hana a shiga da ita ciki,ta cika ta tunzura da taimakon zugar faccalolin ta,budar bakinta ma cewa tayi ita sam bata yarda da cewa ma diyar baffale bace goye a bayanta,tana shakka,tunda shi tunda ya dawo bai nemesu ba bai kuma yi maganar 'yar ba,bai kuma ce tashi bace,yayin da naja itama ta dage kan ba zata koma gida ba...gidan mijinta yau zata kwana,tunda shi ya maidata,babu dalilin komawarta gidansu,sannan 'ya ta baffale ce ko sama da qasa zasu hadu shi ya san da hakan,a nan inna yelwa ta bazama yara nemanshi sai gashi kuwa,tsatstsareshi tayi da ido tana tambayarsa yaushe ya maida naja bai nemi yardarta ba,rudewa yayi ba irin wadda ya saba ba duk sanda yayi mata laifi,ya kuma hau kame kamen cewa naja din ce ta dage kan komawarsu,abinda ya bata mamaki kenan ya daure mata kai,itadai tasan tare sukai maganarsu,ya kuma nemi ta koma din ya kuma amince,to amma duka ba wannan ne babban abinda ya girgizata ba,yadda inna yelwa ke shegantaka masa yarinya tana ba cikinsa bane yayi gum da bakinsa bayan yasan nashi ne,a nan fa halinta na qwatarwa kai 'yanci ya motsa,tace ba zata yarda ba,ta garzaya wajen alqali wanda ya saba shiga rigimar tasu,nan ya tattarasu ya tambayesu,sai a nan baffale ya amsa kaman yana dari dari da inna yelwa,da alamu dai akwai wata a qasa kenan,ganin ya amsa alqali ya kashe case din,naja'atu ta koma dakinta,saidai abinda baffalen yayi ba qaramin bata mata rai yayi ba.
Bayan komawarta sai zaman nasu ya sauya salo,ba wani jituwa can tsakaninsu,haka ma jama'ar gidan abun nasu ya sake qamari,bata shiga sabgar kowa suma basa shiga tata,duk wanda ya sake ya shiga gonarta kuwa zata nuna masa kurensa,bata barin kota kwana,hakan ya sake saka rashin jituwa mai qarfi tsakaninsu,baffale kam tana zaune da shine kawai saboda darajar soyayyar da sukayi a baya bata manta wannan ba,kasancewarta mace wadda bata da saurin mance abu.
Al'amarin ya fara ne lokacin da naja'atu tayi watanni hudu da dawowa gidanta,a sannan kika cika shekara guda a duniya,mahaifin naja'atu da muke kira baffa salihu ya hada mata gara mai yawa,garar haihuwa ce wadda ba'a yi mata ba saboda bata dakinta a sannan.
Ranar kai garar ina cikinsu,a sannan nima ina goyon suwaiba,naja batasan da zuwanmu ba,saboda haka tana sashinta,da sallamarmu gami da guda muka shiga gidan,duk matan gidan suna qasan bishiyar nan da sukan zauna kulli yaumin,sai aka rasa mai amsa mana sallamarmu sai ido suka bimu da shi,ganin haka rakiyar mai bin naja tace mu wuce bangaren najar kawai,kai tsaye can muka dosa,sanda muka shiga gidan mun isketa a sashenta tana dinkin hula,fes da ita ita da sashen nata kasancewarta gwanar tsafta,da farincikinta ta shinfide mana tabarma a tsakar gidanta tana fadin
"Amma kun yimin ba zata,da kun iske ni kuma bana nan fa?"
"Saimu koma da kayanmu mu cewa baffa salihu kince bakiso" dariya aka saki baki daya sannan tace cikin farinciki
"Kayan baffa ai bana mayarwa bane".
Kayan muka soma nuna mata,sai ta dakatar da mu tace bari ta kira sauran matan gidan,tayi hakanne saboda haka ake,a qa'ida ma su zasu tarbemu,uwar mijin kuma ita zata saukemu a wajenta,tana shirin fita da goyonki a bayanta saiga inna yelwa afujajan cikin fushi,sauran surukanta matan 'ya'yanta biye da ita,da kallo naja ta bisu da shi,duk sanda irin hakan ta faru tasan Allah ne kadai yasan sharrin da aka yi mata wajen inna yelwa,Allah ne kadai yasan me akaje aka gaya mata,tasan cewa yau babu zaman lafiya kenan,ta quduri aniyar komai ta fanjama fanjam ba zata lamunci a taka ta ba
"ku tashi ku fito munafukai algungumai irin masifa jinin tsiya,manufukar data gaya muku babu abinci a gidan nan qaryarta tasha qarya...tun kafin ayi daran akai kwandi....tun kafina a haifi uwar mai sabulu balbela take da farinta,bamu gaji yunwa ba bamu santa ba,kuma zuwanta cikinmu bazaisa a fara yunwa ba,ku kwashe tsiyarku ku koma da ita tun rayuka basu baci ba" baba ladi dattijuwar cikinmu,wadda take yaya ce ga baffa salihu tace
"Haba yelwa...haba ke kuwa....idan ana harkar arziqi ai tsiya bata shigo ba,gara ce ta jikarki da aka saba yi wadda bamuyi ba wancan karon saboda najar bata dakinta yanzu muka biya ta..." Tsawa inna yelwa ta daka mata gami da kiranta tsohuwar banza tayi wa mutane shiru,hakan shi ya sake tunzura zuciyar naja itama ta tanka
"Karki sake kiran uwata da tsohuwar munafuka...akan meye ne inna duka wannan masifa da bala'in?,tunda na auri danki ban huta ba...wai duka dai akan baffale ne wannan?"
"Eh...a kansa ne idan kin haifu cikin uwarki sahura da ubanki salihu ki barmin dana kiga idan baqar magana ma zata sake shiga tsakanina dake har abada....kai manu...matsa kuyimin koli koli da kayan wadan nan matsiyatan na daina ganinsu" ta baiwa matasan jikokinta umarni,kafin qiftawa da bismillah yaran sun soma diban kayan suna watsawa farfajiyar gidan,wadda ki cike da kwatami da qazanta,haka suka dinga watsi da duk abinda muka zo da shi yana dilmiya cikin tabi da gulbi muna kallo,tsabar baqinciki naja kuka ta saka ta dora hannu a ka,ana tsaka da wannan abu baffale ya shigo,ranta sai ya danyi sanyi tayi wajenshi tana zayyana masa abinda yake faruwa ga zatonta zai dakatar da su,sai yayi wajen mahaifiyarsa wadda ta dubeshi kai tsaye ta bashi umarni
"Ka saketa baffale idan ni na haifeka,saki biyunta nakeso ka qarasa mata" juyawa yayi ya dubi naja,kai take kadawa cikin kuka
"Karka aikata abinda zai zama dana sani a garemu...karka karya alqawarin daka yimin..."
"Bazan taba dana sani ba don na rabu dake.....naja na sakeki saki biyu....kai manu ku shiga dakinta ku fitar mata da kayanta" ya sake baiwa yaran umarni,kafin kace kwabo kayan ta sun soma watangaririya,tun daga tsakat gida har zuwa katangar bayan gida ta nan suka dinga jefa wasu sai da muka zagaya muka tsince,hatta da suturarta ta sawa basu damu da wankinta da guga ba haka suka dinga watsi da ita.
Mun jata kan ta wuce kawai mu tafi don wasu kayan ma ba zasu debu ba amma ta doje,ta koma ta dubi innayelwa daje tsaye ita da surukanta,wanda kowaccw farinciki take yau naja tabar gidan tsabar hassada da kishin banza mara amfani
"Yelwa....saboda danki kika yimin haka?....burinki ya cika danki ya sakeni....amma ki sani akwai ranar nadama,idan danki ne na barshi kenan har abada,ba danki ba duk abinda ya danganceku ma..." Ta qarashe maganar tana kwantoki daga bayanta,a sannan kina bacci duka bakisan abinda ke faruwa ba,shimfide musu ke tayi,tana shirin juyawa inna yelwa ta saka dariya
"idan kin haifu ke cikakkiyar 'yar halak ce ki sallama mana ita kiga idan ba zata rayu ba" wani irin kallo ta juya tayiwa inna yelwa,ta yiwa baffale nashi sannan ta qaraso cikinmu cikin matsanancin fushi mukayi gaba,a sannan babu wanda yaga rashin dacewar barinki saboda bacin ran abinda suka yi mana,a sannan babu wanda ya zaci wannan qiyayyar zata shafeki ta raba tsakaninki da mahifiyarki,babu wanda ya zaci lamarin zaiyi dogon zango har ya cimma wadan nan shekarun,yadda naja tace ta bar baffale har abada hakan ce ta faru,hatta da qofar gidan ta daina wucewa,hakanan duk wani lamari daya danganceki ta shafeshi a babin rayuwarta,bata zancanki bata yarda ayi mata zancanki,bata rabarki bata yarda ki rabeta.
Hankalinmu bai dawo jikinmu ba sai sanda labarin wahalar da kike ciki ta riskemu,a sannan duka bakifi shejara hudu a amma yadda ake tafi dake tamkar wadda ta shekara goma,duk da tun sanda mahaifiyarki tabar gidan hankalin baffale kacokam ya koma kanki,kulawarsa duka tana gareki,a hankali sai ya soma bagarar dake kema,wanda mutane da yawa sunyi amannar an kawar da hankalin baffake ne daga kanki da mahaifiyarki,ba'a hayyacinsa yake aiwatar da komai ba,a sannan mukayi yunqurin karbowa naja 'yarta amma taci alwashin duk wanda ya taka gidanma babu ita babu shi har abada,a sannan baffa Allah ya masa rasuwa.
Hankalinmu bai sake tashi ba sai da kikayi wayo kika soma bibiyarta da kanki,amma wata iriyar tsana kyara da hantara ta dinga giftawa a tsakaninku,ba wanda bai mamakin wannan al'amari ba,har aka dinga zaton anya ba jinnu ne suka shiga jikin naja sukai amfani da abinda ya faru ba suka farraqaku,saidai daga baya muka fuskanci ras take bata da wata matsala,taja kunnen duk wani wamda yake ganin ya isa ya kawo daidaito kan lamarin,akwai wadanda sanadiyya daidaita lamarinku har yau babu jituwa tsakaninsu da mahaifiyarki,da tawa daga cikin 'yan uwa jin haushin abinda take miki yasa suka fita sabgarku gaba daya ke da ita,suna ganin kunfi kusa ai,duk yadda zasu soki basu kai ya uwar data haifeki ba.....to kinji indo...wannan shine sila kuma mafari"gwaggo asabe ta qarashe fada tana sauke numfashi.
Kuka sosai aysha takeyi,tausayin mahaifiyarta na ratsata sosai na irin wulaqanci da cin zarafin data fuskanta....yayin da wani bari na zuciyarta ke qalubalantar matakin data dauka akanta,ita meye laifinta,ba itace sila ba,ya akayi mahaifinta da mahaifiyarta qarshensu yazo da haka duk sa irin soyayyar da gwaggo asabe ke fadin sun yiwa junansu,anya kuwa batayi kuskuren amincewa da khalipha ba kan cewar zai mata riqo irin wanda yayanta ciki daya zai mata,zai bata family da zatayi farinciki da su,zai bata dama da 'yanci duk kalar wanda ya dace?,ga masoya yadda suka qare...ina ga ita da zatayi rayuwar alfarma a qarqashinsa,ina ga ita da take da tabbacin ba soyayya ce ta hadasu ba,ba itace jigo ba...tausayi ne da taimako da zaiyi ma rayuwarta.
mero ma dake gefe tayi mutuwar zaune tana juya lamarin,ba shakka tana iya tuna wasu abubuwa da suka dinga biyo baya,irin shige da ficen da faccalolin ummin suka dinga yi suna yada cewa aysha shegiya ce,wanda banda Allah nasom baiwar tasa da tuni ya bita,sai ubangiji ya dakushe hakan daga qwaqwale da bakunan al'umma cikin lokaci qanqani da